Showing 27001 words to 30000 words out of 35410 words

Chapter 10 - AKAN AIKINA Complete BY UMMU MAHER.txt

har an kusa gamawa duk da ba iya Gidan su bane,har wani kango na kusa da Gidan su Mumtaz d'in ya had'a ya siya sai gashi gida ya fito d'od'ar yayi kuma girma.




Duk abinda ke faru wa Mlm ya Sani Umma CE kawai bata Sani ba hatta Amal ta Sani,Muta'z ya nemi alfarmar a k'ara wa su Mumtaz sati d'aya akan Wanda ta yi sannan ya ware kud'i masu yawa don akaita d'akin Hutu,koda Umma ta samu Mlm da maganar jikin Muta'z yayi sauk'i kuma gashi har yanzu babu zancen Sallama,sai Mlm ya ce mata eh ai sun fad'a masa sai ta k'ara sati d'aya,daga haka Umma bata kara magana ba ta cigaba da kula da y'arta Mumtaz, don halin da ta ke ciki tana buk'atar kulawa sosai.




Har yanzu tsoron Muta'z Allah dai yasa Mumtaz bata fad'awa iyayenta abinda ya faru tsakaninsa da ita ba,sai dai har yanzu mamaki ya ke yi da yaji babu Wanda yayi masa magana koda kuwa a fuskane don kullum sai sun had'u da Mlm kuma kullum Muta'z cikin yiwa Mumtaz hidima ya ke yi kamar Wanda baisan zafin kud'i ba.gefe d'aya kuma yana k'ara son Mumtaz da ta rufa masa asiri ba tare da ta tuna masa ba.












*MURAT*
Ayanzu fa Murat da Meema abin duniya ya ishesu gashi yanzu komai ya dagule musu don har yanzu basa shiri tun akan abinda ya faru,don shi Murat gani ya ke yi laifin Meema ne ita kuma Meema tana ganin laifin Murat,tofa wannan ne ya had'a musu wata gagarumar matsala don tsakanin Murat da Meema an samu matsala,don ayanzu Murat ya koma kula wata aminiyar Meema suna lalacewarsu,don Meema ta tab'a ganin su awani hotel inda hankalinta ya tashi sosai,har ta yiwa Murat barazanar nunawa duniya vedion sharrin da a kayiwa Muta'z, hankalin Murat ya tashi sosai ya dinga Neman su shirya da Meema ita kuma Meema ta CE Indai yana son su shirya sai dai ya Aure ta,domin kuwa ta gaji da yawon duniya babu shiri Murat ya amin cewa Meema Amman zuciyarsa bata so hakan ba don dai babu abinda zai iyayine,don baiso Auren irinsu Meema yafi son ya Auri Y'ar Gidan mutunci.














*MUTA'Z*




Alhmdulillah ayanzu an kammala ginin Gidan su Mumtaz komai na more rayuwa anzuba musu d'akin Mumtaz kuwa kamar d'akin matar gwamna saboda kyau gaban mirror kuwa kayan shafa ne kala_kala,ga kayan kwalliya turare da dai sauransu gida dai masha Allah.






Mota guda Muta'z ya bada da driver don tuk'a iyayen Mumtaz da ita kanta sarauniyar Mumtaz,wadda har yanzu bata San wainar da ake toyawa ba.koda aka d'akosu daga asibiti Mumtaz kallon motar kawai ta ke yi saboda kyau da tsarinta ga A/C mai dad'i aciki,koda ta shiga motar sai da taja dogon numfashi don motar k'arshe CE ta had'u sosai.da sosai.






Mamaki da rud'a nine suka ziyarci Mumtaz ganin Gidan su ya koma kamar a k'asar waje,Salati ta farayi a fili tana kallon Umma da Mlm tana cewa"Umma kalli gidamu?wani azzalumin ya karbe ya gine mana shi don rashin tausayi.










