Showing 15001 words to 18000 words out of 40261 words

Chapter 6 - A JININSA YAKE PDF BOOK COMPLETE Writing by Zulaihat Sani Kagara .txt

sai ki yi masa
fad'a ya rink'a danne kishi." Ta karkad'e kai. Duk
suka fara dariya,"Kin goye bayan sa kenan?" To
babu ruwa na, kinfi kowa sanin halin yayan ki."Ta
ce,"Akwai k'arya k'ashin wuya ko? Ai ya bada
darasi, ka ga babu mai sake kwatantawa.
Suna ta k'yalk'ya dariya. Naseer kamar ya lashe
ta, sai lkcn ya fara magana, "Kinyi min dai-dai
my sister, jarumta adon namiji, kuma ai kishi
halas ne, duk wanda ya shige maka hanci, ka
daddage ka fyato shi, har sai ya balle k'ashin
wuya. Idan ya suma, ya farfad'o ya gane
kuskuren sa ko tawan?" K'ara aje kai tayi k'asa
tana murmushi.
Sageer ya ce,
"Ok,
irin na ku tsarin kenan?
Lallai jiki magayi, gara shi da ke mai kukan tsiya."
Wasa na ke Sageer,ai yayana yayi min babban
laifi.
Shekaru nawa mu ke tare da shi? Koma dai
menene, sai ya gaya min, ba wai ya je ya jawo
mana tashin hankali ba. Babu wanda ran sa bai
6aci ba akan abinda ka aikata.........."
Ta d'an dube shi a raunane ta ci gaba,"Don
girman Allah yayana ka rink'a gudun abinda zai
rik'a 6ata wasu Abba rai."
Gaba d'ayan jikin Naseer yayi sanyi, ta jefa shi
cikin damuwa.
Yayi d'an shiru kafin ya numfasa."
Ya ce,"Na ji Zarah.
Insha Allahu ba za'a k'ara ba. Kuma na rok'i su
Abba sun ce komai ya wuce.
Ina fatan ke ma za ki min afuwa, ki d'auka cewa
kishin ki ne yayi min yawa har idanuwa na suka
rufe ruf!
Ba na ganin kowa a gaba na, balle ya gaya min in
ji. Ki yi hak'uri, kin ji?"
Ta d'an rausaya kai tana murmushi,"Ya wuce,"Sai
harkar soyayya ko?"
Kunya ya bata sosai, ta rasa madafa. Sageer ya
ce,"To in d'an jira daga zaure ne? Yadda ka so."
In ji Naseer ya sanya hannu cikin tiran da ke cike
da wake ya shiga taya ta. Ta ce,"Yimin
wulank'anci, don na rako ka."
Zarah ta amshe,"Kyale shi Sageer, yi zaman ka ai
kai yayana ne."Maigida na ke, komai sai da izini
na." Ta ce,"Haka ka ke gani, amma ni na san
sabon yayana ya fi power, don haka ka bi shi a
hankali.
Ya dubi Sageer ya ce,"Allah ko? To sannu yaya
ina yini?" Sageer dokar masa kafad'a, suka ci
gaba da hira cikin farin ciki.Daran wannan ranar
Naseer bai iya barci ba. Ba waai k'aunar Zarah
ke masa tuk'uk'i ba, don wannan ta dad'e masa
cikin zuciya. Ammamaganar da ta zame masa
sabuwa, ta kuma hana shi sukuni, ita ce maganar
da kowa yake masa, watau ya rink'a gudun
abinda zai rink'a 6ata wa iyayensa rai. Ko Inna
da ta dawo, ta same su a gidan. Sai da ta fad'i
wannan maganar sbd haka abin yayi matuk'ar
tsaya masa a rai.
Kuma ya rasa mafita, domin shi a ganinsa bai
aikata komai ba, don ran su Abba ya 6aci, akan
gaskiyar sa yake kuma ko a yanzu ba don kotu ta
shiga tsakanin sa da Salis ba, da Salis ya gane
shayi ruwa ne, madara ake zuba masa yayi kauri.
Duk da cewar Baban Zarah ya share masa
hawaye kuma ya hana Salis zuwa wajenta.
Wannan ba zai hana shi k'wato hak'k'in sa ba.
Amma magana ta kau, tunda kotu na tsakani.
Ya juya rigingine, ya numfasa,
"Mece ce mafita a waje na ni Naseer?
