Showing 33001 words to 36000 words out of 40261 words
Chapter 12 - A JININSA YAKE PDF BOOK COMPLETE Writing by Zulaihat Sani Kagara .txt
ruwan
ki da zancan Naseer."
Ta sa hannu ta kar6a tare da godita mai tarin
yawa.
Bata gama rufe baki ba.
Naseer ya bugo sallama, ya shigo, suna amsa
masa.
Bakin sa har kunne,
"Ah!
Alhaji,
na ga motar ka a waje.
Ai ban san za ka zo ba, da ban fita ba."
Ya ce,
"Ai wajen Malam na zo,
shi yasa ban ce ma zan zo ba."
Ya dan duk'a yana gaishe shi.
Bayan ya amsa, ya k'ara da cewa,"Ni zan koma
kenan."
Suka wuce. Naseer ya taka masa zuwa, zaure.
ya sallame shi, ya dawo ya bar su tare da
Malama Balarabe.
Umma na ta k'irgan kudaden ta 'yan d'ari
biyar-biyar sabbabi dubu tara da d'ari biyar.
A bisa dukkan alamu dubu goma Alhj ya so
bayarwa,
sharrin sababin kudi ne, d'aya tayi munafunci
ta like can jikin 'yar uwanta a aljihu.
Naseer na shigowa. Ya amshe su yana fad'in,"Su
Umma kenan, ina nawa kason?
Ta ce,"Ba ga su nan a hannun ka ba,
diba mana." Ya zauna gefenta,"Zarah fa
zan siya wa Cakulet." Ta fige tana fad'in komai
Zarah, bakin ka bai ko gajiya." Yayi 'yar dariya
"Umma ke ma fa kullum sai kin tambaye ni ita,
me yasa na ki bakin bai gajiya?"
"Ban sani ba."
Ni kuwa na sani, son ta ki ke yi."
Ta mike ta wuce
uwar daka, don adana kudinta, ta bar shi nan
yana mata dariya. Kafin ya ce,"Yanzu ma cewa
tayi
in gaishe ki. Na baro Inna shirye-siryen, dambu
na ce su aje min, zan koma in ci. Za ki ci,in zo
miki da shi?"Ta fito kofa, ta
ce,"nagode.......Sallamar Malam ta hana ta k'ara
wani abu." Ya tafi? Ya amsa." Ya tafi. Kai ba mu
wuri. Magana za mu yi." Ya cewa Naseer yana
kallon sa.
Ya kwashe makullai, ya wuce Sabon bangaransa,
ya bude ya shige yayi kwanciyar sa, don hutawa
kafin la'asar ya fita filin sukuwa.
Yana bada baya. Malam ya zauna kamar yadda
Umma ke zaune zugum. Yai dan jim, kafin ya
numfasa ya ce,"Yanzu ya ki ke ganin za'a 6ullo
wa a'amarin nan?"
Gada daya na rasa na yi." Ta ce,"Kai, ko ni?
Ta yadda za'a fahintar da iyayen Zarah, shine
magana."
Cikin damuwa ya ce,"Ashe dai kin fahince ni.
Wallahi Alhj ya cika min ido, sannan ina
ganin girman sa da mutuncinsa, babu yadda
za'a yi in ce masa wannan abu bazai yuwa ba.
Ta ce,"Malam, ai iyakar kauna ce wannan.
Duk wanda ya dauki dan sa ya ba ka, shakka
babu ya gama da kai. Balle irin wadda muke
ganin
matsayin mu bai kai ace mun je neman aure
gidan
Alhj ba,sai ga shi da kan sa ya kawo mana.
Kar6a ya zama dole, idan akwai abinda ya wuce
dole ma,
du ya wajabta a kan mu. Ina gani ka fara zuwa
ka
sami Malam Lawal ka shaida masa ka nemi
shawararsa,ya nisa ya ce,"Haka din za'ayi. To
shi dan gogan fa? Ta ce,"Je dai ka gama da
babbar magana.
Ya mike yana fadin,
"Yanzu kuwa." Ya fice ya barta da zabgegen
tagumi.
Damuwar ta daya, yadda za'a shawo kan iyayen
Zarah, da ita kan ta.
Bus din da M. Balarabe tare da M.Lawal ke ciki,
ita ke tafiya bisa titin da zai kai su Sabon gari.
