Showing 3001 words to 6000 words out of 40261 words

Chapter 2 - A JININSA YAKE PDF BOOK COMPLETE Writing by Zulaihat Sani Kagara .txt

yayin da Sageer
ke nuna shi. Ta ce,"Kullum sai an ba mu lbrn
Naseer. Ya tare fada, ya siya min wannan, ya ba
ni wancan.
Ashe babba ne.
Ajinka nawa?"
Ya ce,"Shidda 6,."
Ta ce ,"Ashe ma ka ku san gamawa.
Lallai Zarah za ta yi kewa, don shekaran jiya ne,
ba ka zo ba ko?
Nan ta ishe ni da magana, Inna yau Naseer bai
zo mkrnt ba.
To mun gode Naseer.
Allah yayi ma ku albarka."
Duk kunya ta rufe shi da kyar ya ce,"Amin.
Malam Umar ya ce,"To an gode, sai ku tashi
kowa ya tafi gida ko?" Kar aga kun dade ba ku
koma gida ba. Mun gode." Suka mike suna
fadin,"Allah ya kara sauki." Iyayen ta suka ce
"Amin."
Sun fice, jim kadan wani yaro ya dawo cikin 'yan
rakiyar Naseer.
Wani kulli leda ne ya shigo da shi,." Wai ga shi
in ji Naseer.
Ya aje gefen Zarah ya ruga a guje.
Inna na ta dariya. Ta kwance bakar ledar, kullin
gugguru da gyada ne a ciki da aya soyayya. Ta
kada kai ta ce,"Allah sarki yaro, shi kuma jininsa
da na Zarah ya hadu.
Malam Umar ya ce,"Shiririta ke nan.
Ko ina ne gidan su?
,"Oho."
Ita kuwa Zarah tuni ta fara diban abin ta tana
ci.
Kwana 2 Zarah na kwance a gida.
Kullum sai Naseer ya je gidan da safe da
yamma. Hakan yasa iyayenta suka san Naseer
sosai.
Innar ta ke cewa"Lallai Zarah Allah ya ba ki
yaya daga sama."
Shi yasa da ya zo, sai ta ce, "Zarah ga yayanki
ya zo." Ko barci take kuwa za ta tashi. Sai dai
Zarah ta warke ta koma Mkrnta, sannan
hankalin Naseer ya kwanta.
A dalilin Zarah. Naseer ya nutsu a mkrnta, ko
sau daya baya fashi, duk da cewar bai bar Polo
ba, domin duk asabar da lahadi in dai akwai
wasa, toh yana can. Ba karamin mmk ya ba
kowa ba. Iyayensa na ta murna, suna yiwa Allah
godiya, duk da dai rigimar sa ta neman magana,
tana nan babu abin da ya sauya.
Naseer kam bai iya zama na cikakkiyar awa 3,
sai ya nemi abokin dambe.
Duk sa'o'insa tsoronsa suke yi, sbd karfinsa,
balle kananan yara.
Ganin ya nutsu a mkrnt, yasa Hedimasta ya
nada shi (Labour prepet). Sosai yake gudanar da
aikinsa, don ba sauki, ga yara.
Zarah ko ajin su kuskuran kallon banza, babu
mai yi mata shi, sbd kanwar Naseer ce.
Kokarinsa da komai, sai ya nuna shi babba ne,
ke sawa yana kara kwarjini a idon kowa.
Allah yayi masa kyau, surar jikinsa kaf bai da
makusa.
Shi ba fari bane, kuma ba baki bane,."
Sannan ya zarce wankan tarwada.
Wasu manyan idanuwa da Allah yayi masa
farare sol!
Su ke sawa duk wanda ta kallai, sai tayi
sha'awar sa.
Ubangiji yayi wa Naseer wannan baiwa.
Wanda adalilin haka ne kawai yake shiga ran
jama'a su kamu da kaunar sa.
Yau suke zana jarabawar share fagen shiga
karamar sakandire (Common Entrance). A
kwalejin Alhuda-huda. Sun yi, sun gama cikin
sa'a kowa ya koma gida.
Ranar litinin suka taru a mkrnt, kamar yadda
aka bukace su.
Hedimasta ya raba masu satifiket da
Testimoniya, sannan ya sallame su, sai ranar da
jarrabawa ta fito, za'a neme su.Suna fitowa,
ana tashi tara. Naseer ya kama hannun Zarah
ya kai ta siyen kayan kwalama. Daga nan aji ya
zagaya da ita, yana ba yara kashedi da gargadin
NI duk wanda ya kuskura ya ta6a masa Zarah,
musamman zai zo mkrntr kuma kashin mutum
ya bushe, idan ya kama shi.
