Showing 12001 words to 15000 words out of 52652 words

Chapter 5 - YAR RAWA COMPLETE DOCUMENT By HAERMEEBRAERH.txt

07 Jul 2024

12068

aikin nan na zo danayi, kin san dana bar nan aiki yawa zai wa Baba, pls ki zo Nijer" ya qarasa da karyewar murya,tausayin kansu ne ya kamata, tabbas tana tsananin son ganin shi, amma dole ta cika wa Ammii burin ta na zuwa ganin 'yan uwan ta, " Kayi hakuri Yah Amee, kai ma kasan yanda nake da burin zuwa Nijeria, ka bari dana je naga yanayin wajen , na gana da 'yan uwan Ammii zan zo Nijer kaji," da kyar ta shawo kanshi ya hakura, bayan ta kammala shirin ta ta gyara Mubarak ne, Abii ya shigo, kallon shi tai ta ga kamar baya cikin hayyacin shi " Maza maza, Lamyah ku fita a gidan ku tafi ta qofar baya, dirver zai dauke ki" " Abii me ke faruwa ne, me yake dmaun ka ka rame kana cikin tashin hankali da damuwa" " Lamyah wannan lokacin bana dogon bayani bane, muje ki tafi," kamk su yai duka ya rungume ya manna masu kisses ya tura su cikin mota, daga masu hannu yai tana daga mashi har motar ta bace ma ganin shi, wani abu yaji an buga mai ta baya wanda ya sa bai qara sanin ina kanshu yake ba......
[1/9, 2:48 PM] Haermeebrah: 💅🏼 'YAR RAWA 💅🏼







BY HAERMEEBRAERH












This page is for u Sweet Shaerreefaerht, Allah ya biya maki dukkan buqatun ki na alkairi. Love u XX❤












Page 8:












Jan shi sukai su dika ukun a qasa, har cikin parlor n, duk inda suka ja shi jini ne ke zuba ya gogu a qasa, idon shi kawai yake budewa yana lumshe su, cikin zuciyar shi yana mai tsanan ta mamakin 'yan uwan nashi, ashe zasu iya aikata mai haka? Gaba daya bai kawo abun nasu ya kai har haka ba, duk a tinanin shi zasu so quntata ma yaran shi ta bangaren gaya ma Lamyah baqaqen maganganu, misali akan mahaifiyar ta, wanda shi baya son koda quda ya hau kan ta in dai da nufin cutarwa ne, ashe gwanda da ya nesanta su da shi, da har su zasu azabtar, daga sama yaji dayan.na tambayar shi cikin fushi " ina sauran kadarorin naka ka aje su" murmushin ganin qarfin halin su yake kawai, naushi mai qarfi dayan su ya sakar mashi a fuska, nan da nan bakin shi ya fara zubda jini tare da hancin shi, daga ido yai da kuma yatsan shi yai alamar kira a gare shi, da hanzari jiki na rawa ya matsa ya zaci fada mai zai kawai sai ji yai Abii ya tattaro yawun bakin shi mai jinin ya tofa a fuskar shi, cikin tsananin bacin rai ya tattare hannun shi zai daki Abii amma sauran suka riqe shi, suna fada mai ya bari su samu abinda suke so, in yaso koma me zai faru daga baya bai dame su ba, don jinin dake zuba a kan Abii ba kadan bane, kan shi kawai yake jin yana juya mashi, da kyar ya budi baki ya fara magana, " Al-Hassan, ban taba zatan ku 'yan uwana zaku min haka ba, ban san cewa kudi yafi zumunci da dan uwa ba, na mallaka maku dukiya ta ta gado duk da dimbin yawan da take da ita, amma bai ishe ku ba, shine sai kun hada da komai dana mallaka saboda tsabar mugunta? To ku sani , ba ku kuka nemar min ba, sannan ban nema domin ku ba, na nema domin iyalina, da al'ummar Rasulullah, dan haka ku min duk abinda zaku min ba samu zakui ba, dan na kula a yanda kuke ko na baku, ko ban baku ba, bazaku bar ni da raina ba" haushi ne ya qara kama Al-Hussain yace " Al-Hassan shiyasa nace maku mu kashe shi kawai, daga baya sai mu nemi dukiyar, mu hada auren 'yar shi da dan gidan Yaya, amma kace ba haka ba, ga shinan yana son bata mana komai" miqewa babban su yai, ya tako gaban Abii, " El-mustapha ka sani tun fil azal bana qaunar ka, bana qaunar komai na ka, tin mahaifan mu na da rayuwa, saboda fifikon da mahaifin mu yake nunawa akan ka, tin da kai dukiya nake son na samu damar mallakar ta, dan haka yanzu ma ba zan fasa ida nufina na kauda kai da abinda ka mallaka ba, ina Lamya" dariyar qarfin hali Abii yayi, " Yah Muhammad, ba zaka taba ganin Lamyah ba har abada, dan ko Nigeria kaje baza ka gan ta ba, Nigeria ba qaramar qasa bace, yanzu haka Lamyah da Mubarak suna hanyar Nigeria, in dukiya ta ce kuma nan ma ba abinda zaku samu banda wanda na baku a baya, wannan gidan ma danake ciki na sai da shi, hatta sauran gidaje na da kamfanoni na na sayar da su, na tattara komai na bayar ma yarinya ta ta kai ma wanda ban hada komai da shi ba, kuma ya ke kula da zuri'a ta da dukiya ta, ina maku nasiha da ku riqe zumunci tsakanin ku da Allah, ku guji son zuciya ko...." kan ya qarasa babban su ya kai mai wani wawan naushi, a tare da yin wata qara, ta bacin rai, bakin shi har kumfa yake dan jin ba abinda zasu samu, " El-mustapha ko ta halin qaqa sai dukiyar ka ta dawo hannun mu, sai na ka salwantar da rayuwar yaran da kk taqama da su, kake tinanin zaka iya katange su daga sharri na," fita sukai suka bar shi awajen bayan sun kwantar da shi a qasa, sun saka bawon ayaba, suka rufe qofar parlorn ta ciki dika biyun, sannan suka bar dayar da ba ma a bude ta sosai a bude, bayan sun kai kujera da table da cup dauke da ruwa a ciki, sannan suka tafi, tafiyar su ke da wuya El-mustapha ya fara ganin duhu gaba daya, baya jin komai kuma baya ganin komai, sannan ya kasa motsa komai na jikin shi, ba kadan ba jini ke zuba a kan shi, kalmar shahada kawai yake maimaitawa cikin ranshi, dan ko lips din shi ba si buduwa, a haka rai yai halin shi, in da daidai lokacin Lamyah ta farka daga baccin da take, Mubarak ya tsanyara kuka mai qarfi, lallashin shi ta hau yi,nan take taji idon ta na fidda kwalla, zuciyar ta ta tsinke sosai, karanta duk adduar da tazo mata take dan samun nutsuwar ta, a haka har suka isa Nigeria, duk doki da murnar ta sai taji komai na sauya mata,tana tsananin kewar Abiin ta da Ammii, bayan sun gama komai ta hada kan kayan ta ne, ta dakko littafin da Abii ya bata na address din inda zata nema, da kuma address din unguwar su Ammiin ta, tinani tai ta fara zuwa gidan su da Abii ya sai mata, in ta huta, ta kwana biyu, sai ta je.




