Showing 9001 words to 12000 words out of 40261 words
Chapter 4 - A JININSA YAKE PDF BOOK COMPLETE Writing by Zulaihat Sani Kagara .txt
Salis.
Da ita yaron ke magana, don haka ta ce,"Ka ce
tana zuwa."
Ta mike da hijabin da tayi sallah ta fito.
Salis na cikin zaure ya sha wankan la'asar, yayi
adon shadda bulu.
Fara'a kawai yake yi, ita kuwa jikin bango ta ra6e,
fuska daure. Ya dan matso yana fadin "Yan
matan da ta dace da sunanta, ya sanyin
la'asar????Ta dirka masa harara. Ya ce,"Wai!
Me ya faru?"
Ta gyara tsayuwa cikin fada ta ce,"Salis kar ka
sake zuwa guna!
Ban da lokacinka, ban da lkcn mai lakacin ka!
Saboda haka ka fita harka ta kawai, idan ka na
son kanka da arziki!"
Ta juya za ta wuce, da sauri ya ce,"Me ya faru
Zarah? Ke da ake neman kashe ni, saboda son da
na ke miki? Labarin da na zo in ba ki kenan, ya
za ki min haka?" Ta juyo ta nuna shi,
"Sharrin da ku ka k'ulla masa a kanka zai kare!
Kuma da yardan Allah, sai ya fito, ba zai mutu a
hannun Alk'ali ba!"ta shige gida, ta bar shi sototo
cikin duhu,"Me yarinyar nan take nufi? Ta san
fadan da muka yi kenan?
O.K, shi ma take goya wa baya, ba ni ba.
Shi ta fi so kenan?" Ya huta, ya ce a fili,"Zan yi
maganin sa kuwa.
Kuma ba zan daina son ki ba."
Ya fita, ya bar gidan ran sa 6ace."
Haka Zarah ke cikin kunci, har zuwa dare babu
abinda ta iya kaiwa bakinta.
Sallamar Sageer, ita suke amsawa yanzu. Ya shigo
duk suna tsakar gida zaune, ya tsugunna, ya
gaida su Inna.
Sannan suka gaisa da Zarah." Sai na dawo na ji
sabon labari.
Wallahi-wallahi Baba karya suke yi. Naseer bai je
da komai ba a jikinsa."Ya ce,"To yau muke tare
da Naseer? Duk iya kiriniyar sa na sani. Kawai
sun san yana jarabawa ne, shi yasa suka ja
maganar, don ya rasa. Sun kuwa yi a kansu. Idan
kuma har son Zarah yake yi, ni na ba shi ita
duniya da lahira. Za ta jira shi har ya sami
madafa.
Ba shi kenan ba? Na ga wani dan kusun uwar da
zai sake zuwa min k'ofar gida."
Ba k'aramin farin ciki ya ratsa zuciyar Zarah ba.
Suka kalli juna da Sageer, yayi mata murmushi,
ta yi sauri ta rufe fuska.
Yayin da Inna ke fad'in,"Ka gama magana
Malam. Allah yasa rabon sa ce."
Sageer ya ce,"Amin.
Ni zan wuce (Police Station) din, in gan shi."
Zarah ta mike,"Baba ni ma in je?"
Me za ki yi a can Zarah? ki yi zaman ki kawai,
wurin nan ba wajen zuwanki ba ne."Ta
marairace,"Zan gaishe shi ne Baba,
kuma......kuma........"
Kuma me?"
Inna ta tambaya.
Ta kwanto jikinta, ta 6oye fuska. Babanta ya
ce,"Ba fa za ki ba. Ki ba Sageer sak'on ko
menene a kai ma sa." Haushi ya kama ta, ta
tashi ta shige daki. Sageer yayi masu sallama, ya
fita.
Yana tsaye gaban kanta aka fito da Naseer. Da ka
kalli fuskar sa, za ka san ya fad'a, saboda bai
saba da wajen ba, ga k'yamar k'azantar da ke
wajen, shi yasa bai iya cin abinci sosai. "Ya aka
yi?" Ya ce wa Sageer.
Ya amsa, "Lafiya lau. Daga gidan su Zarah na ke
duk suna gaishe ka.
Zarah ma ta so biyo ni.
Babanta ya hana.
Ni da abinda na ke son in gaya ma ka, ko an je
kotun nan, kar ka amsa laifin da ba ka yi ba."
Ko na amsa, menene?
