Showing 51001 words to 54000 words out of 78516 words

Chapter 18 - FEERYAL Part 1 Complete Hausa Novels by Rasheeda S Director.doc

da suke tafe cikin mota a hanyar su ta zuwa gidan Alhaji Tahir Abbas da ke maitama,
dan bata tab'a tafiya mai nisa ba, daga gida sai school.
Aunty bata barin ta ko da Miemie ta bukaci suje wani gurin ko gidajen dangin su,
a kan FEERYAL Aunty ta jingine zuwa ko'ina sabo da gudun bakin mutane,
dan duk wanda ya ga FEERYAL d'in ya rinka wuu-wuu ke nan, wani ya fad'i alkhairi wani akasin sa.

A bakin wani katafaren gida mai girman gaske, direba ya yi hon aka wangale masa get.
babban gida ne mai matukar girma da tsaru,
duk da girma da tsaruwa irin na gidan Alhaji Abubakar Fiya,
sai da FEERYAL ta tsaya kallon tsaruwan gidan Alhaji Tahir Abbas.
sabo had'uwan shi shima.

Direba na gaba janye da akwatunan ta tana biye da shi.
suka shige cikin wani katafaren parlour na alfarma.

Tun kafin su karasa cikin parlour'n
Wasu dattijai biyu mace da na miji suka fito daga wata kofa.
ko ba'a fad'a ba kasan Alhaji Tahir Abbas ne Abba'n Aunty da hamaifiyarta Hajja Umma.
suna tozali da FEERYAL a tare suka furta
"Tabarakallah masha'allah."
ganin ainihin suffarta a zahiri yad'are wacce suke gani a hoto.
da gudu Maryar autarsu da ke biye da su,
ta wuce gaban su tana fad'in
"Wow beautiful oyoyo FEERYAL."
ta rungume ta.
Hajja Umma tana kokarin tareta, Abba ya yi saurin shangabanta ya ce
"Barni ni zan tari amarya ta da kai na."
Hajja Umma ta yi murmushi tana cewa
"Saboda ni kishiya ko, ai dai gara ni na fara tsare ta na kakkab'e abinda tazo dashi,
koma da baya na d'ebo sakin kuka na zuba a hanyar shigowar ki,
ya karya abinda kikayiwa Alhaji tsawon shekaru nice amarya nice uwar gida,
daga zuwan ki zaki firgita shi."

"Taho nan amaryata gimbiya FEERYAL rabu da ita."
ya ruko hannunta.
suka karasa suka zauna kan kujera.
Maryam ta kasa zama tana ta kallon ta, kyawun ta ya mugun tafiya da imanin ta.
sai fad'i take
"Wayyo Allah kyakkyawa ce wlh kamar ita tayi kanta, kullum tare zamu rika zama ko kamshin kyan ki zai shafani."
dariya maganar ya bata ta yi karamar dariya, kyakkyawan kumatun ta ya lob'a.
Hajja Umma ta ce
"Tabarakallah masha'allah."

Direba ya aje akwatunan ta ya fita bayan ya gaishe su.
Abba ya ce
"Maryam d'auki akwatin ki kaisu d'akin kusa da naki d'akin ta ke nan, amarya ta ko kina son d'akin sama kusa da na Hajja Umma ne?."
da sauri Maryam ta ce
"Abba a d'aki na zata zauna murika kwana tare."
"A'a ki bari dai a bata d'aki na, ni na sauko kasa,
ai in bakuyi wasa ba sai dai ka ajeta a kitchen ko store."
cewar Hajja Umma tana dariya.
Abba ya ce
"Ai wannan gold d'in tafi karfin zama a gurin da kika ambata, Maryam kaita taci abinci tayi wanka ta huta, sai tazo muyi hira."

Maryam ta janyo akwatunan ta ce
"Taho muje."
babban d'aki ne mai girman gaske komai na bukata yana ciki kamar d'akin matar aure, bana 'yar matashiya mai tasowa ba.

Maryam ta dubi ta tana fad'in
"Shiga bayi kiyi wanka ko nazo nayi miki?."
kafad'a FEERYAL ta make ta ce
"Na iya fa Ammie na ma tana barina nayi ranar da ba school."
"To je kiyi kizo ki sauya kaya muje kici abinci."
ta shige bayi. ita kuma Maryam ta shiga ciro kayan ta tana sakasu cikin wardrobe.

Ko da ta gama ta fito Maryam ta taimaka mata ta shirya tana ta yaba kyawun halittarta, FEERYAL ta zame mata abin kallo.
Maryam ta janyo ta tana fad'in
"Zo muje kici abinci ki rakani gidan wata kawata."
cikin zakuwa ta janyo ta suka fito.

