Showing 6001 words to 9000 words out of 40261 words
Chapter 3 - A JININSA YAKE PDF BOOK COMPLETE Writing by Zulaihat Sani Kagara .txt
fito, tana fad'in,"Yaya na ina
wuni?" Ya maka mata harara. Tayi murmushi, ta
zauna kusa da shi,"Me na yi yayana?
Wannan harara ta bata min fuskar ka, dan yi
murmushi mana, haba Big Bros." Ya dubi Inna
fuska daure, "Kin ji yadda yarinyar nan ta raina
ni ko?" Ta ce,"Kai ka kyale ta." Ta d'auke
alayyahunta ta shige kicin. Shi
kuwa hararar Zara ya ci gaba da yi.
Ta sanyaya murya, ta ce,"Ba ka ga yadda ka yi
ba, me yasa?" Ya ce,"Karatu za ki yi, ko tara
samari?" Ta ce,"Salis ne kawai yayana, don Allah
ka yi hak'uri." Ya ce,
"Zarah! Zarah!! Zarah!!!
Ta amsa."
"Na'am."
Sau nawa na kira ki?" Ta ce,"Ina jin sau 3 ne."
Ya k'ara dubanta," Ki na ma ji ne?"
To shi ke nan." Ki saurare ni."
Ya mik'e yana fad'in."Inna na wuce!"
Ta lek'o ta ce,"To Naseer, agaida su Ummah."
Yayi waje. Zarah na bin sa."Yayana, me zan
saurara na ce?" Ya juyo cikin zaure, ya ce,"Ai ba
ki tabbatar da ko sau nawa na kira ki ba, it
means hankalinki ba a waje na yake ba. Saboda
haka ni zan yi wa tufka hanci, don hankalinki ya
tsaya waje 1."
Ya sa kai ya fice ya bar ta cikin duhu. Yana ji
tana kiran sa, amma kishin daya mak'ure masa
wuya, ya hana shi amsawa.
Bayan sallar isha'i, gidan su Sageer ya nufa. Ya
yaye labulen dakin ya shiga. Kwanon abinci
Sageer d'in, ya bude zai fara ci." Me ka ke yi?"
Ya ce,"Abinci zan ci, zo mu ci mana." Ya ce,"Don
Allah ka rufe abincin nan, ka taso ka raka ni nan
layin sarki." To ka za mu ci abinci mana!"
Kar in rasa wanda zan je nema ne.
Don Allah ta so mu je." Sageer ya rufe abinci, ya
sanyo takalaman sa, ya rufe dakin sa, suka
wuce layin sarki, ba tare da ya san me za su je
yi ba.Kawai Naseer ya ce,"Wani zan je gani."
Suna zauna da abokan sa 2, labarin yarinya
Zarah yake ba su, lokacin da Naseer suka iso
tare da sallamar har da Musabaha, kamar abin
arziki. Naseer ya dube shi ya ce,"Ah! Kai ne
Salees ko?"
Ya ce,"Eh ni ne, lafiya?" Ya ce,"Ita ta kawo
hakan. Na san ba sanni ba, amma watak'ila da,
da rana na zo, da ka gane ni. Well kar mu je da
nisa, kawai gargadin ka na zo yi akan yarinyar
nan Zarah. Ban som in k'ara ganin 'yar k'afan
ka a gidan su. In kunne ya ji........"
Ya juya zai wuce. Salis ya dafo k'afarsa ya
ce,"Dakata mana. Kalle ni, idan ka na takama
kai dan Tudun wada ne, ni ma kazalika haifaffen
Tudun Wada ne, saboda haka karan daji bai isa
ya budewa karan gida ido ba."
Naseer yayi dan murmushi ya ce,"Allah ko?" To
lulaba da kyau ka ji, wannan ba kare ba ne,
kura ce, don uban kare karyar sa."
Sageer ya rik'o shi yana fad'in." Naseer! Dama
rakiyar da ka ce in zo yi kenan, Meye haka?"
Abokan Salis ma suka taso." Me ye haka ku ke
yi? Don Allah ku bari, yawa ne. Zaarah sai
wanda ta za6a, sbd ha..........."
Wani wawan mari Naseer ya tsinkawa, mai
maganar. Shi yasa yayi gum da bak'in sa. Salis
na ganin haka, shi ma ya ware. Sageer ya kamo
Naseer ya ce,"Naseer, kada ka kuskara ka dauko
wannan fitinar! Ka ga k'ofar gidansu ka zo, duk
inda aka je, kai ne mai laifi!
