Showing 6001 words to 9000 words out of 24149 words
kumbura kamar kububuwa,hararar Deedee take kaman idonta zai faɗi ƙasa sannan tace.
"Wai Deedee sau nawa zance ki daina cemin nura ne,nura sai kace wata na namiji,in bazaki iya faɗin Nimrah ba ni ki ƙirani da ainihin suna na,habaaa ni nagaji da wannan sunan wlh,sai kinsa watarana wasu sunji su dinga ƙirana dashi ko"
"To ko kefa ni dama nafison ƙiranki da sunanki Indo (Aisha) miye kuma wani Nura,a garin iyayi duk kun sakawa kanku sunayen ifiritai ƙarfi da yaji"
"Kinji ko kinji ko ina,wai in bazaki faɗi abu daidai ba ki ja bakinki mana kiyi shuru,tukunnama miye yasa kike zunduma min wannan ƙiranne,kina daga zaune kin hakimce. Karma kice na matsa miki ƙafa ganan Saratu zata miki,danni karatun jarrabawa zanje nayi"
"To naji uwar ƙorafi da surutu,dama shi kika iya ai sai danne dannen waya,gashi nan nace kiyimin masa kin tashi kin tsula mata mai kaman ɗanwake,aradu idan ciwona ya tashi aka tambaya cewa zance kece sila"
Ta ƙarisa maganar tana tauna masar kaman tana tauna kashi.
Zaro ido Nimrah tayi sororo tana ƙarewa Deedee kallo,kai tsaye zaka hango tsagwaron baƙin ciki na furucin deedeen.
"Tabb lallai ma tsohuwar nan,haka kawai saiki tsiri cewar ayimiki abincin da mutum ko ido huɗu bai tabayi dashi ba saidai a waya,amma haka mutum zai dage yayi miki. Fisabilillahi ina na taba ganin wata Masar gero,amma haka nayi browsing nayi miki,shine zakice wai tayi mai,idan ba bazan sake yimiki abinci ba mai aikin ki ta dunga miki,ni na tafima bazan sake zuwa sashennaki ba"
Tana buga ƙafa kaman zatayi kuka take maganar.
"Ah ah Nimrah Deedee kika saka a gaba haka kina mata wannan wankin babban bargon saboda bakida mutunci?"
"Hajiya mama ce tafaɗa wacce shigowarta kenan falon"
"Faɗa mata dai da bakizo bama inaga dokeni zatayi,dannace tayi masa yayi mai ina faɗamata shine takemin wannan tujarar,marar kunya kawai"
"Deedee eeee!!,yanzu Deedee haka akayi ?"
Nimrah tafaɗa har idonta yana ƙwalla.
"Ohh ƙarya zatayimiki kenan wuce kije wai aunty Surayyah tana nemanki zaki tayata girki,idan ina kamaki kinayi mata wannan rashin kunyar saina babballaki ingayamiki"
Shigewa Nimrah tayi tana kumbura magana take ƙasa ƙasa wai ta daina yiwa Deedee labarai daga yau.
Kai tsaye sashen Ahmad ta wuce,har sannan bakinta bai daina sababi na abinda Deedee tayi mata.
Tura ƙofar tayi tareda yin sallama,amma shuru babu amsa,shiga tayi cikin falon tana ƙaremasa kallo. Gashi dai anyi shara amma ganinsa take wani iri kaman ba yanda tasaba ganinsa kullum ba.
Tunani ta tafi yi a lokacin baya sanda take zuwa,tana shigowa zata jiyo ƙamshin girki dakuma su farhana suna falo zaune da kayan wasansu. Suna haɗa ido da Aunty Surayyah zata sake mata murmushi su gaisa. In ta gama abinci haka zata zubawa Ahmad su zauna tana bashi a baki yana ci ana hira har yagama,bayan ya kammala ta tashi da sauri ta ɗauko jakarsa. Sunayiwa juna kalamai da cewar basason rabuwa a haka zata rakashi har jikin motarsa. Bazata shigo ciki ba har sai taga yabar farfajiyar gidannasu tukunna.
Daga nan saita tayata su gyara gidan su saka kayan ƙamshi ,sunayi suna hira. Aunty Surayyah abar so ce ga kowa.