Tana isa gidan duk da bai kai kwatan kwatan na su ba amma ta yaba sosai, ta yaba da yanda gidan yake cikin mutane, taga yanda kowa ke harkokin shi, amma wasu na ta kallon ta kan ta shiga gidan, murmushi ta musu suma suka mayar mata ta shige, mai gadin gidan ne ya taso da gudu yana mata sannu da zuwa Nigeria, cikin hausar ta da bata wani fita sosai ta amsa mai cikin sakewar fuska, dakko mata kayan ta a motar da ta kawo ta yai ya shige da su, ya miqa mata keys din gidan, ya koma cike da qaunar ta a ranshi, dan bai zaci zai gan ta da fara'a haka ba, shiga tai cike da adduoi a bakin ta, na neman samun alkairan dake cikin sabon wajen ya kare ta daga sharrin dake ciki sabon wajen, kwantar da Mubarak tai ta nufi dakunan ta leqa,murmushi tai tace " Abii" wayar ta ta zaro ta hau kiran shi taji shiru ta qi shiga, tai ta qoqarin gwadawa amma bata shiga ba, hakura tai tace wataqila ya kashe yana hutawa ne, da wannan tinanin ta fara cire doguwar rigar ta ta zauna daga ita sai gajeran wandon ta da vest ta dauki Mubarak tai daki dashi dan watsa ruwa.