Shi dai Sageer bin sa kawai yake yi, yana dariya.
To wa zai ta6a ta? Bayan Naseer sunan ya gama
firamaren ne kawai, amma kodayaushe yana
can, sai ya tabbatar da Zarah ta yi break, an
koma aji, sannan ya kama gaban sa.
Idan ya ga dama ya zauna rumfar Baban sa,
idan bai yi ra'ayi ba kuma ya buga yawon sa,
musamman idan akwai wasa a filin sukuwa.
Kwalejin jeka, ka dawo ta gwamnati da ke
kufena, ita Naseer ya samu, yayin da Sageer ya
sami kwalejin Alhuda-huda.
Karatu ya kankama, hakan bai hana Naseer kula
da 'yar kanwar sa ba.
Kullum safiya a bakin kofar mkrntr su take
samun sa yana zaman jiranta, sai ya danka
mata kudin tara da dukkan abinda ya ci ya rage
mata, sannan ya wuce." Bai hada wata 3 ba,
gaba daya a mkrntr sunan sa yayi tambari, ko
dama shi ne shugaban ajin su watau (Monitor)
Tun daga Malamai har manyan da ke gaba da
shi, sun san Naseer da kokari da rashin ji.
Babu damar manyar sa su ta6a shi, ana fita
wajen mkrnt, zai tara masa duwatsu.
Suna ji suna gani Naseer ya gagare su, ba'a
dade ba, ya zama abokin kowa, suna kiran sa
HUKUMA.
Ba wanda bai san Naseer Hukuma ba, har
shugaban mkrnt (Principal). A yau da aka kawo
masa Naseer gaban sa da laifin rufewa Malamin
su kofa.Principal ya dube shi da kyau ya
ce,"Mece ce hujjar kullewa Malaminka kofa?"
Yana daga durkushe kyar! Ba alamar tsoro ya
ce,"Duk ranar da babu asanbili, karfe 7 da rabi
yake rufe mana kofa, duk wanda ya zo bayan
wannan lkc, sai dai ya zauna a waje.
Darasin English ya wuce shi kenan. Shi yasa na
gaya kowa yayi kokari yau ya zo da wuri, sai
kuma ga shi yau Malam bai zo ba, sai takwas
saura kwata, dalilin da yasa kenan na rufe kofa,
don shi ma ya makara.
Principal ya tsura masa ido, yana mamaki,"A ina
ka ta6a jin an rufe wa Malami kofa?"
Ya sosa keya ya ce,"A kufena." Nan da nan
Principal ya shaka,"Iskancin ka ya zo kaina ne?
To na lura ba ka da tarbiyya, sbd haka bayan
sajen ya hukunta ka, za ka koma gida ka huta
sati 2, idan za ka dawo kuma da Babanka."
Naseer yayi shiru, ko ajikin sa, shi nan take ma
yake tunanin zai sami isasheshen lkcn zuwa filin
Sukuwa. Yana tsaye garau!
Sajen yayi masa bulala goma masu kyau.
Aka mika masa takardar hutun cewa aji."
Ga wata sanarwa!. Zan tafi Saudiyya, sati 2 zan
yi idan Malama ya sake rufe ma ku, kofa ku aika
min da sako daga can zan sa masa (Road
block' .
Duk suka dau ihu........






Zaharaddeen Shomar
Whatsapp 08168575100






Ajininsa yake 1-02
Posted by ANaM Dorayi on 09:40 PM, 03-Nov-15
Under: Ajininsa yake
_______ NA ZULAIHAT SANI KAGARA_____________Ya
daga hannanyensa sama, ya ce,"Sai na dawo!"
Suka ce,"Hukuma!" Hukuma!!"
Ya ce,"Ko ba'a rarrashe ta ba, hakuri take don
U........in karasa?" Ihu kawai suka yi.
Shi ya jawo hankalin Malamai.
Nan take aka firfito da su waje, duk aka ce su
zube sajen yayi masu biyar-biyar.
Shi kuwa Naseer aka tasa keyar sa ana dukan su
suna ihu."
Abar mana Naseer! A bar mana Naseer!!
Karfe tara da kwata ya dawo gida, lkcn Baban sa
ya riga ya fita.
