Showing 27001 words to 30000 words out of 40261 words

Chapter 10 - A JININSA YAKE PDF BOOK COMPLETE Writing by Zulaihat Sani Kagara .txt

Alhj Basheer ya amsa.
(Laptop) ce a gaban sa, yana ta 'yan dube-
duben ajiyar sa. Koda shigar ta, kwarai ta ga
dakin ya sauya mata.
Ga wasu bakin makamakan hotuna guda 4 da
suka kara kayata kafcecen dakin, daya kai
girman wani falo.
Uku daga cikin hotunan Alhj Basheer ne tare da
Naseer rike da wasu kofuna tare da wasu
kyaututtuka.
Dayan kuwa Naseer din ne shi kadai, ya da wani
katon kofi sama, dariyar da yayi ta kara
kwarjinin fuskar sa. Kai tsaye gaban hotunan ta
tsaya ta zuba ido.
Domin ko alama bata tantama wannan shine
Naseeerrrrrr!!!!......."
Ba wai son sa bane take ya kamata, a'a
kwarjinin sa ne ya debi hankalin ta har ta ji
faduwar gaba, kuma ko alama bata ji tana kin
sa ba.
Tana kokarin kaucewa hotunan, ta ji hannun
Abbanta ya rungumo kafadar ta, ya lika ta
kuibinsa.
Ta dan sauke numfashi kadan, ta ce,"Hotunan
ko sun yi kyau."
Yayi dan murmushi ya ce,"Allah ko?
To ki canka waye a tare da ni? Cikin
zolaya t amsa,
" Bebin ka of course."
Ya ja hancin ta ya ce,
"Stop joking."
Ba ni ce a tare da kai ba Abba?"
A hoto na ce,
kin sani sarai,
come on,
gaya min."
Tayi 'yar dariya,
"Uhmm...........jarumun dan wasan polon nan da
aka kawo ma ka shi, lkcn da ba nan.
Ya ma sunan sa?"
Ta tambaya, tana duban sa.
Haka shi ma yake kallon ta kafin ya ce,
"Sunan sa ya 6ace miki kenan?
Maganar Abba bata da muhimmanci ko?"
Ta kada kai,
Wasa na ke,
ai da shigowa ta na gane Naseer ne."
"To yaya ki na son sa?????"""""
Da sauri ta bar wajen, ta koma bisa wasu
kujerun farin karfe na alfarma ta zauna.
Kunya ce mai karfi ta kamata.
Shi ma ya tako a natse ya zauna gefen ta."
Wannan shine zabin da na yi miki, ina son ki
gaya min yayi, ko bai yi ba?" Kan ta a kasa, ta
amsa, "Yayi Abba."
Ki na son sa?"
Tayi shiru jim.
Sannan ta kalle shi,"Ummi ta ce kana kira na."
Wannan shine kiran, ki ga mijin da na za6a miki,
sannan in tabbarar da ki na son sa.
Ki gaya min."
Abba na ce yayi."
Ba yayi ba,
ki na son sa?"
Alhj fa ya tasa ta gaba, ita kuma duk kunya ta
rufe ta, da kyar ta cije ta daure ta amsa,
"Eh!"
Ta mike a guje, ta bar dakin.
Alhj Basheer ya bi ta da kallo yana dariya,
sannan ya numfasa yayi hamdala ga Allah.
Kai tsaye Nusaiba dakin ta shige, ta fad'a bisa
gado, ta nutse cikin katifa.Ta jima a kife, kafin
ta birkito ta tsirawa fitlun da ke cunkushe suna
lilo a saman tsakiyar dakin ido.
A zahiri su take kallo, amma ko alama ba kyan
tsarin bane cikin ran ta.Zuciyar ta yamutse take
da tambayoyi masa yawan gaske a game da
za6in da Abban ta yayi mata."
Shin waye Naseer?
Wane irin sani Abban ta yayi masa?
Duka zahiri da badini?
Ya za kai kar6e ta, idan ya ganta?
Watakila shi ma hoton na ta ya gani, kamar
yadda ita ma ta gan shi...................
Ta sauke numfashi, ta fada a ranta,"Allah ka sa
aure na da Naseer alkhairi ne."
Ta yunkura ta tashi zaune,
"Yar jakar hannun ta da ta yasar bisa gadon tun
shigowan ta, ita ta jawo gaban ta, ta bude zif
din ta dauko wayar ta.