Washe gari da wuri ta tashi, ta ma Mubarak wanka tayi ta saka dogoj wando da riga sannan ta dora boyfreind jarket mai matuqar kyau da ta kusa guiwar ta, ta zira takalmi ta dora mayafi akan ta, tulin gashin kanta data daure ya bayyana ta qasan qaramin mayafin nata, a haka ta tako ta kulle qofa,mai gadin na hango ta ya taso da gudu ya duqa ya gaida ta, amsawa tai cikin sakewar fuska, " Bala" wani saurayi ne ko nace matashi da ba zai wuce 27 ba ya taho da gudu ya duqa gaban Baba mai gadi " gani Baba" " ranki ya dade ga wanda zai na kai ki duk inda kk so," godiya tai tace mai tana son ya kaita wani kamar wajen cin abici da zata ci ta dan shaqata haka, amsa mata yai da to, ya karbi jakar hannun ta, ya bude mata mota, ta shiga sannan ta mai godiya, mamakin. Ta yake in tana masu godiya, wani qayataccan Hotel ya kai ta, a cikin garin kano, iya haduwa wajen ya hadu, kallon wajen take da sha'awa duk da cewa wajen ba za a kwatanta da ire-iren wuraren da ta saba gani ba, amma ya mata kyau sosai, shiga tai ta ci abinci mai rai da lfy ta tasa aka bawa driver ma dan qin shiga yai ta matsa suka shiga tare, yaci yai qat, yana fadi a ranshi " da haka masu kudi ke kula da masu aikin su ba za a samu masu masu mugunta ba daga masu aikin sun" bayan sun gama ne tai umarnin a hada mata take away, suna gamawa ta miqe ta fara tattakawa, tana ganin yanayin wajen, a yawon da take ne ta hanqo wani waje da mutane suka taru mata na ta rawa, ana kallo, ana tafa masu, abun ba qaramin burge ta yai ba, tana murmushi, taji wani ya mata magana a gefe...


.
[1/9, 2:48 PM] Haermeebrah: 💅🏼 'YAR RAWA 💅🏼








BY HAERMEEBRAERH










This page is for u dear as promised Hafsat Bello ( Maman Afaf) ki huta ❤










Page 9:










Juyawa tai, wani saurayi ta gani, tare da shi akwai wata budurwa, siririya sosai fara mai kyau, ga hushirya, sai dai ko kadan ba ta kama qafar Lamyah a kyau ba, dan kuwa ban bancin dake tsakanin su kamar na Cute one( Hussy)😝 ne da Queen( Hassy)❤murmushi sukai wa juna, daidai nan driver n ta ya iso dauke da take away din su, yana kallon ta gefen saurayin nan sai ya fadada murmushin shi, yace " Aaa manyan gari ana ganin ku dama? Ko dake dama wane mu direbobi da irin ku matan manya? " dariya budurwar tai tai fari da ido, tace " Bala Driver kenan, ai kai na ce maka ina son ka, kai ne dai kk ja baya, ni dai rawa ce ba fasawa zan ba, koma me mutane zasu ce sai dai su fada, amma ni da ka ganni nan ba na yawon banza, rawa a jikina take, dana ji kida zan taka kuwa, so ni ban damu da surutun 'yan unguwa ba" ta fada tare da daga kafada, mamakin irin wannan surutu na wannan budurwa take, daga magana biyu zuwa uku tai goma ita, budurqar ce ta miqawa Lamyah hannu, tace " ni suna na Farha, kuma ina zaune a unguwar su Bala amma unguwar da yake aiki nake nifi" murmushi lamya tai bayan ta miqa mata hannun ta daya da wanda bai dauke da mubarak tace " ni suna na Aishaa amma ana kirana da Lamyah" daga hausar ta ta gane ko wace ce Lamyah, cikin zumudi ta ke magana, " Laaaahhh ke ce wadda aka ce zaki dawo unguwar mu daga dubai? Woww, i mean woww sai gani ga ki, u have no idea yanda na matsu na ga wace ce ke,
dan labarin ya karade ko ina a unguwar mu, mahaifin ki ya kyautata ma 'yan unguwar mu ba kadan ba, ya mana alkairi mai yawa, duk da bamu taba ganin shi ba, ta hannun mai unguwar mu ya isar da dikkan saqon da ya ke son isarwa ga wadan da ke buqatar taimako," Lamyah ce cikin dariya sosai tace " do u really talk like this all the time?, " itama dariya tai ta kada ido tace " yeh haka nake, dan ma kin samu yau bana jin surutu, raina bace yake ban samu shiga rawa ba" ta qarasa cikin jimantawa kanta, kiran sallar azahar ne ya katse su, inda sukai sallama, farha tace ma Bala sai sun hadu a gida, in ba damuwa zata kawi wa Lamyah ziyara, Lamyah ta tabbatar mata ba damuwa, zata so hakan.