Suna zazzaune gidan gaba. M.Lawal ke fad'in
"Malam Balarabe na ka kwantar da hankalin ka.
Wannan ba wata maganar zafi bace, abu ne na
fahinta, na kuwa san M.Umar ba shi da matsala,
zai fahimci komai."
Ya ce,"To ita yarinyar fa?
Ba ka ganin ba za ta yi zaton da man can
Naseer na neman yarinyar bane?
Ka san fa mata."
Ya ce,"Ina baka, ka na roko, kai kuwa.
Na daina Allah ya kaimu lafiya.
"Shi kenan abin cewa.Cikin kankanin lkc suka
sauka a kasuwar mata.
Da kafa suka gangara wajen cinikin sa, inda yake
gyaran kekuna na hawa. Tun daya hango su
yake fara'a har suka iso. Suka yi musabaha tare
da
yiwa juna sallama.Cikin shagon da yake tara
kayan aikinsa nan ya baza ta6arma, suka
zazzauna.Jikinsa na rawa, ya fice minti 3 sun yi
yawa, ya dawo da sassanyan ruwan leda (pure
water), ya aje a gaban su, ya dauko ya mikawa
gudu-guda,"Ku sha ruwa don Allah.
Kai sannan ku da zuwa. Kun dauko rana."
Malam Lawal ya ce,"Gaskiya yau ana zuba
rana."
Bayan sun kammala da ruwan sanyi, sun gaisa,
Malam Lawal yayi gyara murya, ya ce,"M.Umar
wata magana ce gagaruma ke tafe da mu, shi
yasa ka gan mu cikin ranar nan face-face.
Ina kasuwa M.Balarabe ya zo min, hankalinsa
tashe yake ya gaya min Alh. Basheer mai gidan
Naseer ya zo dazu har gida, ya same shi yake ce
masa yana son hada zumunci, saboda kaunar
da yake wa Naseer, watau ma'ana ya ba shi
'yar sa ya aura.
Yayi masa bayanin akwai wacce aka ba shi
tuntuni, amma ya ce babu komai sai hada 2, shi
zai dauki dawainiyar komai. Hakika na san
gaskiya hankalin M.Balarabe a tashe yake, don
bai san yadda zai fuskance ku da zancen ba.
Hatta shi kansa Naseer din bai san halin da ake
ciki ba. Saboda shi Alhj bai gaya masa ba, kai
tsaye wajen Malam Balarabe ya zo.
To shine na ce ba mu ga ta zama ba, dole mu
zo mu baka hakuri, don Allah don son Annabi,
kar wannan abu ya kawo wani sa6ani, a bar shi
a shirin Ubangiji.
Don Allah.............
Da sauri Malam Umar ya dakatar da shi da
hannun sa, kafin ya ce,"Haba Malam Lawal
wanna ai abin farin ciki ne, domin kuwa na
tabbtar da kauna ce da yarda ta sa Alh. Basheer
ya kaddamar da wannan al'amari, shi kuwa
Naseer ya cancani a taya shi.
Murna, saboda ya sami gatan da ba kowa ke
samu ba.
A matsayin na na uba ga Naseer, ina mai
tabbtar ma ku da cewa ni ne zan amshi
waliccinsa ranar dauri auransa a kaduna.
Allah ya nuna mana ranar lafiya.
Malam Balarabe kar ka ji komai akan wannan
abu.
Ina mai murna tare da farin ciki, addu'ar mu
kawai.
Allah ya taya shi rikon su bisa adalci.
Suka numfasa, kalaman Malam Umar sun
matukar gamsar da su.
Malam Balarabe ya ce,"Mun gode kwarai da
gaske.
Sauran Zarah a rarrasan mana ita.
Idan ma zai yuwu, ka turo min ita ni in rarrashe
ta da kai na."
Yayi murmushi,"Babu damuwa, kar ka dora
wani tunani akan Zarah, zan mata bayani,
Zata fahimta Insha Allahu.
Yaushe ne Alhjn ya ce ranar bikin?"
Ya ce,"Ai ina ganin hadawa za'ayi rana , don mu
kawai yake sauarar mu gama kimtsawa.
To shi kenan.
Allah ya kai mu lkcn."
Suka amsa da amin."
Sun dan jima, suna hirarraki akan al'amarin,
sannan suka yi sallama, suka koma.
Malam Umar bai kawo tunanin komai ba, ya
dorawa ransa, illa addu'ar Allah ya za6a mafi
alkhairi.
