Showing 9001 words to 12000 words out of 35410 words

Chapter 4 - AKAN AIKINA Complete BY UMMU MAHER.txt

take ta kallon Ummana ko k'ifta idanu babu.

Tace Umma lafiya klau duk suna gaisheku daman nazo wajen Hanan ne k'awata ce amman a Chart muka had'u da'ita har tazama kusan aminiyata so shiyyasa har muka saba to nazo sau d'aya kafun su tashi muka gaisa.



Umma tace Allah sarki sai kuma kikaji sun tashi?Hanan tace wallahi kuwa Umma kuma naga baya hawa online kwata kwata kuma wayarta ma bata shiga shine nace ko lfy bari inzo inji?sai kuma akace mun sun tashi.




Umma tace wallahi kuwa y'arnan sun tashi amman Allah yasa lafiya dai wayarta bata shiga? Muka had'a baki wajen cewa Amin ya Rabbi.



Hanan tace Umma tunda muka shigo naga kina mun kama da Mahaifina mai marta ba?Umma tayi dariya tace ke y'annan mai marta ba dai saidai kama Umma ta fad'i hakan tana dariya.





Idan kunda d'a Comment sai zan k'ara tyiping.






*More Comments*โœ๐Ÿป


*More tyiping*โœ๐Ÿป




*Ummu Maher ce*
*Tyiping*๐Ÿ–Œ๏ธ


ABOUT MY WORKโœ๐Ÿป


๐Ÿ’š๐Ÿ’š๐Ÿ’š
(แƒฆห˜โŒฃห˜แƒฆ)(แƒฆห˜โŒฃห˜แƒฆ)
*AKAN A'IKINA 2021*
(แƒฆห˜โŒฃห˜แƒฆ)(แƒฆห˜โŒฃห˜แƒฆ)
๐Ÿ’š๐Ÿ’š๐Ÿ’š


*NA*
*RABI'ATU.B.ABDULLAHI*
(Ummu Maher)Miss green๐Ÿ’š๐Ÿ“—








BABI NA 15&16๐Ÿ“


Hanan tace Allah Umma kinyi kama sosai da mai martaba sosai wallahi,don ni da naganki ba kiji yadda gabana yake fad'uwa ba wallahi don tunda nake ban tab'a ganin i'rin wannan kamar ba don ko mu da muke y'ay'anshi ba muyi kama da shi haka ba.




Dariya Umma ta kuma yi a karo na biyu don i'ta abunma dariya ya bata,tace Hanan kenan a'i ita kama haka take ba kiji ance babu wanda akayi kamanninshi shi kad'ai illa Manzon Allah(S.A.W)to bayan shi kuwa gaskiya ko wacce kama da y'sr uwarta,Amman nasha ganin mutanan da suke yi n kama sosai don wani ma in baki sani ba sai kice y'sn uwan juna ne.




Nan dai sukayi ta hira a junansu gwanin sha'awa daga k'arshe Hanan tayiwa Umma kyautar kud'i masu yawa Umma tayi ta godiya sannan na rako ta k'ofar gida ta hau motarta,ni kuma na koma gida ina jin dad'in yadda muka sha hira nida Hanan sai na tsinci kaina a mai tunanin Amal don bata bari na in zauna ni kad'ai ma ballan tana har inyi tunanin wani abu.






***************
A yau ne sakama kon jarrabarwamu ya fito na Waec&Neco don haka nayi saurin zuwa in dubo saka makona Alhmdh na ringa fad'i don jarrabawa ta tayi kyau sosai,Ina cikin murna na dawo gida don sanar da Umma cewa naci jarrabawa har nayi hanyar gida sai kuma na tuno da Malam wato mahaifina don in kai mishi yaga sakamakon jarrabawar don zan i'ya cewa Malam yafi Umma damuwa da karatuna.




Da murna ta na i'sa shagon ina zuwa na fad'a tare da Sallama alokacin yana gyara kaya akan trader d'inshi,ya juyo yace Mamana har kin dawo daga dubo jarrabawar?Nace eh Malam na dubo kuma sakamakona yayi kyau sosai,Malam yace Alhmdh Allah yayi miki Albarka Mamana kuma Allah yasa Albarka acikin A'ikin ki.