Na san ba ni da hak'uri, amma ai sai anyi min na
ke ramawa. Sai kuma a rink'a ganin laifi na." Ya
ja tsaki, ya kada kai mai cike da takaici. Har aka
kira assalatu idonsa 2, ya fito yayi alwala, suka
fita masallaci da Abba.
Bayan cin abincin safe, ya fito k'ofar gida yayi
shiru a tsaye, kusan layin yayi tsit! Saboda duk
wani yaro daya isa zuwa makaranta, ya riga ya
tafi. Duk kadaici ya dame shi, ga yawan tunani,
don haka ya kulle d'akin sa yayi wa filin sukuwa
tsinke. Mutane 2 kawai ke cikin filin, can nesa da
shi suna wasan kwallon Golf. Wata kujera mai
zaman din-din-din ita ya samu ya zauna.
Maganganu barkatai suka yi ta zuwa, suna
wucewa cikin zuciyar sa, musamman wacce ta
hanashi barci jiya.
Rana ta fara yin zafi, ya zamana filin babu kowa
cikin sa, sai Naseer da ke jingine da kujera ya
d'aga fuska sama idauwan sa gaba 1 na rufe,
kawai damuwa ta sanya shi kasancewa cikin
wannan yanayin tsawon lkc, kafin ya fara tsinkar
karar kofatan doki.
A natse ya bude idanuwan sa. Ya juya ya dubi
gefen da yake jin tafiyar dokin. Wani matashi ya
hanga, ya sakar wa doki linzami, in ba ka yi, ba
ni wuri, sukuwa yake yi, babu kama hannun
yaro. Naseer ya saki ido, kaf hankalinsa ya koma
ga mai sukuwa. Nan take damuwar sa ta kau
daga zuciyar sa.
Mai dokin nan shi kad'ai yake atisayen sa.
Sai Naseer da ke masa kallon kauna da
sha'awa."Zagaye karo na 3 kenan zai yi wa filin,
wanna karon k'ure dokinsa matuk'a, babu 6ata
lkc, doki yayi ta haniniya ya d'aga shi sama, yayi
watsi da shi tamkar yadda aka shek'e dussa a
matankad'i. A guje Naseer ya mik'e ya nufi inda
matashin ke kwance shame-shame a sume. Ashe
ba Naseer kad'ai ya ga wannan tashin hankali ba,
har da wasu masu ababen hawa da ke tafiya
bisa titi.
Kasancewar filin yana gefen hanya ne.
Nan da nan suka kawo masa d'auki, inda tuni
Naseer ya fara ceto ran sa, ta hanyar rage masa
wasu kayayyakin da ke jikinsa, kamar su hular
kwanon da ke kan sa da sauran su.
Daga nan aka shiga neman ko za'a samu wata
sheda a jikinsa, wacce za ta bayyana ko shi
wanene da insa ya fito.
Cikin aljihun sa Naseer ya zak'ulo wayar
hannunsa, don haka ya fara neman wace lamba
zai kira.
A dalilin bai san kan wayar ba, dannawa na farko
da yayi, sai ga sunan Yakubu Jah-Jah ya baiyana
watau(Dillied numbers) ya shiga, ma'ana Yakubu
Jah-Jah, shine na k'arshen wanda matashin ya
kira a wayar sa.
Kai tsaye Naseer ya kira lambar. Babu jimawa
kuwa ya d'auka,"Hello bros, ka same ni a gida
kawai!"
Naseer ya ce,"Bai mai wayar bane, dama mu na
son mu shaida maka ne, ya fad'o daga doki,
kuma yana cikin wani hali sbd haka ka hanzarta
zuwa nan filin sukuwa."
Cikin tashin hankali Jah-Jah ya
amsa,"Subhanallah!
Ga-ni nan zuwa Insha-Allahu!
"Naseer ya dubi sauran jama'a, ya ce,"Na sami
wani ya-ce yana zuwa yanzu, ina jin d'an-uwan
sa ne." Yana rufe baki,wanda ya ruga neman
ruwa, ya dawo da ledar (purewater), aka bud'a
ana ta fesa masa.
Amma har ya k'are saurayin bai farfad'o ba.
Suna nan jugun-jugun!
Cike da tausayin saurayin."
'Yan-uwan sa suka iso cikin wata mota k'irar
(Honda Civic), nan da nan suka sa shi a mota,
d'aya daga cikin s ya hau dokin yayi gaba da shi,
jama'a kowa ya kama gaban sa, amma shi
Naseer yana tare da su Jah-Jah da shi suka iso
(Zaria Clinic) kuma da shi aka yi ta kai kawo har
majiyacin ya sami natsuwa bisa gadon asibiti.