Idan kuma auran ya tabbata, to Allah ya zaunar
da su lafiya.
************
Misalin karfe 1:30 na rana Naseer ya farka
barcinsa, yayi alwala yayi sallah.
Bai ci abincin Ummansa ba, don ya sa Inna ta
aje ma sa dambu.
Yana kokarin ficewa.
Abban sa yayi kiransa falo. Can ya iske Umma a
zaune, yana shiga ta ce,"Ka ga abincinka a
kicin? Ya ce,"Ban shiga kicin din ba, kin ma san
na gaya miki Inna za ta aje min dambu."
Ta ce,"Yayi kyau." Abba ya ce,"Naseeer, ban
hankalinka nan.
Alhj Basheer ya ce, ya ba ka auran 'yar sa,
saboda haka ka je ku ga juna, ka yi masa
godiya.
Insha-Allahu da na Zarah za'a had'a, na ma
riga nagayawa Malam Umar, mun gama
magana."
Tun daya fara magana, idanuwan Naseer ke
kafe, yana kallon Abbansa.
Gaba daya tsigar jikinsa ta mike, wani abu ya
taso ya toshe masa makoshi, da kyau yayi iya
cewa,"Abba ai ba mu yi wannan maganar da shi
ba, maganar makaranta kawai mu ka yi, na
kuma gaya maka.
Ina ni, ina neman 'yar Alhaji?Gaban Umma ya
fad'i, ganin yadda Naseer ke magana hankalinsa
tashe. Kan ka ce kwa6o, kyawawan idanuwan
sa, sun kada. Abba ya ce,"Kwantar da hankalin
ka Naseer. Na san akwai maganar Zarah a
gaban ka kuma ka na sonta.Duk na shaidawa
Alhj.
Ya amince a hade.
Ina rokon ka Naseer da ka dubi girman Allah, ka
dubi so da kaunar da dan tahalikin nan yake
nuna mana. Ka kar6i wannan kyauta da hannu
bibiyu. Ka je ku gaisa da yarinyar nan, sannan
ka yi wa Baban ta godiya.."Umma ta
amsa,"Alhaji ya gama maka komai Naseer, ka yi
hamdala ga Allah daya hada ka da mai son ka.
Sannan ina son ka sani, idan ka amshi wannan
kyauta, mu ka daraja, idan kuwa ka butulce.
Wallahi-wallahi ka tozarta mu Naseer.
Sanin kan ka ne, matsayin gidan Alhj ya fi karfin
mu, sai ga shi Allah ya kai ka wajen.
Babu abinda ya dace kai, illa ka kara kusanci da
yi wa Allah godiya ta hanyar amsar wannan
magana cikin farin ciki da zuciya daya.
Ka ji?
Ya dube ta jim, kafin ya ce,"Na ji.."
Ya mike ya ci gaba da fadin,"Ina zuwa."
Abba ya ce,"Ina zaka, ba'a gama magana ba."
Bai ce komai ba, ya dawo ya zauna.
Yaushe za ka Kadunan?
Gobe."
"A'a
yau ya kamta ka tafi.
Menene na jira sai gobe?
Ko kuwa Umman shi?
Ta ce,"Haka ya kamata.
Shi ma zai ji dadi, zai kuma san ka dauki abin
da mhinmanci.
Ya ce,"To Abba."
Ya ce,"To je ka ci dambun, daga can ka wuce
kawai.
To din dai ya sake fadi, ya mike yayi waje har
wani jiri yake gani.
Umma ta bi shi da kallo, ta juyo kan Abba ta
ce,"Naseer da mata 2, wannan mahaukacin
Yaron."
Ya ce,"Sai anyi da gaske.
Fuskar sa akwai alamar tambaya.
Kar kuma ki mance halin dan ki, akwai kafiya."
Ta ce,"Allah zai tsare.
Shigowar Sageer kenan cikin shagon dinki, daga
makaranta yake, kamar tare suke da Naseer,
yayi fakin a sikwane ya shigo.
Ido jajur, bakinsa na rawa,
"Sageer zo!
Ya juya,
ya koma mota.
Nan da nan shi ma Sageer ya sami kan sa cikin
faduwar gaba.
Motars ya same shi ya hade kai da sitiyari."
Menene Naseer?
Ya dube shi zufa sharkarf jikinsa, ya ce,"Alhj ya
kashe ni.