Nace Amin Malam nima ina godiya da ka sakani makaranta har nazamo yadda na zama yanzun Allah yasaka maka da Alkhairi yabarmu tare,Malam yace Amin amman fa ba nikad'aine nasha wahala wajen biyan kud'in makarantar kiba harda Alhaji Don shima ya taka gudummawa Arayuwarmu baki d'aya saidai muci gaba da yimishi Addu'ah ta samun nasara arayuwa.




Amin Malam kullum sai nayi tunaninsu ko wani hali suke ciki gashi ko number d'insu bamu dashi ballan tana in kirawo inji muryarsu,Malam yace A'i jiya yasaka wani ya kawomin wayarshi wai ya kawomun mugaisa.




Nace kai Malam shine baka kirawo niba mungaisa,Malam yace to A'i kinga wayar ba tawa bace shiyyasa amman yanzu zan sai waya sai mudinga gaisawa nace to shikkenan hakan ma yayi.








**************
Meema tace Murat kasan Allah bazaka ringa raina mun wayo ba kana cemun wai Har yanzu baka gama target d'in ba,abunda muka tsara shine kafun yayi wannan tafiyar tashi zamu A'ika ta komai don yana da kyau ace yanzu kasan inda yake maka ciwo ya mayar dakai kamar wani oganka sai abunda yace ka keyi wai shi gashi mai kud'i.




Murat yayi murmushi sannan yace Meema kenan kinsan nafiki hankali da kuma ilimi sannan na fiki Zak'uwa akan abunda zan A'ikata amman yana da kyau ace kasan yadda zaka tafiyar da tsarin A'ikin ka kinga kuwa dole saidai mubi a sannu har Allah ya cika mana burinmu.




Meema tace Hmm nifa kasan Allah Muta'z d'innan mugun haushi yake bani taurin kanshi da kuma jiji da kanshi yayi yawa,shifa ko kallon mata ba yayi ballan tana ma har ayi tunanin wani abu,nasha d'ana mai tarko ina tura masa mata gidanshi wai don suja hankalinshi amman duk abanza babu wani abu da ya cigaba.




Murat yayi dariya i'rin tasu mugaye yace Hmm A'i kuwa zaki dad'e kina ai kawa Muta'z karuwai don shifa yadda kika san ba Namiji ba haka Allah yayi shi kwata kwata baya koda sha'awar y'an mata ballan tana har asamu abunda akeso ta wannan hanyar.




Meema tayi dariya sannan ta tashi ta bud'e fridge ta d'auko wani swan mai sanyi ta kora shi sannan ta d'aukoshi a hannun ta tana tafiya tana yanga kamar zata fad'i don i'ta Meema i'rin matan nanne sirara k'ugun ta kamar zata karye saboda sirantar tata har tayi yawa.




Murat kuwa tuni ya kwalalo mata manyan eyes d'inshi yana kallon Meema dasu donshi Gaba d'aya idan yana ganin Meema baya i'ya komai saidai duk yadda yake jin ta aranshi bata kai Hanan ba don Hanan ji yake indai bai Aureta ba komai zai i'ya faruwa.




Baisan sanda Meema ta zauna ba sai jin muryarta yayi tana cewa Murat ka kwantar da hankalinka kaji Insha Allah Akwai wata hanya da zanbi wajen naga ba ruguza rayuwar Muta'z amman ba yanzu zan gaya maka ba don nasan halinku na maza sai kayi amfani dani wajen biyan buk'atarka daga ka gama kuma ka jefar dani kan titi inda ka kwaso ni๐Ÿ˜.






Murat yayi dariya yace haba haba Meema ni na'isa in wulak'anta ki i'dan na wulak'anta ki in zauna dawa ki tuna fa duk abuna bazan tab'a mantawa dake ba don kinfimun duk sauran mata na duniyar nan.






Nanfa Meema taji dad'in wasa ta da Murat yayi taci gaba da shararomai zance tare da siyeshi da abubuwa kala kala i'rin nasu na y'an bariki shi kuma ya sakar maya hannun Aljihu ta d'ibi yadda take son kwasa.