Notice!zaku ga na bar GRP kuyi hak'uri laifin ogane don baya so,Amman zan cigaba da tyiping insha Allah nagode!nagode!dafatan kun fahimce ni🙏🏻ina missing dinku mussaman Amira da Bilkisu da Kaltum khanna masoyan littafin Akan Aikina na gode na gode,Mumtaz tana gaisheku,duk Maison magana dani sai ya turomin sak'onsa ta private domin bana cikin GRP.🙏🏻🥰






*ILOVE U ALL MY PANS🥰🙏🏻😭*


*Ummu Maher CE*
_*✨AKAN AIKI NA*✨_


By
Ummu Maher (miss green)




Ina gaida masoyan wannan littafi na akan Aikina aduk inda kuke,Akan Aikina fans GRP ina gaisheku ban manta daku ba duk da bana cikin GRP.






No.56&57




Umma ma mamaki ne kwance fal fuskarta ta kalli Mlm tana son k'arin bayani,"Muje Mlm ya CE wa Su Umma sannan ya bud'e get d'in Gidan suka shiga,Mumtaz da Umma bin Mlm kawai sukeyi kamar rak'umi da akala har suka shigo babban farlon Gidan,Mlm ne ya yi musu alamar su zauna cikin kujerun da ke farlon,a d'arare Umma da Mumtaz suka zauna suna ta faman mamaki kujerun ma kad'ai abin kallo ne.




A nitse Mlm ya fara basu labari tunda ga farko har k'arshe ya k'are maganar yana kuka,don tunda ya ke bai tab'a tunanin ko irin wannan Gidan zai shiga da aunan aiki ba,ballan tana ya zama gidansa,babu abinda zai cewa Muta'z sai dai Allah ya saka mishi da alkhairi,don da Mlm ya so yayi taurin kai wajen amsar Gidan Amman kuma daga baya yaji babu dad'i mayar da hannun kyauta baya.






Wani Abu ne ya tsaya wa Mumtaz azuciyarta wai yau Wanda ta tsana arayuwarta wai shine ya Gina musu gida irin wannan?ta kalli Mlm tana matuk'ar jin tausayin iyayenta don tasan basu San munanan halayensa ba da basu amshi wannan Gidan da ya yi musu ba amatsayin rufe musu baki sai dai tasan Mlm bashi da kwad'ayi ko kad'an kawai dai ya amsa ne don ko babu komai yasan filin Gidan sane kuma bayan hakan tasan Mlm baya maida hannun kyauta baya.




Umma ma ta yi murna sosai tana ta saka mishi da alkhairi,Mlm ne ya raka Mumtaz d'akinta a saman bene Wanda ya gaji da had'uwa don irin benen nanne mai rawn kafin ka isa saman,bata gama mamaki ba sai da ta shiga d'akin nata,d'akin ya gaji da had'uwa ta CE"wow so nice"Amman da sauri ta rufe bakinta tuno da cewa Muta'z ne ya saka mata komai ba d'akin sai taji duk bak'in ciki ya kewaye ta.koda ta bud'e sip d'in da ke manne acikin d'akin taga kaya sun kai set hamsin a shirye a goge acikin Sip d'in masu matuk'ar kyau Riga da siket dogayen riguna da k'anan kaya maau kyau da tsari,ga gaban madubi kayan shafa kala_kala.






Da daddare suna zaune kan Dining suna cin abinci suka ji nocking, Mlm ne ya CE Mumtaz ta je ta duba,a hankali ta tashi ta bud'e k'ofar farlon,gabanta ne ya yi wani irin bugawa ganin Muta'z a tsaye yana kallon ta da rinannun idanunsa,yana sanye da wata d'anyar shadda coffee, kasan cewarsa mai haske ba k'ara min kyau suka yi masa ba.




