Showing 30001 words to 33000 words out of 40261 words
Chapter 11 - A JININSA YAKE PDF BOOK COMPLETE Writing by Zulaihat Sani Kagara .txt
guda, muddin zuciya
bata sami abinda take bukata ba.
Na san zan shiga wani hali Nusaiba.
Domin son ki ya riga ya shige ko'ina a jiki na."
Ka barwa Allah komai." Ya ce,"Na bari kuma ina
taya duk wanda ya same ki murna, saboda ba
k'aramar sa'a yayi ba.
Amma zan so ace ki dan yi (Saving) lamba ta,
mu rink'a gaisawa, kafin auran ki ya tabbata.
Zan sami wannan taimakon?"
zan yi (Saving), amma da sharadin gaisawa
kawai."
Da k'yar ya mik'e tsaye, ya sanya mata ido,"To
na gode............... Ya ci gaba da kallon ta,
fuskar dauke da 6acin rai a bayyane.
Shi yasa ita ma ta kasa kallon sa.
Kamar zai sake cwa wani abu, sai kuma ya kasa.
Ya juya da suri ya fice daga falon.
Ya dan jima da fita.
Nusaiba na zaune tana ta sharar kwalla, kafin ta
samu hawayen suka tsaya.
Ta mike cikin hanzari, ta bi shi.
A zatonta ma ba za ta same shi ba, amma tana
tura kofa, ta gan shi zaune da hankicin yana
share fuska.
Kirjin ta ya ci gaba da har6awa, ta tsaya jikin
kofa ta ce,"Allah ya kiyaye hanya,
idan ka yi waya da Madam, ka ce ina gaisheta."
Can k'asan mak'oshin sa ya amsa,"Za ta ji."
Tare da sawa mota makulli, ya bata wuta, bai
saurari komai ba, ya bar wajen.
Nusaiba na tsaye sai da ya 6ace ta dawo cikin
hanzari.
Babu kowa a falon k'asan, don haka ta nufi
6angarenta.
Kai tsaye shirin wanka tayi, dan lkcn kankani, ta
kammala wankanta, ta tsala kwalliya da a
tamfarta mai kyawun gaske.
Kwanciya tayi shiru, tana tunanin abubuwa
masu yawa.
Duk da dai bata son ranta ya na sako mata
Ibrahim, sam ta kasa fidda tausayin a ranta.
Ta lumshe ido ta dawo da hoton Naseer cikin
zuciyar ta,"Me yasa na ke ta faman kuka,
ban son shiga gidan ka?
Ta kasa ba kanta amsa, saboda ba ta ma san
me ranta ke nufi a game da Naseer ba.Ita bata
kin sa,
ita kuma bata wani zazzafan dokin sa take yi ba,
duk da ta hakikance za6in Abbanta ingantace
ne.
Amma kwarai mafarkinta na rikita ta, shi yasa ta
ke masa fassara kala-kala.
Cikin duniyar tunanin ta ne, ta jiyo kwakwazon
Kausar.
"Ahalan-wa-sahalan!
Larabawan Jordan!
Tayi wuf ta diro daga gado, tayo waje, suna
kicin tare da Ummi suna gaisawa, can ta nufa
suka nufi juna suka rungume. Kausar na da
surutu, ga zak'in murya tare da saurin magana.
Suka dubi juna.
Kausar ta juya kan Ummi,"Ummi wallahi
yarinyar nan tana jin dadinta, wai mai karatu ce,
ta dawo kamar fanke!
Suna dariya, ta bata amsa,"A'a kin manta
alkubus ne?
Ta ce,"Ananandai, kin kalli madubi kuwa kin ga
wadannan kumatun?
Ta tamabyeta,
tana ta6a mata kumatu.
Ta doke hannunta tare da fadin,
"Ban sani ba,
masharranciya.
Ni don Allah zo mu je, 'yar sa ido.
Suka wuce rike da hannun juna.
Ummi da dariya ta kada kai."
Kausar kenan!"
Daki suka fada, ta wurgar da jaka gefe, ta zube
bisa gado.
Ina can tunanin ki ya isheni cikin aji, wawan
lakcaran nan, ya ki sallamar mu."
Nusaiba ta zauna gefen ta, ta ce,"Ai ka ji halin
Dan-Adam. Yanzu da bai zo ba, sai ace ya ki
zuwa, don rashin kishin kai."
To kuma sai ya shiga lokacin mu?"