*Wa nene Murat*




Murat dai shine asalin sunanshi wanda i'yayenshi suka saka mai,Mahaifinshi yakasance d'an asalin jihar Kano a unguwar Rijiyar lemo, Sunanshi ee'ro magini wanda babu inda baya zuwa acikin Nigeria don yin A'ikin gini kwararre ne sosai yayi Aurenshi da matarshi mai suna Maryam i'tama y'ar asalin jihar kano ce Unguwarsu d'aya da i'ta.




Sun dad'e Allah bai basu haihuwa ba saida sukayi shekara Goma da y'an watanni sannan ta haifi d'an ta Namiji suka saka mai suna Murat,Suna son Murat sosai.


Tashi d'aya Malam ya koma Bauchi don akwai wata ma'aikata ta masu gini don haka ya tattara iyalanshi suka tafi Bauchi,Kwanansu Hud'u da zuwa Bauchi aka kirawo ee'ro Aikin gini agidan sarauta Yaji dad'in Aikin sosai don ko babu komai yasan zasu samu kud'i sosai don haka yayi sallama da matarshi ya tafi.




Abu da ajali suna cikin Aiki bulo ya fad'o masa atake kuma rai yayi halinshi,don haka aka kai gawarshi hidanshi don a sallaceshi,Matarshi Maryam tayi kuka sosai kamar ranta zai fita alokacin Murat yana d'an shekara bakwai 7 amman duk da haka saida yagane mahaifinshi ya rasu.






Watan ee'ro biyu da rasuwa Maryam ma tabi mijin ta i'tama Allah yayi mata rasuwa,Shikkenan Murat ya dawo maraya babu uwa babu uba,don haka Aka kaishi gidan sarkidon a nemo y'sn uwan i'yayenshi.




Kwananshi hud'u da zuwa gidan sarki Sukayi sabo sosai da Muta'z wanda yakasance d'a tilo da sarki donko bacci Tare su keyi da Murat.
















*Ummu Maher ce*โœ๐Ÿป


Vote
share
And
Commentsโœ๐Ÿป๐Ÿ’Œ๐Ÿ“ฉ
*Tyiping*๐Ÿ–Œ๏ธ


ABOUT MY WORKโœ๐Ÿป


๐Ÿ’š๐Ÿ’š๐Ÿ’š
(แƒฆห˜โŒฃห˜แƒฆ)(แƒฆห˜โŒฃห˜แƒฆ)
*AKAN A'IKINA 2021*
(แƒฆห˜โŒฃห˜แƒฆ)(แƒฆห˜โŒฃห˜แƒฆ)
๐Ÿ’š๐Ÿ’š๐Ÿ’š



*NA*
*RABI'ATU.B.ABDULLAHI*
(Ummu Maher)Miss Green๐Ÿ’š๐Ÿ“—


ุจุณู… ุงู„ู„ู‡ ุงู„ุฑุญู…ู† ุงู„ุฑุญูŠู…
_________________
______
๐Ÿ…™๏ธŽ๐—ฎ๐—ฟ๐˜‚๐—บ๐—ฎ๐—ถ ๐Ÿ…ฆ๏ธŽ๐—ฟ๐—ถ๐˜๐—ฒ๐—ฟ๐˜€ ๐Ÿ…๏ธŽ๐˜€๐˜€๐—ผ๐—ฐ๐—ถ๐—ฎ๐˜๐—ฒ๐—ฑ๐Ÿ“š๐Ÿ–Š
https://www.facebook.com/101679598253281/posts/101680068253234/?app=fbl
_Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa illmantarwa, nishadantar tare da fadakarwa da jama'a bisa harshen hausa _


๐Ÿ”๐Ÿ…™๏ธŽ๐Ÿ…ฆ๏ธŽ๐Ÿ…๐Ÿ”


*BABI NA 17&18๐Ÿ“*




_____๐Ÿ–Œ๏ธ Hakan da mai marta ya ganine ya sa yafi fita Murat sosai sonda yake yiwa d'an shi Mutaz sai ya shafi Murat saboda haka aka saka Murat makaranta i'ri d'aya da ta Muta'z, Hatta kaya tare ake musu komai dai i'ri d'aya sai suka zamo kamar y'an biyu.