Ta mike ta koma jikin wata dirowa, wacce jerin
akwatuna ke bisa kanta." Ta jawo ta tsakiya, ta
binciko (Sim card) na ta, na gida Najeriya ta
dawo bakin gado ta zauna. Sannan tayi aikin
maida shi cikin waya. Jimawa kadan ta nemo
wata lamba mai dauke da sunan KAUTHAR. Ta
kira babu wani bata lokaci aka sada ta da
kauthar. Can ta tsinkayi ihunta, "ba dai kin iso
ba! Cike da faraa tace, "tun yaushe? Ai muna
shigowa kaduna, ana sallar magrib. Zaki zo
goben?" "Me zai hana? Allah ya kaimu goben
lafiya." "To shike nan ki gaida momi." "Zataji".
Sukayi sallama. Tana cire wayar daga kunnanta,
kiran wata bakuwar lamba ta shigo. Tayi zuru
tana kallon wayar a yayin da tuni zuciyar ta ta
aiyana mata mai kiran wayar. Nan da nan
gaban ta yayi mugun faduwa. Hannun ta ya hau
rawa,bata sami motsawa ba sai da kira ya
katse, sannan ta sauke numfashi. Bata gama
numfashibba wayar ta sake daukar ruri.
Hannunta bai daina rawa ba illa ma karawa da
yayi a hakata danna OK, cikin kasala ta kanga
wa kunnanta, murya sanyaye tace, "hello! Ya
numfasa ya amsa, "baki da alkawari. Haka
mukayi da ke? Ta numfasa, yasa ta zama mara
gaskia a zahiri,don haka ta amsa laifin ta, "Ayi
hakuri, ban .... Ya katseta."baki damu dani bako
Nusaiba? Ni kuwa ko alama na kasa sukuni,
gaba daya lissafi na a dagule yake. Nasan ba
zaki gasgata ni ba. Amma zaki sha mamaki idan
nace miki gani a kofar get din ku." Ai kuwa bata
gasgata abin da taji ba don sai data mike
zumbur tsaye tace, "kace me? Dan murmushi
yayi jim, yadda ta firgita, "tsoro kikaji? Tace,
"dan Allah da gask kakeyi? Yace "ai ba karya a
son da nake miki. Kawai na kira babana don
nace masa na iso sai ya cemin shima yna nan
Abujan yazo wani (conference) na kwana biyu,
shine yace in jira shi mu wuce kano tare. Ina
zaune a masauki tunannk ya addabeni ban san
lokacin dana bugo mota na taho ba, ki fito ina
nan waje." Shiru tayi ta rasa meke mata dadi? A
lokaci guda tausayin shi ya dirar mata a zuciya
ya bi ko ina a jikinta. "Me zance da bawan
Allahn nan? Ta tambayi knta. "Hello! Kina kan
layi kuwa? A firgice ta dawo daga duniyar
tunannta ta dan nisa tace, "gaskia Ibrahim da
dai kayi hakuri zuwa gobe kadawo, a san
abinyi."
Gaba daya guiwar sa ta kwabe ya, rasa
kuzarinsa. Murya raunane yace, "Nusaiba ba
kya sona, ita kenn karshen maganar. Abinda na
lura da shi kenan tun farko. Ko kuwa saboda
nace miki ina da mata shiyasa kika zuzzu ke
mun? Ba yaudarar ki nakeson yi ba ina gaya
miki gaskia ce tsakani da Allah. Mata ta batayi
min komai ba shekarun mu uku da aure. Kawai
Allah ne ya jarabce ni da sonki. Tsananin so mai
tada hankali. Nusaiba da kinsan halinda zuciya
ta tashiga tun daga lokacin da kika bar ni a
(Airport), ya zuwa yanzu da baki ce in dawo
gobe ba. Pls ki tausaya min ki fito, in sake ganin
kyakkyawar fuskar ki ko nasamu barci yau." Ba
karamin dafa mata jiki kalamansa sukayi ba,
kwalla fal idanuwanta, sai dai babu abinda ta
iya yi, domin bata ma san wa zata dunfara ta
nemi izinin sa ba. Kana dan siririn hawaye ya
gangaro bisa kuncinta, kafin tace, "duk abinda
kake nufi ba haka bne Ibrahim. Kaga dazu Abba
yayi mun fada yanzu kuwa babu yadda zaayi
insake zuwa ince masa gaka nan, ka sake biyo
ni. Shi yasa nace ka hakura zuwa goben zan san
yadda zan bullowa alamarin. Kaji? Don girmn
Allah kayi hakuri. Ka nemo layin Antina nasan
zata kwantar maka da hankali ka......... Ji tayi
dim!din! Din alamun an kashe wayar. Da bayata
fadi bisa filo, me zatayi? Ba kuka ba. Gaba daya
lokaci guda taji Ibrahim na ratsa ko ina cikin
jikinta, sabd tsabar tausayinsa. Rike hannayenta
kawai taji anyi, gaban ta ya sake faduwa da jin
muryar umminta, "ke! Nusaiba menene? Ta
tarairayo ta, ta tashi zaune.Da sauri ta rungume
Ummin." Na ce menene? Tayi shiru, don bata da
abin cewa.hasali ma ba'ason ranta Ummi ta
riske ta a wannan yanayin ba." Bebin Abba na
ce menene?"Tana kudundune ta amsa, "Ba
komai ummi." Ta ce,"Karya ki ke yi. Haka kawai
ba za ki hau kuka ba,
akwai dalili."ta dago mata fuska,"Dube ni nan."