Nimrah ta ƙarisa tunanin tana dariya idan ta tunata da kuma ɗabi'unta.
To miye kuma nake begenta kaman wacce ta mutu,tana nan fah. Wata zuciyar tace da ita haka.
"Lafiya kika tsurawa falon kallo kina murmushi,kin gagara ƙarisowa?"
Surayyah ce tayi maganar wacce take tsaye daga ita sai kayan bacci masu gajeren wando.
Nimrah tayi mamakin shigar tata,kuma har tsawon wannan lokacin ƙarfe 10:00pm da kayan bacci a jikinta?.
A haka dai ta basar ta gaishe da ita,itama amsawa tayi a daƙile kaman bataso.
Ƙarisowa cikin falon Nimrah tayi ta zauna,rabonta da shigowa part ɗin tayi wata ɗaya da ɗoriya,ko shiyasa take kallonsa tamkar sabon abu,yakoma tamkar matacce daga rayayyen data sanshi.
"Am dama abinci zakiyimin,yace bazaici na masu aiki ba,to i think zaici naki tunda ke ƙanwarsa ce,amma kafin ɗora min ruwan zafi zansha tea"
Tana gama maganar da ƙariso cikin falon ta zauna tareda ɗaukar remote ta sauya tashar da takeyi zuwa nigerin film.
Itadai Nimrah duk abinda takeyi sakin baki tayi tatsaya tana kallonta,gani take ko a mafarki wannan abun bazayyi wu ba ballantana a zahiri,amma gashi ba mafarki takeyi ba kuma yana yiyuwa. Anya kuwa wacce take gabantan Aunty Surayyah ce,kuma gashi ita ɗince ba wata ba. Lallai karka shedi ɗan adam.
Tashi tayi ta wuce ta gabanta zuwa kitchen ɗin.
Komai yana muhallinsa tabbacin yau ba'a dafa komai ba a kitchen ɗin. To me maigidan yaci kafin ya fita.
"Allah sarki Yah Ahmad har na tausaya masa,sauyawar mace lokaci guda haka nan. Ni in hancina ba ƙarya yayimin ba warin shisha ma fah naji tanayi koh? Wai hmmm Allah ya kiyaye,waye zayyi tunanin Aunty Surayyah zata sauya ɗabi'unta haka"
Da haka dai Nimrah ta gama yimata abincin ta jejjera sannan ta gyara kitchen ɗin ta fita. Lokacin ita kuma tashiga wanka,bata ma bari sun haɗu ba.
Amin magana ta wannan layin
09035784150
Sadi-sakhna ce.
⚫ *MUMINA KO AZZALUMA*⚫
Available on:wattpad&arewabook
⚫ _SADISAKHNA_⚫
⚫ *BOOK 1*⚫
⚫ _PART 6_⚫
Wajajen misalin ƙarfe 4:00pm yashigo gidan ya dawo daga aiki. Bai shiga sashen su hajiya ummee ba sashensa ya wuce,kasancewar Surayyah tace masa ya dawo tanason suyi magana.
Yana shiga ƙamshin turare yaji ya kaure falon,amma bana turaren wuta ba wanda yake so. Na air freshner ne,saidai shima yayi daɗi ba laifi yafi babu.
Idonsa sauƙa yayi akan dining inda aka jera kulolin abinci,a ransa hamdala yake Allah yasa surayyansa ta dawo cikin hankalin ta.
Fitowa tayi daga ɗakinta tasaka atampa,saidai ɗinkin zamani akayiwa kayan matsatstse,amma yayi mata kyau sosai ya amshi jikinta.
Da murmushin ta ta ƙariso inda yake ta karbi brief case ɗin hannunsa. Shima sakar mata yayi inda yabita zuwa ɗakinnasa,har yanzu baya ganinta a yanda take kaman da,amma dai dama dama akan kwanakin bayan.
Rigar saman ta rage masa,tana ƙoƙarin cire ta cikin ya riqe mata hannu,haka kawai yaji baya sha'awar cire kayannasa a gabanta,dan ganin yake shifa kaman wata daban ba matarsa ba. Haɗe fuska tayi ganin duk abinda takeyi masa bata gwaninta,ganin hakanne yasa yakamo hannunta tareda yin magana cikin sanyin sauti.