Sun dade ba su min sharri ba." Ya ce,"To wai kai
son Zarah ka ke, ko menene dalilin yin haka?"
Ya juya lafiyayyun idanuwan sa, ya amsa,"Me ka
fahinta?" Ya dan kada kai,"Naseer manya.
In kasan haka ne, sai ka gaya mata kawai,
menene na 6oye-6oye?"
Ya ce,"Ai Zarah yarinya ce, bai kamata in kasa
mata hankali ba.
Ina sa uniforma, tana sa uniform, sai ince ina son
ta?
Da sunan me?
Don kowa ya san ban isa aure ba.
Da fa hankalina sarai. Su Baba ne suke ganin
banda shi."
Yayi d'an murmushi, ya ce,"To ai duk ta kare,
tunda sun gano ka.
Har Babanta ya ce,"In har son ta ka ke. Wallahi
ya baka ita."
Yayi jim!
Yana masa duban mamaki, Ni zaka zolaya?" Nace
wallahi, ka ce zolaya? Maganar da aka yi ta yanzu
a gaba na.
Zarah ma na zaune.
Yayi 'yar dariya, kafin,"Yaya Zarah ta yi?" Tsaf!
Fuskar ta, ta nuna min kai take so.
Ai kun shak'u da Zarah Naseer, dole mata so ka.
Ba ka ga yadda take rawar jiki, ta zo nan ba, aka
hana ta.
Tun jiya hankalin ta yake tashe."Ya lumshe ido,
shiru yana tunanin zucci, kafin ya bude. Dan
sandan da ke tsaye ya ce,"Lokaci yayi." Ya bude
ido sosai,"Ka ce mata, kar ta damu, lafiyar ta
lau, komai zai wuce Insha-Allahu." Dan sandan ya
ce,"Mu je ciki Yalla6ai."Naseer ya dube shi a
dage, ya ce,"Kai ne yalla6ai, ranka ya dad'e yace
Sageer.
Sai da Safe."
Can a mak'oshin ya amsa, don har cikin ran sa
yana bakin cikin ganin Naseer a wannan wurin.
Ya fito ya nufi ciki da tunani. Karatu kawai yake
yi, amma zuciyarsa na cike da tausayi Naseer,
ganin har za'ayi jarabawa 4.
Shi Naseer bai sami ko daya ba, abin ya dame shi
kwarai, don bai da abin yi ne kawai.
******************
Abin kamar wasa, sai da Naseer ya kwashe
kwanaki 3 ofinshin "Yan sanda, sannan takardar
sammacinsa ta zo. Ranar juma'a aka fara
sauraron shari'ar. Malam Balarabe dai babu
ruwan sa, don haka bai ma je kotun ba, su M.
Umar ne da mahaifin Sageer su ka je.
Sageer kuwa yana makaranta, amma gaba daya
hankali sa bai jikinsa. Balle kuma Zarah, wacce ta
fi kowa kunci na ta na tsare.
Tayi iya kar k'ok'arin ta, don ganin ta jure zaman
ta cikin makaranta kamar yadda Babanta ya
tilasta mata tafiya.
Amma sam ta kasa.
Bata fahimtar komai, kwance take kawai bisa
tebur, zuciyar ta na zugin tunanin wane hukunci
za'a yanke wa yayanta?
Saboda Salis ya sha alwashin sai ya sa an d'aure
Naseer, dalilin juya masa baya da Zarah tayi tashi
guda.
Naseer tsaye gaban Alkali, babu fargaba ko
shakkar wani abu, yana saurare aka gabatar da
k'arar sa, tare da laifin da ake tuhumar sa. Alkali
ya tambaye shi,"Ka ji laifin da ake tuhumar ka?"
Ya ce,"Ran ka ya dade, na ji."
Ya ce,"To ka amince da hakan, ko ka na da abin
cewa?"
Naseer ya amsa."
Ban amince ba, ni ban ta6a fad'a da makami ba.
Kawai dukan sa na yi, ya suma."Wani Lauya da
ke zaune tuntuni, cikin rukunin lauyoyin da ke
zaune, yayi fit!
Ya mik'e tsaye ya ce,
"My Lord,
Sunana Barista Usman, ni ne Lauyan mai kare
wanda yake k'ara, watau Salis.
Ina da 'yan tambayoyin da na ke son yi wa
Naseer."
Alkali ya ba shi umurni.
Nan take, yayin da su Malam Umar da M.Lawal
suke cike da fargabar wannan shari'a, gain har
lauya su Salis suka d'auka.
