Showing 66001 words to 69000 words out of 78516 words

Chapter 23 - FEERYAL Part 1 Complete Hausa Novels by Rasheeda S Director.doc

labaran kamar haka
"Jami'an tsaron Nigeria sojoji da 'yan sanda sun sami nasarar cafke 'yan tadaddan nan, kungiyar da akeyiwa lakabi da 'yan d'aukar amarya,
ajiya litinin 5 ga wata,
inda suka yi zuga zuwa d'aukar wata yarinya,
a Maitama gidan shahararren d'an kasuwan nan Alhaji Tahir Abbas, dake cikin birnin tarayya Abuja,
in da jami'an tsaro suka sami labari sukayi fitar gaggawa,
inda sukayi bata kashi sakanin su da 'yanta'addan sukayi nasarar cafkesu, suka kuma kwato yarinyar da yanzu haka tana gadon asibiti,
rahoto ya tabbatar mana da cewa jami'ai uku sun sami rauni, sakamakon musayar wutar daya shiga sakanin jami'an da 'yan ta'addan.
a yanzu haka shugaban na 'yan ta'addan Bala kwari da sauran mabiyan tawagarsa na d'aukar amarya suna nan, a hannun hukuma.
Bala Kwari ya jima yana ta'addanci ba a iya birnin taraiya ba harma da sauran jahoyin kasarnan,
duk yarinyar da yaga ta masa ko budurwa ko matar aure to sai ya d'auketa, shekarar data gabata motocin d'aukar amarya yake garkuwa da su bayan ya d'auke amaryar sai ya sake sauran mutanen ya tafi da amaryar.
wakilanmu suna can ofishin hukuma da asibitin da yarinyar take dan son sanin halin da ake ciki,
ku cigaba da biyo mu dan son salin halin da ake ciki."

Labarin da kasa gaba d'ya ta waye gari da shi ke nan, inda jama'a suka ji dad'in nasarar da aka samu na cafke 'yan ta'addan, tawagar d'aukar amarya, da suka addabi al'umma ana kuma yiwa yarinyar fatar samin sauki.

Wani irin mikewa Daddy ya yi yana ware idanunsa kan TV in da ake hasko labaran,
Aunty da ta fito rike da tray daga kichin ta ja ta tsaya jikinta na b'ari.
da sauri Daddy ya d'au rimut ya kashe TV yana kallonta yana fatan Allah yasa bata ji ba dan yasan ta da iya firgicewa, sai dai alamu sun nuna taji ga yadda gaba d'aya yanayin ta ya sauya.
hannu na b'ari murya na rawa tashiga fad'in
"Innalillahi wa innailaihirraji'un me nake ji haka Daddy ka kunna TV mana, Alhaji Tahir Abbas Maitama, Abba ke nan fa, gidan mu meke faruwa a gidan mu wa aka sace!."
gaba d'aya Aunty ta firgice.
da sauri Daddy ya je ya karb'i tray'n da yake kokarin sub'ucewa a hannunta, ya dire shi kasa kana ya ce
"Ki nutsu Fad'imatu, insha'allah komai yazo cikin sauki, ai kinji basukaiga gudu da wacce suka d'aukan ba aka sami nasarar cafke su,
wace ce cikin su Maryam ce ko FEERYAL?
ya Allah ka tsayar haka."

Aunty ta girgiza kai tana fad'in
"FEERYAL ce ma nasan ita ce ita ce kullum ake kawo wa hari."
"Ko wace ce cikin su Allah mun gode maka da ka kawo mana saukin lamarin, bari na kira Alhaji'n Abuja shima wata kila damuwar ce yasa bai sanar mana ba."

Ya dannan number Abba yayi ta ring ba'a d'agaba.
a b'angaren Abba kuwa wayar tasa a gida ya barta suka taho asibiti inda FEERYAL take.

Sau biyar Daddy yana kira ba'a d'agawa, ganin haka yasa hankalin sa ya soma tashi, sai dai bai nuna ta inda Aunty zata gane har ta dad'a birkicewa ba.
ya dube ta yana cewa
"Bari naje na dawo kada ki tada hankalin ki babu komai, ai kinji da akwai da 'yan jaridun sun fad'a."
ita dai shiru tayi amma Allah ne kad'ai yasan ya take ji cikin zuciyarta.

Daddy na fita yasa akayi masa bukin na jirgi, bada jimawa ba kuwa jirgi ta tashi zuwa Abuja.

Ko da ya isa maitama gidan Alhaji Tahir Abbas, ya taras da ba mutan gidan sai ma'aikatan gidan.
nan suke shaida masa suna asibiti, akayi masa jagora zuwa, A.A FIYA Hospital.