Murmushi ya sakarmin sannan ya rab'a ta gefe na ya wuce ni kuma na rufe k'ofar ina binsa da wani mummunan kallo,aduk sanda naga Muta'z sai naji wata muguwar tsanarsa acikin raina don bana manta sanda ya yi amfani da k'arfinsa a matsayinsa na d'a namiji ya yi min fyed'e,har yau ban San me yake damuna ba da nake b'oyewa iyaye na abinda ya aikata min,tsoronsa?ko me na keji da na kasa fad'awa iyaye na.




Haye wa sama na yi ina sharar kwalla acikin akan kyakkyawar face d'ita,da kwallan tausayi Muta'z ya Bini har na shige d'akina na haye lumtsumemen gadona ina kuka mai cin rai,Muta'z ya cuce ni yanzu idan nayi Aure me zance da mijina matuk'ar ya Gane ni ba budurwa ba CE? Wannan tambayar kullum na ke yiwa kaina Amman na kasa samun amsa,sai dai amsa d'aya na ke bawa kaina Muta'z ya cuceni.






Tun daga ranar sai Muta'z yazo gidanmu da daddare sunyi hira da Mlm kuma ayanzu ya samowa Mlm aikin wani company d'aya daga cikin company Mai Martaba wato Mahaifin Muta'z.


Alhmdh don ko ayanzu munyi ban kwana da talauci,awani yammaci ne Mlm ya sameni a d'akina ina karanta wani novels mai suna ASANADIN ABAYAR SALLAH,na marubuciya Ummu Maher, na ji dad'in littafin sosai ina cikin karatunne Mlm ya shigo,na yi saurin sakkowa daga kan gadon ina gaishesa,ya samu waje ya zauna ni kuma ina k'asa azaune na sunkuyar da kaina,gabana sai fad'uwa ya ke yi,na jiyo muryar Mlm yana cewa.




"Mamana magana na keson yi da ke ta fahimta don nasan halin Mamana idan abin bai miki ba ki fito ki gaya min?don ba zan miki dole ba sai dai ,a irin wannan rayuwar da muke ciki Abu ne mai wahalar gaske samun namiji mai addini,nutsuwa da kuma kamala, wannan yaron Muta'z ne ya ke sonki kuma harya turo magabatansa don ayi mishi iso don ya fara zuwa zance".






Da sauri na tashi tsaye dafe da k'irjina Wanda ya ke sama da k'asa tsabar tashin hankali,Na CE" Baba bazan iya Auren saba saboda bashida hali mai kyau.....








Ummu Maher CE.












Vote
Share
And
Comments.
*_💚💘AKAN AIKI NA💘💚_*


Book 4 last




Na
Ummu Maher(Miss green🍀💚)




58&59


Ina kaiwa nan na koma d'aki da gudun gaske ina kuka,matuk'ar aka takuramin akan Auren Muta'z to babu makawa nasan mutuwa zanyi don ba zan iya rayuwa da azzalumi ba,mak'iyi na,macuci,mazinaci.




Mlm ya kalli Umma sannan ya ce"Bazan tab'a yiwa Mumtaz auren dole ba,ina ganin wannan yaron da mutunci fiye da yadda kike zato,don kafin in sanarwa Mumtaz sai da na yi bincike sosai akan yaron don,yaron d'an manya ne Babanshi ayanzu haka shine sarkin da ke mulkalmu,sarki me adalci da sanin yakamata,zanso Mumtaz ta Auri Wannan yaron badon kud'insu ko wani abuba,A'ah sai don tarbiyyarsa da nagartarsa."




"Ki rarrashi Mumtaz bazan tab'a yi mata zab'en tumun dare ba a matsayina na mahaifinta,kuma nasan wataran itama za tayi alfahari da wannan Auren,don na hango so da kuma tausayin Mumtaz a cikin kwayar idanunsa,don haka zan cigaba da addu'ar Allah ya tabbatar da alkhairi Amin.






Kullum sai Muta'z yazo gidanmu amman bai tab'a ganina ba,don da naji k'arar motarsa na ke guduwa don ayanzu ba wai son ganinsa ne ba nayi ba,a'ah kawai da naganshi sai inji gabana ya yi muguwar fad'uwa.