Umman sa ta ji motsin bude dakin sa da ke
zaure.
Ta leko, don ganin wa ke taba kofar, Sai ta gan
shi.
Fuska yamutse ya ce,"Koro ni aka yi."
Ta ce,"Ka biya kudin mkrnt Naseer, me zai sa a
kore ka?"
Yayi dan shiru, ka fin ya ce,"Laifi na yi Umma.
Ta tsura masa ido, ta ce,"Haka dai, kullum kai ba
ka girma Naseer, balle ka yi wa kanka fada.
Laifin me ka yi kuma?Kai tsaye ya gaya mata
abinda ya faru.
Ta kame ha6a ta ce,"Tirk'ashi! Allah ya shirye ka.
Zaman gida ka fi so ko? To ai shi ke-nan, sai ka
yi ta zama ranka na maka dad'i." Ta juya ta shiga
cikin gida abin ta. Ya tura kofa ya shige d'aki, ya
watsar da littattafansa gefe, ya kwanta ringigine
bisa 'yar katifarsa yayi shiru, can ya ja d'an tsaki
ya ce,"Komai dai ni ne mai laifi, mutum ya raina
mana wayau, sai a k'yale shi?
Mts........."
Ya ci gaba da kuncin rai, wai kullum shine mai
laifi. Da yamma Baban sa ya dawo. Mairo ta
mayar masa da abinda ya faru. Yayi shiru bai iya
cewa komai ba. Suna zaune k'ofar gidan su
Sageer, shi din ke masa fad'a.
Naseer 6ata lokacin ka ka ke yi. Wallahi ina gaya
ma wannan maganar ka na ganin ihun banza
nake, ba za ka gane kuskuren ka ba, sai nan
gaba. Shi karatu ko na k'wana d'aya ya wuce ka,
ai an cuce ka, balle na sati 2. Amma fa sai ka
yarda."
Ya ce,"Me zai faru, idan ban yarda ba? Ya
amsa,"Me kuwa?" Kawai ina gaya ma gaskiya ne."
Ya nuna shi ya ce,"To ashe kai ne babban mai
6ata lokacin sa. Ni nan da ka ke gani, ba'a raina
min wayau. Gidan su Zarah za ni, za ka?"
Ya hahare shi ya ce,"Ban zuwa.." Kar ka je, sai
me?"Yayi banza da shi.
Ya mike ya wuce abin sa.
Sageer ya bi shi da kallo, ya kad'a kai ya ce,"Ina
tausaya ma Naseer.
Allah ya shirye ka." Shi kuwa gidan Zarah ya je
suka sha hira cikin gidansu da Innar ta gab da
kira magariba, sannan ya koma gida.
**************
Washe gari da safe 7:30, kamar yadda ya saba
fitowa yana tsaye gefen titin Kongo, wanda ta
mik'a har (W.T.C). Jar T.Shirt ce a jikin sa da
wandon Jeans. Nan ya saba jiran Zarah, don bata
kud'in tara.Zuwa can ta doso, kayan makaranar
nan sun sha guga, sai d'aukan ido suke yi tamkar
yadda ita kanta Zarah ke d'aukan hankalin
jama'a, sbd tsabar kyau da kullum take kara yi.
Kayataccen murmushi suke wa juna, sai da ta zo
gab da shi, ta ce,"Yayana, ban gane ba, ina
uniform?" Ya tura hannayen sa aljihu ya ce,"Ga
su nan a jiki na."
"Wai ba za ka makarantar bane ko yaya ne?"Ya
zura mata ido yadda take motsa bakin ta, yake
burge shi,"Huta na ke yau." Ta ce,"Wasa da
karatu Yaya na?" Gaskiya ni ma zuwa na bai da
amfani, mu je gida kawai ni ma in cire." Yayi
d'an murmushi ya ce,"Ki na so in yi miki bulala
kenan? Ita ma murmushi tayi,"Ka san Allah, sai
na had'a ka da Inna. Ya sanya mata ido, ya
kasa cewa komai." Ka na ta kallo na, magana na
ke."
Ya ce,"Yau fuskar ki tayi min kama da hasken
zara, sai na tuna ashe zarar ce."
Ta dan shagwa6e fuska,"Kai yayana, maganar
makarantar na ke. Ka koma gida ka sayo
uniform, ka wuce makaranta, idan ba ha ka ba
Inna za ta ji
" Ya ce,"Don Allah ki share."
