Showing 3001 words to 6000 words out of 35410 words

Chapter 2 - AKAN AIKINA Complete BY UMMU MAHER.txt

Bros ya naji kuna tsokanar My mom d'ita,Hanan Ashe kinji i'rin tsokanar da suke yimun KO?Hanan ta rungume Fulani tana cewa K'elesu My mom zamu rama,har wata baturiya ce za'ah had'a ta da my Mom d'ita Tauraruwar Mata kyakkyawa acikin kyawawa.
Fulani tace yauwa gaya musu dai suji?Hanan ta fakaici idon Fulani suka tuntsire da dariya i'tada yayan nata.
Fulani tace waifa akan na fad'a mishi gaskiya akan hawa motar hayar da yake yi shine Mahaifinku ya goyi Bayan shi,Hanan tace gaskiya My Bros kadaina hawa motar haya don Allah.
Mu'taz yace to Fulani kiyi hak'uri na daina,Fulani tace yau d'ana haka nakeso shiyyasa kullum nake k'ara sonka saboda kanajin magana ta.
Sarki Abubakar wato Mahaifin Yarima Mu'taz yayi dariya yace mu kuma da ba'ah sonmu sai ajefar damu ko?kuma tunda abun haka ne kwanannan Baturiyar nan zata shigo tunda abun haka ne.
Fulani tayi dariya tace Hhhh Mai Marta ba kenan Ai kaga y'ay'annan nawa sun isheni duniya da lahira don haka ba Baturiya ba ka Auro Balarabiya.
Mai martaba yayi dariya tare da cewa Hhhh Fulani kenan kishi KO?to naga ne miki kwantar da hankalinki Akwai wata mace da zata kaiki ai babu ita,Ai kuwa yaran nasu suka tun tsire da dariya .
Nandai suka ci suka sha suna maijin dad'in dawowar d'an nasu daga America,Bayan sun gama ne Mu'taz ya d'auki wayar shi ya kirawo Amininshi kuma d'an uwanshi Murat.
Kiran farko Murat ya d'auka yana jin muryar Abokin nashi ya ture Mima daga kusa dashi don yadda ta mak'alk'aleshi sai kace wata mayya ta kalli Murat cikin takaici daga zuwanta gidan za'ah Fara wulak'antata.
don Mima irin mutannan nan ne masu son Kansu matuk'a shiyyasa take mafarkin ace Murat ya zama Nata i'ta kad'ai,saboda yadda Murat yayi Mata yanzu ya tabbatar Mata da cewa Wanda ya bugo yanada wani bugire tare da wani matsayi arayuwar Murat.
Murat shine kasan Na dawo KO kazo mugaisa shine kak'i zuwa KO?Murat ya Sosa kanshi yana cewa Haba Life kayi hak'uri wallahi wani Uziri ne ya b'oye ni Amman yanzu ganinan zuwa ya fad'i hakan yana Mai kashe wayar ya nufi inda Mima take wacce ta gwalalo idanuwa tare da bud'e kunnuwa taji me'ake fad'a.
Ganin Murat yayi hanyar ban d'aki abun ya k'ara k'ular da Mima yau me Murat yake nufi da'ita daga zuwan ta saiya nemi wulak'anta ta,koda ya fito daga ban d'aki kud'i ya watsawa Mima Wanda baisan KO nawa bane.