Likita na duba shi.Yayi matuk'ar auna arziki, don
babu karaya a jikinsa, sai 'yan raunuka da rashin
farfad'owar sa. Sun d'an natsu hankalinsu kowa
ya bar wa Allah al'amarin sa. Naseer ya matso
kusa da Jah-Jah ya mik'o masa waya da wasu
kudad'e kusan dubu hudu da d'ari biyar, ya
ce,"Ga kayayyakin sa, ni na aje sbd sha'anin
mutane, wani da zuciya 2 ya kan zo taimako."
Yakubu yasa hannu, ya amsa tare da duban
Naseer,"Gaskiya ne, kuma mun gode Allah ya
saka da alkhairi. Ya sunan Malamin ne?"
Ya ce,"Naseer suna na."
Fuska cike da fara'a ya ce,
"Ah!
Ashe takwarar maras lafiya ne. Shi ma sunan sa
kenan, kuma k'ani na ne, uwa d'aya uba d'aya."
Ikon Allah, to Allah ya ba shi lafiya, ni zan
k'arasa gida." Ya amsa da amin.
Ya mik'a masa hannu, suka yi sallama. Sannan
yayi sallama da kowa har da iyayen su Yakubun
da ke wajen, ya tafi. Cike yake da al'ajabi tare da
tausayin takwaran na sa.
A lokaci 1 yana jin dad'in had'uwarsa da
mutumin da yake burge shi a duniya, sbd wasan
tseren polo, watau Yakubu Jah-Jah. Tuni ya
mance da damuwar da ke ran sa, ya tsunduma
tunanin yadda zai yi ya k'ulla zumunci da su
Yakubu.
Don shi ma ya sa mu ya kutsa cikin wasan polo,
wanda ya jima cikin mafarkinsa. Yana tafe, yana
addu'a Allah ya cika masa burin sa, idan akwai
alkhairi, babu wanda bai ji lbrn abubuwan da
suka wakana ba, iyayen sa, Sageer tare da Huril-
aininsa Zarah. Haka yake kiranta(Huril-aini),
watau sanyi idaniya.
**************
Da yamma bayan sallar la'asar can ya nufa, ya
tarar da takwaran nasa ya farfad'o, kuma
Alhamdulillah, ya d'an murmure, yana amsa
gaisuwa sosai. Yana isa. Yakubu ya gabatar da
shi ga k'aninsa, domin tuni yake da lbrn irin
gudumuwar da Naseer ya bayar. A nan ya kai
magarib, suna ta hira da Yakubu Jah-Jah.
Washe garei k'arfe 10, ya isa asibitin, bai iske
kowa ba, sai takwaran sa Naseer. Bayan sun
gaisa, ya tambaye shi jikin sa. Ya ce,"Ah jikin an
gode Allah." Zauna mana." Ya ja kujera ya zauna,
yana fad'in"Kai kad'ai ne? Ina yayan na mu?" Ya
ce,"Ka san shi ya kwana, so ya koma gida, ya
d'an huta, sai Mama, ta d'an zaga ne."
Ya ce,
"Ok.Sun d'an yi shiru, na 'yan dak'ik'a kafin
Naseer da ke jingine da filo ya ce,"Ai na ji sauki,
ni yau ma na so a sallame ni, amma yaya ya
hana, wai in dai bari zuwa gobe a tabbatar da
komai Normal." D'an murmushi yayi,"Gaskiya ne,
gara dai ka d'an kwana biyun." Ya ce,"Wallahi
sam na rasa dalilin da yasa hawan doki bai
amshe ni ba, fad'owa ta ta 3 kenan fa."
"Ah!
Haba dai? To saboda me?"
"Oho!
Ni abin ma har ya fita min a rai ko dama yaya ke
matsa min, wai yana son na gaje shi. Ni ina zan
kai wannan wahalar?" Naseer ya kad'a kai cike da
fara'a, "Ni kuma ka san wani abu! Bala'in son
hawan dokin nan na ke yi. Tun ban da wayau na
ke zuwa kallon sukuwa, ai na sha yin hannu da
yayan na mu, ba dai zai gane bane." Ya ce,"Ka ce
za ka zama mutumin yaya sosai, domin shi ido
rufe yake neman masu sha'awar wasan polo."
Zuciyar Naseer tayi fes!