"Am sorry dear ina sauri ne kije ki haɗamin abinci kafin nazo yunwa nakeji sosai"
Ɗan murmushi tayi tareda ɗaga masa kai tafita daga ɗakin,alamun ta yarda da abinda yace ko kuma yanayin muryar tasa tayi tasiri a kanta.
Bayan ta fita binta yayi da kallo tareda sauƙe ajiyar zuciya,gabaɗaya bayason ganin ya kebe tareda ita. Bayan da hakan shine abinda yafi komai sakashi nishaɗi. Kwata kwata sai yaji yakasa samun nutsuwa,musamman dayaga yanda take binsa da wani mayen kallo na sha'awa.
"Ya Allah mai yake damuna ne tsakani na da matata,ya Allah idan har akwai wani dayake boye wanda yakamata nasani gameda ita Allah ka bayyanamin shi,ya Allah ka dawomin da ita kamar yanda take a da"
Ruwa ya watsa sannan yasaka wasu kaya marasa nauyi ya fito falon.
Tana zaune a falo idonta akan tv,kulolin suna rufe kaman yanda ya gansu ɗazu bata buɗe ba.
Zama yayi kusada ita tareda cewa.
"Barkanki da gida,mai kika dafamin ne yau ɗin naga wannan shiri da akayi dominni?"
Ɗan murmushi tayi tareda yin fari da ido sannan tace.
"Sirrine saidai muje mu gani tare nida kai"
"Ohh kenan ƴan aiki ne sukayi yauma?"
"Ahah ba ƴan aiki bane yau sukayi,yau basu ma shigo part ɗinnan ba."
Bai sake cewa komai ba gudun kar ya ja magana,tashi yayi zuwa wajen dinning ɗin.
Itama biyoshi tayi a baya ta buɗe ɗaya flask ɗin wanda yake shine babba.
Shinkafa ce amma anyi steaming ɗinta da vegitables da kuma curry,tayi kala shar gwanin kyau da bada sha'awa. Saurin runtse ido Surayyah tayi jin wani mungun yawu daya taru a bakinta marar daɗin ji. A haka ta ɗauki cokali tafara zuba masa abincin a plate har saida yace ya isa tukunna.
Ɗaya flask ɗin ƙaramin shima ta buɗe,miya ce a ciki tasha nama na ƙaramar dabba,shima sai kamshin curry ne yake tashi. Subahanallahi wannan karon kam ji tayi kaman jiri zai ɗibeta saboda ƙamshin curryn daya haɗe wajen.
Ganin tatsaya sororo batada niyyar yin magana yasa Ahmad janye plate ɗin daga gabanta ya zuba salat ya fara ci.
"Uhmm yayi daɗi sosai amma bake kikayi abincinnan ba ko,don wannan ba irin kalar girkin ki bane"
Jin yana magana bata kulashi ba yasa ya ɗago ya kalleta,suna haɗa ido kaman jira yake taji wani amai da bata shirya masa ba yana shirin fitowa.
Tagudu tayi hanyar kitchen domin yafi mata kusa,a wajen sink ɗin wanke wanke tasake shi tafarayi. Tun tanayi shayin da tasha yana fitowa har yazamo babu komai sai ƙaƙarin kawai.
Ganin abin yaƙi ci yaƙi cinyewa yasa ahmad yabiyo bayanta,a bakin kitchen ɗin ya tsaya yana kallonta harta gama ta zuba ruwa.
Juyowa tayi suka haɗa ido saikuma ta ɗauke nata idon.
"Miye yake damunki,ko kinci wani abu ne ya bata miki ciki?"
"Ahah i don't think so. Kawai ina buɗe flask din abincin can naji zuciyata ta tashi. Ina zuwa bari naje na duba wani abu"
Wuceshi tayi tanufi ɗakinta da sauri.
A bangaren ahmad kuwa bai koma wajen abincin ba a kujera ya zauna ya kunna aljazeera.
Surayyah ce tafito daga ɗakinnata da wani abu a hannu,tana zuwa ta ajiyewa Ahmad a kan cinyarsa. Abin gwajin cikine na fitsari.
Ɗauka yayi ya duba inda yabada red line guda biyu dara dara.
Zaro ido yayi daya fahimci abinda hakan yake nufi.