Ke manta, don Allah ina tsaraba ta tukuna?
Dan murmushi tayi,
"Ni in gaya miki tun jiya da na jefar da jakar ko
ta kanta ban sake bi ba.
Ita ce can?"
Ta fadi tana nunuwa.
Mikewa ta yi ta tanyo ta," Ina fatan kin kawo
min turarukan nan?"
Bude dai ki gani." Ta wurgo mata dan makulli.
Tasa ta bude dan kankanin kwadon da ke
makale jikin zif din.
Ta wangame Jakar. Su 2 suke fiddo kaya kala-
kala na sawa, turaruka , mai iri-iri, a goguna da
dukkan kayan kyale-kyalen mata.
Kausar ta darji na darza, ta maida jakar ta.
Bayan sun kammala da tsaraba.
Nusaiba ta kira Mariya 'yar yarinyar da ke masu
aiki, ta kawo wa Kausar abubuwan kusa da ba
ka za6in ta. Da kofi jus a hannun ta, ta dubi
Nusaiba ta ce,
"Bebin Abba kenan, to yanzu kuma sai me?
Ta dan ta6e baki, ta ce,"Sai me kuwa?
Zama tare da Abba na, gani ga shi."
Tayi 'yar dariya, ta aje kofi k'asa,"Magulmaciya,
ai karyar korar samari, ta kare.
Dole yarinya ta tsaida na aure, ko mu samu
wani Sugar Daddy mu mik'a masa."
Ta zungura kafadar ta,"Aniyar ki ta bi ki. Kin san
ma me ke faruwa?"
Sai kin feshe ni."
Ta dan karkace kai, ta bata labarin Ibrahiim
yadda suka hadu a jirgi.
Ta kwa6e fuska ta ce,
"Amma guy din yayi, sai dai ya dan kwafsa,
tunda yana da mata.
Ajinsa ya sauko."
Ya sauko?"
"Eh,
mana,
kin san fa ni duk harkar kishiya ba ni a ciki."
Dariya ta bata,"Ke bakin kishinki zai hallaka ki,
ina ruwanki da ita?"
Ai ni duk inda ta fadi, sha ne, ni dai rokona
Allah ya hada ni da na gari.
Aje wannan maganar, da alama so ya kamaki."
Eh,
ya kamani,
sai dai abin ba zai yiwu ba."
Ta dan ware ido."
Don me,
bayan ki na sonsa?
Matar ce jaraba?"
Ta dan nisa ta ce,"Abba na ya za6a min miji."
Mai-maita don Allah?"
Na ki maimaitawa, kada Allah yasa ki ji."
Na ji abin ne kamar a oldings days.
Me yasa Abba yayi maki haka?"
Ya ga shi ne ya fi dacewa da ni,
kin kuma san Abba ba zai kai ni gidan wahala
ba."
Ta kada kai tare da yamutsa fuska,"Ni kuwa kin
ga inda za'ayi daga dani kenan.
Abar ni in darje, in za6i wanda ya kwanta
min."ta zuba mata ido, kafin ta ce,"Kausar
kenan.
Kawata kaza kanki da motsi."
Ta ce,"Allah ya isa,
banza!
Ta 6alla mata harara, ta juya tare da sakin
wawan tsaki.
Don na mutu a tausayinki, shine zaki wulakanta
ni.
Allah yasa mai duka ne, Abba bai sani ba,
kullum yayi ta jibgarki, kamar 'yarsa."Ta sa
dariya, ta sa hannu ta jayo ta,
"Kawalli kenan.
To huce, ki ji wani dan bayani...........Ta katse
ta,"Ba wani bayani, kawai ki gaya wa Ummi ke
ga wanda ki ke so.
Kar fa ki manta, wanda ba ka so, ko kallon sa
ba ka so yi balle aje ga biyayyar aure. Amma ke
na ga alama za ki yi wasa da rayuwar ki."
Ta ce,"Ba haka bane kuma zan so ki dan natsu
ki fahimci abin da zan ce."
Ina jin ki."
Ta ce,"Na dade ina wani nazari akan auratayya a
wannan zamanin.
Ta yadda aka maida aure abin wasa ko kuma
ince don wani jin dadin bukata, sa6anin ibada
kamar yadda ya zo daga Manzon mu.
A zamanin da can kamar yadda a kakanin mu
suke ba mu labari, sai ranar da aka kai ki dakin
miji, sannan za ki san wanda ki ka aura, haka
shi ma mijin, a lkcn zai san ki.