Lauya ya matsa kusa da Naseer, suka k'arewa
juna kallo, sannan ya ce,
"Ranar lahadi daya ga watan nan da muke ciki,
da daddare ka je k'ofar gidan su Salis, ko zan san
abinda ya kai ka can?"
Naseer ya amsa,"Gargad'i na je yi masa, akan
k'anwata Zarah, don ba na son ya rinka zuwa
gunta." Ya ce,"Wane irin gargadi ne da za ka bi
mu2m har k'ofar gidan sa, ka rufe shi da duka.
Sai da ya daina numfashi, sannan ka yi k'ok'arin
da6a masa Wuk'ar da ke jikinka?"
Hankalin Naseer ya k'ara tashi, idanuwan sa suka
kad'a jajur!
A fusace yake magana,"Ba haka bane!
Tare da aboki na Sageer muka je, na yi masa
gargadi da baki, na ce kar ya sake zuwa wajen
Zarah.
Shi ya fara kai min duka, duka 1 na yi masa, ya
fad'i sumamme.
Abokan sa 2 na wajen, kuma suna gani!
Lauya yayi d'an murmushi ya ce,"Malam Naseer.
Lokacin da ka yi wa Salis lilis!
Har ya suma ka yi iya k'ok'arin ka, don ganin ka
dank'arawa Salis wuk'a.
Amma ba ka sami nasara ba, sbd abokan sa da
suka fi k'arfin ka.
An kira 'Yan sanda sun zo wajen, har suka tafi da
kai ofishin su.
Amma abin mmk, babu wuk'ar nan a tattare da
kai.
Ko za ka gayawa kotu inda ka 6oye ta?"
Ya k'ura Lauya ido, kamar shi ma ya sumar da
shi yake ji, ya jima kafin ya ce,"Had'iye ta na yi."
'Yan kallo na ta dariya.
Alkali ya ce kowa ya natsu.
Sannan ya ce,"Nan a kota ka ke Naseer, ka kula
da harshenka."
Barista Usman ya gyara zaman kot d'insa, ya
ce,"Kowa ya san wuk'a bata had'iyuwa gare ka,
amma kowa ya ji da bakin ka ka ce tare da
abokin ka Sageer ku ka je k'ofar gidan su Salis.
Bincike ya nuna Sageer ya gudu kafin 'Yan sanda
su zo.
Menene dalilin gudun sa?"Ya kad'a kai tare da
fad'in,"Ni ma ban sani ba." Lauya ya dubi Alkali
ya ce,"My Lord, dole Naseer ya ce, bai san dalilin
gudan abokin Sageer ba, domin shi ya mikawa
wukar ya gudu da ita kafin isowar 'Yan sanda.
My Lord, kudirin Naseer ya kashe Salis da ya sami
damar yin hakan, sbd haka na ke rokon wannan
kotu mai adalci, da ta daga sauraron wannan
k'ara zuwa 27 ga wannan wata da muke ciki, don
ba ni damar tattara shaidu na, wadanda za su
tabbatar wa kotu wannan tuhuma da ake wa
Naseer gaskiya ne.
Na gode."
Ya koma kujerar sa ya zauna.
Zuciya kamar ta kashe Naseer.,
Kiri-kiri an lauya magana, ta zama sharri har ana
neman jawo Sageer ciki Ba shi kad'ai ba, hatta
Malam Umar haka zukatan su ke tafasa, shiru
kawai suka yi suna sauraron jawabin Alkali.
"Kotu za ta ci gaba a wannan watan kamar yadda
lauya ya buk'ata.
Sannan kotu ta buk'aci a kawo mata Sageer a
wannan ranar.
Shi kuma Naseer za'a aje shi a ruman har zuwa
wannan ranar."
Al'amarin daya fari a kotu, ya daga hankalin
kowa, hatta Malam Balarane da ke ikirarin babu
ruwan sa cikin rigamar da Naseer ya jefa kan sa.
Sai dai bai fito fili ya bayyana damuwar sa ba.
K'ala bai ce wa su M.Umar ba, har suka k'are
bayanan su.
Shiru na tsawon sakwanni bai tanka ba.
M.Umar ya ce,"M. Balarabe ko ba za ka ce komai
ba, ai ko tofa 'yar addu'a, don samun al'amarin.
Ya dube shi tsakar ido ya amsa,"Naseer ba ya
buk'atar addu'a, sai hukunci.