A parlour suka sata gaba sai taci abinci tad'an ci dai ba laifi dan ita ba ma'abociyar cin abinci da yawa bane,
yogurt da cake sune abin cin ta.

Sosai suka rika janta ajiki a wunin ranar harta saki jiki da su.
taga soyayya da kauna da kulawa kamar zasu goya ta.
Alhaji Tahir Abbas yana gida bai fita ba saboda zuwan FEERYAL, ya kira Aunty video call suka sha hira tamkar suna tare.
bayan sun gama waya da Aunty Maryam ta mike tace tazo suje ta rakata.
Hajja Umma ta ce
ta bari sai gobe yanzu yamma ta yi.

Da daddare ma a parlour'n sama suka yada zangon su, sai da suka kai karfe 12 suna hira kafin Abba ya ce suje su kwanta.

Washegari Maryam ta ja FEERYAL sukayi gidan kawarta a nan unguwar su.
suna shiga gidan da
Haulat kawar Maryam d'in suka fara cin karo.
Haulat ta kasa amsa sallamr da Maryam takeyi.
ta kurawa FEERYAL ido.
"Ke dalla ina sallama kinyi shiru bazaki amsaba."
"Wow wannan fa a'ina kika samota, ko ba'in turawa kukayi?."
Haulat ta fad'a tana nuna FEERYAL tana ware idanunta sosai a kanta.
"Ni dad'i na dake hauka ke kam baza'a yi miki surprised ba ana miki zaki iya mutuwa, d'iyar Aunty Faty'n Lagos ce."
"Ke da'alla serious Maryam kar ki shigar da ni, wannan dai ba bahaushiya bace, da gani ruwa biyu ce baturiya balarabiya."
"Da gaske d'iyar Aunty Faty ce jiya ta zo, kin wani barmu a tsaye komu koma ne kin wani tsare ni da tambayoyi."

"Yi hakuri taho mushiga ciki wlh ganin ta ne yasa ni shiga yana yin nan, zo na rike hannunki ya sunan ta?."
Haulat tayi maganar tana ruko hannun FEERYAL.
"Ya salam ashe ana ganin irin su a zahiri ba a TV ba."
dariya Maryam tayi ta ce
"Wlh ke da a kauye kike bansan ya zaki kare ba."
"Ke dai Maryam barni nafad'i gaskiya ta, wlh yarinyar nan so beautiful, ta tafi da ni gaba d'aya."

Haulat na rike da hannunta suka shige parlour'n su.
Maryam ta zauna tana dariyar Haulat da gaba d'aya ta rud'e da ganin kyan FEERYAL.
a gefen ta ta zaunar da ita tana rike da hannunta bata sake ba, ta dubi Maryam tana fa??in
"Wai dan Allah kuma da gaske d'iyar Aunty Faty'n Lagos ce, ko dai abokin kasuwan cin Abba ne yazo da 'yarsa daga wani kasan,
yanzu wannan 'yar Alhaji Abubakar Fiya ne?."
fuska Maryam ta had'a ta ce
"Abin da na saba miki, kin ga tabon sa a goshi na ai, karya ba."
"Allah baki hakuri kawata, lallai kuwa babu ko shakka kwanciyar hankali ma yana karawa mutum kyau, d'iyar Alhaji Abubakar Fiya jika ga Tahir Abbas ai abin bana wasa bane, sai dai ita wannan kyan nata na daban ne tamkar ta had'a jini da larabawa ko turawa,
watakila Alhaji Abubakar Fiya ya had'a jini da su, duk da cewa Aunty Faty ma badaga nan ba a kyau."
Maryam ta sakar mata hararar wasa ta ce
"Yauwa yanzu kika gyara kalamanki ai muma dai kinsan muna da kyau, har da namu kyan ta d'auko makoyi ne dai yafi gwani."
"Lallai kuwa yarinya kin fito a dai-dai d'iyar Alhaji Abubakar Fiya jikan Tahir Abbas."
"Sai kin kiramin sunan uba, kiji dad'i ina Haulat banson cin fuska."
"Suna da inkiya ba cin fuska bane."
dariya duk sukayi.
Maryam ta ce
"Wai ya naji gidan shiru ne, Momma fa?."
"Unguwa suka tafi dukan su,
sun je gidan tsohuwar ta, yanzu haka sai yamma su dawo,
ni ma dama zan gama ne na bisu can d'in,
tun da kunzo muyi hira kawai."
nan suka cigaba da hira wanda rabi da kwatan hirar duk akan FEERYAL ce.
Haulat taki barin su su tafi tana ta jansu da hira.
ita dai FEERYAL da ido kawai take binsu, hakan nadaga cikin dabi'ar ta rashin magana da yawa, bata daga cikin yara irin masu yawan surutun nan.