"What are you pregnant? Me hakan kenan yake nufi"
"Kaman ya ahmad,bakayi farinciki ba dasu Farhan zasu samu ƙani ko ƙanwa ko ƙannai."
"No yaushe hakan ta faru naga......."
"Me kakeso kacene Ahmad,ba naka bane komai,abinnaka har yakai kayimin wannan ƙazafin har yakai ka ƙi amsar gudan jininka. Yaushe ka tsaneni haka?"
Cikin ɗaga murya take faɗin hakan saikuma ta fashe da kuka. Hanyar ɗakinta ta nufah da sauri kaman zata tashi sama.
Jikin Ahmad ne yayi sanyi,duk yana jinta wani iri a zuciyarsa amma yasan cikin jikinta bazai wuce nasa ba. Shi ba wai yana nufin cikin jikinta ba nasa bane,kawai abinne yazo masa a bazata,sam sam bai shirya ƙarayin zuri'ah da ita ba da wannan sabin halayyar tata. Sai yaji inama lokacin da tace zata cire implant ɗinta tanason haihuwa bai biyeta ba. Glass ɗinsa dayake gefe ya ɗauka yasaka tareda sake kallon PT ɗin,gani yake kaman bai kalla daidai ba.
Tana shiga ɗakin tagoge hawayen tareda yin wani murmushi.
"Ta ƙare maka Ahmad amjad"
Wayarta ta ɗauka ta danna ƙiran zeezah,bata daɗe tana ringing ba ta ɗauka.
"Hello mrs Amjad ya akayi ne?"
"Am pregnant zeezah,ni kaina bansani ba sai ɗazu,gabaɗaya har yanzu bangama yarda ba. Shima naga da alama bayyi farinciki da samun cikin ba. I think zan xubarshi idan har zai batamin plan"
"What!!! Pregnant ohhh god oooo,nima ji nake kaman wasa kike. Kutt mai ma kikecewa ki zubar kuma? Ke dallah banza wannan wani sabuwar babbar dama ce nasakashi a cikin kejinki. Ko bakiyi tunanin hakan ba"
"Waye banzar kinfara rainani fah"
"Sorry oga surry kawai naji ƙwaƙwalwar taki tafara sanyine,wannan mutuminnaki yana son susuta ki,to amma cikinshi ne,naga kwanannan gabaɗaya ƙauracemiki yake"
"Kiji ki dawani zance,to kafin ya ƙauracemin fah. Sannan kema da kika sanni har kike wannan zargin. I think kinsan halina duk tsiyata bana hulɗa da maza"
"Ehh hakane kam,kenan a ranar kika samu cikin"
"Ehh inaga hakanne"
"Wayyo Allah i can't wait to see this tafashashshiyar drama"
"Mtsww kanki ba ɗaya ba yanzu dai sai anjima."
Tana kashe wayar zama tayi a bakin gadon tana shafa cikin tana murmushi.
"Zeezah kenan lallai har yanzu kema baki sanni ba,a tunanin ki zan zubar da cikinnan ne. Duk wannan yunƙurin danakeyi na jawo hankalin sa duk dan na samu wannan cikinne. Bansani ba ashe Allah yagama taimakona yabani tuntuni. Yanzu aiki zai fara wannan yaran sune makamina na yaƙar muradina a gidannan"
Tana gama faɗin hakan ta ƙara ɗaukar wayarta.
Dr.Najeeb naga ta ƙira,daga can ya ɗauka.
"Hello ran gimbiya ya daɗe ya......."
"Kaga ba wannan ba ina zuwa yanzu zakayimin gwaje gwaje akwai abinda nakeson comfirming"
"Okay okay to shikenan sai kinzo gimbiyata"
Kashe wayar tayi tareda jan tsuka,bata ma gama jin abinda yake faɗa.
"Maye kawai"
Ta faɗa tana wurga wayar tsakiyar gado.
Amin magana ta wannan layin
09035784150
Sadi-sakhna ce.
⚫ *MUMINA KO AZZALUMA*⚫
Available on:wattpad&arewabook
⚫ _SADISAKHNA_⚫
⚫ *BOOK 1*⚫
⚫ _PART 7_⚫
"Hajiya ummee"
"Na'am"
Ta amsa tareda ɗaga ido ta kalli Nimrah wacce ta tashi zaune daga kan kujerar da take. Itama hajiya mama wacce take zaune zuba mata ido tayi hakama Zainab.