Damuwa ta 1 ce, yaron nan da aka jawo shi cikin
fitinar da bai ci ba, bai sha ba.
Shi kad'ai ke buk'atar addu'a.
Ubangiji Allah ya ku6utar da shi."
M.Lawal ya ce,"Insha-Allahu baki dayan su za su
ku6uta, duk da dai mu ba mu da k'arfin d'aukan
lauya, ai Allah na nan, za mu gaya masa ya duba
mana.
Ni zan k'arasa gida M. Balarabe, kuma ina ba ka
shawara fushin farko ba na ka bane.
Ka sani bakin mahaifi dafi ne ga 'ya'yansu, yayin
da suke cikin fushi da su.
Saboda haka ka sanya wa ranka ruwan sanyi, mu
rungumi k'addara.
Ya mik'e, ya na k'ara fad'in,"Malam Umar ni zan
wuce, sai yadda hali yayi kenan?"Ya ce,"To Allah
ya jishe mu alkhairi, ya kuma sauka mana
wahala."
Ya amsa da amin, duk suka yi Musabaha.
Ya wuce ba tare da M.Balarabe ya k'ara tofa
wani abu ba.
Bayan tafiyar M.Umar, ya dube shi, ya ce,"Malam
Balarabe ka yi wa girman Allah, ka sanya wa
ranka cewar wannan abu mukaddari ne daga
Allah, babu makawa sai ya faru." Ya ce,"Shi fa
Allah baya d'ora wa bawa abinda ya fi k'arfin sa,
sai abinda shi bawan ya d'ora wa kan sa.
Idan yayi taka tsan-tsan da rayuwar sa, yana
kiyayewa, sai Allah ya taya shi kiwo.
Shi yasa Ubangiji ya ce,"Idan kun ga sharri, to
daga gare ku ne, sai ku binciki kan ku.
Amma shi ya ce yana 1 daga cikin imani yarda da
k'addara mai kyau ko maras kyau.Na yarda cewa
Naseer shi ya jawo wa kan sa, sai dai kai ina son
ka yarda da cewa kaddara ce Allah ya dora
maka, babu makawa sai ka ga wannan 6acin ran,
amincewar kuwa shine ka daina fushi da Naseer,
ka taya mu addu'a Allah ya ku6utar da su."
Yayi shiru kamar ba zai tanka ba, tsawon lkc.
Sannan ya sauke numfashi ya ce,"Na ji Malam
Umar, na kuma gode. Allah ya bar zumunci,
amma kar ka manta, na yi rantsuwa ba zan yi
kaffara ba."
Malam Umar ya mik'e rai 6ace, ya fice daga
rumfar Malam Balarabe.
Babu Sallama.
Malam Balarabe ya bi shi da kallo, kawai na
tausayin su ya lullube shi, ya kad'a kai, ya ce a
ran sa,"Naseer na da gatan sa, amma shi bai san
hakan ba.
Allah ka shirya."
Haka hankali Sageer yake tashe, jin cewar shi ma
ana buk'atar sa a kotu da laifin shi ya gudu da
wuk'ar da ake zargin Naseer ya je kashe Salis da
ita.
Bai san lokacin da ya kawo kan sa gidan su Zarah
ba.tana kwance ruf da cikin, gefen tabarma da
suke tare da Innar ta,har ya gama gaisawa da
Inna Zarah bata iya dagowa ta dube shi ba, sbd
jin muryar sa ma k'ara dagula mata lissafi yayi,
wasu sabbabin hawaye suka cika idanuwan ta
tam!
Kayan makaranta ke jikinta, don bata iya cire su
ba, tunda ta dawo ta sami yadda shari'ar ta kaya
a kotu, ido jajur!
Sageer ya dubi Inna,"Yanzu mecece mafita
Inna?"
Gaba 1 tausayi yaran ya gama kashe mata jiki.
Ya nisa ta ce,"Mafita 1 ce Sageer, ita ce addu'a
wajen Allah.
Ka kwantar da hankalin ka.
Insha Allahu za ku ku6uta.
Kar ka damu ka ji?"Ya ce,"Shi kenan Inna. Allah
ya taimake mu." Ta ce,"Amin." Ya sauke
idanuwan sa, inda Zarah ke kwance, yayi kiran
ta,"Zarah! Bata amsa ba, ya ci gaba,"Kiyi hak'uri
Zarah." Dasauri ta mike cikin sassarfa, hawaye na
zuba ta nufi daki. Dai-dai k'ofa ta tsaya tana
fad'in,"Sai Allah ya tsinewa Salis!wannan sharri
yayi yawa.