Su Abba suka cika da mamakin ganin Daddy dan basuyi sammanin ganin nasa ba, saboda basu sanar musu da me ke faruwa ba.

Abba ya tari Daddy yana fad'in
"Ina da shirin nimanka, amma bayan na tabbatar da farkawarta, dan bansan ta inda zan fara sanar da kai, inda amanar da ka bani ta kasan ce ba."
Daddy ya girgiza kai yana cewa
"Ko a gurin mu idan Allah ya kaddara hakan zata faru sai ta kasance, amma ya jikin nata ta farfad'o kuwa?."
"Har yanzu dai amma ance bacci take."
kai Daddy ya jinjina tare da fad'in
"Allah ya bata lafiya, babu dai abinda suka mata ko?
kuma babu abin da sukayi muku komai lafiya dai ko?."
"Basuyi mata komai ba firgici ne yasa ta shiga dogon suma, amma an sami nasarar cirota a dogon suman yanzu dai tana bacci tun daren jiya amma kikita yanzu ya tabbatar mana idan ruwan da ke jikin ta ya kare zata farka,
babu wanda suka cutar a cikin mu."
"Allah ya bata lafiya, ya tsare na gaba."
cewar Daddy yana sauke numfashi tare da goya hannunsa a baya yana d'an zaga gurin.

Major Sadam da Inspector Nasir ne suka shigo da Dr Imran.
suka shige ICU.
har lokacin FEERYAL na kwance bata ko motsi sai dai numfashin da take saukewa a hankali.
Major Sadam ya dubi Dr Imran jiki ba kwari yana fad'in
"Dr takai 9h tana baccin nan ace har yanzu bata farka ba,
wai ina Dr can yake ne anya ba wani abin yamata ba ace har yanzu tana bacci bata farka ba,
no! ina banma yadda ba kirawo shi, je ka kirashi yazo nan, oya kirashi maza ya zo nan!."

Dr Imran ya ce
"Zata farka daga zaran ruwan nan ya kare mud'an jira zuwa karewar ruwan."
"Kai wai wani irin ruwane ma wannan ace tun cikin dare yana shiga jikinta ace har kuma yanzu bai gama ba,
a cire wannan ruwan tafarka tukun a maida mata."
ya mika hannu yana kokarin zare cannula hannunta.
da sauri Dr Imran ya ce
"Kar ka soma! idan ka maida ita dogon suma ni da kai bazamu iya dawo da ita ba, karshe abinda ake gudun ne zata kasance, ko tantama babu wannan numfashin da kake gani ma, bazaka sake ganin sa ba,
mutuwa zata yi!."
da karfi Sadam ya janye hannunsa ya yi baya da sauri yana fad'in
"What!."
kai Dr Imran ya jinjina tare da cewa
"Tabbas! Dr A.A Fiya baya ma kasar bare ya bata taimakon gaggawa kamar dai yanzu a inda take d'innan,
farkawarta batare da karewar wannan ruwan ba, barazana ce ga rayuwarta,
shi ya saita ruwan a kan dai-dai awannin da yakamata ta farka,
ba ruwa gama gari ne da ka sani ba, ruwa ne mai d'auke da sinadaran magunguna na musamman masu inganci a cikin sa,
dan haka ka jira cikawar awannin koda kuwa wuni zatayi ta kuma kwana a haka."

Inspector Nasir ya ce "Shike nan Major kadai ji a bari kar aje a b'allo wata likin, amma shi Dr yaushe zai dawo?."
murmushi Imran ya yi yana fad'in
"Bana ce ba duk san da ya yi ra'ayi zai juyo."
jinjina kai Nasir ya yi tun a jiya ya fahimci likitan mai tsastsauran bahagon ra'ayi ne,
irin wanda ba'a sasu ba'a hanasun nan,
babu kuma d'igon tsoro a gare shi.
sai kuma ya yi murmushi dan ya burge shi ba kad'an ba.

Fad'a Major Sadam ya soma yana fad'in
"Shine ya bar patient ya tsallaka ya tafi, shi da ya fara ba sai ya karasa ba, idan ya sake aka sami matsala na rantse shima sai ya yi freezing."
hannunsa Nasir ya rike ya jasa sukayi waje.

Dr Imran ya yi karamar dariya yana girgiza kai.
irin dai yafad'i son ransa, baisan da wa yake zancen ba.
shima ya biyo bayan su bayan ya tabbatar da komai dai-dai cikin room d'in.

