Showing 39001 words to 40261 words out of 40261 words

Chapter 14 - A JININSA YAKE PDF BOOK COMPLETE Writing by Zulaihat Sani Kagara .txt

ku
zauna.
Akwai motoci guda 2, su ma sai ranar tarewa
za'a tare da su. Sannan kar ka manta da
maganar da mu ka yi akan makaranta, ina
jiranka."A lokacin da yake kara nuna kaunar sa ga
Naseer.
Shi dan gogan tunaninsa daban ne.
Domin kuwa cikin ransa yake saka wadannan
kalamai,"Lallai Alhj dan siyasa ne.
Ai na dade da sanin wannan wayon masu kudi.
Da za'ara 'ya'yan su sun rasa miji, sai a sami
wani mai yunwa a lika masa, a ba shi gida da
mota.
Shi kenan an kama shi a hannu, sai yadda aka yi
da shi.
Allah ya hada ka da Naseer, mu je a siyasar."
Kayataccen murmushi yayi, suna kallon juna da
Sageer kafin ya ce,"Ban san avinda zan ce ba
Alhj. Na gode."
Ya fadi yana dan rankwafawa, Sageer ya taya shi
godiya.
Bakin Alh. Basheer baya rufuwa, ya ce,"Kauna ce
Naseer, kar ka ji komai ni Babanka ne.
Yaya sunan ita waccan 'yar tawa?
Ya shafi keya, ya ce,
"Zarah."
Yayi murmushi ya ce,"Ashe kanwata ce, shi ke
nan ga Nusaiba ga Antin Jordan.
To Allah yasa albarka."
Sageer ya ce, amin.
Suka yi shiru na 'yan dakikai, kafin Alhj ya lura,
kamar kunya duk suke ji, don haka ya ce,"Za ku
karasa gidana ne?
Sageer ya amsa,
"Eh."
Ya ce,
"O.K.,
to ku na iya tafiya, zan kira Nusaiban, in gaya
mata ku na tafe." Sageer dai ke magana,"To mun
gode." Suka mike, suna k'ara godiya, suka yi
waje.
*******************
(Go slow) ne ya 6ata masu lkcn bisa hanyar su ta
zuwa unguwar Rimi, sakamakon mutuwar wata
babbar mota akan titi.
Naseer ya ja dogon tsaki, saboda takaicin zaman
da suke a mota, ga rana ta fara zafi.
Sageer ya dube shi ya kauda kai.
Tuntuni yake son yi masa magana a kan
alkawuran da Alhj yayi masa, watau gida da
canjin mota, amma yayi shiru, saboda yana
gudun 6acin rai. Shi yasa ko yanzu da ya ci birki
da yin dogon tsakin sa, kallon sa kawai yayi, ya
kyale.
Da kyar da ji6in goshi suka sami wuce dogon
cunkoson motocin.
Sannan suka fada titin da zaikaisu kayatacan
gidan Alh. Basheer.
Nusaiba ma gab da kammala shirin ta, lkcn da
Baba Mai gadi yayi sallama ya kira Mariya mai
aiki, ya ce ta gaya wa Hajiya bak'i sun zo.
Sama Mariya ta haye ta shaidawa Ummi, ita
kuma ta umurce ta da kira mata Nusaiba.
Jimawa kadan Nusaiba ta shigo, ita kanta Ummi
sai da gaban ta ya fadi, saboda tsabar iya adon
Nusaiba,Komai ta sa yana amsar jikin ta. Wani
lallausan farin les ne ke jikin ta, wanda aka yi wa
ado da zare kalar samaniya.
Shi yasa hatta abin wuya, da 'yan kunnenta, kalar
samaniya ne. Haka nan warwaraye, sai bungus
din su da ke hannunta na hagu. Haka takalmin
kafar ta suke irin daya da gyalen da ta yafa,
wanda gaba daya ta tattara launanin farin ciki, ga
duk wanda ya kalle ta.
Tamkar yadda ko wace zuciya ke a ji a duk
lokacin da samaniya tayi luf-luf!
Cikin wannan launin mai sanyaya idanuwa.
Ummi ta dafa ta ta ce,"Naseer ya iso, ki maza ki
kai shi babban falo, a kai masa duk abinda ya
dace.
Ta ce,"To Ummi." Tana kallonta. Ki tafi mana, ko
sai na ce kin yi kyau? To kin yi kyau Bebin Abba."
Da sauri ta juya cikin hanzari ta bar dakin dauke
da murmushi, bisa fuskarta.
Ummi ta kada kai ta ce,"Allah sarki Bebin Abba.
Allah yayi miki albarka.."
Su Naseer na tsaye jingine da mota, inda suka yi
fakin a harabar aje motoci. Nusaiba ta danno,
tana takawa d'ai-d'ai. Gaba dayan su sai da suka
rasa kuzari.
Kwarai Nusaiba tayi wa Naseer kawarjini a idonsa
har yasa jikinsa yayi sanyi, sai dai cikin zuciyar sa
Zarah ta riga ta kame, ko alama bai ji wani
matsugunni da zai aje Nusaiba ba.
Sallama tayi masu, tana dan murmushi, suka
amsa ta ce.
"Kuyi hakuri, ku na ta tsayuwa ko?
Sannun ku da zuwa."
Sageeer ya ce,
"No,
kar ki damu.
Ai ba mu wani dade ba.
To ya ki ke?
Ta ce,"Lafiya lau.
Ku k'araso ciki mana."
Ta fadi tana duban Naseer ido cikin ido. Kwarjinin
Naseer ya zarce na yadda ta ji, a ganin sa na
farko a hoto, shi yasa tayi saurin kauda idonta.
Bismillah!
Ta wuce suka biyo bayanta
zuwa babban falon gidan,