Ba tare da ya kalleta ba yace inkin gama ki rufemun gida bai jira me zata ce ba yayi tafiyarshi tana ta masifa tare da nadamar zuwa don ba haka bokanta yace Zai faru yace Mata matuk'ar ta kwanta da Murat to komai yazama Nata domin Murat zai dinga binta kamar wani doki da akala.
Hira ce ta kaure sosai don tsakanin Murat da Abokin nashi kuma Amininshi Murat kuwa wani Abu ne acikin zuciyarshi a game da Aminin Nashi yana rok'on Allah ya nuna mishi Ranar da zaiyi maganin shi ranarda zai cika burinshi akanshi Ni kuwa Nace KO wani buri ne Murat yake b'oyewa oho?.
Hanan ce ta fito sanye cikin Doguwar wato Arabian gown gaban rigar yasha ado gata farar fata fatarnan Tasha jan lalle Wanda zaka rantse da shi aka haifeta dashi, Murat ya bita da I do kamar maye.
tana zuwa tayiwa kanta mazauni akusa da yayan Nata,ta kalli Murat ba tare da sakin fuska ba kamar yadda ta taho tace Ina wuni tana wani yauk'i kamar ba tason yin magana.
Murat ya shafa kanshi yanajin son yarinyar har Cikin zuciyarshi don duk wulak'amcin da Hanan take yimai bai tab'a nuna Mata ba saboda tun tana k'arama yake sonta.
K'anwa ta KO Nayi miki laifine kike kame mun fuska Murat ya fad'i hakan lokacin da ya d'auko tufa ya saka abakinshi yana jin dad'in tufar har Ranshi,Hanan tayi saurin cewa Wallahi babu abunda yake damuna kawai dai Kaina ne yake ciwo,cikin tashin hankali yace Hanan kinsha magani kuwa,Hanan ta tashi tana tafiya tana cewa Eh nasha yanzu ba tareda ta sake magana ba ta fita daga farlon don kwata kwata yanzu batason Murat tun Ranar da ya nemata da wata buk'ata ta tsaneshi ba kuma wai tsanarshi tayi ba A'ah kawai dai abun da yayi Mata ne ya saka gaba d'aya yanzun bata son ganin shi,har a zuciyarta tanason Murat sosai Amman yariga da ya b'ata rawarshi da tsalle.
Mu'taz ya kalli k'anwar tashi Bayan ta fita sannan ya kalli Aminin nashi yaga gaba d'aya hankalinshi yana kan k'anwar shi Hanan,KO meye ya shiga tsakanin su Oho?.
Shidai A'iya saninshi yasan cewa Murat da Hanan suna matuk'ar son junansu to meye ya faru,to KO Hanan ta gano Aminin nashi yana Neman matan banza Oho?A kullum Addu'ah ya keyiwa Abokin nashi na Neman tsari daga halinda Murat ya fad'a.
Mu'taz yace Murat ka k'eleta zata sakko kasan Mata kaidai Ka cigaba da Jan hankalinta asannu komai zaizo da sauk'i sai Abu na gaba da Zan gaya maka Murat kayi k'ok'ari kadaina kula matan banzan nan kasani Allah bata bacci kuma yana kallon ka don haka ka kiyaye dokokin ubangiji sai shima ya kiyaye ka daga fad'awa azabarsa.
Murat yaji haushin maganar Abokin nashi don haka ba tare da ya nuna mai ba aka cigaba da hira Inda Murat ya nuna wa Aminin nashi ya daina duk wani hali na banza.








