Showing 12001 words to 15000 words out of 54884 words
Chapter 5 - ZUMA A BAKI! Complet by Autar manya.txt
jikinta ba andafata da kayan miya.
Saka hannu nai na soma ci bakina ɗauke da bisimillah.
Ko kaɗan babu daɗi sema bauri amman yadda nikejin tsoron anty uwani wadda ta kasance kamar yayar anty ce domin da babanta da baban su babanmu da babansu anty uwa ɗaya uba ɗaya suke, itama tana nan cikin garin tofa tana aure da ƴaƴanta duka acan waɗanda taima aure.
Yasani cin kazar ina korawa da tsumin kwakwa da dabinon data mikon na wannan jarkar.
Seda na kammala sannan na mika mata kwanon ina yamutsa bakina sabida baurin daya gamen bakin nawa.
Anty uwani ta fita haka nan su anty zulfa sun fita sun barni a ɗakin ina faman tunanin abinda ke faruwa babu mai bani amsa a wannan lokacin hakan yasa na koma saman gado nai lamo ina tunanin rayuwa.
Ƙarfe goma da rabin safiya dubban mutane suka shaida ɗaurin auren UMAR MUHAMMAD SARKIN GIDA da amaryar shi AISHA YUSUF NUHU, akan kimin sadaki naira dubu hamsin wanda abokin ango yayan amarya imran shiya bada wannan kuɗi.
Bayan an kammala ɗaurin aure can na hango ango cika daji sanye cikin rigar shadda fara ƙall mai golden ɗin aiki wadda imran yay shige da ficen ganin ya ɗinko musu a safiyar yau shida humaira da kuma imran ɗin.
Bakaramin kyau umar yay ba haka ya dinga mikawa mutane hannu suna gaisawa bakin shi ɗauke da matsanan cin murmushi.
Daga wajan ɗaurin aure gidan su suka wuce inda zuwa wannan lokacin dangin shi na can katstsina sun zo tare da ƴan uwan innah.
Sosai suma suke gudanar da aikace aikacen girkin ƴan bikin.
Ɗakin inna ya wuce ya sami kakarshi iyatu zaune aifa tana ganinshi ta fashe da kuka ta rungume shi sabida ta tuna marigayi mahaifin shi seda ƙyar ya bata baki duk da shima ɗin yana cikin kewar mahaifin nashi domun wannan karamci na iyayen humairah kaɗai ya nuna masa yadda mahaifin nashi ya kasance mutum nagari domin ya shuka kairan ne shiyasa yanxu shi yake girba.
Sosai suka gaisa da ƴan uwanshi yana kokarin fita yaji muryarta a bayan shi.
"Hammah umar ina tayaka murna".
Kozasuyi shekaru dubu basu haɗu ba baze manta da itaba nuratu ce ɗiyar kwanwar mahaifin shi wadda ta rasu.
Da murmushi ya juyo ya dubeta nuratun daya sani ada a yanzu ta sauya wannan ƴar gayuce ƴar boko wayayya.
Sosai yay mamakin yadda ta goge.
Muryarta tace ta katse mai tunani.
"Hammah baka da zumunci tunda ka dawo kano nima na ɗaga hankalina hakan yasa babana ya daukeni daga gabansu tsoho ya kaini wajan matarsa inda anan nai karatu har nai candy yanzu ina jiran result ne na faɗa jami'a kasan yanzu Dady ne ɗan majalissarmu fa".
Zaro idanu yay tabbas baban nuratu ada daya sanshi kansila ne amman yanzu harya kai wannan mataki lallai Alhaji uba bakori yanzu ya taka ƙasa dole nuratu ta goge.
"Masha Allah sekuma a fitar da miji ba".
Yafaɗa yana kokarin fita.
Saka hannu tai ta kunshe fuskarta.
"Hammah ka bani phone no: ɗinka zanna kira muna gaisawa Dady ma yace na karɓa masa".
Tafaɗa tana miko mai wayarta wadda ta kasance iphone 11pro zaro idanun shi yay yana bin wayar da kallo kafin ya amsa ya saka mata numbern kana ya fita.
Da gudu ta biyoshi tsakar gidan kuma tana mai cewa.
"Hammah ga Dady ya ɗaga wayar"
Ta miko mai amsa yay yana karawa a kunnen shi.
