Showing 18001 words to 21000 words out of 40261 words
Chapter 7 - A JININSA YAKE PDF BOOK COMPLETE Writing by Zulaihat Sani Kagara .txt
su da ogan sa.
Tare da sallama suka shiga k'aton ofishin daya
amsa sunan ofis.
Kyakkywan Alhajin wankan tarwada na zaune
bisa lafiyyar kujerar sa. Sanyin A.C na ratsawa ta
ko'ina cikin ofishin gwanin dad'i.
Cikin fara'a da walwala ya amsa sallamar su,
sannan ya ce,"Yakubu kun iso?
Bismillah ku zauna mana."
Kujera 2 da ke gabn d'in, su Yakubu ya jawo ya
nuna wa Naseer ya ce ya zauna.
Duk sun natsu a zaune.
Shi dai Naseer haryan muzurai yake yi irin na
bak'unta.
Sun kwashi gaisuwa cikin girmamawa, haka shi
ma Alhj ya amsa yadda yakamata.
Daga nan Yakubu ya ce,"Alhaji wannan shine
Naseer, ina fatan babu wata matsala."
Yakubu ya amsa,"Insha Allahu ba na haufi a kan
sa, sai dai ka gani da idon ka.'a
Murmushi Alhj yayi, sannan ya ce ,"To shi kenan,
ina son k'arfe 2 mu had'u a fili."
Ya juya kan Naseer ya ci gaba,"Naseer, ka saki
jikin ka, za mu had'u k'arfe 2 a fili, don ganin
yadda ka ke gudanar da sukuwar ka.
Ba wani abu. Sai mun had'u d'in ko?"
Ya ce,"Shi kenan Alhj. Na gode."
No problem." Alhj ya fad'i yana jawo dirowar
gaban sa. Makullai ya d'auko, ya mik'awa
Yakubu,"Don Allah ka tabbatar da su Musa sun
dawo da dawakan nan guda 3 akan lkc. Kuma a
ba su abinci a kyale su su huta."
Ya ce,"To Alhj. Muna iya tafiya ko?" Ya ce,
"Yes,
ai ina ganin babu wani abu, idan ma akwai.
I will call you."
Ya amsa da,
"O.K Sir."
Suka mik'e suna fad'in,"Mun bar ka lafiya," Sun
kai k'ofa.
Alhaji ya sake kira,
"Naseer!"
Ya juyo da sauri tare da amsawa.
Ya ce,"Kar fa ka ji komai, cikin ranka, tunda
Yakubu ya yarda da kai, ni ma na amince da kai.
Kawai gwaji ne, don in gani da ido na."
Naseer yayi murmushi, kafin ya ce,"Babu komai
Alhj. Ai gwaji dole ne a ko'ina haka k'a'idar take
na gode kwarai."
Shi ma Alhj murmushin yake yi, yana duban
Naseer, sannan ya ce,"K'arfe 2 insha Allahu."
Yakubu ya janyo kafad'ar Naseer yana
fad'in,"Allah ya kai mu lafiya."
A haka suka bar ofishin.
Cikin mota bisa hanyar su ta zuwa bargar
dawakin Alhj. Naseer cike yake da farin ciki tare
da doki cikin zuciyarsa.
Kwarai ya k'osa karfe 2 tayi su hadu da Alhj a
filin sukuwa.
Yakubu ya dube shi ya ce,"Ka ga oganmu ko?" Ya
amsa,"Kwarai na gan shi, da gani kuma Alhj zai yi
saukin kai."
Ya ce,"Kwarai kuwa. Alhj Basheer Rufa'i Dabai
kenan. Wanda ya gaji d'umbin arziki daga
mahaifinsa Alhj. Rufa'i Dabai. Su 2 ne shi da
kanwar sa, ita tana Jordan tare da mijin ta. Yayi
aiyukan gwamnati da dama. Daga baya ne ya aje,
ya ci gaba harkokinsa na kasuwan cin da ya gada.
Bayan wannan garejin motocin, yana da wani a
Mando, wanda ake siyar da manyan motoci zalla.
Yayi k'arfi sosai a harkar polo, dan kusan zan iya
ce maka duk Arewa babu club din da ya kai na
sa ingattatun dawakan polo.