Tunda Murat ya taso yaga son da I'yayen Muta'z suke yimai da yadda suke narkar mai da dukiya sai abun ya tsaya masa aranshi yake jin cewa kamar son DA suke nuna mai na k'arya ne Saboda gaba d'aya yaga i'rin dukiyar da suke nar karwa akan d'an nasu.




Don haka Murat ya rik'e cewa tabbas sai yaga bayan Muta'z sai dai ya rasa ta inda zai Fara A'ikata b'ar narsa,Har Allah ya kawo lokacin DA suka shiga jami'ah alokacin ne kuma rayuwar Murat ta k'ara samun ta waya,Saboda gaba ki d'aya Murat ya canza hali,ya kuma canza abokai musamman ma da yaga acikin turawa yake,A'ikuwa Ana cikin haka ya had'u da d'an wani attajiri a makarantar nan danan suka k'ullah abokan taka dashi ya Fara koya masa harkar bin Mata,Muta'z kuwa koda ya gane abunda Murat ya keyi ba k'aramun tashin hankali ya shiga ba saboda aduniya banda i'yayenshi da k'anwarshi babu mutumin da yake so irin Murat yake kuma fatan rayuwarshi tayi kyau sai gashi ya b'ata rayuwarshi tun kafun aje ko'ina.






Har kullum Muta'z fad'a yake yiwa abokinshi akan yaji tsoron Allah Amman sai ya nuna mishi cewa ya fishi tsoron Allah don haka Muta'z ya cigaba da yiwa abokinshi addu'ah akan Allah ya shirye shirin addinin islama๐Ÿ™๐Ÿป.






Koda lokacin exam yazo Murat baiyi wani abun azzik'i ba don saka makonshi baiyi kyau ba Sam,Muta'z kuwa saka makonshi yayi kyau sosai da sosai,saidai daga lokacin da ya duba na Murat sai Murna ta koma ciki don ganin irin saka makon da abokin nashi ya samu.






Mai martaba yaji haushi sosai don duk abunda Murat ya keyi babu Wanda bai sani ba,saboda akwai masu kula da duk wani motsinsu sai dai su d'in basu sani ba don ya nemi kada su sani.






Allah ya taimaki Muta'z ya samu A'iki da gaggawa,shi kuwa Murat babu abun Arzik'i don haka Mai martaba ya d'aukeshi manager a company d'insu Amman lokaci d'aya Murat ya lalata Company ya zama gaba ki d'aya babu wani abu mai tsada cikin Company.




Hakan ne yasa Muta'z ya bud'ewa Murat Company na kanshi Wanda zai dun ga juya kud'inshi da kanshi I'dan ma ya cinye ruwanshi tunda Allah ya gani yayi mishi abunda yake ganin ya dace.










*Cigaban Labari*




Wani i'hu Mumtaz tayi tare da tsalle sai gata a tsakar gida,Umma tace ke Mumtaz wai meye yake damunki kina wani i'hu kamar zaki fasa mun Kai,Mumtaz tace Umma yanzu naji a radio Ana cewa Ana Neman masu son gurbi a jami'ah kuma harda ni acikin wad'an da aka suka samu gurbi a jami'ar.




Umma dariya ta Fara yi tana cewa Allah mun gode maka da ka amsa Addu'ar mu Allah ya taimaka,Allah ya baku sa'ah baki d'aya Allah ya sa i'dan kunyi karatun nan Allah yasa ku taimaki junanku Amin ya Rabbi.






Muna cikin murnar mu sai ga Mahaifina ya shigo shima ya ta yamu Murna sosai,Da daddare yace inzo muje kasuwa dashi,Bayan munje ya siyo min hija bai sun Kai biyar da ta kalmi da dogayen riguna masu kyau da kamala.








*Washe gari*




"Umma tace Kai Y'annan kinga yadda kika yi kyau kuwa cikin kayannan kinyi kyau sosai Wallahi,Dariya nayi lokacin da nake saka hijabina da yasha guga k'alk'al dashi gwanin ban sha'awa,simple make_up nayi ban shafa wani Jan baki ba hoda na shafa da lipstick na saka kwalli fuska ta tayi fayau nayi kyau gwanin ban sha'awa.