Har kusan azahar suna gidan sai da Hajja Umma ta kira Maryam a waya ta ce ta dawo mata da jikarta yanzun nan, kafin suka tafi.

Washegari kuwa gyaran gashi Maryam ta d'auke ta suka tafi.
suna shiga shagon kallo ya dawo kansu.
daga nan suka wuce gidan Aunty Zainab yayar Aunty da take binta.
FEERYAL taga kauna a gidan ita da 'ya'yanta kamar zasu goyata, har Aunty Zainab tace a bar mata ita tayi mata kwana biyu.
Hajja Umma ta ce
maza-maza a dawo mata da ita.

Duk in da Maryam zata je da ita take zuwa duk wanda ya gansu tare kuwa sai ya tambaye ta a ina ta samo ta, idan ta ce dasu d'iyar Aunty ta ce suyi ta shan mamaki.
Wad'an da suka san Aunty'n nata kuwa da mijin da take aure sukan gaskata hakan a take, dan sanin ko waye mijin Aunty'n nata.
dan cewa suke kud'i zai iya komai wata kila akwai dangantakar nesa da kud'i ya iya janyo sa.
ma'ana ya na da dangi da suka shafi wata kabilar ba hausa ba, wan da har ya kaiga samun d'iyar da ta yiyo kamarsu.

Satin FEERYAL guda a Abuja a ka samar mata makaranta ta fara zuwa.



Lagos

Tun da Ajeemal ya sami labarin barin FEERYAL gidan gaba d'aya yaji ba dad'i.
Miemie ma har kuka tayi ta kaurace wa sashin kakan nasu, ko wani abin tab'awa Ammah ta bata ta kai wa Hajiya, sai dai ta je ta kaiwa Ameerah ko Sahla ko Nabila ta ce su kai mata, inji Ammah'n ta.

Ajeemal ne zaune a parlor'n Mommy yana cin abinci.
Mommy na hakimce a kan kujera tana kallon TV.
su Ameerah da Sumayya suka shigo da uniform a jikin su dawowan su daga school ke nan.
tun kan su karaso parlour'n Sumayya ta ce
"Mommy kiji wai Ameerah zata zana paper a primary 5, na ce ta bari next year muma sai da muka kai 6 kafin muka zana, wai ba wanda ya isa ya hanata, dan taga kawayen ta sunce zasu zana this year."
baki Ameerah ta murgud'a mata cikin tsiwa ta ce
"Sai na zana sai ki hana ai ina ruwanki da ni 'yar sa ido."
Mommy tayi saurin cewa
"Ina ruwan ki da ita Sumayya in tace zata zana,
kinsan dai Ameerah ba jahila ba ce kwakwalwar ta na ja,
ko a primary 4 take tace zata je JS kinsan dai zata iya ko, babu abinda 'yan JS d'in zasu nuna mata."

Ajmal daya bi Ameerah da harara ya ce
"Mommy wannan ce me kwakwalwar, dan baki tab'a zaunar da ita bane, in banda rashin kunya babu komai a kanta,
ai mai )?wa)?walwa sai FEERYAL yarinyar akwai ilimi har mamaki basirar ta yake bani."
da sauri Mommy ta katse shi ta hanyar buga masa tsawa
"Rufamin baki ita FEERYAL d'in kanwar uwarka ce ko kanwar uban ka,
sai taje can ta karata da kwakwalwar ta mara amfani dan da uba ake ado, mun jefar da kwallon mangoro mun huta da kuda,
kada ka sake ambata min sunan mayyar aljanar can,
ni harma na mance da ita,
shine bari ka tuno min da ita kana so ka b'ata min rai,
to kafita idona na rufe kada na sake jin sunan 'yar nan a bakin ka, bare har ka danganta min ita da 'ya'yana!."

Kai ya girgiza ya ce
"Allah baki hakuri Mommy."
ya mike ya d'au plt d'in abincin sa ya yi waje.
ta bisa da harara tana fad'in
"Ai ba'a barka banza ba, sai na mike tsaye a kanka."