D'oki ya mamaye zuciyar sa.
Ina yanzu Yakubu zai zo ya ce su tafi fili, ya koya
masa sukuwa? Bai gama tunanin sa ba.
Maman ta fito bayi.
Naseer ya tsugunna ya gaida ta, ta amsa tana
mai jin dad'i a ran ta. Kuma kwarai take yaba
Naseer cikin zuciyar ta, tun jiya da ta fara ganin
sa. Wannan
A JININ SA YAKE!
Farin jini ga kowa, duk inda ya kutsa. Allah yayi
wa Naseer wannan kwarjinin. Da ita suka ci gaba
da hira, babu zato sai kiran sallar azahar suka ji.
"Wai har k'arfe 1 ta yi.,"Naseer ya duba
agogonsa, ya fad'a. Ta ce,"Ai babu wai a ciki.
Lokacin ne ya gangaro irin na k'arshen zamani
komai a gurguje, shi yasa kafin D'an-Adam ya
farga, ya cinye lkcn sa a duniya cike da dogon
buri fal zuciyar sa, domin shi yana ganin kamar
jiya aka haife shi.
Mutane k'alilan suke gane kanana alamomin
k'arshen duniya, suna ta tabbata a fili, har su
kan yi k'ok'arin su gyara halayen su, su koma ga
Ubangiji.
Amma da yawa daga cikin mu. Yanzu ne suke
bude sabon faifan cin duniya da tsinke, ta ko
wacce hanya.
Ubangiji ya shiryi zukatan mu ta yadda za mu
gane cewar mun fa kusan zama abin tausayi.
Kwarai mahaifiyar su Yakubu ta kashe jikin
yaran, kowa numfashi ya sauke Naseer ya
ce,"Allah yasa mu dace." Suka ce,"Amin."
Ya mik'e ya ce,"Bari in yi sallah in koma gida."
Shi ma dayan Naseer d'in, ya sakko yana
fad'in,"Mu je ni ma in yi sallar." Suka fita tare, ita
ma Mama alwalar ta shiga yi.A harabar asibitin
suka had'u da Yakubu na fakin. Gun sa suka
nufa suka yi masa barka da zuwa, sannan suka
gaisa da matarsa da ke tare da shi. Shi ma
masallacin ya bi su. Uwar gida kuma ta wuce
cikin asibitin.
Fitowar su masallaci, babu 6ata lkc k'anin Yakubu
ya fesa masa lbrn hirar da su kayi da Naseer,
baki har kunne ya jawo kafad'ar sa, ya ce,"Haka
na ke so Naseer A. Daga yau na sanya maka
Naseer A.
Wannan kuma ya zama B, tunda ragon maza ne.
Insha- Allahu wasan polo kamar ka iya shi. Zan
koyar da kai sukuwa, idan har ka mai da
hankalin ka kwarai, to kuwa zan ba ka mamaki.
Yaushe ka ke son fara zuwa koya?"
Wannan albishir ba k'aramin kid'ima Naseer yayi
ba, ji yake tamkar an biya masa aikin hajji. Bakin
sa ya k'i rufuwa,"Ai ni ko yanzu ka ce in zo mu je
da gudu zan bi ka yaya, domin ni a rayuwa ta, ba
ni da burin da ya wuce min in zama d'an wasan
polo." Yakubu ya ce,
"To yanzu yadda za'a yi, gobe idan Allah ya kai
mu, aka sallami takwaranka, bayan sallar la'asar,
sai mu had'u a fili.
Har wannan kalalan ma sai ya hau ba kyale shi
zan yi ba." Suna dariya Naseer B ya ce,"Kai yaya,
tunda dai ka sami wani Naseer d'in, ba shi kenan
ba. Sukuwar nan fa da zan iya da tuni ina
Kaduna ana fafatawa da ni..............."
"Shiru don Allah!
Nan ka fi auki wajen maida zancen.
Doki kuwa hawan shi ya zama dole yaro." Suka
shiga yi amsa dariya, yadda suka ga ya marairece
baya son hawan doki.
******************
Abin nema ya samu wajen Naseer, mafarkin sa
ya tabbata gaskiya. Yau ga shi a filon sukuwa
bisa doki ana koya masa sukuwa.
Abin ya ba su Yukubu mamaki ganin yadda
Naseer ke sakarwa doki linzami kamar ba hawan
sa na farko ba kenan." Lallai za'a da Naseer,"
Haka Yakuba Jah-Jah ke fad' a zuciyar sa.