Rayuwar makaranta rayuwa ce mai dad'i kuma rayuwa ce mai sauk'i Amman idan ka d'au keta da sauk'i kuma idan baka nuna Kai d'an wani bane zaka zauna lafiya DA kowa,mutane da dama suna d'auka ta y'ar mai kud'i ceni saboda yadda lau nina yake,Nidai farace niba doguwa ba niba gajeriya ba ma'ana tsaka-tsaki.




I'na da dogon hanci Wanda ya k'aya ta fuska ta,ga d'an baki na k'arami mai kyau da tsari idanuna manyana masu wani i'rin launi mai kyau gwanin sha'awa,Hmm kyau da tsari saidai Wanda yaga Mumtaz.




Samari kuwa ta ko'ina zuwa suke wai suna sona Don takai i'dan naje makaranta bana fita daga class saboda yawan da samari suka yimun,A lokacin da nafara zuwa Makaranta na had'u da wata k'awata mai suna Zainab Bashir,Zainab mutuniyar kirki ce sosai don tana da d'abi'u masu kyau gata DA k'ok'ari sosai shiyyasa komai tare muke yi a cikin aji sai muka zamo abun sha'awa agun kowanni d'an ajinmu dama wad'an da ba y'an ajinmu ba .




Mun k'ulla k'awance mai k'arfi da Zainab,alokaci k'an k'ani y'an gidanmu suka Santa nima y'an gidansu suka sanni don kuwa watarana DA k'er muke rabuwa.






**********


Akwana a tashi asarar mai rai a yanzu muna lavel 3 inda muka k'ara dagewa a game da karatunmu na y'an jarida wato Mass Com,Allah yana bamu sa'ah a cikin karatunmu,Saidai ayanzu babu abunda yake da muna sai talaucin DA muke ciki nida i'yaye na.




Daman shagon da Baban su Amal ya bawa Babana shagon haya ne kuma asannu y'an unguwa suka karya mishi jarinshi da bashi don tsaba gen mugunta duk kud'in mutum sai kaji yace a bashi bashi toda i'rin wannan ne fa suka karyawa BABA na jari.






Shi kuma Mahaifina yana kunyar ya bugawa Alhaji waya ya sanar dashi halin da yake ciki,Saboda haka yaja bakinshi yayi shiru kuma ayanzu ya Fara Neman A'ikin da ya dace dashi Amman har yanzu Allah bai kawo ba.






Watarana ma haka nake tafiya makaranta ba tare da naci komai ba,Zainab kuwa kullum sai tazo da abinci makaranta duk saboda ni saboda tasan ni ba ma'abociyar cin abincin makaranta bace saboda haka take zuwa da abinci.






Duk itama Zainab ba kud'ine dasu ba Amman sun fimu rufin Asiri tunda Mahaifin ta yana A'ikin gwam nati sannan kuma yana da makarantar Islamiyya ta kanshi saboda haka yake samun kud'in da zai biyawa y'ay'anshi dukkanin buk'atunsu na yau da kullum.






Duk yadda Zainab za tayi Dani akan inci abincin da nazo dashi bana ci,don duk yadda muke dakai matuk'ar ba abincin mahaifiyata bane bana cinshi duk da d'inshi kuwa.












***********
Mai babban d'aki i'tace Mahaifiyar Mai martaba kyakkyawar tsohuwa mai farar Aniya,kamar kullum Muta'z da k'anwarshi sunzo gaishe da mai babban d'aki wacce suke Kira da Hajja,bayan sun gaishe ta suka zauna suna tsokanarta wai ta fiya cin goro gashi bakinta ya duk yayi ja.






Hajja kuwa tana jinsu ba tare da tace komai ba tayi dariya don ta shirya Rama i'ya shegen da suke yi mata,don haka ta kishin gid'a da filo Sannan ta k'ara gutsirar goronta ya bada k'araras sannan tace.






Hmm Ni kuwa Hanan i'na Saurayinki kuma yayanki Murat i'na yake?kwana biyu ban ganshi ba kada dai ace haryanzu bai daina rashin d'a Arshi ba?.




Sosa kai Hanan ta farayi tana cewa wallahi tsohu warnan matuk'ar mutum yazo wajen ki sai kin nemi b'ata mishi rai,yanzu meye laifinmu don munce kina cin goro A'i lafiyarki ake kare miki.