Ya ce,"Da shi na ke magana, daya sanya min
baki?" Yana rufe da baki, ya ji saukan naushi.
Cikin zafin nama Naseer yayi kukan kura, ji ka
ke yi dim! Ya sakarwa Salis naushi a mukamuki.
Nan take kamar almara. Salis ya fad'i a sume.
Abokan Salis suka rude. Sageer ma ya firgice, ya
rinka jan Naseer, yana fad'in,"Ka gani ko?" Ka
ga irin ta ko?"
Su kuwa abokan Salis cikin gida suka shige,
neman taimakon jama'a."Ka zo mu tafi Naseer!"
Yana jan sa, yana tirjewa,,"Babu inda za ni!" Ka
kyale ni. Duk abinda suka ga dama su yi!"
Ya ce,"Haba Naseer! Me yasa kai zuciyarka bata
kulla maka alkhairi ne? Dubi fa abinda ka aikta?
Ka na zaton iyayensa za su kyale ka ne? Wallahi
da na san abinda za ka zo ka yi aikata kenan.
Sam da ban biyo ka ba, ba za ka ja min masifa
ba wallahi! Ya dube shi da kyau, ya ce,"Sageer!
Bi tannan, in bi ta can, idan ka kuskura muka
had'u, sai na fasa maka baki!
Yana sa aya ya wuce, ya bi ta inda ya nuna,
suna jin abokan Salis na fad'in Ga shi can zai
gudu!
Sageer ya shafa a guje, ya tsere. Shi kuwa
Naseer ja ya yi, ya tsaya har gayyar jama'ar
suka zo gunsa.Me yayi maka, za ka kashe shi?"
Ya ce,"Ku zuba masa ruwa, ya farfad'o, sai yaga
maku."
Samari suka yi caa! Za su rufe shi da duka,
mahaifin Salis ya hana, don tuni ya tura daya
daga cikin abokan Salis din ofishin 'Yan sanda.
Ana ta kwaranniya, ga Salis a kwance shame-
shame. "Yan sanda 2 suka iso, nan take suka
wuce da Naseer da laifin yunk'urin kisan Kai,
kamar yadda aka shaida ma su. Salis dai sai da
ya hau gadon asibiti a daren nan, sannan ya
farfado.
Wuyan sa a kage, bai iya juyawa ta gefen da
Naseer ya naushe shi.
Kai tsaye gidan su Naseer, Sageer ya nufa. Yana
ta hak'i, kamar ran sa zai fita.
Malam Balarabe da Mairo, suka firgice.
"Menene Sageer?" Ya ce,"Ba lafiya Baba, ina
zaune Naseer ya ce in zo in raka shi layin sarki.
Ashe fad'a za shi yi. Wallahi Baba ban sani ba, a
takaice dai ya naushe masu yaro ya fad'i, suma
yayi mutuwa yayi? Allah kad'ai ya sani, ya zo
ma mu gudu, ya ki. Can na baro shi, ban san
halin da ake ciki ba!"
Mairo salati da d'auka, shi kuwa Malam
Balarabe cewa yayi,"To ba shi kenan ba, ka
koma gida abinka, ka yi kwanciyar ka.
Tsuntsun daya ja ruwa, shi ruwa zai yi wa
banzan duka.
Idan sun so ma, kar su bar shi da rai, babu
abinda zai dame ni."
"Baba...." Ya katse shi,"Babu ruwanka na ce! Ka
wuce gida abin ka, idan kuma kai ma can d'in
za ka sake komawa, to Bismillah!
Amma ni Balarabe ba ni a cikin wannan
maganar." Tuni Umma ke tsiyayar
hawaye,"Sageer mu je, ina ne, suke fad'an?" Ya
ce," A layin sarki ne." Malam ya ce,"K'ofar zaure
ban ba ki izinin takawa ba.
Yauwa." Ya sa kai, ya koma d'aki. Umma ta
koma bisa tabarma, ta tallabe kai ta
ce,"Wannan yaro, wannan yaro. Allah ka shirye
shi.Sageer ya tsuganna ya ce,"Umma ki yi
hak'uri, ki daina zubda masa hawaye." Ta dube
shi cike da damuwa ta ce,"Bari fad'i Sageer, ya
zama dole in yi hawaye, don bansan masifar da
Naseer ya jaji6o mana ba wannan karon. Me ya
had'a su da yaro?" Ya ce,"Ni ban san
takamaiman zancen ba, amma na ji wai yana
masa gargad'i akan Zarah."