Zaune Daddy ya ke cikin parlour'n sa yana kallon labarai a TV, kira ya shigo d'aya daga cikin wayoyin sa da suke zube kan table d'in gaban kujerar da yake kai.
Dr Omar sunan daya bayyana kan screen d'in wayar kenan.
ya janyo wayar tare da picking na call d'in,
ya kai wayar kunne tare da yin sallama.
da sauri cike da girmamawa Dr Omar ya amsa sallamar yana d'aurawa da fad'in
"Barka da warhaka ranka shi dad'e, ya gida ya kokari ya ji da jama'a."
"Alhmdulillah, Dr Omar ya aikin ya masu jiki?."
"Alhmdulillah gashi nan muna ta fama kam sai godiyan Allah, guri ya kacame, Alhaji dama akan batun mu na rannan ne na kuma kiran ka, Allah yasa dai ban matsa da yawa ba,
a gafarce ni dole ne yasa ni hakan,
dan Allah Alhaji a taimaka a sake mana magana da Dr mu asibiti tana bukatar sa."

Daddy ya gyara zama tare da sauke idanunsa kan kofa. inda yajiyo muryar Aunty da ta shigo da sallama kana ya ce
"A'a wai har yanzu bakuyi magana da shi bane, dana ji shiru ai na d'auka kun rigada kunyi magana."
"Kwanaki munyi magana da shi har ya amsa min kan cewa zai dawo, to ganin shiru sai na sake tuntub'arsa da batun,
to dai har yanzu ban sami kwakkwaran amsa a gurin sa ba, kasan mutumin namu sai ana had'awa da lallami, idan ya baud'e bazamu iya karkato shi ta dad'i ba,
yanzun nan muka fita mitin all Doctor's gaskiya na fahimci irin gudunmawar da zamu samu 100%
idan yana cikin mu, gaba d'aya mitin d'in nan a kansa ya kare, na tayaya zamuyi ya dawo cikin mu,
kwanaki munyi taro a government house mai girma Gwamna da kansa sai da ya tambaye sa,
a ranar ma sai da na kirasa na sanar masa,
sai dai is not serious ni nasan baya bukata dama can ni nayi ta tirsasa masa,
da bibiyar sa har hospital d'in sa,
kafin ya yarda ya fara zuwa general hospital,
ni da kaina na shigar da takardun sa badun yaso ba,
dan Allah Alhaji a samana baki cikin lamarin muna bukatar sa."

Daddy ya jinjina kai ya ce
"To ba damu insha'allah zamuyi magana da shi."
Dr Omar ya yi ta masa godiya kana ya yi masa sallama ya kashe kiran.

Daddy ya maida hankalin sa kan Aunty data karaso ta zauna gefen sa.
ta tsiyaya masa had'in lemun da ta had'a da kanta cikin kyakkyawan cup, ya yi sanyi kuwa amma ba sanyi mai cutarwa ba,
ta tad'ago ta mika masa.
ya gyara zamansa da kyau ya karb'i cup d'in yana binta da murmushi sannan ya ce
"Nagode Ammie'n FEERYAL."
murmushi tayi masa tana rufe ragowar lemun.

Ya kai cup d'in bakinsa ya kurb'i lemun ya lumshe ido yana jin dad'in sa na rasa cikin bakin sa.
kana ya bud'e idanun nasa a kanta ya ce
"Ya yi dad'i sosai fa, kunyi waya da FEERYAL yau kuwa? nayi ta gwada lambar hajja Umma baya tafiya, Alhaji kuma ya ce min yana Kano yau sai gobe sai koma."
"Kafin na zo nan munyi waya da ita a wayan Maryam, nima na kira wayan Hajja Umman bai tafi ba, Maryam take ce min wai FEERYAL d'in ce ta cinye cajin wayar nata da game."
dariya Daddy ya yi ya ce
"Da kyau mana, gobe zansa a kai mata sabuwar waya,
sai tayi ta buga game ta barwa Hajja Umma nata."

Murmushi Aunty tayi tare da mikewa tsaye, tana jin kewar d'iyarta, damma kullum suna tare a waya suna kallon junan su ta video call.
Daddy ya yi saurin fad'in
"Ina kuma zakije Fad'imatu?
ki zauna mana ki tayani hira."
"Daddy ka shanye lemun nan duka akwai wani a fridge zan karo maka, anjima ka shigo kaci abinci dan naga alamun kafara jin yunwa."
tayi maganar tana son kawar da nasa batun, dan tasan yanzu haka Umma Karima tana hanyar zuwa side d'in nasa, dan itace da shi, kuma tana da tabbacin taga shigowar ta, dan takan aje 'ya'yan ta a hanya suna mata gadi.
tayi saurin nufar kofa tun kafin ya dakatar da ita.