Da yamma kuwa sai ga Farha ta iso cikin shigar ta kamar kullum doguwar riga da mayafin ta, wanda cikin kayan qananan kaya ne, sallama tai Baba Mai Gadi ya bude mata, duqawa tai har qasa ta gaida shi, tace mai ina Bala, yace yaje makaranta, dake yana BUK ne , yana a 200 level ne, sallama tai wa baban.ta shiga ciki, knocking tai a qofar inda Lamyah ta bude mata, tayi zufa.sakamakon rawar da ta tiqa, dan da suka dawo tai wanka tai sallah, ta zauna bayan ta sallami Mubarak ta bashi abinci ta hada shi da abin wasannin shi, stumin rawar ta ya motsa, daga nan tai ta rawa, data gaji ta ci abinci tai brush, sannan ta dawo ta dora daga inda ta tsaya, tana kan rawar ne Farha ta katse ta, dan gajeren tsaki tai, tana budewa da ta ga ita ce, cikin sakewa ta bude mata ta mata izinin shiga, dan sai take jin ita kam tayi qawa, dan runguma ta mata irin ta larabawa, ita ko Farha bata saba ba sai taji daban, wajen zama ta nuna mata ta wuce kitchen, kan ta dawo sai ganin Farha tai tana ta tiqar rawa, abun ya burge ta, aje ruwan tau sukai ta rawar sai da suka gaji suka zube kan kujera suna dariya tare da maida nunfashi, " gaskiya yau naji dadi sosai, ashe kema haka kk iya rawa?" " Hmmmm ai in kk ce rawa daya kenan, duk qawaye na na fisu iyawa, dan kuwa ko a makaranta in ana yi na fi kowa, dana fara kowa komawa gefe yake ya hau kallona, amma kuma ke taki salon rawar daban yake, BELLY DANCE kk yi," " eh haka ne, don mu ta can ita ake yi, rawar Larabawa kenan ai, shiyasa na keyin ta nima, in ina yi Abii yana cewa i am the best dancer ever" tinawa da Abii n ta ya sa kwalla ta kawo mata, tashi tai ta dakko wayar ta ta sake gwada layin shi, amma yanzu ma a kashe, kuka ne ya kwace mata, hankalin Farha ba qaramin tashi yai ba, nan take ta matsa kusa da ita, tana son dora hannun ta a bayan ta ta lallashe ta, tana tantama,janye hannun tai, daga baya kuma ta qara dorawa cikin inda inda, ta fara magana " me.... ya faru... kk kuka?" " Farha Abii na tin da nazo bai kira mu ba yaji, ya muke, sannan ina son naji ko yana lfy, gabana na mugun faduwa inna tina shi, hankali na na tashi kwarai" bubbuga bayan ta Farha tai itama ta share hawayen ta da suka fara ambaliya, tace" kiyi hakuri Lamyah kinga gwanda ke, kina da uban da zaki kalla ko mai daren dadewa ki tabbatar da cewa naki.ne, ni kuwa da dama tin kan a haifen nawa ya rasu, tawa uwar ta baro dangin miji da suka takura mata, ta zo nan ta rayu dani, har Allah yai cikawar ta, yanzu shekara biyu kenan, wannan rawar da kk gani dazu, ita ke riqe ni, banda kowa, ba wani nawa dan ban san dangina ba," kuka ne yaci qarfin ta, wanda ya bawa Lamyah tausayi matuqa, lallashin ta tai, ta labarta mata itama labarin rayuwar ta, gaba daya, da iya wanda ta sani da wanda taji labari, Farha ta matuqar tausaya ma Lamyah, " Lallau bahaushe yai gaskiya, in kaga jarabawar wani, naka sau ya zama nafila, sai dai ke da gatan ku ,ni kuma banda kowa," " Farha kin yi kowa, dan zan so ki dawo nan da zama mu zama kamar sisters, kinga Mubarak yanada yayu uku kenan, duk sanda mukai waya da Yah Amee na zan bashi labarin ki, dan shima tin da nazo bai kira ni ba , bari dai na duba me ke damun wayata ne, dan gaba daya kamar an canjan komai haka take, ita din ce dai amma is like komai ya sauya, No Abii kawai nake iya gani," dubawa tai sosai sai taga wani sabon layi ne na Nigeria aka saka mata, kuma ba Number din kowa, sai na Abii, itama sai yanzu ta kula sam no kamar ba daidai bace, wani irin tashin hankali ta shiga, meke faruwa ne, ta sunkui da kanta qasa tana nazari, ga zufa dake karyo mata, wani tinani ne ya shige ta, ta miqe kamar an mintsine ta, fadi take" Noooo Noooo pls this is not happining again pls" sai ta rushe da wani marayan kuka, ta durqusa ganin kukan ta ne yasa Mubarak rarrafawa ya rungume ta, yana kuka, lallashin shi Farha tai dan ita Lamyah gaba daya bata hayyacin ta, kuka kawai take" Farha sun kashen Abii na, tabbas shima yasan zasu kashe shi, na rasa shi kamar Ammii na, yasan zasu rava mu da shi, shiyasa ya turo mu nan, Abii meyasa kai haka, baka bari mun kaisu qara kotu ta bi mana haqqin mu ba? Abii me yasa ka basu dama, akan dukiyar ka? Daka sani ka basu, komai ko zamui yawo tsirara, zamu haqura da juna, Abii.." nunfashin ta ne ya fara sarqewa, ruwa Farha tai saurin bata, da kyar ta shq kuka kawai take ba qaqqautawa,

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login