wanda ba kowa ke shigar sa ba.
Naseer da Sageer, sun ga launanin abubuwan
rayuwar duniya cikin falon nan, kai ka rantse ba
za'a ta6a barin duniyar ba.
Bayan sun zauna, ta gaishe su cikin kunya da
ladabi.
Abin ya burge Sageer, yanayin yadda ya ga
Nusaiba.
A na shi gannin, bai ga wani abin ki ba. Shi kuwa
Naseer ba dole bane ya so wannan yarinya, duk
da tana ingattatun abubuwan bukata. Shi abin
daya sani Zara yake so, ita ya za6a, ita kuma
yake son ya aura ya zauna da ita iya rayuwarsu."
Bayan sun kammala gaisawa, ta mike tana
fadin,"Minti 2,." Sageer ya ce,"Mun baki."
Ta fice tana fara'a.
Suka kalli juna jim.
Sageer ya fara murmushi.
Naseer ya kauda kai. Nan da nan ya hadiye
murmushinsa, ya gyara zama a kujera.
Ya fara lissafin zuci. Da sallama ta sake shigowa,
dauke da dogon tire fari, shake da kayan lashe-
lashe da shaye-shaye.ta aje masu.ta zuba
(Drinks)' kala-kala, ta koma ta aje gaban sa, "Ku
sha ruwa."
Sageer ya ja robar Swan, ya dauki kofi,"Mun gode
Malama Nusaiba." Ta koma gefe ta zauna.
Sageer ke ta magana." To, ga fa aboki na Naseer.
Ni kuma suna na Sageer.
Ya ki ka gan shi? Ya dan sadda kai kunshe da
murmushi ta ce,
"Dai-dai."
Yace kin tabbata, yadda ki ka yi mana dai-dai,
haka shi ma yayi miki? Ta gyada kai, tare da
fadin "Na'am."
A karkace Naseer ke kallon ta, tana amsawa, ya
numfasa, kamar wanda zai fadi wani abin kirki.
Duk da yana son yayi mata magana, amma
rashin sanin abinda zai fadin, yasa shi yayi shiru,
kamar ba shi ba.
Saboda haka ya bar Sageer , yana yi masa tad'in.
Ya ce,"Gaskiya mun gode da fatan Allah ya sanya
albarka a cikin abinda za'a kulla.
Sannan wani hanzari ba gudu ba.
Abba yayi miki bayanin akwai uwargida ko?
Ta ce,
"Eh."
Ya ce,"Ina fatan za ku hade kan ku kamar Ya da
Kanwa. Zarah babu ruwan ta, kuma tana da
hakuri da hankali. Koda aka gaya mata zai aureki,
addu'a kawai tayi, tare da fatan samun hadin
kan ku."
Hankali kwance ta ce,"Insha Allahu babu matsala,
domin shi shirin Ubangiji kullum alkhairi ne ga
bayin sa, idan ka ga akasin hakan to laifin daga
mu ne 'Yan-Adam.
Saboda haka ni ma ina mana fatan alkhairi tare
da fahintar juna."
Sageer ya jinjina kai, ya ce,"Amin.
Naseer ka ji, ko kuma in bari in ba ku wuri ku
gaisa."
Ya dan muskuta ya ce,"Ina jin ma idan ma za
kayi zaman ka, babu damuwa, ai ni da kai ba
bambanci.
Duk abinda ka fadi tamkar ni ne na fade shi."
Ya riga ya gano shi, don haka ya ce,"Haka ne,
amma waka a bakin mai ita, ta fi dadi, ko
Malama Nusaiba?
Ta ce,"To ni me zan ce?
Ya mike ya ce,"Bari dai na jira ka a mota.
Malama a fito lafiya."
Ta ce,"Kuwa ba ka zauna shiru kai kaidai a mota.
Ta mike, "Zo mu je." Ta fice ya bubbuga kafadar
Naseerr, sannan ya bi bayan ta.
Wata kofa ta bude, sai ga su a wani matsaikaicin
falo. Ta ce ya zauna ta kunna masa T.V. "Wane
( Channel) Ka ke so? Ya ce,"Bar min labarai, na
gode."
Ta fita, jimawa kadan suka dawo tare da Mariya,
dauke da kayan abinci da na sha, ta aje masa."
Duk ni kadai?
Tayi murmushi," Duk kuma na ke son ka cinye."
To na gode."
Ta sa kai ta fita.
Sageer yayi kishingide a kujera, ya cigaba da
kallon sa.
Tana sallama babban falon. Naseer na daukan
waya, "Yaya B, ya aka yi ne? Ka na wane gari ne
yanzu?
Ya ce,"Tafiyar nan bata yuwu ba B. Sai dai mun
hadu, ka ji labari. Ina ma Kaduna a halin
yanzu.......
Takaici yasa Naseer B, ya kashe wayar sa. Jin
shiru. Shi yasa shi ma ya cire ta a kunnan sa.
Ya gama 'yan latsen-latsen sa tsawon lokaci,
kafin ya dubi inda Nusaiba ke zaune. Kanta a
sunkuye yake, don haka ya ci gaba da hararar ta.
Jikinta ya bata ana kallon ta, saboda haka ta dan
dago ba zato suka hada ido.
Yayi sauri ya janye na sa...................
______________________________
Masu karatu, yaya za ta kaya ne? Wace badakala
za ta faru a wannan labari? Ga Naseer Ga
Nusaiba, cikinsu wa zai ci gari? Na yi gaba a
dangaraman jirginmu na (MAIZAR AIRLINE). Mue
je zuwa, wai mahaukaci ya hau Kura.




Zaharaddeen Shomar


Whatsapp 08168575100

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login