In dai ana maganar polo, idan aka ce maka
(DABAI RIDERS), to anyi maka kankat! A gaskiya
na ci gajiyar Polo kuma babu abinda zan cewa
Alhj. Sai Allah ya saka masa da alkhairi. Shi ya kai
ni Makka, yayi min aure, ya ba ni gida. Sau 3
yana can zamin mota. Da zarar ya ga ta tsufa, ta
soma ba ni matsala, zai sa aban wata. Saboda
haka na ke son ka kwantar da hankalinka, ka
natsu ka nunawa Alhj Jarantakarka. Insha Allah
wata rana za kayi dariya.
Naseer ya cire tagumin daya zabga, ya sauke
numfashi, kafin ya ce,"Lallai yayaka mori Polo.
Allah yasa muna da rabo muma.
Kuma yarda Allah ba zan ba ka kunya ba." Yayi
yar dariya ya ce,"Ai na sani kai ne Naseer Jah-
Jah."
Ya ce,"Me ake nufi da Jah-Jah?" Alhj. Ya soma
lak'aba min.
Da zarar na hau d'oki, shi kuma ya shiga yi min
kirari kenan,
Jah! Jah!!
Mu je Yakubu!
Ina jin dad'in kirarin Alhj, Sannu a hankali sunana
ya zamana ba'a kiran sa zalla, sai an lak'aba Jah-
Jah."
Ya ce,"Gaskiya ne, ba kai kad'ai ba, ni kaina
kirarin yayi min, tun ina yaro k'arami na ke
begen sunan."
Dariya Yakubu yayi.
Shi kuwa Naseer tambaya yake," yayansa ba sa
yin Polon?"
Ya amsa,
"Ai 'yar sa guda 1 ce a duniya, tana ma can
Jordan tare da k'anwarsa can take karatu.
Kawai tausayin Alhj ya ji ya kama shi.
Shi yasa ya ce," Allah Sarki, yanzun duk dukiyar
nan 'yarsa 1?
Allah ke nan." Ya ce,"Wallahi kuw.
Oh, har ta shiga jama'i. Nusaiba sunan ta, ni na
ke kiran ta Baby N. Tana ce min Jah-Jah, kamar
ita ta rad'a min sunan. Gaskiya yarinyar na da
tarbiya ga ilimi. Shekarunta 15 ta sauke Kur'ani,
ga sanin harshen larabci ko yanzu ma abinda
take karantawa kenan a can Jordan din "Arabic
and Islamic Studies)."
Naseer ya nisa, ya ce,"Amma ya kyauta daya
banbanta da wasu masu kudin ko kuma in ce
wasu 'yan boko ma sun maida kan su tamkar
Yahudawa, saboda takamar abin duniya." Ya
ce,"Ai Allah ya taimake shi,"Ubangiji ya k'ara
shirya mana zuri'a."
Naseer ya amsa da Amin."
Ba k'aramin mmk Naseer ya sha ba bargar
dawakin Alhj Basheer, domin dakawai 12 ke
harbin iska, sun kai sun kawo a girma da koshin
lafiya. Ya kubu ya zaga da shi ko'ina tare da
gabatar da shi ga jama'ar da suka iske a wajen.
Daga bisani Yakubu ya bude wani k'aton falo
mai kunshe da kayan alatu, kuma da gani an
tanade shi ne, don hutawa da gudanar da taro.
Anan suka zauna. Yakubu ya ci gaba da gudanar
da aiyukkan sa, kamar yadda Alhj ya umurce
shi, ko kuma ana iya cewa ya saba yi a
kodayaushe.
K'arfe 2 bayan salar azahar. Su Naseer na filin
sukuwa, ba jimawa Alhj Basheer ya iso cikin
tsaddadiyar Jeep din sa. Bayan sun kwashi
gaisuwa, sai suka rankaya wajen da wasu yara
ke rike da dawakai guda 2. Naseer ya hau 1.
Alhj ya ce Musa daya daga cikin yaran sa ne, shi
ma ya hau 1. Suka dai-daita sahu, kafin Yakubu
ya hura usur, watau ya ba su umurni tashi. Alhj
Basheer ya sha mmk, domin Naseer yayi wa
dokin Musa Fintak'au!
Wanda shi ma Musan yana 1 daga cikin wanda
suke taka rawar gani a (DABAI RIDERS).
Alhj ya dubi Yakubu, ya ce,"Za'a da Naseer,
gaskiya shi ma yana Jah. Kuma kawai yaron ya
shige min rai, tunda ku ka tafi, na ke ta tunanin
sa." Yakubu yayi murmushi, ya ce,"Haka
ne,"Naseer na da hazak'a ba k'aramin mmk zai
bayar ba, nan gaba, idan ya k'ara gogewa."