Da na san duk abinda yake min ba saboda Allah
bane, da tuni na rabu da shi."
Cike da tsananin mmk Sageer ya ce,"Me yasa ka
ke wannan maganar?"
Dazu da safe ya zo kai tsaye ya sami Abba ya ce
wai ya ba ni 'yar sa in aura.
Me yasa?
Don me?
Wai kuma Abba ya amsa masa, maimakon ya ce
ba zai yuwu ba kawai.
Yanzu saboda Allah me su ke son in gaya wa
Zarah?
Kai ni gaba 1 ma ban ji ina wannan ra'ayin ba,
don haka ba zan aure ta ba.
Su da suka kar6a, sa san yadda za su yi."
Yana maganar sa. Sageer na kallon sa, shi kan
sa zuciyar sa ta girgiza, saboda Zarah da ke
tsakani, amma da yayi tunani nan da nan yayi
amfani da kwakwalwarsa,"Yanzu ka na nufin
babu zaancan Zarah!
Wai in hada su 2 ayi biki gaba 1, sbd an gaya
masa yawon kida za ni!Dan murmushi yayi ya
ce,"In don haka ne Naseer, ai babu laifi, za ta
fahimce mu. Amma magana ta gaskiya. Alhj
kauna ya nuna maka.........
Zaharaddeen Shomar
Whatsapp 08168575100
Ajininsa yake 1-10
Posted by ANaM Dorayi on 04:42 PM, 09-Nov-15
Under: Ajininsa yake
_______ NA ZULAIHAT SANI KAGARA_______
.Cikin zafi ya katse shi,"Sageer fita a motan nan!"
Ba zan fita ba Naseer....."Ka fita na ce ko?
"Ba zan fita ba Naseer, me yasa kai kullun ba ka
son gaskiya? Ko kuwa ka na nufin dole sai na
goya ma baya, mu kwance wa iyayen mu zani
kasuwa?
Ba haka rayuwa take ba Naseer, ina kuma mai
tabbatar maka cewa ba karamin kaunar ka Alhj
yake yi ba, tunda har ya ce ka hada su 2, ka
aura.
Ya kamata ka duba wannan, idan ma ba ka
dauke shi a hakan ba, sai ka duba darajar su
Abba, su duka amshi maganar."
Wani mahaukacin kallo yake masa. Wanda ya
nuna Zahiri lallai kura tayi lafiya, da tuni ya
kashe masa baki, ya gama sarewarsa kaf, sannan
ya ce,"To na ji Baba na, sai anjima ko?"
Sageer ya karkada kai cikin murya mai taushi, ya
ce "Naseer, Zarah na da tunani, tana da hankali,
domin ta ta6a yin wasu maganganu wajen nan,
wanda yasa ka ga na hakikance za ta fahimce
mu.
Ka ban izini in je ni kadai in yi mata bayani, zan
dawo ma da amsa."
Ya nuna shi,"Ban aike ka ba! Babu kuma
ruwanka a cikin wannan maganar. Fita-fita kawai!
Yayi jim, suna kallon juna, sannan ya ce,"Naseer
saurin fushi ba naka bane, ka bi maganar nan a
hankali tare da dogon tunani kafin ka yanke
hukunci. Auran mata 2, a lokaci daya, ai na dan
gata ne, yaushe rabon da ka ji anyi irin sa?
Kamar Naseer ya kwarma ihu yake ji, saboda
bakin cikin Sageer ya ki fitar masa daga mota.
Zuciyar sa na ta kara tafarfasa.Sageer na hada ka
da Allah da Manzonsa ka fita a motan nan, ka ki
ko? Ya ce,"Ai ita kanta wannan motar Alhj ne ya
ba ka ita, menene damuwar ka akan zama na a
cikinta? Zuciya ta shake shi tamau! Idanuwansa
suka kara firfitowa jajur! Ya ce,"Haka ne, ka kuma
kyauta da ka tunasar da ni.
Saboda haka ga ta nan ka maida masa abar sa."
Cikin za fi ya hankade murfin motar, yayi waje.
Ganin haka yasa Sageer ya fito ya tarbe
shi,"Zancan bai kai haka ba Naseer. Tunda na
gaya ma gaskiya ba ka yarda ba, shikenan. Ta
Malam bata wuce amin.