Dr Imran ya yi mamakin ganin Daddy a asibitin tare da su Abba.
ya karaso ya shiga gaidashi cikin girmamawa,
Daddy ya amsa yana tambayar sa ya mai jikin dai?
ya ce da sauki sosai.

Bayan a wanni uku wanda ya yi dai-dai da awannin 12 kenan FEERYAL ke kwance a asibitin.
sai a lokacin ruwan ya kare bayan mintuna 15 da karewar nasa kuwa ta farka.

Su Daddy Abba Hajja Umma Maryam sunyi matukar farinciki da farkawar nata,
zo kaga Major Sadam yakasa zaune ya kasa ysaye.
Inspector Nasir sai dariya da tsiya yake masa.

A b'angaren Dr Imran ma yaji dad'in farkawar nata ya d'agata a ICU ya canza mata d'aki.
su Daddy suna cikin d'akin suna ta yi mata sannu da murnar ganin lafiya bayyane a gareta.


Dr Imran ya koma office d'insa ya na zama yakira number Dr A.A Fiya.
sai da ya kira sau uku a na hud'u ya d'aga.
Dr Imran ya ce
"A.A ban kira ka naji ko ka isa lafiya ba, tun dawowa na daga kaika airport dana shiga asibiti har yanzu ban fito ba, ko wanka banyi ba,
ashe guduwa kayi ka barmin aiki,
kaifa kasan aikin ka sai kai, kafara ka barwa mutum yarasa ta inda zai kare,
to dai gashi munsha da kyar 'yar da kake sawa mutuwa gata ta farka da bakin ta rau, Allah ya amsa ka mata jinya ta warke."
tsaki yaja ya ce
"To meye na kirana kana fad'a min wannan, sai ka sanarwa 'yan'uwanta ba ni ba."
"To ai kai ne kayi jinyarta shiyasa nake sanar maka nasarar da ka samu, ga Daddy a nan a tare da su nayi mamakin ganinsa a nan."
d'ip yaji ya kashe wayar tun kan ya karasa abinda zai fad'a
Dr Imran ya ciro wayar yana binsa da kallo,
bai damuba dan shi ba bakon sanin halin sa bane...........!






Mommyn Twins ce



??/\ *FEERYAL* ??/\


*NA*
*RASHEEDAT S DIRECTOR*


( _Book 1_)


*~Free page~*



*_Littafin na kud'i ne 500 account no 3170524141 Rashida Salihu first bank ka-ki tura shaidar biya ta WhatsApp number ta 08034690723*

*____________________________________*

*???[???VAINUWA ???VRITER'SA??]Fq??*
*???VSSOCIATION??B惙?_*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation


*_domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan_*???a???_

https://bakandamiya.com/group/71/Kainuwa-writers-association

*____________________________________*




??T???20




Aunty ganin shiru-shiru Daddy bai dawo ba,
ta d'aga waya ta shiga kiran sa.
sai dai har kiran ta yanke bai d'aga ba,
hankali tashe takuma maida kiran a karo na uku, nan ma har ya yanke bai d'aga ba,
abinda Daddy bai tab'a yi ba ta kira sa a waya duk abin da yake zai bari ya d'aga kiran ta,
sai gashi yau ta kirasa har sau hud'u baya d'aga kiran ta.
ba karamin masifar tashin hankali ta shiga ba, lokacin da ta kira wayoyin su Hajja Umma Abba Maryam basu d'aga ba.
sai ga Aunty na hawaye tama rasa me ma zatayi sai kai kawo take sakanin parkour zuwa bedroom.

A b'angaren Daddy kuwa wayarsa ya mance cikin motar kamfanin sa na abuja da akaje d'auko sa a airport, sabar damuwar son sanin halin da FEERYAL take ciki.
su Abba kuwa wayoyin nasu duk a gida suka barosu.

Jin kirar yayi yawa ne direban ya d'auko wayar ya biyo sa da shi cikin asibitin.

Aunty na rike da waya tana zaga guri da ambaton sunan Allah yayin da wasu hawaye ke fita a idon ta batare da tasan suna zubowa ba.
Baba Rabi na ta tausasata tana cewa
"Insha'allah komai zaizo da sauki muyi ta addu'a."
da sauri ta d'ago wayar jin shigowar kira, bata tsaya duba mai kiran nata ba tayi saurin picking call d'in,
ta kai wayar kunnen ta.
jin muryar Daddy yana fad'in
"Hello Fad'imatu."
bata san san da ta fashe da kuka ba tana fad'in
"Daddy kana ina ka bani tsoro ina ta kiranka baka d'agawa, su Abba basa d'aukar waya, dan Allah Daddy kazo, ni zanje Abuja hankali na bazai kwanta ba in banje naga halin da suke ciki ba."