Amma abin mamaki sai ki ga sun zauna lafiya.
Mutu ka raba. Da tafiya tayi tafiya, anyi karatun
boko, wai an waye, sai aka ce wannan tsarin
auran dole ne.
Aka soke wannan tsari, aka ce abar kowa ya
aure za6in sa.
Sai ga shi a lkcn auran za6in abubuwan sun
rikice.
Aure ya zama wasa, an maida saki ba a bakin
komai ba.
Wallahi wani auran ko Shekara ba'ayi za'a fara
sa, in sa.
Wani lokacin ma ki tsince su a kotu.
Shi yasa a nawa ra'ayin, ban ta'allaka soyayya
zalla ba a cikin zama aure.
Dole sai da addini,
"Kyan asali,
"Tarbiya.
"Hakuri,
"Juriya, da sanin me zai je, ya dawo?
Wannan shine abubuwan da kakaninmu suka
rinka dubawa wajen auratayya.Ina son ki
sani,abinda babba ya hango. Yaro ko yahau
rimi, bai zai gano shi ba.
Ita kuwa zuciya a kodayaushe kyale-kyale tafi
so, duk wanda ya biye mata kuma, karshen
al'amarin ba zai yi kyau ba.
Saboda haka Abba yayi dai-dai da yayi min zabi.
Ubangiji Allah ya taya shi zabi.
Abu na gaba da na ke so ki yi koyi da shi
kawata, shine kar ki hakikance wa ran ki dukan
abinda zuciyar ki ta bukata.
A kodayaushe ki fi rinjaye bisa za6in Allah."
Kausar ta numfasa ta ce,"In yi miki ta Indiya,
Vah! Lak lak shukran, mere dost! Tana
murmushi ta amsa, " Ki na nan da Indiyancin ki,
na dai ji shukran godiya ce, wannan larabci aka
sata.
Na ce da kyau, godiya dubu-dubu kawata. Ai kin
yi nasiha, na kuma gamsu Pyar ho gaya." oh ba
za ki daina Indiyanci ba kenan, me ki ke nufi?"
A sannu a sannu za'a so juna. Wai ma waye
gayen da yayi sa'a haka? Ta ce," Ban san shi ba,
hotonsa kawai na gani a dakin Abba, shi yake
gaya min dan wasan Polon sa. Yaro ne mai
hankalu kuma ya fita gidan mutunci...
Comment dinku yana karamin Karin gwiwa, so
keep it up
Zaharaddeen Shomar
Whatsapp 08168575100
Ajininsa yake 1-09
Posted by ANaM Dorayi on 04:39 PM, 09-Nov-15
Under: Ajininsa yake
_______ NA ZULAIHAT SANI KAGARA_______
.
Sunansa Naseer."
Tayi fit, ta ce,"Naseer Jah-Jah!"
Ke ba fa Yakubu Jah-Jah ba.
Naseer aka ce ta ce, tun yaushe tutar Yakubu ya
sauko, ai yanzu Naseer shi ke jah.
Ki na nufin shi Abba ya za6a miki?"
Ta zura mata ido,"Kin san shi ne?"
Ta miko hannu,"Ke dai ban hannu tukuna."Ta
bata suka tafa, jikin Nusaiba ya k'ara sanyi,"Don
Allah san shi?"
"Ba dole ba, ni da na ke bin Daddy kallo. Sai
yanzu na k'ara yarda da maganar ki, komai
babba ya hango.
Yaro bai iya ganinsa ko ya hau abinda ya fi rimi
tsawo.
Naseer na shan yabo wajen kowa, sannan kowa
na son sa.
Lallai Abba ya san abinda ya dace da ke."
Dan lumshe ido tayi, ta ce a hankali,"Masha-
Allah."
Sannan ta bude suna duban juna,"Kin ga abinda
na ke ke gaya miki ko?"
Yanzu me ya rage?"
Kawai mu jira lokaci, biki mu guwangwaje, ranar
ni kai na sai na hau doki.
Shi kan sa Jah-Jan dole ya daga min kafa.Ta
bata hannu suka tafa.
Nusaiba ta ce,"Kin ga yanzu dole a nemo kayan
aiki, ina littafan hausa? Ta ce,"Suna nan, amma
fa na aje na Momin Zariya ban karan ta su
yanzu."
Don me?"
Wasu maganganu tayi akan 'yan (Flashing) ya
bata min rai, kai tsaye na buga waya na zagi
banza."