Cikin kulawa Alhaji uba ke taya umar murnar auren shi sabida yadda yasan umar sosai domin indai zezo ganin nuratu ada tofa tare da umar ze ganta haka nan kominsu tare suke shiyasa ko siyayya zema ƴar tashi baya ware umar domin batada magana seta hammah umar ada ɗin haka ma ayanzu kusan kullum setace mai hammah umar kaza da kaza, tsananin son nuratu da dadyn keyi yasa yake son umar domin nuratu ita ɗaya ce mace da Allah ya basa ragowar ƴaƴan matarsa mazane su biyu kuma yarane.
Seda suka kammala wayar sannan umar ya amshi numbern dadyn kamar yadda dadyn ya umarta numbern accnt ɗinsa ya tura mai wanda atake anan yay mai transper dubu ɗari biyar yace yay hakuri lokaci ya kure ga tasa gudun mawar a sai kayan tea ba yawa.
Komawa cikin ɗaki tayi shiko wayarsa ya saka ya kira dady yaymai godiya sannan ya fita wajan abokanshi kiran imran yay gefe tare da amsar accnt number shi yay masa transper na kudin fantin ɗakin shi wanda anan humaira xata soma zama kafin aga abinda Allah zeyi.
Sannan ya wuce pos ya ciro dubu ɗari biyu.
Kai tsaye gida ya kuma dawowa kiran maryam kanwar shi yay wadda take kokarin shiryawa sannan yace ta kira mai anty maimuna kanwar inna wadda suka xo a ɗazun daga katstsina, Bayan tazo ne ya damka mata kudin yace mata suje kasuwa tare da maryam su ɗan haɗo kayan lefe koya dai suke.
Hakan ce ta kasance suka amsa maryma ta shirya suka wuce kasuwa wanda suka haɗo kayan lefen masu ɗan dama tare da akwati guda biyu karami da babba sukayo gida.
Shiko fita ya kumayi ya damkawa wani abokinshi mai suna salim kuɗin kayan abinci, sannan ya koma wajan tarin abokanshi sukai sallar azahar kana sukaci abinci daga nan suka wuce gidansu amarya.
Amman shi imran bai bisu ba ya wuce ne wajan masu faitin ɗaki domin a gyara muhallin amarya.
Lokacin da suka karasa gidan su humaira motar kayan gadon da baba yay rawar ganin saimata ta karaso seda suka tsagaita aka gama fitar da kayan sannan suka shiga cikin gidan gaishe gaishe sukai da dangin kafin abokanshi su bukaci ganin amarya.
Ina can ina bacci anty uwani tazo ta tashan kamar daga sama naji maganarta akaina domin ko kaɗan ban san budirin da ake ba.
"Humaira tashi ga angonki yazo ku gaisa da abokanshi"
Bata bani damar magana ba ta gyaran fuskata muka fita waje gaba ɗaya jikina rawa yake zuciyata rawa take dajin furuncin ta ni akaima aure!!!
*ZUMA A BAKI*
300 Naira masu amfani da banki zasu tura ta 0078174806 starling bank.
Shaidar biya ta 08142105218.
Marasa banki kuma katin MTN na naira 400 ta numbern dake sama.
AUREN BARE COMPLT #500 anemi numbern dake sama gamai so.
*GABA ƊAYA SADAUKAR WANE GA*
*HAJIYA ZULAIHAT* ( *MRS DR BASHIR*)
*Kainuwa dashan Allah, Rabbi ya ƙara lafiya da wadata mama*🌹
*11&12*
Haka na bita jikina babu ƙwari har zuwa tsakar gidanmu wanda ya cika da maƙota tare da ƴan uwanmu.
Gabana bai kuma faɗuwa ba seda naga ta miƙani cikin hannun Ya Umar wanda yake tsakiyar abokanshi fuskar nan tashi ta ƙara haskawa tai wani irin cika da annurin angon ci.
Hannu na ya damƙe da ƙarfi yana matsamin shi batare dayaji kunyar anty uwani ba yaɗan janyoni jikinshi abokin shi yaja mana hoto.
Haka yayta rungumeni ana mana hotuna wanda rabin hoton kukane harda majina a fuskana.
A fakaice yake saka hannunshi yana sharemin har aka gama kana muka shiga ɗaki akai mana tare da ayiya da anty da su umma.
Fafur yaƙi yarda ai mana da abokanshi haka suka kammala gaisuwar su suka wuce waje zuwa anjima kuma azo ɗaukar amarya.
Ɗakinmu na nufa aguje! hayewa nayi saman gado ina rafka kuka.
Cikin tsananin tashin hankali sakina ta shigo ɗakinmu jikinta da kayan makaranta.
Zubewa tai saman katifar danike kwance tana hucin bala'i!