Aiko tana sa kai sukayi kicib'us da Umma Karima.
kallon tuhumar me ya kawo ta sashin baran kwanan ta ba Umma Karima ta bi Aunty da shi.
itako batama bi ta kanta ba tayi gaba a binta,
tana jin miyagun maganganun da Umma Karima take aika mata su bata ko waiga ba.........!





Mommyn Twins ce






??/\??/\ *FEERYAL* ??/\??/\


*NA*
*RASHEEDAT S DIRECTOR*


( _Book 1_)


*~Free page~*



*_Littafin na kud'i ne 500 account no 3170524141 Rashida Salihu first bank ka-ki tura shaidar biya ta WhatsApp number ta 08034690723_*

*____________________________________*

*???[???VAINUWA ???VRITER'SA??]Fq??*
*???VSSOCIATION??B惙?_*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation


*_domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan_*???a???_

https://bakandamiya.com/group/71/Kainuwa-writers-association

*____________________________________*







??T???16





Rayuwa mai shud'ewa, mai tafi a sanu a sannu.
bayan wani lokaci mai tsawo....
rayuwa mai kyau da tsafta FEERYAL take gudanar da shi yanzu, babu tsangwama bare kyara,
tsantsar kauna da soyayya mai had'e da kulawa Abba da Hajja Umma da Maryam da duk wasu danginsu suke nuna mata.
in banda su da suka san wace ce ita babu wani baren da yasan asalinta,
abinda kowani bare ya sani shine ita 'yar Hajiya Fatima ce kuma d'iyar Alhaji Abubakar Fiya jika ga Tahir Abbas.

Sannu a sannu FEERYAL nakara girma da wayo ya yin da kyawunta ke dad'a karuwa yana tsole idon duk mai kallonta, wanda hakan yake son zamowa barazana a rayuwar ta.
dole Alhaji Tahir Abbas ya samar mata da security bayan direban da yake kaita makaranta ko kaisu unguwa idan zasuje da Maryam.
security na tare da su sabo da harin da wasu fitsararrun maza suke kawo mata.


Lagos
Da misalin karfe 1 da rabi na dare.
(Zero Club)
baka jin ko mai sai tashin sautin kid'an daya karad'e ciki da wajen Club d'in.
maza da mata ne a cakud'e, suna ta tikar
rawa cike da fitsara suna rungumar junan su.
gaba d'ayan su 'ya'yan manya ne, 'ya'yan masu kud'i masu fad'a aji.

Wasu kuma suna zaune suna ta aikin bushe-bushen shisha ya yin da 'yanmata ke makale a jikinsu, suna ta badakalar su.

Zaraddin dake zaune ya baje kafa,
ya yi doguwar mika, kana ya aje mabusar shishar dake rike a hannunsa yana aikin busawa,
ya janye budurwar dake rungume da shi, tana ta aikin shafa shi.
ya mike yana duban agogon dake daure a hannunsa kana ya ce
"Beb zan shiga gida 2 saura yanzu nasan sunyi ta kiran wayoyi na ma suna mota."
mikewa tayi ta sakalo hannayen ta a wuyansa ta narke murya tare da kashe masa ido irin na gogaggun 'yanmatan bariki.
"Din wai yaushe ne zaka waye kana babban yaro ace kamar kan nan wai har yanzu ba'a dai na sama ido a gida ba,
me zai hana mu kwana a nan kawai."
hannunsa ya tura cikin rigarta yana wani sakin murmushin gefen baki, sannan ya zaro hannun ya d'an ture ta a jikin sa.

Da sauri ta dad'a matso shi tsoron ta d'aya kada ace yarabu da ita ke nan, dan tun d'azu ta lura da kallon da yake ta bin wasu sabbin 'yanmatan da suka shigo d'azu.
Ziyad ya mike ya yana fad'in
"Ke yayan Dad d'in sa fa dodo ne mugun tsaro ne da shi, kinsan kuma duk iskancin mu munajin maganan nagaba."
Zaraddin bai kulasu ba ya sa takalminsa ya nufi hanyar fita.

Da sauri Ziyad ya bishi yana fad'in
"Din kar ka mance gobe ne fa Birthday party Neela, kar mu kuma jin kunya a gaban su Bash,
irin na birthday Seena 1 ko 2 million ya kamata mu rike mushiga filin nan da shi."
kai Zaraddin ya gyad'a yana shigewa cikin motar sa.
dai-dai lokacin da Seena budurwar da suke tare da shi d'azu ta karaso.
ta bud'e gefen mai zaman banza ta shiga ta zauna.
"Din muje mu kwana agidan ku, yau bazan iya kwanan nan ba, baka nan."
ido yad'an tsura mata sai kuma ya juyar da kansa ya yi wa motar key yana

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login