Yana rufe baki. Dokin Naseer na isowa. Ya ja ya
tsaya gaban su Alhj.
Alhj da kan sa ya rik'e masa, ya sauka,"Good!
Sukuwa tayi yadda ake so Naseer. Saura mutum
1 na ke so ku kara.
Ina Dogara?
Yakubu kira shi ya hau doki."
Kowa ya san Dogara, shi yake rufa wa Yakubu
baya, kuma shine na 2 cikin wadanda Alhj
Basheer ke ji da su ko'ina."
Amma ko alama gaban Yakubu bai fad'i ba, da
kiran Dogara. Domin yana da yakinin Naseer zai
iya karawa da shi kan sa Yakubu."
Don haka kai tsaye ya kwala wa Dogara kira.
Daga gefen da suke tsaye.
Ya baro sauran, ya iso gun su Alhj.
Alhj ya ce ya hau dokin da Musa ya sauka.
Cikin ji da kan sa ya kama doki ya d'are, kamar
yadda Naseer yake tsaf!
Bisa na sa.
Suka ja sahu. Yakubu ya bada umurnin tashi.
Kowa ya baza wuta, suka sakar wa dawakai
linzami. Me zai faru? Kafin wani lkc Naseer ya
6ace 6at!
Sai k'ura.
Duk Jama'ar wajen shewa suke yi.
Alhj kuwa rungume hannayensa yayi ya kasa
cewa komai, amma cikin zuciyar sa ba karamin
alfahari yake yi ba da samun Naseer.
Musamman ganin Yakubu ya fara manyanta,
yana buk'atar hutu nan d'an lkc k'ank'ani.
Bai gama tunanin dogon burin da ya d'ora akan
Naseer ba, Naseer din ya iso cikin sassarrafa ya
diro.
Yakubu ya rungume shi. Duk Jama'ar wajen
suka yayyame shi ka dauka gasa ce ake yi.Alhj.
Ya kamo kafad'un sa, ya juyo sosai ya dube shi,
bakin sa har kunne. Alhj ya mik'a masa hannu,
suka yi musabaha, sannan ya ce,"Welcome to
DABAI RIDERS.Daga yau ka zama Naseer Jah-
Jah." Dai-dai lkcn da Dogara ke k'arasowa
wajen, gaba d'aya jikinsa babu kwari kamar an
zare masa laka. Duk 'yan wasan da ke wajen sai
hannu suke ba Naseer suna taya shi murna don
haka shi ma Dogara yi mika masa ya
ce,"Congrats."
"Na gode."
Inji Naseer yayin da shi tuni Dogara ya bar
wajen dauke da wata irin hassada cikin zuciyar
sa.
To ai dama haka D'an-adam yake, tara ne bai
cika goma ba.
Duk inda ka kai ga dumbin masoya, dole ne ka
sami wanda a rayuwa ba ka yi masa ba.
Wani lkcn kuma zai iya zama hassada.
Muna iya cewa zuciyar Dogara ta shiga wani
garari na musamman take yanzu akan Naseer,
ganin yadda Alhj yayi maraba da shi, domin
burin sa duk lkcn da Yakubu ya zama tarihi a
(DABAI RIDERS), to shine zai maye gurbinsa. Sai
ga shi da rana tsaka wani ya zo daga sama
kuma take yanke Alhj ya kira shi da Jah-Jah.
Suna mai tsada da muhimmanci a gun Alhj
Basheer.
Lallai Naseer yayi wa Dogara shigar sauri a bisa
dukkan alamu kuma ya zama kishiryarsa, sai dai
ce Allah ya tsare sharrin shaid'an.
Ba kankanin farin ciki Naseer yake ciki ba, a
tarihi rayuwar sa kaf!
Yana jin ba shi da wata rana da ta fiye masa ta
yau. Don haka ne ma yake ganin ba shi da wata
kalma wacce zai yi wa Yakubu godiya da ita,
balle Ubangiji daya nufe shi, ga kai wa wannan
matsayi da ke cikin ran sa, ga cimma wannan
matsayi da ke cikin ran sa tun yana yaro
karami.
Saboda haka ya kara kaimi fiye da ko wace
rana, don ganin ya ba maras da kunya.