Ta ce,"Zarah? To shi me ya dame shi da
saurayin Zarah? Auranta zai yi?"
Ya amsa,"Bai ta6a yi min magana a kanta ba,
sai dai bn san abinda ke cikin ran sa ba a game
da ita." Ta sauke numfashi ta ce,"Dubi wannan
abin kunya, akan budurwa, ya je yana haukan
banza, idan ya kashe d'an mutane, ya yake son
mu yi da ran mu? Yanzu kai Sageer ka yi
hak'uri, ka koma ka bincika mana halin da ake
ciki ka ji?"
Ya ce,"Ya zama dole Umma, bari in tafi. Allah
shi kyauta."
Ta ce,"Aamin."
Ya mike ya fice.
Nan ta ci gaba da zama a kunci, tana mai
tsananin al'ajabin halayen Naseer, kamar ba su
suka haife shi ba, don ko 1 bauko halayyar su
ba. Ta nisa face,"Kuda, ya haifi zuma.
Allah ka shirya mana!
Tsaye Sageer yake a cikin jama'ar da suka taru,
suna ta maida labarin fad'an da aka yi karya da
gaskiya.
A nan yake jin Naseer na hannun "Yan sanda a
anan caji ofis da ke kusa da su.
Jikinsa na rawa, ya bazama ofishin. Cike yake
daga waje, daga ciki kuwa abokan Salis suke ta
bada bayanan yadda abin da ya faru
(Statement).
Shi kuwa Naseer yana tu6e, a bayan kanta. Yana
isowa, mai magana lkcn ya ce,"Yauwa ga shi
nan, tare suka zo, amma shi raba su yake yi,
yana ta jan sa, ya k'i tafiya.Sai da ya sumar da
shi." Dan sanda ya ce, wa Sageer shi ma ya
fad'in abinda ya sani.
Tiryan-tiryan ya maida wancan, dan sanda ya
ce, ya dubi mahaifin Salis ya ce,"Duk mun ji
bayanin kowa, kuma hakan ya tabbatar mana
Naseer na da laifi dumu-dumu, saboda haka za
mu tsare shi a
a nan a bisa laifin tada husuma, har zuwa lkcn
da Salis zai sami sauki.
Sajent!"ya amsa,"Sir!" A wuce da Naseer cikin
Cell."Sageer ya d'ora hannu a ka yana
fad'in,"Inna-lillahi-"Wa-Inna-ilaihir raji'un!"
Insfesta ka yi hkr, ka ba ni shi beli. Gobe za mu
fara (Exams), ka ga za ta wuce shi."
Dan sanda ya gyara fuska, ya ce,"Ya san da
jarabawar, ya je neman fad'a? Bata dame shi
bane, da ta dame shi, karatu yakamata ya
zauna yayi, ba fad'a akan budurwa ba. Saboda
haka babu, har sai Salis ya bar asibiti. Kuma
gaba d'aya abinda aka kashe a asibitin, za'a
kawo (Bill) nan, shine zai biya. Na gama da ku."
Sageer ya na ji, yana gani, aka wuce da Naseer
ko gezau bai nuna a fuskar sa ba.
Har goma da rabi na dare. Sageer na aikin
rok'on a ba shi Naseer akan beli, amma dan
sandan nan ya k'i, anan iyayen Salis suka bar
shi, kuma da gani akwai wata 'yar muna-muna
tsakanin insfesta da iyayen Salis.Sha d'ayan
dare, ya bar wajen ya koma gidan su Naseer,
har sun kulle k'ofar gida, ya buga. Malam
Balarabe ya bud'e, ya shigo ya kwashe kaf!
Halin da ake ciki ya fad'i. Malam ya balbale shi
da fad'a,"Me yasa ka ke wahalar da kanka akan
wanda bai san ciwon kan sa ba? Shin ba cewa
nayi ka tafi gida abinka ba? Yanzu k'arfe nawa
ne?" 11 ta wuce, kai ma so ka ke ka 6ata wa
naka iyayen rai ko?