"To me ya hana ka zuwa?"
Ya ce,"Hmm......laifi na yi."
"Wane irin?"
"Ke dai zo mu je in raka ki, na gaya miki a
hanya.
Suka wuce ya na labarta mata.
Ta dube shi,"Kai yayana, saboda Allah me yasa
haka?"
Ban kyauta ba ko?"
Ya tambaya. Ta ce,"Gaskiya ba ka kyauta ba,
don wanna 6ata Record ne. Don Allah kar ka
sake.
Ya numfasa ya ce,"An gama.Kuma sai da ki ka
fad'a na gane ban kyauta d'in ba.
"Tayi 'yar dariya, yana kallonta,"Yayana, kai
kullum ba ka sanin ka yi laifi, sai na fad'i?
Amma in na ce ka gyara, sai ya gagara."
Ya dan ja ya tsaya,"Me ki ka ce in gyara, ban
gyara ba?" Ita ma ta tsaya,"Da kana gyarawa,
yaushe za'a ba ka hutun dole? Yadda yayana ke
so na, ya kamata ace komai na ce, ta zauna.
Yanzu ni ka ga babu yadda za'ayi in tsallake
maganar ka."
Yayi murmushi, suka ci gaba da tafita, yana
tad'in,"Komai ki ka ce, ba na tsallakewa, ke ce
ba kya ganewa." Ta dube shi kamar yadda yake
kallon ta, ta ce,"Na sakar ma yayana." Suka yi ta
tafiya har kusa da mkrnt, sannan ya ja birki ya
ce,"To bari in bar ki anan, amma Zarah hak'uri
za tayi, yaya bai da kud'in (Break)."
Ta shagwa6e a gaban sa,"Ni a'a.
Allah ni na saba kashe kud'in yayana."
Ya d'aga lallausan gashin girar sa, bak'i wulik!
Yana kallon ta.
'Yar dariya yake yi mata.
Ita kuwa shagwa6ar ta take,"Allah ni ma zan
koma gida!"
Ya laluba aljihu, ya ciro Naira 20 ya mik'a mata.
Ta amshe tana fad'in,"Dama tsoka na ce?
Shi kenan ni ma ba zan rage maka abinda na ci
ba."
Ya ce,"Har kin isa. Ki na son bulala kena." Ta yi
murmushi ta ce,"To na gode, sai na dawo. "Ya
ce," A dawo lafiya." Ta juya ta shiga cikin 'yan
mkrnt, tana tafe tana waigen sa, shi kuwa yana
tsaye, ya kama tafiyar ta k'ule masa.Ya sauke
numfashi, ya juya ya dawo gida. Sati 2 suka
cika. Naseer zai koma makaranta. Malam
Balarabe ya ce bai san zancan bin sa
makarantar ba. Ran Naseer ya 6aci, ga shi yana
son komawa makarantar, don kar Zarah ta ce
shine bai son zuwa. Sageer ya samu a karo na
farko ya rok'e shi, su je ya rarrashi Baban sa
yayi hak'uri, su tafi makarnta gobe tare. Abin ya
ba Sageer mamaki k'warai, kuma yayi farin cikin
jin hakan.
Saboda haka babu 6ata lokaci, suka same shi da
daddare. Sageer yayi ta rok'o a madadin
Naseer. Malam Balarabe ya ce,"Sageer ni na
haifi Naseer, amma ko alama Naseer bai san
mutuncina ba, bai san mahimanci na a gare shi
ba.
Tun da abin nan ya faru, ban iya cewa da shi
k'ala ba, sbd takaici da 6acin rai, amma Naseer
bai san ya durk'usa gaba na ya ce Baba ka yi
hak'uri akan abin da na aikata ba. Sai yanzu ne
zai ce in zo muje makaranta? Me zan ma sa?
Bayan ba ni da amfani a gun sa? Sageer ya kara
duk'awa ya ce,"Baba ka yi hakuri, ka yafe
masa." Ya ce,"Naseer yaro ne?" Shekarunsa
goma sha takwas, yayi hankalin da zai san 6acin
ran iyayensa.
Babban kuskur ne a gare shi.
Amma shi komai yayi, sai ya d'auka dai-dai ne.
In banda tsageranci, menene na rufewa Malimin
ka k'ofa, don shi yana rufe ma ku? Ashe za ka
iya rufe min gida, duk ranar da na yi dare a
waje. Ka kiyayi duniya Naseer, ranar da za ta
koya ma hankali sai ka gwammace ba ka zo
cikinta ba."