★★★★★
Mumtaz kiyi sauri fa mutafi makaranta kinsan fa yau Malamin nan zaizo kinsan ba shida mutunci KO kad'an Amal ta fad'i hakan tana Mai shiga d'akin don ganin Aminiyar tata bata da niyyar fitowa,Wow wata yarinya a hango wacce ba zata wuce sha biyar ba tana shafa Mai A fatarta Mai kyau da tsantsi,Mumtaz kenan yadda mak'erin budurci ya k'erata komai Nata yayi kyau masha'Allah.
Mumtaz tace daman sauri na ke tayi kafun ki fito nasan kina zuwa zaki addabe ni shiyyasa nake ta sauri,Au haka zakice KO inji Amal dake shirin fita.
Mumtaz tayi saurin janyo ta tana bata hak'uri,Amal tace to sai kiyi sauri idan ba haka ba intafi,Nandai Mumtaz ta gama shiryawar ta suka fito don zuwa makaranta inda sukayi wa Umman Mumtaz sallama suka tafi ganin sha'awa.

*Wacece Amal*
Amal dai y'ar wani mutuncr Mai kud'i d'an Asalin jihar Kano ne matar sa y'ar Niger ce Buzuwa ce Jamal su biyu ne ita da Yayan ta Mai suna Ibrahim,Mahaifinsu Alhaji Abdullahi sun dawo Bauchi da A'iki ne saboda transfer da'akayi mishi saboda haka suka dawo Bauchi da zama,Alhaji Abdullahi bata son zama cikin masu kud'i wato bata son zaman G.R.A.saboda yace baka sanin halin da talakawa suke Cikin zama cikinsu kuma zai k'ara maka I'mani tare da tausayi da jin k'ai don haka koda ya su da mak'ofta suke da su Mumtaz don haka tunda ya bud'e i'do yaga halin da suke ciki Saiya ringa taima ka musu ya bud'ewa Malam shago a Bayan gidansu yana siyarda kayan masa rufi,Mumtaz kuwa tuni sunyi saboda Mai k'arfi tsakanin ta da Amal,hakan da Alhaji ya ganine koda za'ah saka Amal Makarantar gaba da Primary wato Secondary tare yakaisu yayi musu komai tare.












*UMMU MAHER CE*




Miss green💚📗✍🏻


Share👉🏻👉🏻👉🏻
And
*Comments*
*Tyiping*🖌️
ABOUT MY WORK✍🏻


💚💚💚
(ღ˘⌣˘ღ)(ღ˘⌣˘ღ
*AKAN A'IKINA 2021*
(ღ˘⌣˘ღ)(ღ˘⌣˘ღ)
💚💚💚




*Labarin gaske✍🏻*


*Na*
*Rabi'atu.B.Abdullahi*
(Ummu Maher)Miss green💚📗


بسم الله الرحمن الرحيم
_________________
______
🅙︎𝗮𝗿𝘂𝗺𝗮𝗶 🅦︎𝗿𝗶𝘁𝗲𝗿𝘀 🅐︎𝘀𝘀𝗼𝗰𝗶𝗮𝘁𝗲𝗱📚🖊
https://www.facebook.com/101679598253281/posts/101680068253234/?app=fbl
_Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa illmantarwa, nishadantar tare da fadakarwa da jama'a bisa harshen hausa_


🏔🅙︎🅦︎🅐🏔




*WATTPAD Link*
https://www.wattpad.com/?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=invitefriends.
____________👉🏻👉🏻👉🏻