Ya karkad'a kai."To maza ka wuce gida, da safe
kuma ka shirya ka tafi jarabawar ka, kar ka
saurare shi!
Maza sai da safe."
Ya juya ya tafi, ran sa in yayi dubu toh ya 6aci.
Abu 1 yake wa Naseer bak'in ciki, gobe ba zai
samu zana jarabawa ba.
Washe gari karfe 7:30 Zarah ke k'arasowa bakin
titi, sai dai yau babu yayanta a wajen, kamar
yadda kullum safiya shine mutum na 3 da ke
faranta mata rai, daga iyayenta, sai shi.
Don haka ta tsaya shiru cike da mamakin me ya
hana yayanta zuwa yau? Ta kusan minti 5r a
tsaye, sannan ta wuce jikinta duk ya mutu.
Kuma ko alama zuciyarta bata cikin sukuni har
na rashin ganin Salis jiya da daddare, kamar
yadda yayi mata alk'awari.
Ta fe take tana zancan zucci fad'i take,"Ina ka
ke yayana?" Zarah." Ta ji an k'wala mata kira.
Ta waiga gefen da aka kirata, firgici. Bak'in get
din ofishin "Yan sanda ta hango Sageer tsaye da
kayan makaranta.
Da sauri ta tsallako. Hankali tashe, ta
tambaya,"Ina yayana ne?" Ban gan shi ba yau."
Cike da damuwa ya amsa,"Ai yayan nan naki,
sai a hankali.
Yana nan ciki."
Ta k'ara ware ido ta-ce,"Ban gane yana nan
ba?"
(Police Station)Na ga ka nuna!
Ya ce,"Eh mana.." Hankalinta ya k'ara tashi,"Wa
ya kawomin shi?" Bata jira ya bata amsa ba, ta
wuce, ya biyo ta, yana fad'in,"Wallahi tsautsayi
kawai, jiya ya je wajen wani wai shi Salis, suka
fara gardama akan ki, sai fad'a. Kin san halin
yayan naki, k'ashi daya ke gare shi, yana dukan
sa, ya fad'i a sume."
Tun da yake magana, ta rage sauri. Yana sa
aya, ta juyo ido cike da kwalla ta ce,"Shi da Salis
suka yi dambe? To saboda me?"
"Oho!
Amma a kan ki ne Zarah. Naseer bai son Salis
na zuwa gun ki, gargad'in da na ji yana masa
kenan.
Abin ya kai su ga dambe."
Ta tsura masa idanuwanta da suka cika tam!
Da hawaye, ta ce," Za'a bar ni in gan shi?"
Ya amsa,"Ban sani ba. Ni ma yanzu na kawo
masa abinci, mu je mu gani.
Suka shige cike, da k'yar aka sake yarda su gan
shi,don bai jima da komawa ba. Ana fito da shi,
suka yi ido 4 da Zarah, sai ya juya, ya koma ciki
da saurinsa. Kamar za ta burma ciki, ta bi shi,
kira take,"Yayana! Yayana ka zo mana, in gan
ka!" Dan sanda ya ce,"Yan mata, ihunki fa yayi
yawa wajen nan. Hala saboda ke aka yi fad'an?"
Bata iya cewa da shi komai ba. Sageer ke jawo
ta waje. Zarah, ki yi hak'uri ki tafi makaranta, ni
ma yanzu zan wuce."Insha Allahu na san zuwa
anjima, za'a bada belinsa.
Yi hak'uri."
Tayi tsaye tana share k'walla." Zo mu je." Suka
fito bakin titi. Sageer ya tare mai mashin, ya
yana fad'in,"Ki wuce Zarah, kin ga lokaci yana
kurewa." Ta ce,"Zan ta fi." Mai mashin ya ja,
suka tafi. Yana waigen ta, yana nuna mata
alama da hannu ta wuce, har suka yi nisa.
Tsaye kawai take kikam! Ta rasa na yi.
Tunanin ta, me ya kai Naseer fad'a da Salis?Nan
take ta samo amsar. Wani ni'imamman farin ciki
ya lallube ta.
In banda abin yayana, ai sai ya gaya min kai
tsaye, menene na fad'a da Salis? K'walla suka
cika idanuwanta, tana kallon ofinshin "Yan
sanda,"Ba zan iya zama cikin aji ba, kai kuma ka
na tsare a nan yayana. Ta goge kwalla ta
kwashe sauri sauri sai gida.