Ka yu hakuri ka koma motar ka." Ya ce,"Ka san
Allah sai ka maida ta, ka ga daga nan ya ba ka
tukuicin 'yar, ba shi kenan ba.
An raba gardama?
Ransa bace ya ce,"Allah ya tsare ni. Ka san ba
haka na ke ba, ba kuma zan zama ba."
Uban tsaki ya ja.
Sageer na kallo, ya tsare dan aca6a ya dare, ya
bar shi nan yana kwala kira.
Jingina yayi da motar rungume da hannayen sa,
yana kada kai.
"Rigima sabuwa, me yasa su Abba suka kar6i
maganar nan, ba tare da sun shawarci Naseer
ba? Kodayake suna ganin sun isa da shi ne.
Yakamata Naseer ya gane hakan." Ya numfasa ya
ce,"Allah ka dai-daita, idan da alkhairi." Ya bude
mota ya shiga, ya ja ya maida ta gidan su
yayimusu bayanin yadda suka yi da Naseer din.
Nan ya tafi, ya bar su da hannu a kunci cike da
zullumi me zai je, ya dawo?
Filin sukuwa mai mashin ya aje Naseer, ya fiddo
kudi ya mika masa, yayi gaba abinsa, shi kuwa
waje ya samu ya zauna, ya rasa abinda ke masa
dadi a duniya.
Abin kamar a mafarki yake ganin sa. Zuciyarsa na
yi tayi masa saka iri-iri, yana shigewa.
Wucewar minti 15 da zaman sa, wayarsa ta
buga.Da kyar ya ciro ta. Ya duba lambar. Abba
ne ke kiran sa. Kawai yasan Sageer ya je gidan
kenan, don haka ya maida wayar aljihu, ya ki
dauka.
Mikewa yayi ya sake neman dan aca6a ya dare
suka yi wa Tudun Jukun tsinke. Yakubun da ya je
nema, bai dawo ba, amma Naseer B yana nan,
don haka bayan sun gama gaisawa da mutan
gidan, dakin Naseer B suka zube a katifa.
Naseer B ya kare masa kallo, kafin ya ce,"Ban ga
motar ka ba?
Ya ce,"Gida na bar ta." Ya ta6e baki,"Aca6a ka ke
son hawa?
Jin dadi." Yayi shiru bai tanka ba.
Wai baka da lafiya ne? Na ga kana yi kamar mai
ciwo?"
Ya kada kai, ya ce,"Masifa ce ta same ni."
"To fa, wacce irin masifa?
Bai 6ata lkc ba, ya warware ,masa halin da ake
ciki. Take, yanke Naseer B ya turnuke da bakin
ciki.
Hassada ta kama shi, yayi kasake tamkar mai
tunanin abin kirki."
"Taf!
Lallai Naseer wawa ne, abin farin ciki ya sa me
shi, amma ya ce masifa."
Auran jari?
Mutum ya sami wannan, ai ya haye. Mts........
Ya ja dogon tsaki,"Da ni na sami haka, ko ma
wace yarinya na ke nema, ai don uban ta dole ta
daga min kafa, ta nemi wani mijin, yaushe zan
tsaya bata lokaci na auran su su 2?
Wani wawan tsakin ya kuma mamaitawa, sannan
ya ce,"Yanzu kai ina mafitar ka?
Ya ce,"Wallahi ban sani ba, ni dai yarinyar nan
ban ta6a ganin ta ba, kai koda ma na ganta, ba
za ta yi min ba, tunda ina da wacce na ke so.
Ni abinda ya fi bata min rai, wai kai tsaye Abba
ya samu.
Ai da sai ya kira ni ya ce Naseer 'ya ta ta rasa
miji don Allah ka aureta. Zan maka komai.
Ka ga ni na san bayanin da zan masa.Naseer B
ya zazzago idanuwan munafunci ya ce,"Gaskiya
ne.
Ai dama idan ka ga irin haka, kwantai yarinya
tayi, ake neman kai da ita. To yanzu kai zama za
ka yi haka kawai, ba za ka ta6uka komai ba?
Kamar yayi kuka yake kallon sa, domin hawaye
ne tamke a idonsa,"Me zan iya yi B? Bayan na
gaya maka. Abba yayi ruwa, yayi tsaki kamar su
za su zauna da ita.
Mts!
Ya kama baki yana kada, kada,"Amma ka ban
mmk. Shi kenan an maka auran dole.