Ga Amal kullum tana gidanmu muna shan hira,ita ma hirarta a kullum bai wuce in Auri Yarima Muta'z ba,don a cewarta munyi matuk'ar dacewa da juna,don kullum idan yazo suna shan hira shida Amal,kuma kullum baya gajiya da bawa Amal sak'o ta kawomin,har waya sabuwa dal ya kawomin.




***
Ranar wata asabar ina zaune ina shan iska a farfajiyar gidanmu,ina sanye cikin riga da siket ns atamfa holand na tufke gashina,na siraro d'an kwalin ta tsakiya gashina ina shan iska,sai naji ajikina kamar ana kallona,saurin juyowa na yi sai da gabana ya fad'i na daburce har na yarda d'ankwalina a k'asa,na yi saurin duk'awa don d'auko d'ankwalin,sai na ji hannun mutun dab dani na sunkuya shima ya sunkuya tare muka d'auko d'ankwalin hannayenmu na gogar na juna,babu abin da na tsana irin had'a idanu da Yarima Muta'z, don wani abu na ke hangowa acikinsu wanda ya ke sakawai gaba kid'aya inji kwarjininsa ya bai bayeni,don duk tsiwar dana d'auko zanyi mai sai naji ta tafi.


Cikin voice d'insa mai dad'i ya ce


"ykk My pricess"
Saurin d'ago kaina na yi sannan na tashi zan tafi,ya ruk'o hannuna gaba d'aya naji na fad'a kan k'akk'arfan k'irjinsa,muka had'a ido ban san sanda na tashi da sauri na shiga gida ba,gaba na yana dukan³,shi kuwa shafar gashin kansa kawai ya yi yana jin kansa kamar wani sabon ango.








MURAT
______
***
"Meema wallahi kin cuceni,kin cuci aminina da kika k'ara bani kwarin guiwa wajen cutarsa da kuma cin amanarsa,Allah bazai tab'a barin mu ba,matuk'ar hakkin Muta'z yana kanmu,kuma ki sani Meema bazan tab'a auren wulak'an tacciyar mace irinki ba,wacce ta gaji da duniya,duniya ta gaji da ita......




" kai Murat sai ta zancen ka wallahi tallahi daman kai can Azzalumine macuci,don haka kada ka sake cewa wai ni ce na saka kan hanya?"kuma ka ke tatsuniyar cewa ba zaka Aureni ba,kasan abinda ma bazai tab'a yiyuwa bane?"ko kana so?ko baka so?dole sai na Aureka,domin kuwa a lokacin daka rabu dani to fa awannan lokacinne zan toni asirinka kowa yasan waye kai".




Wani kyakkyawan mari Murat ya kifawa Meema sannan ya nuna ta da yatsar sa ya ce"Wallahi Meema kinyi k'arya ki gama lalacewarki sannan ki ce wai yanzu in Aureki,bazan tab'a Auren Karuwa,fasik'a irinki ba,don haka ki nemi me Aurenki Amman ba ni ba.




Wata shewa Meema ta yi sannan ta ciro wani fefen vedio ta ce"wannan vedion Murat shine rayuwarka kuma shine Ajalinka bazan tab'a bari wannan vedion ya kufcemin ba,domin ina da irinsa yafi 100,kuma ka duba wayarka ka gani.












Kuyi hak'uri anyi min rasuwa ne shiyyasa na yi tyiping kad'an.








Taku har kullum Ummu Maher💔
Miss grèèn💚.


kunga yanzu bana grp so duk masuyin comments yana isomin.


Ku yad'a
Sannan
Kuyi comments✍️
*_AKAN AIKI NA_*






By Ummu Maher
Miss green🍀








60






....wallahi Fulani ina masifar son yarinyar tare da tausayinta,Amman kinsan wani abin mamaki?