Tayi zuru, kwalla na diga." za6in Abbanki ne, ba
kya so?"Da sauri ta kada kai,"A'a Ummi. Allah
ba haka bane. Ta ce,"Nusaiba, sanin kan ki ne
Abbanki ba zai cutar da ke ba, haka kuma ba
zai so ya ganki cikin irin wannan damuwar
ba.idan kin san bakya son Yaron nan, to ki gaya
min gaskiya, in rarrashi Abbanki ya hakura da
wannan abu.
Shi yana can daki, yana ta murna yana sa miki
albarka, ke kina nan ki na ta koke?
Bebi na,
ke kadai gare mu,
ba za mu so wani ciwo ya kama mana ke ba,
har mu rasa ki.
Menene gaskiyar magana?"ta goge hawaye,
kalaman Umminta suka sanyaya zuciyarta.
Ta dube ta ta ce,"Ummi wallahi duk abinda da
na gaya wa Abba na, gaskiya ne."
To menene dalilin kuka?
Ta sunkuyar da kai kasa, ta warware mata
labarin Ibrahim. Ummi tayi shiru, kafin ta nisa
ta ce "Lallai Ibrahim abin tausayi ne, amma bai
kamata ki kwanta ki na koke-koke ba, sai kiyi
addu'a.Allah ya sanya masa hakuri."Ta ce,"Ni
dai ko, Ummi ki gaya wa Abba na gobe, idan ya
zo, ya kira shi,
ya ba shi hakuri.
Ya gaya masa ina da wani."
Ko ba haka ba?".......






Zaharaddeen Shomar


Whatsapp 08168575100






Ajininsa yake 1-08
Posted by ANaM Dorayi on 08:10 AM, 09-Nov-15
Under: Ajininsa yake
_______ NA ZULAIHAT SANI KAGARA_______
.Ta shafa kanta ta ce,"Haka ne Bebina,
to ki daina kuka. Naseer yaron kirki ne, don ya
fito daga gidan mutunci. Sai ki ci gaba da
addu'a.Allah ya tabbatar da alkhairi.
Yadda ki ka faranta mana rai.
Insha-Allahu ke ma za'a faranta miki.
Allah yayi miki albarka."Amin Ummina." Ta ce,
tana dubanta. Ummi tayi murmushi, ta dan kama
ha6arta ta ce,"Ila gadan! Insha-Allahu. Inji
Nusaiba fuska sake.Ma'ana ta ce,"Sai da safe."
Ta amsa da "In Allah ya yarda."
Ummi ta mike ta bar dakin, tana waigen
'yarta.Wata ajiyar zuciya tayi, ta koma da baya ta
sake kwanciya.
"Allah gani gare ka, ka za6a min wanda ya fi
zama alkhairi."
Idonta kuri, ta kasa barci.ko alamar sa ma bata
ji.ji take kamar son Ibrahim yana neman ya
rinjaye ta."
Zakakan kalaman sa sun yi ta zuwa, suna dawo
mata a rai, irin labaran daya rinka zuba mata a
jirgi.
Idan ta rufe ido, shi take gani.
A karo na farko daya zauna kujerar da ke gefen
ta, ya yi mata sallama." Assalamu-
alaikum.............!
Kawai ta kan tsinci bakin ta yana sake amsa
sallamar, ba tare da sanin tana yi ba.
Dare ya tsala, ta rasa me zuciya ta ke da
Ibrahim?
Don haka tayi wuf, ta mik'e ta nufi bayi, ta
shiryo lafiyayyar alwala, ta fito ta nufi sallaya.