Ya k'ara sunkuyar da kai ya ce,"Ka yi hak'uri
Baba, in Allah ya yarda ba za'a sake ba."Sageer
ya ce,"Baba, ka amince goben za ka d'in?" Ya
ce,"Ya zama dole, tunda ka sa baki Sageer, don
ka fi shi hankali, da ace yana koyi da kai, ai da
ba haka ba.
Ni dai bn ma sa mugun baki ba, iyakata da shi
add'ur Allah ya shirye shi. Amma daga yau in ya
sake d'ebo rigimarsa, ko alama ba ni a ciki. Kar
ma ku dunfaro ni. Ina fatan kun ji abinda na
ce,"Sageer ya ce,"Insha Allah."
Ya ce,"Allah ya kai mu goben.
Allah yayi maku albarka." Suka amsa da "Amin-
Amin."
**************
Washe gari Malam Balarabe ya maida Naseer
makaranta. A gaban (Principal) da sauran
Malami Naseer ya d'auki alk'awarin ba zai sake
sa6awa dokar makaranta ba.
Shugaban makaranta ya ce idan ya sake korarsa
za su yi, don fitinar sa ta ishe su.
Malam Balarabe yayi ta ban hak'uri, sannan aka
sallame su. Malam Balarabe yayi gida. Naseer
yayi aji. Akwai Malami a cikin ajin, don haka a
salihin sa ya shige. Sauran d'alibai na ta
bayyanar da farin cikin su bisa fuskokin su. Bai
kula kowa ba, ya wuce mazaunin sa, ya zauna a
d'aure.
Malam na bada baya, duk suka yanyame
shi"HUKUMA! HUKUMA!!" Ya dube su ya
ce,"Yawa ku ke, kowa ya zauna, in ba ku wani
labari." Suka zauna sauraron sa.
Ya mike ya zo gaban allo ya tsaya.
"Gata nan, gata nan ku!" Suka ce,"Ta zo mu ji
ta!" Ya ce,"Da Naseer ne da Englishi Master,
wata rana sun fita farauta, sai Naseer ya kafa
Malam, ya na da A B C D.
Englishi Master zai k'wace, dambe ya kaure.
Naseer ya kada Malam, ya na da A B C D a
gwafa, ya auna masa koda ya mike, sai ya rubta
wa Naseer SUSPENSION."Gaba d'aya suka d'au
dariya da tafi har da masu fito, ya ce,"A
saurara!
Sati 2 Naseer ya dawo, amma da sabon
alk'awari." Ya kame kamar soja, hannun sa ma
dama saitin kunne sa, ya ci gaba,"Na d'auki
alkawari ga makarantar kufena. Zan zama mai
ladabi da biyayya. Zan maida hankali ga
karatuna, zan tabbatar da ci gaban ta, idan ba
haka ba, kora ce!"
Ta yadda ya aje salon kalmar k'arshe KORA ce!
Shi yasa duk suka d'auki tafi,"Yayi! Yayi!! Allah
ya bar mana HUKUMA!" Ya ce,"Hukama na
ofishin principal, sbd haka kowa ya d'auki
wannan alkawarin, kar fushinta ya kama shi." Ya
d'auki alli ya rubuta bisa allo.,"Ya ce,"Wannan
shine Nationar Anthem d'inmu.
Suna ta hayaniya. Malamin Geography na tsaye
yana kallon su, sai dai suka gan shi tsulum! Ya
karasa shigowa.Da turanci yake magana,"Meke?"
Naseer ya ce,"Ba komai." Ya aje alli, ya wuce
wajen zaman sa.
Malam ya dubi allo ya karanta abinda Naseer ya
rubuta, ya dube su da kyau ya ce,"Wa ya
rubuta wannan?"
Baba wani 6oye-6oye Naseer ya d'aga hannu.
Ya ce,"Ya mik'e tsaye.
Tsaf!
Ya tashi fuska d'aure. "Menene wannan?" Ya
k'ara kirnewa, ya ce,"Sabon alk'awari ne, New
testament ba." Dariya ta kubce masa, yayi d'an
murmushi, ya ce,"Naseer ba ka ji ko?" Ya dan
duk'a ya ce,"Allah ya shi taimaki Malam!"
Suka d'auki dariya. Malam ya ce,"K'wana 2 ba
na ganin ka, ina ka je?" Ya amsa"Saudiyya."