Sabon yayi kenan, namiji da auran dole. Na ga ko
matan ma ba yarda suke yi ba.
Wata ta sha fiya-fiya, wata ta banki kalanzir,
koda yake Malamai sun ce yin hakan mutuwar
kafirci ne. Sannan kai ma na ka na lokacinka ai
ba za ka mutu saboda 'yar Alhaji ba.
Amma ina ganin ai za ka iya daukan jaka, ka bar
masu garin, sa gane kuran su."
Ya dube shi da kyau ya ce,"Ka na nufin in yi
tafiya ta kawai?"
Sosai ma."
To Zarah fa?
Ai ita ina son ta ba zan iya barinta ba." Ya
ce,"Ita ma ta hada na ta komatsan ku sa kai."
Takaici ya kara lullube shi ya buga tsaki ya
ce,"Abin kuma ya zama iskanci.
Ba fa Indiya ka ke kallo ba, wannan zahiri na ke
gaya maka.
Ina za ni da 'yar mutane?
Ya ce,"Idan kuwa mafita ka ke nema, dole cikin
biyu ka dauki daya, ko ka hakura da su duka,
ko ka aure su gaba daya har da wacce ba ka
son.
Ka kuwa ce ba ka son ta, yaya za'ayi ku zauna
tare?
Ransa ya kara baci ya ce,"Yaya za'ayi kuwa? Kai
ka na da mafita, amma suna da kamar wuya.
Ka dan nemo mai sauki ne, zai fi.."
Mai sauki bai wuce ka yi tafiyar ka, ka ba kwana
2. Alhj zai ji haushi, ya soke zancan. Idan ka
dawo, a nemi Abba gafara, ka ga shi kenan,
waccan magana ta tashi, dole a bar ka da Zarar
ka. Wallahi ta ma fi dacewa da kai, duk da ban
ga waccan ba."
Ya nisa ya kwanta a katifa rigingine, sakwan 2,
bai ce kala ba.
Yana zancan zuci ya kafin ya ce"Yau din nan zan
6ace masu kuwa.
Ya 6alla masa harara, ya ce a ransa,"Ai sai ka
6ace, tunda a wajen ka masifa ce ta same ka.
A dakin yayi sallar la'asar, duk irin kiran wayar
da Abba ke yi, babu wacce ya amsa.
Kira na karshe daya shigo, shine na Zarah,
misalin hudu da rabi, shi ma bai dauka ba, don
bai san ma ta inda zai fara yi mata bayani ba.
Take nan ya kashe wayoyinsa duka biyun.
Karfe biyar dai-dai Yakubu ya dawo, su biyun
suka fito tarbar sa,"Bakin sa har kunne ya fito,
"Ah! Jah-Jah.
Dama ka na nan?
Ban ga kafafuwan ka ba?
Yayi dan murmushi ya ce,"Tana gida."
Jaja ya miko masa hannu su kai musabaha,
Yakubu ya ce,"Congrats!
Sai na ji daddan lbr wajen Alhj.
You're so lucky Naseer.
Nusaiba akwai hankali ga natsuwa.
Ka zama dan gata, mata 2, lokaci guda.
Allah ya tayaka rikon su.
Yake yayi, domin tumi zuciyar sa ta kara firgita.
Watau Alhj har ya fara shela 'yar sa tayi miji.
Lalai zai ji a salansa.
Bai ce komai ba.
Ya ce,"Na gode yayanmu.
Amma yayanmu ai ina ganin kamar bn isa rike
mata 2 ba."
Ya ce,"Why not, kai ba namiji bane? Babu
abinda zai gagare ka, dukkan su a karkashin
ikon ka za su zauna, illa iyaka ka sa ido akan ko
wacce, ka fahimci halin ta.
Sannan ka yi iyakar yin ka, ka tabbatar da cewa
babu gutsiri tsoma a cikin gidan ka.
Daga karshe kai karan kanka ka tsaida adalci.
Shakka babu gidanka za'a zauna lafiya.
Ko dama na gaya maka Nusaiba bata da
matsala.
Kafin in taho ma, na je mun gaisa ina mata
tsiya, ta gudu.
Ya dafa kafadar sa, ya ci gaba," Ka yi sa'a
Naseer. Alhj na kaunar ka.
Ka rike masa amana, ka ji? Da kyar ya hadiye
miyau, don ya fahimci Yakubu ba zai gane ba,
saboda haka yayi masa ta