*******************
Kafin shekara 1 Naseer ya wuce duk inda
tunanin mai karatu zai kai a duniyar wasan
polo. A kowane lungu gabas da yamma kudu da
arewacin Nijeriya. Dole ne ka ji sunan
Naseer
Jah-Jah
a bakin masoyan wasan tseren polo. Wannan ba
karami matsayi ya samawar Naseer ba a cikin
zuciyar Alhj Basheer.
Wanda ta kai ga akan dole Dogara ya sakar wa
Naseer ragamar (DABAI RIDERS), ya tattara
kayan sa ya canza sheka, don ba zai iya ganin
irin gatan da riritawar da Alhj Basheer yake wa
Naseer ba.Ana iya cewa ko Yakubu bai sami
irinta ba. Domin ko kafin Naseer ya hade
watanni 6 a wasan Polo. Alhj Basheer da kan sa
ya nemi sanin mahaifin Naseer kuma ba 6ata
lkc, ya kulla zumunci da shi mai karfi gaske.
Sanin mahaifin Naseer Malam Balarabe, ba mai
karfi bane, shi yasa Alhj ke yawan yi masa
alkhairi akai-akai. Kwarai a halin da ake ciki
yanzu Malam Balarabe yana alfhari da Naseer
kuma yayi imani a polo abincin Naseer yake. Shi
yasa Allah ya shimfida masa so da kaunar
sukuwawan da shi a da yake ganin ba karamin
saba masa yake yi ba.
Sai dai duk da haka yana yi wa dan sa huduba
da kar ya mance da ci gaban karatunsa, kamar
yadda kullum Sageer da Zarah tare da iyayen ta
ke masa matashiya akan gyara jarabawar sa,
don ci gaba da karatunsa na gaba. Amma shi
dan gogan ya riga ya raja'a akan abin da ya sa
gaba, Kuma yake da buri a kan sa. Ko alama
baya waiwaye, wanda hausawa ke wa kirari da
adon tafiya.
Inda ya sa gaban sa, kawai can yadosa bil hakki
da gaskiya.
A yan tsakanin ne kuma Sageer yayi nasara
samun gurbin karatu a (poly) da ke Gaskiya,
Tudun-Jakun Zariya, a fannun kasuwanci
(Businees Admin).
Baba 6ata lkc, ya kama karatun zango-zango,
kuma abn mmk duk tare da gudumuwar aljihun
Naseer karatun na Sageer ke tafiya.
Bayan haka bai daina zuwa wajeb dinkinsa ba, a
halin yanzu ma ya kware babu irin dinkin da ke
gagaran sa, ta nan ma baya rasa taro sisi, duk
da dai ogan sa, bai yaye shi ba. Yana nan tare
da shi.
Haka al'amuran suka rinka tafiya dai-dai da
yadda Allah ya shirya wa kowa rayuwar sa.
Soyayya tsakanin Alhj Basheer da Naseer kuwa
kara shiga ran Alhj take yi tamkar yadda Naseer
ke kara fito da (DABAI RIDERS) a duniyar Polo
ciki da Wajen Najeriya, watau kasashe
makwantan mu.
Tuni Yakubu ya sakar wa Naseer kambunsa
gaba 1, yana mai alfaharin shi ya kawo wa Alhj
gwarzon Da, wanda yake ganin ma ya na taka
rawar da shi bai taka rinta ba.
Shi yasa kullum kirarinsa da babbar murya yake
masa,
"NaseerJah-Jah!"
*****************
. BAYAN SHEKARu BIYU.
A cikin shekarun biyun nan, ba sai mun tsaya
dogon surutun irin tambarin da sunan Naseer
Jah-Jah yayi a duniyar Polo ba.Musamman a
cikin garin su da unguwar su, idan aka yi
la'akarin da irin kwarjinin sa tun farko, balle
yanzu daya kasance duk wanda ya dube shi, ya
san yana hutawa,kuma yana kan lokacinsa,yayi
fad'i, ya yi zabgege, ya k'ara fari da ka ganshi,
ka ga d'an wasan motsa jiki. Maganar kyau da
iya shiga irin ta sutura, abin ba dama, domin
Naseer ya dad'e da gogewa wajen iya tsafta.
Don haka ya zarce wa tsara.
Ya zama abinda bature ke kira (TALK OF THE
TOWN), wato abin hira a gari.