Inna-lillahi wa-inna-ilaihir-raji'un! Ki zage ta? Ta
figo jakar ta tana fadin,"Bari ki gani, kullum
yawo na ke da littafin, koda musu zai tashi in
nuna shaida."
Ta jawo shi, ta ta bude mata wajen, ta karanta.
Tana gamawa ta dube ta.
"Amma kuwa Kausar kin ba ni mmk. Yanzu ke
saboda Allah ina hankali a cikin irin wannan
(Flashing) Haka kawai ba sa ki aka yi ba, ki
dauki waya ki hau (Flashing) sama da goma sha,
har dan cajin mutum ya kare.
Menene amfanin sa?
Ke ko ni da ne ke kawar ki, na yi miki haka,
dole na kure ki, ki zage ni.
Ai babu abinda ya fi kona rai a game da harka
waya irin (Flashing), saboda ba ka san a wane
yanayi mutum yake ba, watakila ma cikin jama'a
yake, balle wannan da aka ce har cikin dare yin
sa ake yi.
A gaskiya ban goyi bayan masu wannan dabi'a
ta Flashing)
babu iyaka ba.
Kar kuma kin mance, su masu hulda da jama'a
ne, ke ki na (Flashing), wata can na yi, ko ma
ince wasu, ai kin ga dole abin yayi masu yawa
har su ji zafin abin."
Ta kwada mata harara, ta ce,"Suyita jin zafin
mana, mu muka sa su rubutun? Ta ce,"Ayya
kawata.
Ban so ki kasance cikin irin mutane masu ci,
suna share baki ba.
Ma'ana duk mutumin da zai miki abinda za ki
amfana da shi.
Ya fi gaban wannan furucin da ki ka yi. Ba
karamin kuskure ki ka yi ba, da ki ka ce kin zage
ta.
Domin Manzon mu Annabi Muhammad (S.A.W)
ya ce,"Kada ku kasance cikin wadanda za su
tashi ranar gobe kiyama suna matsiyata, alhalin
sun yi ibadar su daidai. An tambayi.
Mai girma da daukaka, wanene matsayin
lahira?"
Sai ya ce,"Shine wanda zai zo da aikinsa cif-cif!
Amma ya ha'inci wannan, ya zalunci wancan, ya
shiga hakkin wannan.
Sai ya kasance an debe ladarsa, an biya su, har
ta kai ga ba shi da sauran lada, daga nan za'a
fara diban zunubansu ana dora masa.
A karshe zai tashi a tutar babu. Wa-iyazubillahi!
Saboda haka ki daina daukn irin wadannan
abubuwan na shiga hakkin jama'a a kankanin
zunubi.
Ubangiji bai yafe hakkin wani har sai shi wanda
aka zalunta ya yafe, ina fatan kin fahimce ni? Ta
sauke tagumi ta ce,"Duk jiki na ya yi la'asar.
Allah ka tsare mu da tashin matsiyatan lahira.
Bari ma dai ki gani."
Wayarta ta dauko,"Me za ki yi?
Ta ce,"Neman afuwa."
Dan murmushi tayi,"Ina son ki wajen daukar
nasiha. Nemo ta mu gaisa. Daga nan mu nemi
shawarwari."
Cikin dan kankanin lokaci waya ta sada su da
Momin Zariya. Jimawa kadan ta dauka tare da
sallama. Kausar ta amsa,"Na san ba za ki gane
ni ba Momi, amma an ta6a kira na fadi wata
magana maras dadi akan maganar da aka yi sbd
'yan flashing.
Gaskiya na yi tunani na ga abinda na yi bai da
ce ba in kira ki, in ba ki hakuri.
Momi ta ce,"Haka ne, kuma har ga Allah ya
wuce. Rashin fahinta ke sa wa mutane ke ganin
ba'a kyauta ba. Amma da an san irin kashin da
'yan flashing ke yi, da irin ku ba su zage mu ba.
Bayan wannan wai har kiran waya ayi hankali
tashe, ace don Allah ki bugo anyi mutuwa.Jiki na
rawa zan kira, wai sai ki ji ana kyalkyar dariya.
Menene wannan?
Yanzun saboda Allah don ka kira mai irin
wannan marasa hankali, wanda bai san inda ke
masa ciwo ba. Ka yi laifi?"
Ta nisa ta ce,"Tafdi!
Lallai wannan rashi hankali ne, abinda kuwa ya
raba mutun da dabba kenan hankali.