Hijabinta da zani, ta daura ta dora hijabi, tayi
niyyar nafila.
Bayan ta kawo raka'a 2 masu kyau, sannan ta
zauna ta dukufa addu'an Istahara.
Sai da ta kammala, sannan ta sami nutsuwa
cikin ranta.
Ta sake mikewa ta kawo wutiri, kafin wani lkc ta
soma jin barci.
Nan bisa sallayar ta, barci mai nauyi ya dauke
ta....
Tana ta tsala kuka, kofar wani tsalelen gida mai
kyan gaske, ba za ta iya sanin tsawon lkcn da
tayi tana zuba kukanta ba, mai tsuma zuciya da
ban tausayi. Kafadar ta, ta ji an dafa, wata
sansanyar murya ta kira sunan ta
"Nusaiba!,
Ta dago idanuwa jajur!
Ta dubi mai kiranta.
Naseer ne dafe da kafadar, suka zuba wa juna
ido.
Jim!
Sannan ya ce,"Taso mu shiga ciki."
Ba musu, ta mike, yana jaye da ita har bakin
kofa. Ja tayi ta tsaya cak! Tare da shirin fizge
hannun ta. Cikin sauri ya sake kamo ta,"Kar ki
k'i shiga gidan ki Nusaiba, ki sa ni ke uwar
'ya'yana ce. Ba a son raina............."
"Nusaiba!
Ke Nusaiba, ki tashi asuba tayi...Cikin mafarkin
muryar Umminta ke kwala mata kira.
Firgigi! Ta tashi, hawaye ne sharkaf a fuskar ta,
nan da nan ta kawo salati tare da share
hawayen, sannan ta amsa kira." Na tashi
Ummi."*****Allah Sarki***
Ta dafe goshi, jikinta tamkar an mata shegen
duka, da kyar ta mike ta nufi bayi, ta fito da
alwala, don sallatar asubah.
Tana ta lazimi bisa gadon ta.
Amma tunanin mafarkinta take yi. Menene
musabbabin kukunta? Babu abinda ta kawa wa
ranta, illa watak'ila Ibrahim ne zai zame mata
k'arfen k'afa.
Idan son shi ya hanata yi wa iyayenta biyayya,
ai ya cutar da ita. Naseet dai ta gani kiri-kiri,
amma ta kafe ta k'i shiga gidan sa. Nan da nan
ta daga hannu sama."
"Ya Allah na roke ka, kar ka kawo min ranar da
zan yi musu da iyaye na. Allah ka musanya
wannan kuka nawa, ya zama farin ciki a gare ni.
Allah ka daidaita zuciya ta akan tsananin son
za6in su Abba.
Ya Allah ka amsa, don albarkar da ka yi wa
Manzonka. Muhammad (S.A.W)." Haka ta koma
ta kwanta, ranta cunkushe har wani 6arawon ya
sake dauke ta.
Kamar a mafarki ta ji rurin wayarta, ta bude ido
cike da mamakin ba irin barcin daya dauke ta
mai nauyi gaske. Ta dauko waya ta duba.
Abban ta ne.
Da sauri ta dauka."
"Abba na!"
Ya ce,
"Duk gajiyar ce?
To ki zo mana in gan ki,
kafin na fita."
" 'Yar kunya ce ta sata murmushi,"Yi hakuri
Abba,
gani nan."
Ta diro da sauri, tayi bayi ta wanke baki da
fuska.
A gurguje ta sauya kaya, ta fice.
Lokacin kafe 9 dai-dai.
Da gudunta ta haye 6angaren Alhjn, ta tura kofa
tare da sallama.
Ya amsa yayin da take takowa cikin sauri tana
fadin,
"Kaifa asbahta ya Abba!
Shima fara'a yake yi, har ya iso inda yake
zaune. Ita ma zama tayi, ta yada kai bisa
kafadarsa."
Abba ina kwana?"
Lafiya lau."
Na ce duk gajiyar
ce har karfe 9 ban ga Bebina ba?"
Ta ce,"Barci ya sace ni." Ya ce,"Ummanki ta
gaya min sak'onki, kar ki damu, zan kira shi ya
zo yau, don in yi masa bayani kin ji?
Sannan ina ganin ma tare za mu fita, mu je ki
za6i irin motar da ki ke so.
Akwai sabbabin shigowa kala-kala, sai kin darje
Bebina."
Bakinta har kunne, ta k'ara langwa6e masa,"Na
gode Abba na."