Ta yadda ya tsara rayuwar sa. Abin ya na da
ban sha'awa, saboda babu girman kai, babu
wulakanci kuma abin hannu sa bai tsokane
masa ido ba. A duk lokacin da yake gari, za ka
ga samari na yawan sintiri gidansu.
Can kuma 6angaren tauraruwar sa, komai tafiya
yake dai-dai da ci gaban da aka samu, domin
kusan a yanzu Naseer shine ragamar karatun ta.
Bai kyashin kashe ko nawa ne a dangane da
hidimar Zaran sa.
Wani abin sha'awa da ya fi kowa, a cikin
gidansu yake shirin fitar da wani gini mai bn
mmk. Kasancewar gidan k'aton gaske ne, ko
dama rashin kud'i ne yasa yake a wulak'ance.
Tuni aka fitar wa iyayensa 6angarn su. Shi kuma
na sa 6angaran aka shimfida filat mai d'akuna
3. Ba shi da buri daya wuce ya tsara wa Zarah
abubuwan da zai fiddo ta daga cikin tsara,
tunda ga shi Allah ya ce su huta."
Kwatsam!
Allah da ikonsa sai ga takarda daga k'asar
Ghana zuwa (DABAI RIDERS), suna neman izinin
d'aukar Naseer haya na wata 1, don gudanar da
wasa a wata kungiyar wasan Polo da ke can
Ghana.
"Al'amarin yayi wa kowa dad'i.
Musamman Alhj Basheer da Yakubu kuma babu
6ata lkc.
Alhj ya amince masa da tafiyar, babu wani
sharad'i ko wata tsatstsaurar doka.
Ranar tafiyar sa, yayi sallama da kowa, sannan
ya nufi gidan su Zarah. Tana zaman jiran sa,
kamar yadda ta san yana tafe. Kallo daya yayi
mata, ya gane hankalin ta a tashe yake, ya
karkade kai ya ce,
"Wai ke ba za ki daina wannan kuncin ba?
"To ko in fasa ne?"
Ta ce,"Kasan ban isa in hana ba."
Da sauri ya tari numfashin ta."
Kina ganin ba ki isa ki hana tafiyar nan ba?
Lallai za ki sha mamaki, idan aka wayi gari gobe
ki ganni a garin nan.Me zan samo a Ghana,
wanda ya wuce farin cikin ki?
Look Zarah!
Ina ganin ke har yanzu ki na daukata a
matsayin yayanki ne, ba ki san cewa akwai
banbnci ba.
Wallahi, kin ji na yi miki rantsuwa ko? Muddin
ba ki saki jikin ki akan tafiyar nan ba, zan fasa
ta, kuma babu wanda zai sani dole. To kila ko
su Abba su cika min ido.
Ta numfasa ta ce,
"Wai!
Ai kuwa na gode Allah, tunda akwai su Abba,
don na san zai wuya inji sanyi a raina, bayan na
san yaya na zai bar ni tsawon wata 1, "Alhali
ban saba ba."
"Dan murmushi yayi, kafin ya ce,"To ai ba zan
bar ki haka kawai ba, kin ga wannan?
Sabuwar wayar ki ce dalilin siyan kawai don
murinka sanin halin da muke ciki ne,
kodayaushe. Amshi nan."Ta saki baki tana kallon
kwalin rantsatstsiyar wayar da aka ce tata ce a
lkcn 1, kuma tana tambayar kanta yaushe
yayana ya siyo min NOKIA ta hannu na?"
"Kin amsa na ce, ki ka baje min ido, ki na kallo
na." Tasa hannu ta k'arba,"Amma dai yayana ka
na son kashe kudi, ita wannan Sabis d'in bai
zuwa Ghana ne?"
Dariya ta sake ba shi, ya ce,"Ina jin hakan a jiki
na, zuciya ta na gaya min tana gargadina da
cewa kai Naseer kar ka bar Nijeriya, ba tare da
ka sakewa k'anwar ka sabuwar waya ba, don ka
san ta hannunta ta shekara."
Zai iya kasancewa ta fara bada matsala. To kin ji
dalili,
da a sami matsala,
gara ayi wa tufka hanci.
Ko me ki ka ce?"
Ta d'an rausaya kai cike da mamakin yayanta,
ta ce,
"Godiya kwando-kwando yayana.
Allah ya k'ara bud'i."
Bai amsa ba.
Wayar sa ta hau ruri, ya jawo ta cikin alhu ya
duba lambar. Alhj Basheer ne, kamar yadda
yake a rubuce cikin wayar (Alhaji). Ya dube ta ya
ce"Mintu 2, "Sannan ya danna Ok."