Babu ko sallama, ta fito dakin. "Ke! Lafiya?"
Innar ta, ta tambaya, kuka ta fasa,"Inna 'Yan
sanda sun kama yayana! Ta dafe kirji a firgice ta
ce,"Me yayi?" Bakinta na rawa, ta mayar da
abinda ya faru. Inna ta d'auki salati, kan ta ya
d'aure"To ki yi shiru, bari Baban ki ya fito
wanka. Kai yara babu hankali, koma dai menene
cikin zuciyarsa, ai sai yayi hakuri, menene abin
fad'a?."
Shigowar Malam Umar yasa tayi shiru,."Me ya
faru? Inna ta amsa,"Naseer ke hannu 'Yan
sanda. Wai jiya sun yi fad'a da yaron nan daya
zo gun Zarah jiya, har sumar da shi." Ya ce,"To
saboda me?"
"Oho!"
Yayi dan tsaki ya ce,"Yara ba sa jin magana,
menene abin fada anan? Ko shi ma sonki yake
yi?"
Ta sunkuyar da kai ta ce,"Nima ban sani ba."ya
ja tsaki. Inna ta ce,"Idan ma sonta yake, me zai
kai shi, fada in banda abin Naseer. Shi ma ya
san babu yadda za'ayi mu hana shi, mu ba Salis
in har ya furta.
Allah shi kyauta.
Yanzu yaya za'ayi Malam?" Ya ce,"Bari in shirya,
in je in ga Baban na sa, sai a san abin yi.
Ke kuma ga shi kin makara.
Ki bata sauran 20 din nan, maza ta je ta hau
mashin ya kai ta.
Ya fice daga dakin. Inna ta dauko 20 din ta
bata,"Tana bayan mashin hankalin ta na ofishin
'Yan sanda.
Haka suka wuce tana kallon wajen har suka
k'ule.
Malam Umar ke wa su Malam Balarabe sallama
a k'ofar gida. Tare da Mallam Lawal mahaifin
Sageer.
Bayan sun yi Musabaha, sun gaisa sai ya
ce,"Magana na ji babu dadi, shine bari in zo in ji
yadda aka yi?"
Malam Lawal ya ce,"Zaman nan da ka ganmu
nan, rarrashi kawai na ke yi.
Malam Balarabe ya ce babu ruwan sa a ciki.
Sannan baban tashin hankali, na je ofishin, don
in yi belin sa." Yan sandan, suke gaya min
iyayen wancan yaron, sun ce kara za su kai
kotu, wai da wuk'a ya zo, yana neman kashe
shi."
Da wuk'a?
Ya ce,"Sharri ne kawai, don Sageer ya gaya min
tare suka je, kuma babu komai a hannu Naseer.
Dukan sa kawai yayi, ya suma. Shi kuwa Naseer
tun yana yaro haka Allah yayi shi da karfin
tsiya.
Malam Umar ya kada kai cike da damuwa,
"Wannan al'amarin bai yi dadi ba. Su kuma bai
kamata su yi haka ba. Menene amfanin yin
sharrin?" Malam Balarabe ya amshe,"Laifin su
ku ka gani? Karan banin da ya kai shi,ya ta6a
masu yaro. Shi zai fidda shi. Saboda haka kar ku
wahalar da kan ku, ku kyale shi, su koya masa
hankali."
Malam Umar ya ce,"Ba kuwa za'a kyale shi ba."
To wallahi babu hannuna acikin, kun ji kuma na
rantse.." Ya ce,"Shi kenan Malam Balabare,
amma ina tabbatar maka, bai kamata ka yi
saurin rantsuwa ba. Tunda abin ya zama haka,
mu sai mu je ko?
Ya fad'i yana kallon Malam Lawal, duk dacewar
ba su taba sanin juna ba, sai yau.
Ya ce,"Taso kawai mu tafi." Rai 6ace suka bar
wajen, tamkar yadda ran Malam Balarabe ke
bace.
Ya jima a zaune, yana tunani da tambayar kan
san "Yaushe Naseer zai daina bata min rai?"Ya
ce,"Taso kawai mu tafi." Rai bace suka bar
wajen tamkar yadda ran Malam Balarabe ke
bace. Ya jima a zaune, yana tunani da tambayar
kan san."Yaushe Naseer zai daina bata min rai?"