Amma in tamabaye ka mana Abbana?"
Ya ce,"Me zai hana?
Ta ce,
"Shi Naseer wacce yake hawa?
Ya ji dadin tambayar ta, domin kawari yana son
ya rink'a jin zancen Naseer a bakinta."
Ya ce,"Uhm........... A halin yanzu dai (Civic)
yake hawa."
Ta dube shi da sauri "Abba sirikin (Dabai
Motors) ke hawan (Civic)?
Dariya yake yi, kafin ya ce," Kina da gaskiya, da
ni tunanina, sai zai fara angwaci, zan canza
masa.
Amma tunda haka ki ka ce, za'a bari ku je tare
ku Za6i irin daya.
Ya yi miki hakan?"
Ta gyada kai,
"Yayi Abba,
mun gode."
Tana shiru Hjy Zulaihat na shigowa da tiran
kayan abinci Alhjn. Nusaiba ta mike da sauri ta
amsa, ta kai bisa shimfidar da yake zama, don
cin abinxin.
Bayan ta gaida Ummi. Suka baje nan suka karya
tare.
Suna hira. Hjy Zulaihat bata bar dakin Abba ba,
sai 10:30, ta koma dakin ta, don yin wanka."
Tana shiga, wayar ta da ke ta faman ruri ta
katse.
Kai tsaye can ta nufa, ta dauka, ta duba (Missed
call) 5, duk lamba 1, wacce Ibrahim ya kira jiya."
Ya salam!
Ta fadi ido rufe Da sauri ta kira." Allah ya ba ki
hakuri, wayar ma ba za'a daga ba?"
Murya sanyaye ta ce,"Wallahi ba ni a dakin, ina
can wajen Abba na ne, ka hakuri, ka ji?
Sanyi ya ji cikin ransa, ya ce,"Ya zan yi, so ya
kama ni, ai sai yadda akai da ni.
Za ki sami fitowa ko sai gobe?"
Tace,"Maida wukar, gani nan fitowa."
Tana jin saukan numfashin sa ya ce,"Don Allah
kar ki dade,
na k'osa."
Ta aje waya, ta nemi wuri gefen gado, ta dan
raba hankali tayi shiru, ba tare da ta fahimci
dalilin shirun ta ba.
Can ta nisa, ta mike a natse, ta gyara zaman
mayafinta da kyau, ta baro daki ta koma wajen
Abbanta."
Suna nan tare da Ummi. Kai tsaye ta shaida
masu Ibrahim ya dawo. Ya dube ta da sauri, ya
ce,"Je ki ce ya shigo, ku same ni a falon baki."
Ta juya ta fiti cikin hanzari.
Zaune yake cikin mota (Camry), yayin da ta
budo get ta fito. Suna hada ido, zuciyar sa ta
hau bugawa, tamkar za ta tsaga kirjin sa. Cikin
kuzarinsa ya fito, baki har kunne. Da sallama ta
karaso gunsa. Ya amsa." Sannu da zuwa."
"Ke ma sannu da fitowa.
Ya mutan gida?
Ya jin dadin ki?
Tayi d'an murmushi,"Duk suna lafiya, amma jin
dad'i, ai ku ke da shi."
Kallon ta kawai yake yi, zuciyar sa kamar anyi
masa albishir da aljanna.
Wani kayatacen murmusji yayi, kafin ya
ce,"Wane jin dadi zan yi, bayan har yanzu ban
kama dahir ba?
Jiya zuciyata kamar za ta k'one, sbd tsabar
rashin ganin ki.
Me yasa za ki min haka?, So na ne ba kya yi ko?
Ta dan yi shiru jim.
Sannan ta ce,"Ba haka ba ne, amma yanzu mu
shiga ciki.
Abba ya ce yana son ganin ka."
Ya fadada fara'arsa cike da jin dadi ya ce,
"Rana kawai za'a sa mana,
mu je in ga Abban."
Yana kulle mota, jikinsa har rawa yake yi, haka
ta sa ma sa ido, tausayin sa zalla cikin ranta."
Ta wuce, ya biyo bayan ta, tayi masa jagora
zuwa falon baki.
Falon ya shiryu, iya shiryuwa.
Shi kan sa masaukin ya kayatar da shi.
Ta nuna masa kujera, ya zauna, kafin ta ce,
" Miniti 2."
Ya ce,"1 na ba ki."
Ta wuce tana dan murmushi.