Suna magana da Alhj.
Amma ita Zarah kallon sa take yi, kasancewar
hankalin sa ba ya gunta. Sai ta sami damar kare
masa kallon da ta jima da mancewa da ranar da
ta yi masa irin wannan kallon.
Nan take zuciyar ta, ka karan ta mata ba
k'aramar sa'a ta yi ba, da samun Naseer.
Kwarai ta tantance Naseer watanne, tamkar
yadda take Zarah.
Anya kuwa 'yan mata za su kyale mata Naseer
d'in ta ita kad'ai, yadda ya shiga yana fita gari
da kashashen duniya da irin wannan baiwa da
Allah yayi masa???"Nan da nan kishi ya rufe ta,
idanuwanta suka fara kad'awa, sannan kafe
suke tana kallon sa, ba tare da ta san tana yi
ba.
Kusan minti 2 da kammala wayarsa. Shi ma yayi
zurun yana maida martani.
Ganin idanuwan ta sun fara ja, shi yasa ya
murza yatsunsa biyu, suka yi k'ara bisa fuskar
ta. Cikin kunya ta sunkuyar da kai. Sai kuwa
tambaye yake,
"Menene?"
Ta ce, "Ba komai."
Kin san Allah, ban yarda ba, kuma ba zan bar
wajen nan ba, sai kin gaya min ko menene ki ke
tunani." Ta riga tasan halin yayan na ta, don
haka ta d'an dube shi, ta ce,
"Mata na zuwa kallon polo a Ghana?"
Tambayarta ta d'aure masa kai, kuma take ya
gane me take nufi. Amma sai ya nemi sanin
dalilin tambayar ta,
"Me ya sa ki ka ce haka?"
Sannan ba ki ta6a tambaya ta hakan ba, sai
yau?
Shiru tayi, ta rasa bayanin da za ta yi, don ita
ma ba'a son ranta tayi masa tambayar ba.
Jin tayi shiru tsawon 'yan dakikai, shi ya sa ya
ce,
"Zarah, dube ni nan."
A karkace ta dube shi, jim ta sauko ido.
"Zarah, son ki ba karya bane a ciki rai na.
Kar ki mance, tun bn san me zuciya ta ke nufi a
game da ke ba, har na gane so da kaunar ki na
ke yi.
Ma"anar tun yarinta, har zuwa sanin ciwon kai
na, ban jin akwai abinda zai cire min soyayyar ki
Zarah. Don kin jima cikin raina shekaru masu
yawa.Saboda haka ki kwantar da hankalinki, ni
yayanki nai miki alkawarin har abada ke kadai
ce, ba kari balle maganar canji. Kin ga zancen
mata na zuwa kallon Polo ko ba sa zuwa, duk
ba matsala da ta shafe mu bace.
Kin amince?"
Kad'a kai tayi, ta d'an nisa kafin ta ce,"Na gode
yayana, amma maganar k'ari, ka na nufin babu
zancen kishiya?" Da sauri ya amsa,
"Nufe na kenan Zarah.
Kin isheni rayuwar dauniya, domin komai na ki
yayi min yadda ra'ayina ke buk'ata."
Wannan karon ta kalle shi ido ciki ido, sannan ta
ce,
"Ban ji dad'in wannan maganar ba yayana, don
ka shigo hurumin da ba na ka ba.
Wannan hukunci ne na Ubangiji, wanda bai
kamata ko ma ince bai halasta ko wane D'an-
adam yayi shishshigi a cikin sa ba.
Ka ga dai........."ya katse fuska daure,
"Me ki ke nufi?
Na yi miki k'arya kenan?"
Ta ce,"Ban ce ka min karya ba,
amma magana ta gaskiya, duk macen da aka yi
mata alkawarin ba za'a yi ma ta kishiya ba, ta
yarda ta amince.
A hakikanin gaskiya ta yaudare zuciyar ta.
Don shi aure al'amari ne na Allah, tamkar
haihuwa da mutuwa.
Ubangije ne kadai ya san yadda ya shirowa
bawan sa rayuwa.
Shi yasa na ke ganin bai halasta masoya su
rinka yi wa junansu ko wane irin alkawari a
hurumin da ba na su ba.
Ina fatan yayana ya fahimce ni....?
Tun da take mgn, yake kallon ta, sai dai laffuzan
ta kawai