"Ki nutsu Fad'imatu ki saurare ni, ya isa haka kibar kukan nan, bani hankalin ki a nan Fad'imatu, uhm kina jina?."
hawayen ta ta share ta ce
"Eh."
"Yauwa ki kwantar da hankalinki yanzu haka ina abuja gani nan tare dasu Alhajin Abuja,
duk suna cikin koshin lafiya,
d'iyarki ma tasami lafiya tana bacci yanzu haka."
wani numfashi ta sauke ta ce
"Daddy shine ka tafi baka fad'a min ba, baka kuma tafi da ni ba,
to kasa ayi min bukin yanzun nan nima zanzo bari naje na shirya."
"A'a Fad'imatu ki saurare ni, basai kinzo ba kiyi zaman ki,
ba gani a gurin ba."
"Daddy ni dai ina so naga FEERYAL basu mata komai ba ko, me yasa to take asibiti?."
"Babu abin da suka mata razana tayi tashiga dogon suma, kuma ansami nasarar cirota daga dogon suman yanzun nan muna tare muna hira da ita,
bata jima da komawa bacci ba, kar ki damu zan taho miki da d'iyarki."
numfashi mai karfi Aunty ta sauke tanayiwa Allah godiya,
kana ta ce
"Ina su Hajja Umma?."
Daddy ya masa ya mika musu wayar.
jin muryoyin su yasa hankalin Aunty dad'a kwanci.

Bayan Abba sun gama waya da Aunty.
ya dubi Daddy ya na fad'in
"Dama ina fargabar cigaba da zaman FEERYAL a gurin mu a irin wannan lokacin,
munyi magana da kwamishinan 'yansanda yake ce min da da hali da an d'aga yarinyar a nan, sabo da
mai tawagar d'aukar amarya yana da mugun hatsari sosai,
dan yana da mutane da yawa kuma an shaidesa bai tab'a kaho hare ya tashi a banza ba,
zai iya yin komai duk da yana tsare amma akwai idanunsa a waje,
bare kuma ya kai hari an samu nasarar cafkesa zai iya ninka haushin sa,ya yi abinda ba'ayi sammani ba,
ta hanyar waiwayo wa kuma d'aukarta, tun da akwai sauran tawagar sa a waje,
yanzu haka suna ta kan bincike don su sami nasarar cafke sauran tawagar nasa."
Daddy ya jinjina kai sannan ya ce

"Ni ma nayi wannan tunanin, sannan kuma nasan hankalin Fad'imatu bazai tab'a kwanciya ba har in ba ta ganta ba, zan tafi da ita, har zuwa san da komai zai lafa."


Kwanan FEERYAL d'aya a asibiti in aka had'a da daren da aka kawota biyu ke nan.
da yamma Daddy ya bukaci a sallame su ganin jikin nata ya ware sosai, suka tattara sukayi gidan Abba.
'yan'uwa da abokan arziki da makota suka rika tururruwa zuw???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~?a gaida FEERYAL da musu jaje.
ancika tam a parlour sai jajanta lamarin ake 'yan cikin unguwar kuwa sai bada labarin yadda suka tsinci kansu lokacin da ake musayar wuta sakanin 'yan ta'addan da jami'an tsaro.
FEERYAL dai na zaune tana bin kowa da ido bata iya ce da kowa komai dama can ita ba mai yawan magana bace,
ga kuma faruwar lamarin da har yanzu yana jikinta tsoro da firgici mai had'e da fargaba, sai ta dad'a zamowa very silent.

Kiran Inspector Nasir ne ya shigo wayar Maryam ta mike tanufi bedroom d'in su.
ta zauna bakin gado tare da d'aga wayar tana jingina bayanta a jikin gado.
"Hello, Nasir ya aikin?."
"Lafiya lau, ya fargaba?."
"Hm har yanzu ban gama dawowa normal ba, fargaba yaki sake ni, har yanzu ina ganin abin a idona."
dariya ya yi yana cewa
"To FEERYAL kuma tace yaya ke nan, ita da ta shiga hanunsu taga yaki a kan idon ta."
"Ai FEERYAL tafini tsoro a mugun razane take har yanzu, kar kaga yadda take ciccire ido a parlour, da zataji karar wani abu yanzu dogon suma zata koma."
dariya duk sukayi.
Nasir ya ce
"Maryam ba kin ga girman irin son da Major Sadam yake yi wa FEERYAL ba,
ki duba kiga irin babban taimakon da ya yi mata,
yabada jikin sa da ransa wajen ceton rayuwarta daga annun 'yanta'addan can,
bai bari sun tafi da ita ba sai da ya tabbar da ya kwato ta a hannunsu,
Sadam yana son FEERYAL wlh bakiga halin da ya shigaba ranar, sai da ta farfad'o kafin hankalin sa ya kwanta,
haka ya wuni ya kwana bai d'and'ana komai a bakin sa ba, har sai da ta farfad'o kafin
ya samu ya sawa cikin sa wani abu."