Hakuri za ki yi Momi aikin jama'a ki ke yi, dole
ki rinqa ganinsu iri-iri..
Tayi murmushi,"Wannan ya zama dole, ban
kwana da kowa, ban tashi da kowa.
Duk wanda ya gyara, ya sani, haka duk wanda
ya 6ata, ya sani.
Shi Dan-Adam ai tara yake, bai cika goma ba,
babu wanda zai ce ya wuce zagi a doron kasa.
Saboda haka ni duk wanda ya zage ni, na yafe
masa, ni ma ina rokon wanda yake ganin na
6ata masa, to ya yafe mi. Saboda halin rai."
Kausar ta cika da al'ajabi, har ta rasa ta cewa.
Jim kadan ta ce,"Ga kawata Nusaiba, za ku gaisa
ta ma kusa aure, sai ki bata shawarwari.
Nusaiba ta amsa, ko dama sifikar a bude take,
tana jin komai.
Bayan sun gaisawa.
Momi ta kara da cewa,"Shawarwari suna nan
jibge, cikin littafai. Idan mai karatu ya natsu, zai
fahimta, ba wai dadin lbr kawai ba.
A karshe sai ince bayan hakuri, a kara da juriya.
Jurewa kwaramniyar aure, shi ke sa wa zama ya
dore irin na iyaye da kakkanin mu. Allah yayi
yagora, ya zaunar da mu lafiya da mazajenmu."
Ta ce,"
Amin.
Mun gode
Momi.
Don Allah zan tambaye ki, ina fatan ba za ki yi
fushi ba?"
Ta ce,"Allah yasa na sani.
Don Allah shekarunki nawa?
Kuma 'ya'yanki nawa?
Ta ce," Bana ina da shekaru arba'in da daya 41.
'Ya'yana takwas 8,, sai daya da Allah yayi wa
rasuwa.
"Wai, lallai Momi kin mika, to Allah ya raya su,
rayuwa mai amfani, ya jikan wanda ya rasu.
Mun gode."
Ta ce,"Amin, ni ma na gode."
Kausar ta daga murya,"Sai anjima Momi, ni suna
na Kausar!
"To Kausar, ke kuma yaushe ne auran na ki?"
Ta ce,"Da saura Momi, karatu na ke yi." Shi
kenan Allah ya za6o na gari. Sai Anjima."
Amen.
Suka kashe waya.
Nusaiba ta budi Kausar,"Kin ji ko?" Ta ce,"Borin
kunya kawai na ke yi, ashe sa'ar Momina na
zaga. Daga yau Insha Allah ban sake ba.
Ta ma yi wani littafi TARKON AMANA, ban
karanta shi ba.
Amma gobe zan shiga kasuwa."
Tana dariya, kawai suka tsinkayi kiran sallah
cikin masallaci dake like da gidan."
Wai azahar ce tayi,? Inji Kausar. Nusaiba ta
ce,"To da zauna nan kina zagin mutane, sai dai
ki ji wuf a kabari. Ta shige bayi ta bar ta da
kwakwazo,"
Banza!
An dai yafe min, ko dama da wa da na zaga??"
*******************
Shi kuwa Abba bayan kammala shirin sa, misalin
sha dayan rana ya bar gida bai zame ko'ina ba,
sai Zariya.
Malam Balarabe na zama jiran sa kamar yadda
ya shaida masa ta waya cewar yana tafe, don
gabatar da wata magana. Shi kan sa da ya iso
gidan su Naseer, ya ga sauyi.Koda ya shiga ciki
kuwa abin ya ba shi mmk. Kuma Naseer ya kara
burge shi, ganin yadda ya gyara gidan su
gwanin sha'awa, cikin falon da aka sauke shi.
Nan ma komai ya ji dai-dai k'arfin samun
Naseer, hakika kowane ya zo, za'a fita kunya. An
kuwa fita kunyar Alhj domin tarba ta
musamman aka shirya masa, duk da cewa
Naseer kan san bai san da zuwan Alhjn ba,
kuma Abba bai gaya masa ba.
Saboda lkcn da Alh. Basheer ya yo waya.
Naseer bai gida.
Bayan natsuwar su, su biyu a cikin falon. Alh.
Basheer yayi gyaran murya, ya fara gabatar da
abinda ke tafe da shi, "Na san zakayi mmkn
zuwa na, ba saboda zumuncin da ke tsakanin
mu ba.