Hajja tayi dariya sannan ta kalli Muta'z tace Hmm wallahi Muta'z na kusa in gayawa ubanka ya nemo maka Mata kowa ya huta so kake kazama tuzuru agida KO to wallahi da Meemi Zan had'aka y'ar wajen Hajara wallahi kuwa kaji narantse daman irinku take so kyawawa.




Tuni Muta'z ya gimtse fuskarshi don yasan halin tsohuwarnan yanzu ta had'ashi da mai martaba,don duk abunda tace shi yake yi baya tab'a tsallake maganar Mahaifiyarshi Hajja.






Cikin Fushi Muta'z ya tashi zai fita don baya son hirar tasu tayi nisa don in akwai abunda ya tsana bai wuce zamcen Aure yanzu ba don babu yadda zai yi da Hajja ne shiyyasa,Karo yaci da wani Abu kamar mutum don haka ya d'ago kanshi don ganin waye?Meemi ya gani taci uban make-up tayi kamar y'ar tsana daman gata kamar zata karye,tsaki Muta'z yayi wuce warshi ba tare daya kalle ta,don haka Meemi ta juya tare DA cewa zaka sani yanzu Zan had'a maka muna finci kawai saita Fara kuka ta shiga wajen Hajja.














*Ummu Maher ce*
*Tyiping๐Ÿ–Œ๏ธ*




ABOUT MY WORK๐Ÿ“š






๐Ÿ’š๐Ÿ’š๐Ÿ’š
(แƒฆห˜โŒฃห˜แƒฆ)(แƒฆห˜โŒฃห˜แƒฆ)
_*AKAN A'IKINA 2021*_
(แƒฆห˜โŒฃห˜แƒฆ)(แƒฆห˜โŒฃห˜แƒฆ)
๐Ÿ’š๐Ÿ’š๐Ÿ’š




*NA*
*RABI'ATU.B.ABDULLAHI*
(Ummu Maher)Miss green๐Ÿ’š๐Ÿ“—


ุจุณู… ุงู„ู„ู‡ ุงู„ุฑุญู…ู† ุงู„ุฑุญูŠู…
_________________
______
๐Ÿ…™๏ธŽ๐—ฎ๐—ฟ๐˜‚๐—บ๐—ฎ๐—ถ ๐Ÿ…ฆ๏ธŽ๐—ฟ๐—ถ๐˜๐—ฒ๐—ฟ๐˜€ ๐Ÿ…๏ธŽ๐˜€๐˜€๐—ผ๐—ฐ๐—ถ๐—ฎ๐˜๐—ฒ๐—ฑ๐Ÿ“š๐Ÿ–Š
https://www.facebook.com/101679598253281/posts/101680068253234/?app=fbl
_Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa illmantarwa, nishadantar tare da fadakarwa da jama'a bisa harshen hausa _


๐Ÿ”๐Ÿ…™๏ธŽ๐Ÿ…ฆ๏ธŽ๐Ÿ…๐Ÿ”




*BABI NA 19&20*๐Ÿ“




Hajja tace"Meemi me ya faru kike kuka gayamun Wanda ya bugeki yanzu in sab'a mishi?,Sai kuwa Meemy tace"Wallahi Hajja Yaya Muta'z ne ya ringa rankwashi na har saida wajen yayi ja saboda wai na biyo hanyar daya bi.
Hajja kuwa tace"Ni nasan daman wannan yaron yana da mugunta don kawai kinzo gidansu saiya nemi ya dinga takura miki toko ubanshi bai isa ya hanaki zuwa gidannan ba,ballan tana shi d'an yau.
Meemy kuwa da ta b'oye a bayan Hajja ta fito tana yiwa Muta'z gwalo alamun ta samu nasara,Muta'z "yace Haba Hajja wanman yarinyar muna fukace babu abunda ta iya sai dai ta ringa had'amu fad'a dake,Sai kuwa Hannan ma "tace wallahi Hajja kinfi son Meemi damu i'ta ko fad'a bakya yimata amman mu kullum cikin yimana fad'a kike ko kunyar Mai martaba bakyayi.
Hajja "tace inyee wato ma

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login