Ɗauke kanta tayi tamayar kan Hajiya ummee tareda cewa.
"Wlh ummee gaskiyar Yah Ahmad ne Aunty Surayyah ta sauya sosai,wai fah ashe masu aiki take sakawa su na yimasa girki yanzu,dayace bazaici bane shine tace wai na yi masa. Kunga kayan data saka kuwa,hmmm wlh ko turai iyakaci bingil bingil fah sannan warin........."
"Ke ke ke ya isheki haka banason munafurci,wato Nimrah kina nan da Gulmarki koh,ina ruwanki mata da gidanta,dan ta ƙiraki kinyi masa girki wani abune,idan batada lafiya fah. Shine kinje kin gano zaki zo kina fesawa ko,wato kullum ina rabaki da irin wannan halin bakyaji.
Shima ai inajin labarin abinda yakeyi,wai shi tana nuna masa hali ba yanda ya saba gani ba. Shikenan kullum ake kwana a gado. Kokuma dan yasha mangwaro yazama ƙwallo sai akace ya yasar. To wannan halin sakarcin ba a nan gidan ba. Yacigaba dayi duk lokacin da muka haɗu zaiga yanda zanyi dashi"
Hajiya Mama ce tafara faɗa,ta inda take shiga ba tanan take fita ba. Hajiya ummee kuwa murmushi kawai tayi batace ƙala ba.
"Hmmm mama kenan wlh kema dan bakiga yanda ta koma bane,da saita baki mamaki,kuma indai yanda nagani ne to abin a tausayawa yah Ahmad ne"
"Tausayi yaci ƙaniyarsa shida tausayin. Dan yaga yana abu ba'ayi masa magana shine yaketa yi koh. Sanin kansa ne iyayen yarinyar nan ba ƙana nan mutane bane. Duk lokacin da abinda yakeyi yaje kunnnensu ba abin kunya zai jawo mana ba. Waye zai yarda a dunga yiwa ɗiyarsa haka,har wani yace shi bai yarda da itaba. Yasan bai yarda da itan ba yaje ya auro ta hadda zuri'ah"
"Mama wlh ki daina wannan faɗan bayan bakisan mai take faruwa ba"
"Ke in baki tashi kin bar wajennan ba kema sai naci malafar ubanki,ƴar kare da surutu sai kace rediyon fulani"
Filon dayake gefenta ta wurgeta shi,hakan yasa ta tashi ta fita daga falon da gudu tana dariya.
"Mamar yara wannan faɗan dai da alama ita dai Nimrah ta tsokanoshi ne amma ba da ita ake ba damu ake"
"Hmmm addah kenan ki barni dashi naga ke lallabashi kikeyi,haka kawai mata tana nuna maka ɗabi'u masu daɗi kana jin daɗi kana yabonta,saidan kuma kaga ba yanda ka saba gani ba saika fara nuna mata baƙin hali. Gashi itama wannan ganin yanayi harta fara ɗebowa tana fesarwa. Su mata ai sun gaji sauyawa daga lokaci zuwa lokaci. Idan kuma juna biyu ne da ita fah takeyin hakan. Shikenan sai yace baisan zance ba. Ina halin dattaku anan. Kanason zama da mata kuma bazaka jure ƙalubalenta ba"
Ta daɗe tana faɗan saida tayi dan son ranta kafin tayi shuru.
"Ka ƙirani amma tun ɗazu kaƙi cemin komai,sai saƙe saƙen zuci kakeyi. Mai yake faruwane naga abinnaka yanzu yafi ƙarfin magana saidai addu'a"
"Saleem cikine da ita fah?"
"Wacece mai cikin,wai Surayyah?"
Ɗaga kai yayi batareda buɗar baki yabashi amsa ba.
"To menene don tanada cikin,wannan ne haihuwarta karon farko dazaka ji abin kaman sabo?"
"Hmmm bazaka gane bane saleem,wai ni kowa baya ganin ya take ne saini kaɗai nake gani. Dukkan ku bakwa ganin sauyawarta ne. Nafaɗa muku akwai abinda yake tattareda Surayyah wanda ba daidai bane,amma babu wanda zai yarda dani. Har ila yau bangama da wancan ba kuma ace wai cikine da ita a yanda take nan zata ƙara rainamin yaro inaa bazai yiyu ba."