Ɗakamin duka tai a saman bayana da sauri na miƙe ina sosa wurin ina kallonta.
"Wato humaira munafunta ta kike ko? daman kinsan yaudarar ɗan uwana zakiyi yasa kika lasa mai ZUMA A BAKI! na soyayyarki daman auren ƙato zakiyi?"
Tafaɗa tana zubar da ƙwallah!
Cikin ruɗu na miƙe sosai ina kallonta nima a wannan karon na kasa daurewa kukan na saka kamar ita.
Kana cikin tattausan lafazi na dubeta.
"Haba sakina tayaya zakice bani son Nazir bayan kinsan sonsa ajininah yake?".
Nisawa nayi na daƙiƙu kafin nace.
"Wallahi! shigar sauri sukamin,sakina bansan da auren nan ba domin raina zuciyata a halin da ake ciki yanzu sunfi naki tafasa domin bana son wancan matsiyacin ko kaɗan".
Nafaɗa ina hucin takaici.
"Tayaya zan musawa mahaifana dole na amshe sa a hakan duk da banji sonshi ko guda a raina".
Zabura tai tare da mikewa tana huci!
"Haka ma zakice kenan xakije ne ki bashi jikin ki kome?"
Sekuma ta zube akan gwiwo yinta ta kama nawa hannun.
"Dan Allah humairah kada ki bashi kanki ki adanawa yayana kanki kinga mu yarane bamufi shekaru 16 ba tabbas kika yarda dashi ze sakaki yoyon fitsari".
Da ɗimuwa na dubeta ina zare idanuna.
"Daman ko baki ceba ni ina zan iya da wannan ƙaton tabbas ya shigeni mutuwa xanyi tabbas zanyi iya karfina domin ganin na kare kaina".
Murmushi ta sauke tare da jinjina kanta.
"Meze hana ki ɗauki makami ayayin dayazo kusantarki ki masa barazana?"
Da sauri na dafata.
"A,a sakinah babu ruwana domin bana son duk ƙina dashi nai ajalinshi baki gudun rai yazo ya tarar da ajali nazo na shiga uku? tabbas bazanyi haka ba inawa mata ma masu yin hakan addu'a akan su dena domin ba ɗabi'a arziki bace ba sabida gudun tsautsayi suzo rai yay halin shi agarin son zuciya nidai ba ruwana sauya wata shawarar".
Wani shegen murmushi ta saki.
"Kai daɗina dake akwai kwanya kawata to ki dinga karta mai tujara da cin zarafi aduk sanda zezo miki har Allah yasa yaji yagaji dake ya sakeki yayana ya aure ki".
Murmushin nima na sauke.
"Aikam gwara haka, akan nai masa bazarana domin wannan matsala ce gagaruma".
Sakina ranta tai jin bazanci amanar yayanta ba.
Sosai mukacigaba da hira wadda rabinta akan, yadda xan kuntata wa rayuwar aurena da ya umar take.
Se lokacin ma na tuno da wayar da nazir yabani wadda na cusata cikin kayana.
Da sauri na ɗaukota sakina ta saitamin ita kiranshi mukai.
Seda sukai maganganun su da sakina sannan ta mikomin wayar.
Kukanshi na gulma ya soma reran yana cewa duk sanda yaji labarin na bawa Umar jikina tabbas ze kashe kansa ya huta.
Da irin waɗannan mugayen kalaman ya ribacen wanda harna manta da igiyar auren dake kaina(wa'iyazu billahi)har nai masa alkwarin tafiya da wayata gidan mijina akan muna magana dashi.
Sosai ya kasheni da kalaman soyayyar shi harya Lasa min ZUMA A BAKI wadda ta kaini ga na sallama mai zuciyata na kuma ji duk duniya babu wanda ya isa ya rabani dashi.
Naji kuma duk duniya bani da maƙiyi kamar Umar.
Seda na saka nafisa ta kawowa sakina abinci taci sannan mukai sallama ta tafi akan setazo gidana.
Waje mai mahimmanci naiwa wayar a cikin kayana.
Ina nan zaune anty zulfa tazo tana cemin sunyi jere sedai ban sami falo ba dan haka gado kawai aka saka da suf a ɗakin kujerun kwa suna waje za,a mayar dasu wajan kafintan domin babu wuri.
Kauda kaina nai ina ayyana matsiyaci daman ai fitina ce zata sakashi yay auren amman meyake dashi mai kuma ya tanada daze iya rikeni yana ta karatun shi ga hidimar gidansu.
Katsemin tunanina tai.