Ya tsira masa ido, yana kad'a kai,"Hajji ko
umrah?"Ya ce,"Umrah." An dawo lafiya? Ina
tsaraba?" Ya nuna allo ya ce,"Ga ta nan kuwa."
Malam d'aurewa yayi ya ce,"To ka share." Ya
k'ara duk'awa ya ce,"Allah shi taimaki malamin
binciken yanayi."
Ya fito yana na tafawa, ya d'auki abin share allo
ya share."Malam an share." Ya ce,"Ka ci gaba da
tsayuwa anan." Ya dubi d'alibai ya d'aga gira ya
ce,"Soja kenan a fakaice." Nan ya ci gaba da
tsayuwa har darasi ya k'are , kuma hakan bai
hana shi abinda yake so ba, duk da cewa ya san
tsayuwar ma horo ce aka ba shi.
Naseer kam sai addu'a.
**************
Sannu a hankali. Malamai da iyayen Naseer
suna hak'uri da shi. Har ga shi gobe ake sa ran
za su fara rubuta jarabawar su ta karshe watau,
(WAEC). D'in su. Da yammacin wannan lahadin
ce. Naseer ya d'auki wankan sa yayi tsaf!
Cikin gogaggen yad'in sa ruwan madara yayi
kyau sosai, dan shi Naseer akwai son gayu, ga
kuma tsafta.
Zai yi wuya ka gan shi a yamutse. Kayan sa
kuwa duk inda zai nemo guga, sai ya nemo, sbd
babu yadda za'ayi ya sanya kaya ba guga. Ya
dan goge sandal d'insa bak'i, kai tsaye ya wuce
gangare gidan su Zarah. Bai nemi Sageer ba,
saboda ya san zai yi wuya ya fita yawo, saboda
karatun jarabawa.
Yana cusa kai cikin zaure, idanuwan sa suka
nuna masa wani abinda bai ta6a jin fad'uwar
gaba ba, sai akansa. Zarah ke tad'i da wani
saurayi, wanda ita ma a yau d'in nan suka
had'u da shi.
Sarai Naseer ya san saurayin a nan layin sarki
yake, sai dai ko gaisuwa bata ta 6a had'a su
ba.Nan take kishi ya lullube shi, mahaukacin
kishi kuwa, don sai da ya ji zuciyar sa ta kulle,
ta tattaro ta dawo iya wuya. Duk da cewar bai
ta6a furtawa Zarah kalmat so ba, illa iya ka
komai take so, shima shi yake so.
Tana ganin sa,tayi sauri ta rufe fuska da
hijabinta, har ya wuce cikin gida, bata bude ba,
haka kuma babu wanda ya tanka ma wani.
kujera ya ja tsakar gida, suka gaisa da Inna,
tana tsakar alayyahu. Ya jawo faranti yana
tayata."Amma gaba d'aya hankalin sa bai jikin
sa." Lafiya Naseer?" Ya ce,"Lafiya lau Inna, me
ki ka gani?" Ta ce,"Na ji ka yi shiru ne, ko anyi
fad'an da su Umma ne?" Ya kada kai,"Babu
komai wallahi." To duk tunanin jarabawar ce?"
Ya ce,"Jarabawa ai mun gama da ita. Insha
Allahu babu abinda zai gagara."
Ta ce,"Allah shi yarda Naseer, ai ba na haufi
akan dan nawa." Ya mika mata alaiyahun da ya
tara a hannunsa, ta karfa tana yankawa.
Zarah ta yi sallama ta shigo, suna hada ido, ta
rufe fuska da hannayen ta, ta fad'a daki. Ya
ce,"Ki fito kawai, yau bulala za ki sha." Inna ta
ce,"Yakamata, haka kawai ana zaune k'alau, za
ta fara jawo mana samari, wai shi nan auran ta
zai yi, ba yaudara ya zo yi ba."
Shi d'in ya fad'i haka?"
Inna ta ce,
"Eh,
ai sai da Babanku ya fita, ya tsare shi a zauren.
Zuciya ta k'ara shak'e shi, da kyar ya
amsa,"Inna Zarah ai yarinya ce, kuma karatu za
ta yi."
Ta ce,"Ni ma shi na gani, amma Malam ya ce
tunda da gaske yake, sai ta tsaida shi, tana
gama karatun, ayu da shi, idan Allah ya
nufa.'Kyar yake kallon Inna. Zarah ce ta d'auke
masa hankali da ta

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login