"Bazai yiyu ba kaman ya,kaifah kace tariga ta samu cikin,to me zakayi mata"
"Idan zata yarda Saleem zubda cikinnan za'ayi,ko nawane ta faɗa zan bata idan har zata zubda shi wlh"
"Innalillahi wa inna ilahi raji'un,kai gaskiya ahmad ba ƙalau kake ba zancen gaskiya,dolene naje na samu baba na faɗamasa halinda ake ciki,wai yau cikin dayake jikin Surayyah kake shirin zubarwa,kaida har kyautar kujerar makka ka bawa nurse ɗin datayi mata gwajin cikin su farhan"
"Hmmm wai fah kallon marar hankali kukemin ko Saleem? Inama zan buɗe zuciyata na nunamuku yanda nakeji,inaga da zaku yarda dani. Kwanciya danayi da ita tasamu cikinnan har yau kuma bazan manta ranar ba ji nake kaman na tabka wani babban zunubi a rayuwata da bazan iya gogeshi ba. A da abin baya damuna sosai amma ganin sakamakon daya biyo baya ya ɗagamin hankali ba kaɗan ba. Inama zan koma baya na goge wannan lokacin,inama zan buɗi ido naga bata cikin rayuwata,da saina fi kowa farinciki a rayuwata"
Sororo Saleem ya tsaya yayi yana sauraransa,gabaɗaya maganganun gani yake kamar ba daga bakin ahmad ɗin suke fitowa ba. Ohh idan kana raye a duniya kana numfashi to zaka ga komai ma.
"Ni yanzu kafi ƙarfina bansan mai zance dakai ba,kawai a matsayina na abokinka taimako ɗaya zanyi maka shine zan dunga yimaka addu'a a kullum idan nayi sallah,akan Allah ya yayemaka duhun daya lullubeka,domin ba ƙalau kake ba"
Yana gama faɗin hakan ya tashi daga office ɗin yafita cikeda damuwa.
Ya rufe ƙofa kenan sukayi ido huɗu da Surayyah wacce ta shigo office na farko inda sakatariya take.
Tun kafin Saleem yayi mata magana ta jefa masa gaisuwa,hannunta da wata farar takarda mai kaman envolope.
Wucewa tayi zata shiga office ɗin ahmad ɗin,maganar sakatariyar ce ya tsaida ita. Wacce take sake tuna mata gargaɗin da Ahmad yayi mata akan kada ta sake shigowa nan ɗin.
Wani kallon ina zuwa kanki tayi mata kafin tashige cikin office ɗin,duk abinda yafaru Saleem yana kallonsu har ta wuce shima yayi ɗan guntun murmushi yabar wajen.
"Mai ya kawoki nan,ba nace komai kike buƙata ki bari na dawo ba?"
"Haba Ahmad amma ai ka bari na zauna koh?"
Tayi maganar da murmushi akan fuskarta,jan kujera tayi ta zauna,saida ta lila na ɗan sakanni kafin ta ajiye masa takardar a gabansa.
"Daga asibiti nake nayi gwaji da duk abinda ake buƙatar mai ciki tayi, ina ɗauke da ciki na tsawon wata uku,what will suprise you ƴan biyu ne saidai ba kaman su farhana ba su dukka mazane"
Ɗagowa yayi da sauri ya kalleta,twins kuma wai maza he can't imagine.
Komawa yayi a hankali ya jingina da jikin kujerar tasa,jin cewar ƴan biyune kuma maza sai yaji kamar ya fasa furta kuɗirin dayayi niyya,saidai kuma inaaa zuciyarsa taƙi aminta sam da lamarin.
"Nasan bawai albishir na cikin kikazo kiyimin ba,maganar danayi jiyane ya kawo ki,nawa kike buƙata ki zubar dashi?"
Wani murmushin ƴan duniya Surayyah tayi kafin taja dogon numfashi.
"Ahmad kenan,kaman yanda kake iƙirarin na sauya kaima kanka ka sauya,nayi tunanin dana faɗamaka mai yake cikina zaka sauya ƙudurin dayake ranka,amma sainaga koda akan