Insha-Allahu sai ya ga k'arshen sa!"
Ta juya cikin d'aki da gudu.
Sageer ya ce,"Yaya za mu yi Zarah? Sai hak'uri
kawai."
Ya juya kan Inna,"Bari in koma Inna, ki gaida
Baban. Gobe asabar. Insha Allahi zan je in ga
Naseer d'in." Ta ce,"To Allah shi kare."
Ya amsa da
"Amin."
Ya mik'e ya bi Zarah d'aki. Can yayo ta
rarrashinta har suka shirya tafiya gidan yari gobe,
ganin Naseer, ba tare da sanin su Inna ba, don
kar su hanata.
Karfe 10 na safiyar asabar a k'ofar gidan yari tayi
masu. Sun jima suna neman yadda za su yi, a
bar su ga Naseer d'in, kafin suka sami
amincewar hukumar gidan mazan. Suna zaune
cikin wani d'an d'aki wanda za'a iya cewa ofishin
gandirebobin ne, aka fito da shi.
Bak'in k'ofar yayi tsaye ya sanya wa Zahar ido.
Kwanaki 5r kenan, amma ji take tamkar shekaru
5r ne.
Rabon da ta sanya shi a ido. Tausayinsa yasa
take ganin ya rame, ya dishe kamar ya shekara
yana ciwo. Hawaye kamar fanfo, suka tsunke
mata.
Naseer ya juya da sauri cikin 6acin rai ya ce wa
gandiroban,"Maida ni ciki!"
Ko kafin Sageer ya ce wani abu, har Naseer ya
kai bak'in k'aton gate d'in da ke k'argame a
bakin babbar k'ofar da za ta kai ka ciki.
Gandiroba na biye da shi,"Ba ka son ganin su
ne?"
"Eh!"
Ya amsa ba tare da ya waigo ba.
Gandiroba ya bud'e get, yayin da Sageer ke
k'arawa wajen,"
Naseer!
Naseer magana na ke so mu yi! Ya shige ciki, aka
rufe, sannan ya juyo ya ce,"Idan za ka zo, ka zo
kai kad'ai, ban da Zarah!
Ya wuce cikin sassarfa ya bar wajen.
Sageer yayi tsaye, yana kallon sa, har ya daina
ganin sa.
Ya tako a hankali inda Zarah ke durk'ushe, kanta
cikin guiwa.
Ya ce,"Zarah!
Taso mu tafi." Da kyar ta mik'e, gaba 1 Gandiroba
da ke wajen, babu wanda bai kalle ta ba, wasu
ma dariya ta ba su, ganin yadda Sageer ke jan
hijabinta, tana jefa k'afa kamar makauniya.Daya
daga cikin su da ke zaune gaban wani katon
tebur da alama yana daya daga cikin manyan
wajen.
Tsam!
Ya mik'e ya nufo su, abinka da yare kuma babu
musulunci, yana zuwa ya rungumo kafad'un
Zarah ya shiga rarrashin ta,"Kin kuwa san yadda
ki ke da kyau, ki ka zauna ki na kuka? Don
wannan tsohon mai laifin, ya ce bai son ganin
ku?"
Da sauri ta kwace kafad'un ta, ta balla masa
harara." Tsohon mai laifi?
Yayana ba tsohon mai laifi bane,sharri aka yi
masa, kuma Allah zai fitar da shi! Tuni ta bar
Gandiroba nan a tsaye. Sageer ya biyo ta. Dariya
suka ci gaba da yi, abinda ya k'ara hassala
zuciyar Sageer. Gudun mai zai faru, idan ya
tanka, shi yasa ya rufawa Zarah baya, suka bar
harabar wajen.
Tafe suke. Zarah na koken,"Kiri-kiri yayana ya ce
baya son gani na, me yasa?" Ya ce,"Ai ba zai so
ganin ki a yanayin da yake ciki ba. Ba zai so ki
rink'a kuka ba Zarah.."
Ta ce,"Ba wani Sageer, akwai abinda yayana ke
nufi." Bai nufin komai, yakamata ki gane, ba
kowane zai jure ganinsa a haka ba.
Kawai ki manta Zarah, addu'a kad'ai za ki taya
mu."