Ya kada kai ya ce,"Allah ka shirya min." Ya
mike, ya shiga gida, ya mayar wa Umma zancan
kai Naseer kotu inji iyayen Salis.
Idanuwanta suka kada, cike da tashin hankali ta
ce,"Wannan sharri ne, na san Naseer bai jin
magana, amma bai ta6a daukan makami ya hari
wani da shi ba.
Gaskiya Malam bai kamata ka tsame hannunka
daga maganar ba."
A fusace ya ce,"To ai sai ki dauka ki maida min.
Ya ja tsaki, ya bar gidan, ya wuce kasuwa. Ya
bar Mairon, kamar ta aza hannu bisa kai tayi
kuka.
Duk iya kokarin da su Malam Umar suka yi, don
ganin su kwantar wa iyayen Salis hankali, don
su janye kudirin su, sam sun ki sauraron su, shi
mahaifin sa ma ya ki yarda su gan shi ido da
ido.
Abokan Salis din ke gaya masu, an ma riga an
shigar da kara.
Takarda kawai suke jira a aiko ofishin 'Yan
sanda...........
Zaharaddeen Shomar
Whatsapp
08168575100
Ajininsa yake 1-03
Posted by ANaM Dorayi on 11:44 AM, 04-Nov-15
Under: Ajininsa yake
___ NA ZULAIHAT SANI KAGARA___________
Al'amarin bai masu dadi ba ko alama.
Karfe 11:30 duk suka koma gida. Inna na zaune,
duk tunani ya addabe ta.
Malam Umar ya shigo. Yadda ta lura ran sa a
6ace yake, yasa nan da nan ta gane ba ayi
nasara ba.
Hannu ta a kunci, ta ce,"Ya dai Malam?"
Ya jinjina kai ya ce,"Ai komai ya kwa6e A'i.
Iyayen Salis sun kai shi kotu."
Kotu?"
Me yayi zafi? Shi Salis din rauni yayi sosai?"
Ya ce,"Ko alama, duk da dai ban gan shi ba,
amma an ce ya bar asibitin.
Abin ma dasharri ya zama, wai dawuka ya je
kashe shi......."
Da sauri ta katse shi,"Wannan karya ne. Naseer
bai daukan makami, bar shi dai da saurin duka
ga karfi." Ya ce,"Babban abin tashin hankali ma,
shi Malam Balarabe ya ce, ba ruwan sa ciki.
Saboda haka al'amarin sai addu'a
. Mu jirar ranar da za'a shiga kotu.
Ni takaici na yaron nan jarabawa suke yi.
Mts!"
Yayi tsaki, ya kardada kai.Ta ce,"To yaya zai yi?
Ba dole yayi hkr ba. An san abin akwai 6acin rai.
Allah shi kyauta."
2:15 Zarah ta shigo gida a dokan ce, duk a zaton
za ta ji an ce yayanta ya baro ofishin 'Yan sanda,
sai ma ta ji wani labari sabo. Ta ha de kai da
guiwa, hawaye na ambaliya.Inna ta ce,"Hak'uri
za ki yi Zarah, haka Allah yaso, fatan mu kawai
Allah ya takaita abin. Tashi ki zubo abinci ki ci."
Ta girgiza kai,"Ba zan iya ba Inna. Ya za'ayi wa
yayana sharri, wanna ai zalunci ne."
To ya za'ayi? Tun da ya riga ya bi shi, har gidan
su ya ta6a shi, ai bai da mafita, sai dai Allah.
Allah ya isa.
Wallahi!
Kuma Salis din zai zo ya same ni!"
Ta tashi fu......... ta wuce.
Daki ta nufa ta kifa bisa gado, tana murzar ido
hawayenta bai yanke ba.
***************
Bayan sallar La'asar. Inna ta gama shirinta tsaf!
Ta tsaya kan Zarah da ke zaune bisa sallaya,
tunda ta idar da sallar, "Tunda nayi-nayi da ki
tashi ki tafi Islamiyya, kin ki motsi, ni zan tafi
layin Labadiya in yi wa Umman Naseer jaje. Sai ki
kula da gidan, ga miya can na dora, idan kuma
kin ga dama abincin na ki yana nan a kicin din."
Ta sa kai ta fice, ba tare da Zarah ta ce, wani
abu ba. Minti 10 bayan tafiyar Inna sai yaro yayi
sallama, ya shigo ya ce ana kiran Zarah inji