Nan take ya dorawa Naseer kyakkyawan zato.
Nan suka wuni filin sukuwa, sai gab da kiran
magarib suka dawo.
A daran ranar, suna tare da Sageer bisa hanyar
su ta zuwa wajen Zarah. Sageer ke fad'in,"Gobe
ne fa za mu fara zuwa shagon koyon d'inki."
Naseer ya ce,"Taf, ai ni gobe tun safe Jah-Jah ya
ce in fito, zai yi wuya zuwa na koyon d'inkin
nan." Sageer ya dube shi,"Ka fasa kenan?"Ya
ce,"Zan iya cewa hakan, don ka san da abin
nema ya samu a guna." Amma kuwa bai kamata
ka fasa ba, kuma a ganina sukuwa ba za ta hana
ka koyon wata sana'ar hannu ba."
Da wutsiyar ido ya kalle shi, ya ce,"Ita sukuwar
ba sana'ar hannu bace? Idan na kware. Yakubu
yayi min hanya manyan su. Allah ya taimake ni, a
na haye." Ya ce,"Haka ne.
Allah ya tabbatar da alkhairi. Ina ganin ma dai
zan bar ka anan, bari in wuce shagon, in yi masa
tuni, ina nan zuwa gobe."
Sarai Naseer ya gane ya yi fushi ne, amma ya
share, ya ce,"To, sai mun had'u." Take nan
Sageer ya yanke hanya, shi kuwa Naseer ya mik'e
zuwa gidan su Zarah.
Zarah na ta wanke-wanke, yayin da Inna ke
tankad'an garin tuwo. Sallamar Naseer suka
amsa, ya shigo da fara'ar sa mai tattare da
albishir cikin zuciyar sa. Sau guda Zarah ta kalle
shi, ta maida kai bisa aikin ta.
Innar ke fad'in,"Ah, d'an Inna." Ya k'araso gabn
ta ya tsugunna,"Sannu Inna, ina yini?" Ta amsa
tana duban sa, sannan ta tambayi mutun gida?
Ya ce suna lafiya.
Ta ce,"To yaya an je sukuwar?" Ya amsa,"Na je
Inna,
kuma Yakubu ya yaba da kamun ludayi na.
Sai a taya ni da addu'a. Allah ya tabbatar da
alkhairi." Ta ce,"Insha-Allahu za mu yi maka d'an
Inna.
Allah yasa ka na da rabo ciki.
"Kullum yana jin dad'in kalaman Inna, kuma har
da hakan ke k'ara masa soyayyar Zarah cikin ran
sa.
Ya amsa da,"Amin Inna."
Sannan ya dubi inda Zarah ke aiki, kanta sunkuye
yake, dad'e duniya bata san da shigowar sa ba,
amma gaba daya hankalin ta ya taru ya koma
inda Naseer ke tsugunne.
Ya juya kan Inna ya ce,"Inna kin san wani abu!
Zarah ta daina gaishe ni, ko sannu da zuwa bata
min, ni ba yayan ta bane? Bata da kunya ko
Inna?"
Murmushi Innar ta yi kafin ta ce,"Wannan kuma
ai tsakanin yaya da k'anwar sa ce, ni na shiga?"
Ta sunkuci kwanon garin ta tayi kicin, ta bar
Naseer nan yana kallon yadda Zarah ke kwad'o
masa harara.
Yana ganin Inna ta shige kicin, ya sunkuci kujera
ya nufi gunta ya zauna.
"Baki da kunya ko? Ni ki ke harara?"
Ta aje kai k'asa, ta ce,"Na ji ka na min sharri ne,
ni ce bn gaishe ka?"Ya ce,"Ai da, da zarar na
shigo gidan nan, ke za ki fara tarba ta.Ni kuma
abinda na fi so kenan kodayaushe in rink'a ganin
fara'ar ki. Idanuwanki suna duba na. Da kin san
irin farin cikin da ki ke sanya ni, da ba ki daina
ba.
To wai ma sbd me ki ka sauya?" Akaikace ta
dube shi,"Ni ina zan sani, ni ma haka kawai na ji
ba ni iyawa."
Ya ce,,"Ni kuwa na san dalili, in fad'i?"
Ta ce,"Fad'i mana."
Ya dubi hanyar kicin.
Inna ta raja'a bisa aikinta.