Ta sauke numfashi ta ce,"Yadda yayana ke so na,
haka na ke son shi Sageer, ya kuwa zama dole in
yi kuka, tunda yana cikin wani hali. Na san
yayana jarumi ne, komai zai iya jurewa, amma
zama cikin wannan shegen gidan rayuwar kunci
zalla cikin sa.
Salis ya bi son zuciya zai kuma ga 6acin ta yarda
Allah."
Dai-dai suna tsayuwa bakin titi. Sageer ke
fad'in,"Zarah yayenta kenan, soyayyar ta d'aure
min kai. Shi kuma Salis ai har da kishi, ga mari ga
tsinka jaka. Kin fa san mu maza mun fi ku zafin
kishi, illa iyaka na mata ne ya fi bayyana. Dole
Salis ya rasa na yi, tunda kin ce ba ki tare da shi.
Yayan ki, ki ka fi so ko?"
Ta saci kallon sa tana d'an murmushi ta ce,"Kai
wanne ka ke ra'ayi?" Yayin da wata bus ta tsaya
gaban su. Ya ce,"fad'a 6ata baki. Shiga mota
kawai mu isa gida." Suka shige cikin mota, ta
sauke su inda suke son sauka. Sageer ya biya
kudi.
***************
Washe gari Sageer na tare da Naseer a gidan
yari, kuma ya samu nasarar ganin sa. Zaune suke
suna nemar wa juna mafita.Gaba d'aya hankalin
Naseer a tashe yake kuma ya fi karkata ga
k'aunar jefa Sageer cikin maganar da babu
hannun sa a ciki. Saboda haka ya dage yana
fad'in,"Koda wasa Sageer kar ka kuskuara ka
amince da laifin da ake so a k'aga ma. Don na
lura Lauyan nan, shegen kan sa ne. Saboda haka
ka lura da laffuzan da za su fito bakin sa. Sannan
ka ba shi amsa."
Ya ce,"Ni ma d'in kai na fi ji Naseer, na san ka
ba ka da tsoro, don girman Allah kar ka fad'i
abinda zai 6ata ran Alkali, a zo kuma abubuwan
su k'ara rikicewa."D'an murmushi yayi." Ai taka
tsan-tsan na ke yi, sbd ba na son Zarah ta
dauwama a kuka, ba don haka ba, da tun
shekaranjiya na amsa da wukar na je, ka ga Alkali
ya huta, take a nan zai yanke hukunci."
Naseer kenan, to Allah dai ya fida mu lafiya. Bari
in lalla6a gida, me zan cewa mutuniyar?" Ya
ce,"Ka gaya mata idan har ta san tana sona, to ta
daina min kuka, lafiya lau na ke, damuwa ta 1
ce, yanayin da take na rashin kwanciyar hankali.
Muddin kuwa ta natsu, ta maida hankalin ta a
makaranta, shakka babu, ni ma zan sami
nutsuwa.."
Suka mike yana fad'in,"Zan isar da sak'on insha-
Allahu.
Sai mun had'u a kotu." Ya wuce Sageer na tsaye
na kallon sa. Gandiroba ya bi bayan sa. Kafin ya
fice, ya juyo suka had'a ido,"Ka gaya mata ta ci
gaba da lissafin kud'in (Break) d'in ta Insha
Allahu da na fito, zan biya su."
Murmushi Sageer yayi ya ce,"Zan fad'i." Yasa kai
ya fice, tare da ,mai tsaron sa. Sageer ya sauke
numfashi cike da tausayin abokinsa, sannan ya
fito yana fad'in cikin ran sa, "Da yardar Allah sai
ka bar gidan nan."
27 ga wata kotu ta cika mak'il!
Kasancewar litinin ce masomar aiki, ko nasara na
tsoronki. Ci gaba da shari'ar su Naseer aka fara
saurara. Gaba d'aya kowa ya hallara har da
shedun da lauyan Salis ya ce zai gabatar.
Ba wasu bane, illa abokan Salis da aka yi abin
akan idanuwan su, amma maimakon su fad'in
gaskiyar lamarin, sai suka goya wa k'arya baya,
suka tabbatar wa Alkali tabbas Naseer ya sumar
da Salis, sannan yayi k'ok'arin da6a masa
shar6e6iyar wuk'a.
Bayan Alkali ya gama sauraron shedun lauya, kai
tsaye yasa aka shigo masa da Sageer cikin akurkin
kotu.
Bayan yayi rantsuwar