*BABI NA 7&8📝*


Wannan dalilin ne yasa Mumtaz da Amal suka taso tare komai suke yi hatta abinci tare suke cinshi,suna son Junansu sosai da sosai.
hatta bacci wani lokacin tare sukeyi,I'dan safiya tayi Mumtaz ta koma gida duk ranar da basu kwana tare ba kuwa to Da sassafe zasu had'u don har mafarkin junansu sukeyi.
Mumtaz bata da tsoro ko kad'an,Amal kuwa akwai ta da tsoro don y'an gidansu ma sun santa da tsoro kamar farar kura.
Koda fad'a Akeyi da Amal to ka tabbata sai Mumtaz ta shiga ciki anyi da'ita saboda i'ta daman tun tana k'arama bata da tsoro ko kad'an hakan ne yasa yara suke tsoron Mumtaz.
Hajiya Mahaifiyar Amal bata san Wannan alak'ar tsakanin Mumtaz da Amal,A cewar ta wai Mumtaz zata shafawa Amal gayyar talauci,Shiyyasa take ta k'ok'arin rabasu ta k'arfi da yaji.
Saidai duk wannan abun da takeyi bai saka yaran sun daina son junansu ba,Gashi kullum Ibrahim Yayan Amal ya dawo daga wajen Aiki sai ya tambayi Mumtaz I'dan kuwa bai ganta ba to sai yaje gidan.
Hakanne yake k'ara tunzura Hajiya Wato mahaifiyar Amal,don gani takeyi duk Mumtaz ta kwace mata iyalai,don Alhaji Yanzu taimakon su Mumtaz yakeyi sosai.
Hajiya fa ta dage sai ta raba,Amal da Mumtaz iyakar k'arfin ta,don wataran ma Idan Mumtaz tazo gidan korar ta takeyi ko kuma tayi ta zagin iyayenta wai matalauta matsiya ta.
Zagi dai kala kala babu wanda Mumtaz bata shanshi awajen Hajiya,abun takaicin kuwa i'dan Mahaifin Amal yana nan bata nunawa Mumtaz wani abu ballantana ma har wani ya gane meke faruwa.
ko kud'in makaranta idan Alhaji ya bawa Mumtaz fakar idon Alhaji a keyi ta karb'e,Idan Amal tayi mata magana yanzu ta zane ta wannan abun ya tsayawa Amal aranta don tsakani da Allah bata jin dad'in yadda Mahaifiyar tata takeyiwa Aminiyarta.
Don haka rannan ta shiryawa Uwar tata tsiya ta d'au aniyar sai ta gayawa Dadynta don du abunda mahaifiyar tata ta keyi bai sani ba.
Rannan suna Zaune dukkansu Afarlo har Mumtaz,sai kuwa Amal ta kar kace bakinta tace Dady zanfad'a maka wata magana,Dady ya gyara zamanshi yace to Uwata ina jinki wani abune ya faru?.
Eh Dady daman nadad'e inason in fad'a maka akan abunda Momi ta keyiwa Mumtaz ne?Ai kuwa sai Momi tace to Uwar y'an sharri kedai kamar canza mun ke akayi mai bak'in hali kawai,kuma kirufa mana bakinki anan Noncense kawai.
Alhaji yace haba Hajiya ki tsaya mana yarinyar ta fad'i gaskiyar ta Tafara magana kin tsayar da'ita meye dalilinki?to banason i'dan ina magana da yara na kina saka mana baki kina jina ko?.
Momi kuwa abunnan ya k'ona mata rai ta kasa cewa komai sai zuciyarta da take mata zafi,Ita kuwa Mumtaz batason Amal ta fad'awa Dadynta wannan maganar don zai i'ya haddasa musu rigima k'arshe a dawo da abun kanta.
Alhaji yace ina jin ki Mamana me Mamanki ta keyiwa Mumtaz yanzu in d'auki mataki akanta,sai kuwa Amal tace Dady wallahi Mama kullum idan Mumtaz tazo nangidan saita zageta wai y'ar matsiya ta y'ar talakawa,Wallahi Dady wataran ma idan ka bamu kud'in skull karb'e na Mumtaz, ta keyi wataran ma ta hanata shigowa gidannan wai ita bata gaji Arzik'e ba.
Alhaji fa ranshi idan yayi dubu to yab'aci don me Hajiya zata dunga wannan jahilcin I'ta ta manta a yadda ya Aure ta take Mahaifin ta Saran icce yakeyi Amman bai talaucinsu ba ya Aureta amman yanzu har tana da bakin zagin y'ay'an mutane.
Kwala mata kira Alhaji yayi koda tazo yaci mata mutunci sosai yace kuma duk ranar da ta sake yiwa Muntaz wani abu to Wallahi bai yafe mata ba,Hajiya kamar ta shak'e y'ar tata saboda haushi.
Nandai taringa bashi hak'uri amman ko sauraron ta baiyi ba yayi tafiyarsh,yana mai jin haushin matar tashi don ko kusa bai kawo abunda ke faruwa zai faru ba.
Ibrahim ya kalli Mahaifiyar tasu yace Gaskiya Hajiya wannan halin bai dace ba kwata kwata,don Allah yayi mutun cikin talauci ba yana nufin baya sonshi ba,A,ah sai don Allah yagwada imanin mutun amman bai kamata mutane suna k'ok'arin nunawa ubangiji izza ba.
Hajiya tace yumun shiru sallamammmu kawai sunje sun tsaface ku dukkanku bakwa ganin laifinsu,kullum yabonsu kukeyi mutanenda talauci gadonsu ne abarsu suyi abunsu mana amman wai taimakonsu sukeyi.
toni bana cikin wad'anda aka sallama,don haka ni bana cikin wadanda aka sallama.




kuti hakuri nqyi tyiping kad'an wani uzuri ne ya rik'eni.