Jimawa kadan, ta dawo dauke da tire cike da
ingantattun abincin karin safe, ta dire a gaban
sa, ta ce,"Abba ya ce," Ka yi (Break-fast), ga shi
nan zuwa ku gaisa."Ya ce,"To, na gode kin kuwa
san rabo na da abinci?, Ta dan dube shi yayi da
take harjada masa abubuwan cikin filet, ta dan
kada kai,"Tun wanda na dan ci jiya a jirgi."
Ido waje ta ce,"Kai haba, me yasa? Ya
ce,"Tunaninki kawai, sannan abinda ki kai min
jiya, ko alama bai min dadi ba.
Shima ya taimaka wajen hana ni cin abincin
dare.
Ina son ki Nusaiba, so mai ban mamaki, domin
ni ban ta6a zaton zan so wata 'ya mace, kamar
yadda na so mata ta ba.
Sai ga shi tashi guda, kin rikita ni Nusaiba, har
ina neman zarewa.
Allah yasa yadda ki ke zuba min abincin nan, ki
zabu min shi a cikin gidana."
Ba ta ce komai ba, domin kalaman Ibrahim
nema suke su kidima ta.
Kai Nusyy mene abin kidimawa a wannan
kalaman! Nima idan nadage zan iyasu...
Koya kukace?
Aje masa tayi a gaban sa, ta mike a hankali ta
ce,"Don Allah ka ci da yawa, bari inje in dawo.
Don me?"
Please!
Ki zauna,
kan dole ta zauna, saboda a gaskiya bata son
yadda Ibrahim ke cusa mata ra'ayin sa, tana
tsoron kar a wayi gari ta kama da tsananin son
sa, wanda zai iya wahalar da ita, kafin ta manta
da shi.
Tsit!
Tayi a zaune,
ba eh,
balle a'a.
Shi yake ta ba cikin sa abinci, wani lkcn ya kan
yi santi da gangan, don tayi dariya, amma ina!
Sai dai tayi murmusji, ta kauda kai,
Bayan ya kammala, ta tattara kayan, ta dauka,
yana fadin "Ki cewa Mama na gode da (Break-
fast)
Ta dan juyo, ta dube shi ta ce, "Zan fadi."
Ta sa kai ta fice.
Shiru yayi, yana mamakin kansa, domin shi
abinci, idan ba na matar sa ba, duk gaibu ne.
Ba wani sakin jiki ya ci shi yadda yakamata.Yayi
kasake yana tunanin tsiyar da Ummansa take
masa." Da kafin kayi auran. Abincin wa ka ke
ci?"
Uban 'yan gulma!
Kada kai yai, yana wani bazawarin murmushi.
Hannun sa daya yana shafar cikin sa har da
wata gajeruwar gyatsa.Sallamar daya tsinkayo
ce, ta sa ya dai-daita sahun sa.
Yana amsawa, yana ganin Alhj yayi sauri ya
mike tsaye, yana masa sannu cike da
girmamawa."
"Zauna mana."
Inji Alhjin.
Sannan ya zauna,
suka ci gaba da ganawa."....
Nusaiba tare da Umminta suke hira a babban
falo. Bayan wucewar minti 20,. Alh. Basheer ya
dawo, ya cewa Nusaiba,"Ki je ki sallame shi,
mun gama magana."
Ta mike ta nufi falon baki, ilahirin jikinta a mace
yake, sbd tsabar tausayin Ibrahim.
Koda ta iso bakin kofar, haka ta tsaya kusan
minti 3, kafin ta tura kofar ta shiga.
Bai iya amsawa ba, kan sa a saye cikin guiwa.
Zuciyar ta, ta k'ara raunana.
Suka zauna shiru tsawon lkc, kafin tayi karfin
hali, ta katse shirun."
"Ibrahmin don girman Allah, ka yi hakuri kaji,
mu yi addu'ar Allah ya sa hakan shine ma fi
alkhairi a gare mu."
Ya dago ya dube ta, ido jajur!
Ya ce,"
Na yi Nusaiba, ni zan koma."
Nan da nan idanunwanta suka kawo kwalla,
murya raunane ta ce,"Bana so in yaudare ka ne
Ibrahim shi yasa, don Allah kar ka dauki
wannan abu da wata fuska."
Ya kada kai, ya ce,"Hakan ya na da kyau
Nusaiba, babu 6oye-6oye ko rufa-rufa.
Abba yayi min kalamai ma su dadi da kwantar
da hankali, sai dai kin san abinda rai ke so, bai
ta6a samun nutsuwa lkc

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login