Amma watakila dalilin zuwa na, ya ba ka mmk.
Sai dai a hakikanin gaskiya, ba abin mmk bane
ga shirin Ubangiji, domin shiya hada ni da
Naseer kuma ya sanya min kaunarsa.
Kaunar tayi yawa Malam Balarabe, har na ji ina
son hada zuri'a da ku.
Ma'ana 'ya ta Nusaiba na ba Naseer."
Gaban Malam Balarabe ya fadi ba kadan ba,
sannan ya rasa a wane yanayi yake?
Ana wata ga wata kenan, ya ma rasa wane,
bayani zai yi?
A matsayi da girman Alh. Basheer, ya d'auki 'ya
ya ba su, ai kar6a ya zama dole, don ko
mafarkin bai ta6a gigin tunanin wannan abu ba.
Kwarya ta bi kwarya...........Inji hausawa.
Allah mai iko. Bakin sa har kunne ya ce,"Kai!
Kai!! Kai!!! Alhaji wannan sako da girma, yake,
mun gode, Allah ya saka da alkhairi, ya taya mu
rik'e amana."ya ce,"Amin, sauran magana kuma
Naseer ya je su ga juna, domin jiya ta dawo
daga Jordan, ta kammala karatunta." Ya
ce,"Madalla, kawari Naseer ya gaya min
shekaran jiya har yake ce min ka yi masa
maganar makaranta, ka na son ya ci gaba.Na
ce,ai shi ya tsaya shishirinta da yanzu ya gama.
Sai dai akwai wani hanzari, ba gudu ba Alhj,
wanda ya zama dole in fade shi. A hakikanin
gaskiya akwai wata yarinya da aka ba Naseer
tuntuni, jira ake ta gama sakandirinta ayi auran.
Bana ma za ta gama. Ka ji abinda ya sanya ni a
damuwa, ban kuma san yadda za'ayi ba?"
Shi kansa Alh. Basheer zancen ya motsa
zuciyarsa, jikin sa yayi sanyi jin shiru yana dogon
tunani. Amma ko alama ran sa bai jirkita da
wani bakon tunani ba, tsabar kaunar Naseer ke
nuna masa babu wata matsala. Ya dubi Malam
Balarabe ya ce,"Ai Naseer mijin mace 4 ne, so
ina ganin ba wata matsala, na riga na ba shi
Nusaiba, ya hada duka ya aura, na dauki nauyi
komai. Allah ya taya shi riko bisa adalci."
Fafdi! Wace irin kauna kuwa Alhj ke wa Naseer?
ko alama Malam Balarabe bai san irin ta ba.
Ashe akwai sauran irin su Alh. Basheer a
duniya?
Ya karkada kai ya ce,"Ba ni da bakin godiya Alhj.
Bari dai in kira Maman shi, ta taya ni."
Ya mike da rawar jiki, ya leko ya kwalawa
Umma kira. Ta amsa, ta same su a falon saye
da bakin hijabin ta, gefe ta zauna. Sannan
Malam Balarabe ya mayar mata da bayani. Ita
kan ta, ta ji dadi fuskar ta, ta nuna karara, sai
dai tunani dan gogan take yi, jin cewar bai ma
san da zancen ba.
Da wace fuska zai dauki al'amarin? Bata da
amsa tilas, Naseer ne zai fayyace komai.Wannan
tunani shi ya sace mata guiwa. Bayan ta gama
murna da godiya ga Alh. Can ta koma kuryar
dakin ta tayi zaune gefen gado tana jujjuya
al'amarin cikin ranta. Tare da tambayar kan
ta."Wane irin bayani za mu yi wa iyayen Zarah?
Ta nisa ta ce,"To ya Allah kai ka shiryo wannan
al'amari, ina rokonka ka sanya mana fahimtar
juna."
Tana gama addu'ar ta, ta jiyo kiran Malam, ta
amsa.
Ya ce ta zo Alhj zai koma.
Ta yo waje, nan tsakar gida ta iske shi, suka yi
sallama tare da kara kwarara godiya.
Hannu ya zura aljihu, ya debo kudin da shi
kansa bai san ko nawa bane, ya mika mata.
Ta kada kai ta ce,"Alhj ai mu ne za mu bada
tukuici.
Ya dubi M.Balarabe." Malam,
Naseer d'anta ne ko d'a na?"
Ya amsa yana murmushi,"Ita ma ta san dan ka
ne Alh. Ya juya kan ta,"Amshi na ce, ba