*UMMU MAHER CE*


*Share*
And
*Comments*
*Tyiping*🖌️
_ABOUT MY WORK_✍🏻


💚💚💚
(ღ˘⌣˘ღ)(ღ˘⌣˘ღ)
*AKAN A'IKINA 2021*
(ღ˘⌣˘ღ)(ღ˘⌣˘ღ)
💚💚💚


By Rabi'atu.B.Abdullahi👉🏻
(Ummu Maher)Miss green💚📗


بسم الله الرحمن الرحيم
_________________
______
🅙︎𝗮𝗿𝘂𝗺𝗮𝗶 🅦︎𝗿𝗶𝘁𝗲𝗿𝘀 🅐︎𝘀𝘀𝗼𝗰𝗶𝗮𝘁𝗲𝗱📚🖊
https://www.facebook.com/101679598253281/posts/101680068253234/?app=fbl
_Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa illmantarwa, nishadantar tare da fadakarwa da jama'a bisa harshen hausa_


🏔🅙︎🅦︎🅐🏔





*BABI NA 9&10*📝
Ibahim yayi shiru yana sauraron Hajiya da gaba ki d'aya i'don ta ya rufe da masifa wai yanzu an asirceshi ya zama d'an hannu.
Ibrahim ya kalli Mahaifiyar tasu yace haba Hajiya Mumtaz fa yarinya ce mai hankali da tarbiyya bata damu da dukiya ba kwata kwata haka ma i'yayen ta mutanen kirki ne.
Hajiya tace yimun shiru mara kunya harni zaka kalla kace mun iyayenta mutanen kirki ne,to waye ba na kirki ba?tambayar ka na keyi kabani amsa mana?.
Amal tayi saurin cewa kiyi hak'uri Hajiya don Allah kidaina zagin Mumtaz a gaban ta babu dad'i i'rin wannan gaskiya Momi...tun kafun ta k'arasa ta wanke ta da mari tana masifa kamar wata zautatta.
Ke dan ubanki dani kike ko da ubanki?I'na cewa yanzu kika had'ani da ubanki wai na zagi Mumtaz k'anwar uwarki ko?to bari kiji wallahi tallahi ba don yau ke y'ata ce ta cikina ba yau da kinga i'skanci muraran.
Don haka this is the last worning idan kika k'ara kai k'arata wajen ubanku saina naka saki banza mara sanin ciwon kanta.
Duk abunda Momi tayi Mumtaz na kallon ta kuma tana jinta amman ba tace komai ba,saboda yadda ta d'auki Momi kamar mahaifiyar ta don haka Mumtaz ta tashi ta koma gidansu ba tare da tace komai ba.
Amal tabi k'awar tata da kallon tausayi don tasan Duk wanda aka yiwa wannan zagin to tabbas sai yaji aranshi babu dad'i,don zagine na cin mutunci duk mai hankali idan aka yi mishi wannan zagin sai yaji a zuciyarshi babu dad'i.
to haka dai rayuwa ta dinga tafiya har kawo i'yanzu da Mumtaz da Amal suke makarantar gaba da primary wanda Alhaji Mahaifin Amal shine ya d'auki ragamar karatunsu.


*Cigaban labarin*
Mu'taz ya kira Murat yafi sau goma amman bai d'aga ba, Cen aka d'auki wayar Mu'taz yayi saurin cewa haba abokina me yasa baka d'aga waya akan kari?.
Muryar wata yarinya yaji tana cewa to A'i saika k'ara kira mai wayar baya kusa,ta d'an d'aga murya kad'an tace Honey ana kiranka awaya.
Mu'taz kuwa don haushi bai jira abunda zaice ba,ya kashe wayar saboda haushin Murat ya keji sosai ba don Murat Amininshi neba da tuni ya rabu da shi yayi yadda yakeso tunda rayuwar daya zab'arwa kanshi kenan.
Ya rasa gane kan Murat

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login