Fulani ta girgiza kai alamar a,ah.


"Amman yarinyar nan ko ganina bata San yi bansan ko me na yi mata ba,don Allah Fulani kije gidansu ki farauto min zuciyarta ko Allah zaisa ta so ni.






Shiru Fulani tayi har ya gama maganar sa,tana mamakin Yarima Muta'z ko yaushe ya yi Auren oho?har ya ke son k'ara wani Auren Amman sai ta daure ta ce" ni kuwa wannan wata yarinya ce mai sa,ah irin wannan Yarima kamar kai a ce an samu yarinyar da zata k'i ka?ko dai wani Abu ka yi mata da bata sonka?ni dai nasan babu macen da zata had'u da kai ta ce bata sonka,don komai kana da shi na nagarta ilimi,addini,tarbiyya,kyau,nasaba,hak'uri,da kuma yiwa iyayenka biyayya.




Don haka irinku mata suke so,don haka na yi maka Alk'awarin nemo maka Aurenta kuma Insha Allah komai yazo k'arshe.




Rungume Fulani Yayi sannan ya manna mata kiss a kumatunta,don bashi da tamkar Mahaifiyarsa.










"Hajjo in zo ki rakani wajen Fulani ta damamin wannan furar ta ta,mai dad'i ke Idan mutun yazo gurinki saiki cikani da wasu magarya alhalin ba k'oshi zanyi ba,"to uwar masifa muje kisha gero ma ba fura ba".








Suna shiga sashen Fulani suka ga Murat yana zaune suna ta hira da Fulani,Mimee ta sunkuya ta gaishe da Fulani cikin shagwab'a tace"don Allah Mama ki dama min fura insha wallahi indai bansha fura ba sai inga kamar cikin jikina zai zube wallahi."


"Ah ai kuwa yanzu Muta'z ya gama shan nasa,bari akawo miki yanzu kinji y'ata,ba a b'ata lokaci ba Mimee ta shiga shan furar ta babu k'akkutawa,don tunda ta samu ciki yau kusan wata 7 kenan take masifar shan furaDon fura tana d'aya daga cikin abinda take masifar son sha tunda ta samu ciki.








....tun safe Umma da Mlm suke shiri don Muta'z ya gaya musu zuwan Mahaifiyarsa,Amman Mumtaz tana cikin d'akinta ko lek'owa bata yi ba,don wani azabar zazzab'i da ciwon kai ta ke ji.






"Mumtaz!Mumtaz!!INA kika Shiga ne tun safe kina d'aki don mugun halinki da ki ka koya to wallahi maza maza ki sakko tun safe nake aiki kina.....




Maganar ta ce ta tsaya jin Takun shigowarsu Muta'z da Mahaifiyarsa,rasa inda zata sakasu ta yi Mahaifiyar Muta'z kawai ta tsaya tana kallonta tana yi mata wani irin kallo.,.








To Ku biyoni anan gava don jin wani irin kallo Mahaifiyar Muta'z ta ke yi wa Umma,Mahaifiyar Mumtaz?shin me ya janyo wannan kallon?.












*Ummu Maher CE*








Share&cmnt.
[11/22, 15:19] 🥰Ummu Maher🏕️⛱️: *_AKAN AIKI NA_*








By
_Ummu Maher_
_*Miss green*_


Wattpad
Rabiatu222






64&65


.....Da sauri Fulani ta rungume Umma sannan ta CE"Jamila daman kina raye tun kina jaririya aka yarda ke aka nemeki aka rasa,Allah mungode maka da Bayyanarki don babu tantama Jamila ke ce don kamarku da mai Martaba har ta b'aci wallahi".






Mamaki da firgici ne suka kama Umma sosai don ita dai tunda ta taso a rayuwarta bata San kowa ba sai Mlm da Iyayenshi sai dai basu b'oye mata komai na rayuwarta ba,sun gaya mata cewa tsintarta a ka yi a gefen hanya.