Sannan ya duk'o k'asa-k'asa ya ce,"Saboda Baba
ya ce ke mata ta ce, ko ba haka bane?" Bata
dube shi ba, ta amsa,,"Yaushe Baban ya fad'i
hakan? Ai ni bn da labari." Murmushi yayi ya
d'an yarfa ruwan d'auraya, don ta zolaye shi,
yayi jim, yana kallon yadda ruwan ke gangara
bisa kyakkywan kuncin ta.
Take nan zuciyar sa ta d'auki zugi, sbd tsabar son
da yake wa Zarah. Jin yayi shiru yasa ta bude
shi.
Yanayin da yake zahiri ya nuna ya shagala, d'an
murmushi ta yi, da gangan ta tsunduma kwanon
da ta wanke cikin ruwan daurayar, ruwan ya
fantsale har bisa fuskar sa.
Yayi lallausan ajiyar zuciya, sannan ya lumshe
ido, ya bud'e a natse yake fad'in."
"Kin rama ne?
Kamar ma ba ita ta aikata ba, ci gaba ta yi da
aikin ta. Ya d'auraye kwanon ya kife mata shi."Ba
ki ganni a doki ba yau." Ta ce,"Na gan ka mana."
Ya k'ara duban ta, kamar yaya? Biyo ni ki ka yi?"
Ta karkada kai," A raina na ke ta aiyana ka, ka
tsere Yakubu Jah-Jah.
JUMAT KAREEM




Zaharaddeen Shomar


Whatsapp 08168575100






Ajininsa yake 1-05
Posted by ANaM Dorayi on 11:18 AM, 06-Nov-15
Under: Ajininsa yake
_______ NA ZULAIHAT SANI KAGARA_______
.
." Ya ce,"Wane ni, rufa ni ki saya." Ta ce,"Ai na
san yayana ba shi da wasa, yau da gobe za'a kira
ka Jah-Jah.
Ta d'an dube shi,"Ko ba haka ba?"
Yana murmushi ya amsa,,"Komai ya fito bakin ki
alkhairi ne, Insha Allahu don haka nace haka d'in
ne." Ta ce,
"To Allah yayi yagora."
Ya ce,"Amin."
Ta jima da gama wanke-wanken yana yi mata
d'auraya. Amma suka ci gaba da zama wajen
suna hirar har gob da kiran magariba. Sannan ya
sallami Inna ya koma gida.
Sati 2 sun yi wa Naseer yawa, domin a cikin 'yan
wad'annan kwanakin ya kasance sai Yakubu yayi
da gaske yake tsere masa bisa doki.Ba k'aramin
mamaki ya ba kowa ba, musamman Yakubu da
k'anin sa Naseer B. Haka ya burge abokinsa
Sageer da Zarah, ranar da suka ziyarce shi a filin
sukuwar, don ganin yadda atisayen ke tafiya.
Tabbas Naseer gwarzo ne kuma Allah yayi masa
baiwa cikin jinin sa.
Safiyar lahadin yau, ita ce ranar da Yakubu ya
ajiye, don gabatar da Naseer ga uban gidansa a
Kaduna, sbd sosai ya tabbatar da Naseer ba zai
ba shi kunya ba.
Tsaf! Naseer ya kammala shirinsa, ya fito cike da
albarkar iyayensa.
A k'ofar zaure suka had'u da Sageer tare suka
gangaro har zuwa marabar da za ta kai Sageer
shagon da yake koyon d'inki. A nan su kayi
sallama Naseer ya wuce gidan su Zarah. Suka yi
sallama da juna, don bai iya wucewa, ba tare
daya salleme ta ba.
Nan ma ya sami k'arin addu'a daga iyayen ta.
Sannan kai tsaye d'an acaba ya aje shi k'ofar
gidan Yakubu Jah-Jah da ke Tudun-Jukum.
Babu 6ata lkc suka damki hanyar Kaduna, cikin
motar Yakubu.
A cikin tafiyar awa 1 kacal!
Suka iso k'ofar katafaran garejin siyar da motoci
wanda yake d'auke da sunan (DABAI MOTORS'!
Cikin kallon tsoron da Naseer yayi wa garejin, yayi
zaton akalla akwai sababbin motoci na gani, na
fad'a sama da 200.
Domin kuwa motoci ne fululu!
Wannan na zagin wancan.
Yakubu yayi masa jagora zuwa 6angaren ofishin
wajen inda suka fara magana da sakataran sa,
wanda a fili ya nuna sun jima da sabawa da
Yakubu.
Nan take ya sada

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login