"Humairah ki rike Umar da kyau domin zakiji daɗin shi sabida yarone shi mai zuciya zokije kiga lefen daya haɗo miki wallahi duk duniya zama da mai sonka yafi komi daɗi ina kyautata zaton nan gaba Allah zewa Umar ɗaukaka sabida darajar kyautatawa mahaifa".
Duk abinda take faɗi bayamin daɗi sema ƙaramin wutar ƙiyayyarshi datakeyi haka nan ban motsaba harta gama ta fita.
Sema kifa kaina danai a saman kafita ina kuka wanda ya haifar min da ciwon kai mai zafi.
Ina jin ana kiɗan ƙwarya a ƙofar gida amman ban leka ba ana magariba nai sallah na koma na kwanta.
Baba ne ya aiko kirana saka mayafi nai na fita zuwa ɗakinshi.
Anan na tarar dashi dasu anty zaunar dani akai agabansu nasiha baba yakemin akan zaman aure da sauransu kafin anty itama ta ɗora da tata baffama haka haka nan umma sannan su anty uwani suka ɗagani wanka suka kuma sakani nai sannan aka bani rigar leshi ja na saka sosai suka shiryani nai kyau kai gaskiya ƴan uwanmu akwai zumunci.
Mota guda ɗaya aka kawo sabida kusane dan haka dagani se umma da anty uwani aka zuba cikinta.
Har aka shigar dani gidan inna kuka nike kamar babu gobe.
Ɗakin inna aka kaini inda danginshi suka karban hannu biyu inna da kanta takaini ɗakina.
Zaunar dani tai a bakin katafaren gadona, ɗakin yana bada kamshin turare na musamman.
"Toni dai bana suruka dake domin ke ƴatace Allah ya bada zaman lafiya".
Tafaɗa da murnar ta domin yau jinta take a farin ciki yaro yay aure.
Sosai ƴan uwanshi suka cika ɗakin suna faman tayani murna har su umma suka tafi ban saniba.
Basu bar ɗakin ba se wajan goman dare seda su maryam suka share ɗakin suka kuma kunna turare sannan sukaimin sallama suka tafi ɗakin ya rage dagani se halina
Haka nan gidan yayi tsit alamun mutan gidan sun kwanta domin garin yanayin sanyine wanda daman tun a ɗakina naji suna cewa zasu jesu kwanta da wuri sabida gobe zasu wuce katsinah.
Haka na cure a wuri ɗaya duk tsoro ya kamani.........
*TOFA ANZO WAJAN* 😜
*ZUMA A BAKI*
Naira 300ne ga masu amfani da banki ta nan 0078174806 starling bank, shedar biya ta nan 08142105218, marasa banki kuma MTN card na 400 naira a turo ta numbern dake sama.
*AUREN BARE*
Cmplt #500
Mai so yanemi numbern dake sama.
*GABA ƊAYA SADAUKAR WANE GA*
*HAJIYA ZULAIHAT* ( *MRS DR BASHIR*)
*Kainuwa dashan Allah, Rabbi ya ƙara lafiya da wadata mama*🌹
*13&14*
Najima a zaune har aka ɗauke wutar nepa kafin naji dirin takun shigowar mutane domin yadda aketa turo ƙofar waje,Ƙara takure jikina nayi wuri ɗaya ina jan mayafin jikina, sallamar suce ta kuma jefani a halin tsoro ta cikin mayafina nake leƙensu su huɗu ne suka shigo ɗakin amman babu ya imran cikin su nadai shaida ɗayan salim ne abokinsu se ragowar mutum biyun da ban ganesu ba sabida duhu shima salim danya kunna tourch light ɗin wayar shine yasa na gane shi.
Su uku ne abokan nashi shine cikon na huɗun.
Zama sukai a saman carpet ɗin tsakar ɗakin domin ba kujeru shikuma ya zauna a gefen gadon danike, salim ne ya soma gabatar da addu'a kafin ɗayan naji ya soma mana nasiha sosai akan zaman takewar aure.
Shikuma ɗayan danaji salim yace masa Mj bazaka ce komi ba? shinaji yace
"Nidai abinda zance wa ango shine yabi mana kanwa a hankali kada ya zage azo ana kirana na bada first aid"
Dariya suka saki nan ma sukaita shaƙiyan cinsu irin na abokai yadda baice komi ba nima haka bance komi ba har suka gama suka dire ledojin hannun su tare da damin kuɗi.
"Amarya ga kayan tea nan da kaza da kuɗin sayan bakinmu kinsan abinka da talakawa babu yawa Saduwar alkairi Allah ya bada zuri'a ɗayyiba".