Da sauri Fulani ta d'auko wayarta ta kira Hajja don ta shaida mata.






"Wai wani jarababben ne ya ke damuna awaya ne?idan na ce kada a siyomin waya sai an siyomin to nidai babu ruwana wallahi da munafinci"...




Maganarta ce ta tsaya cak,jin abinda Fulani ta ke fad'a hannu na rawa Hajjo ta saki wayar ta fad'i k'asa wan war, Meema ce da ke kwance saman kujerarta tana shan fura ta hango Hajjo zata fad'i k'asada k'er ta tashi don taro kakar ta.




Hajjo kuwa da kanta taje wajen
[11/22, 20:15] 🥰Ummu Maher🏕️⛱️: Mai Martaba don shaida masa abinda ke faruwa don hankalinta ya tashi sosai da jin wannan maganar,shima cikin tashin hankali ya biyo Hajjo suka fito dogarai suka biyosu don bud'e musu k'ofa,cikin sauri Mai Martaba ya fara tuk'a motar cikin gaggawa,rabonda ya yi tuk'i kusan shekara 20 kenan.






Da kwatancen Fulani Allah ya kawo su Hajjo lfy harma da Meema,kai tsaye suka shiga cikin Gidan,hankalinsu gaba ki d'aya ya karkata ga maganar Momi.








"Inna lillahi wa inna ilaihi Raji'un"


Muryar Hajjo ce ta karad'e d'akin sannan ta tafi da saurinta ta rungume Umma tana mai godewa Allah da yasa taga y'arta tun kafin ta mutu don a kullum addu'arta taga y'arta don duk duniya tana son ta tunda kuma ta haifeta aka ga irin son da ta ke yi mata shikkenan aka tsani yarinyar har sai da aka had'a baki da wata baiwa aka yardar mata da y'a,sai da aka gane kuma Allah ya Toni asirinta ta fad'i gaskiya sun had'a baki da kishiyar Hajjo don ita bata da y'ay'a,Mahaifiyar Meema ita ce ta biyu sai Kuma Mahaifiyar Mumtaz Auta kenan wadda ta b'ata tun tana k'arama.


Ko da Mlm ya ce su Hajjo su bada wata shaidar bayan kama da Umma ta ke yi da Mai Martaba,nan ta ke Hajjo ta tashi ta ce Umma ta ja hannun rigarta akwai tawadar Allah,haka kuwa a kayi tana bud'ewa kuwa sai ga tawadar Allah.




Da sauri Umma ta tashi ta k'ara rungume Hajjo tana mai jin dad'in ganin Mahaifiyarta duk da bata Santa ba sai yanzu,Addu'ah Mai Martaba ya fara yi sannan aka fara hira gwanin ban sha'awa,Muta'z ma yazo nan ya dinga jin wani farin ciki a cikin zuciyarsa don daman tun ranar da ya fara ganin Mumtaz yasan cewa jininsa ce don yadda ya ke sonta kamar rai.







Yawan maganar da akeyi ne ya tasheni daga dogon baccin Dana samu,ina tashi naji ciwon kan gaba kid'aya babu shi, daga ni sai wata doguwar rigar bacci pink colour tana da siririn hannu,gashin kaina ya bazo baya duk ya warwatse alamun daga bacci na tashi,na fara sakkowa saga upstar ahankali cike da nutsuwa na fara kiran Umma!Umma!!.


Tunda na fara sakkowa mutanen wajen hankalinsu ya dawo kaina kowa yana jinjina wannan halittar mai kyau da tsaruwa,Fulani kuwa cewa ta yi Lallai dole Muta'z d'inta ya gigice don duk yadda ya kai da kyau to fa wannan yarinyar k'arshe ce.




Ita kuwa Meema tun kafin ma tasan wacece taji tana wani matsanancin kishi da Mumtaz, don Meema da taga hankalin Muta'z duk yana wajen

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login