Zama Maryam ta gyara sannan ta ce
"Nasir FEERYAL ita ta ta baku babban gudumawa wajen cafke 'yanta'addan da kuka jima kuke son kamasu kuka kasa,
bawai ita kuka taimaka ba ita ta taimake ku, ta baku damar cafke su,
Nasir bakasan waye FEERYAL ba,
FEERYAL tana da wani b'oyayyen baiwa da ba kowa ne ya sani ba, sai idan ka zauna da ita zaka san hakan,
ina da tabbacin FEERYAL ita ce silar taimakon ku wajen kama b'arayen nan, bance kun gaza ba ina mika jinjina ga jami'antsaron mu,
kuna kokari kam yadda ya kamata,
amma a wannan fannin kam tambas FEERYAL ita ce Star d'in wasan."

"Hm Maryan ke nan ke dai duk in da aka biyo sai kin toshe, to naji FEERYAL ta bada gudumawa wajen cafke tawagar d'aukar amarya, tun da ita akazo d'auka, har muka samu nasarar kamasu,
amma fa ki sani, Sadam sadaukar da rayuwar sa ya yi yafito gaba da gaba suka gwafza shi da kansa ya harbe Bala Kwari shugaban tawagar d'aukar amarya,
bayan ya harbe mutum uku cikin 'yan tawagar nasa."

"Duk wannan bajintar bayan da ta gama nata aikin ne, mance kawai duk yadda zan gaya maka bazaka fahimta ba,
amma lokacin da zaka fahimtar na zuwa,
san da mukayi aure FEERYAL tazo gidan mu."
"To shike nan Allah ya kaimu lokacin,
bayan ma kina ta jan lokacin please Maryam ki bari
na turo gida a sa mana rana, ban san me kike jira ba,
ko so kike sai kin had'a digiri na biyu ban sani ba."
dariya ta yi ta ce
"Ban ce ba dai ni kam, kai kam to meye matsalar ka bayan sadakinka yana hanu."
"Kin fi kowa sanin matsala ta, dan na bada sadaki iya haka bai wadatar ba, ke d'in nake bukata a kusa da ni,
bari komai ya lafa hakuri na ya kare yanzu kam."
shiru tayi tana saurarar sa.
"Kinyi shiru kina jina ba, kin manna min hauka ina."
"Na'isa yaushe Nasir d'ina ya sami tab'in hankali."
tayi maganar da muryar dariya.
"Saura kad'an ai bakisan rashin aure yana tab'a kwakwalwa ba."
ido ta waro ta ce
"Bana fata ya tab'a maka hankali,
last year insha'Allah zamu kasan ce ma'aurata, shike nan?."
"Yauwa yanzu naji batu, duk da dai har karshen shekara ya min nisa, za'a janyo lokacin."
nan suka cigaba da hira irin dai na masoya.


Daddy ne zaune a parlour'n Abba bayan sunyi sallama da ba'i mazan da suka zo wa Abba jaje.
Daddy ya gyara zama tare da duban agogon hannunsa, kana ya dubi Abba sannan ya ce
"Alhaji mu zamu wuce zamubi jirgin karfe 7, gashi har 6 ta kusa."
"Ah wai yau ne zaku tafin inace sai gobe, ai yanzu dare zatayi, da ka bari zuwa gobe dai."
"Babu ko mai zamu wuce yau har an shirya mana tafiya karfe 7."
"To shike nan bari nayi musu magana zanyi kewar amaryata, amma fa daga zaran komai ya lafa zaka dawo min da ita,
amma wani hanzari ba gudu ba, ya zakayi da Hajiyar ka, kana ganin babu matsala komawar nata can,
ko dai zanyi magana da Aliyu ne a kaita can kasar Lebanon, in yaso zuwa jibi angama shirya mata komai sai ta tafi."
Daddy ya ce
"Babu komai insha'allah zanji da komai baza'a sami wata matsala ba in Allah ya yarda."
"To Allah ya sa, in dai kaga hakan zai janyo wata matsalar to barin kasar natama gaba d'aya zaifi bata tsaro."
Abba ya fad'a yana mikewa ya nufi b'angaren Hajja Umma.


Tun

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login