Ban tanka suba.
Haka ya miƙe ya rakasu mintuna Biyar ya dawo ɗakin wanda a dai dai lokacin aka kuma dawo da nepa ɗakin ya haska da farin ƙwan lantarki.
Cire mayafina nai naɗan fito da fuskata ina kallon yanayin ɗakin kafin na mayar da idanun nawa kanshi.
Yanxu ba farar shadda bace ba jikinshi wani light blue ɗin yadi ya saka mai shara-shara domin ana iya hango white singlet ɗin dake jikin shi se hular daya ɗora wadda tai marching da kayan jikin shi.
Zaune yake a bakin gado yana tube takalmin ƙafafun shi ya kammala yana cire sabar anan nai katari da farar ƙafarshi wadda tai kamar ta jarirai sabida goguwa da kyau da ɗaukar hankali.
Murmushi ne a saman kyakykyawar farar fatar fuskar shi kamar koda yaushe sedai wannan karon murmushin nasa ya bayyana fararen haƙoran shi tas-tas waɗanda suke ajere masha Allah farare kamar ƙanƙara.
Ya kammala ya tube rigarshi yabar singlet takowa yay zuwa gabana wanda naji kamar na saka hannu na makeshi.
"Zanje nayi wanka sabida nagaji zafi nakeji kiduba cikin ledojin nan ki fitar da kayan ciki sabida karsu lalace"
Yadda yake maganar ban tanka shiba kamar yana magana da dutse harya gama ya fita kafin na miƙe da sauri na nufi bakin ƙofa na soma aiwatar da ƙudirin dake zuciyata.
Rufo ƙofar nayi da sakata na koma nai kwanciyata a saman gado batare dana tube kayana ba.
Yana fita bakin rijiya yaje ya kindimi ruwan cikinta ya nufi ban ɗakinsu dake gefen ɗakin shi dayake daman can bayin shi daban dana su inna sannan daga ɗan gaban bayin akwai wani ɗan ƙaramin ɗaki wanda anan akai mata jeren kayan kicin ɗinta inda ya zamana kenan ɗaki ɗaya da kicin da banɗaki ya rabata da mahaifiyar shi akomi inba a tsakar gida ba.
Duk sanyin da ake tsulawa baiji ba haka ya kammala wankan nashi ya fito dagashi se gajeren wando dayake darene duk sunyi bacci yasa ya fito a hakan.
Sosai yakejin mugun sanyi na kaɗashi a wannan karon ya nufi gaban kofar ɗakin sedai turawar farko yajita a rufe jikinshi ne yay sanyi ga uban sanyi dayake ji gakuma baison ya buga ƙofar su inna su farka sabida kofar ƙarfe ce gakuma dare sound ya ɗauke.
Dubara ce ta faɗo masa ya ɗan leƙa ta window inda Allah yaso bata kashe ƙwan ɗakin ba.
Yana hangota saman gado tana sharar baccinta hankali kwance.
Domin bata saki labule ba.
Awannan karon ya shaida kiyayyar da humaira take mai duk uban wahalar dayasha yau bataji tausayin saba sema rufo masa kofa datai a daren farkon su bayan tafi kowa sanin uban sanyin da ake a garin wanda yake saka mutum tsuma da kaɗawar jiki.
Cikin ɗan ɗaga murya kaɗan yace mata.
"Ki tashi ki buɗemin kofa na saka kayana inma kwanciyar ce bakya so dani xan fita naje shagon salim na kwana"
Sarai ina jinshi amman ban motsaba sema tura kunnena saman pillow danai domin bani son jin muryarshi ko kaɗan.
"Aisha please ki taimaki marayan Allah wallahi sanyin nan zemin illah"
Tashi nai tsam na tako gaban labule zan sauke domin bani son wannan magiyar da gayya na ɗaga muryata.
"Ya Umar ka mutu mana karewar illah kowa ma ya huta da jarabar nacinka ko angaya maka ka mutu inada asara ne akwai dubun ka dake jiran wannan ranar agareka domin su kasance dani".
Wani irin tsuma jikin shi keyi domin bata taɓa bata mai rai kamar yau ba tabbas yau ze nunawa humairah iyakarta ze shayar da ita ruwan mamaki wani zazzafan kishi yaji wanda ya haifar mai da sarawar kai da jan idanun shi ya dubeta.
"Nace ki buɗen kofa kona ɓalla na shigo ko wallahi!"
yafaɗa yana firfito mata da manyan idanun shi waje.
Tsorone ya kamani daman mai hakuri bai iya fushi