Showing 21001 words to 24000 words out of 55059 words
Chapter 8 - MATAR MAHAUKACI END Book Complete Document Writing Mrs Sadauki .txt
na ɓari ta ɗaga "kije STM na turo maki saƙo"ƙit ya kashe wayar.Farida ta dube ta tace "miye?"tace "Abban Kalil ne wai na je STM ya turo min saƙo".
★★★ *MARADI*
Tun da Abbasi ya dawo ya shaidawa Daddy ya samu matar aure,amman sam Daddy yace bai lamunta da auri bazabarma ba.Juyin duniya yayi amman abu ya cuttura wannan dalili ya sa Abbasi shiga yanayin damuwa ya rasa yadda zai yi da ransa ga Atine ta sako sa gaba da zancen Maryam alhalin tuni an aura ma Ƙanensa ita.
Ya na kwance ya na malolowa kan capet Daddy ya shigo,duban sa yayi sai ya ji tausayin sa hakan yasa yace "Abbasi ka tabbatar da ingancin tarbiyyar yarinyar?"ai da sauri ya tashi ya na jinjina kai Daddy yace "ok to Allah sa alkhairi ni ba komi yasa ban son auren ka da ita ba sai dan ƴan Niamey sangartattu ne basu iya komi ba sai Bariki da iya yi na banza ko girkin ga sai a hankali"Abbasi yace "ita dai wannan ba haka ta ke ba"Daddy yayi gaba ya bar sa nan ya wuce ƙurya ɗakin Atine.
"Hajiya lafiya yau kika ƙume ɗaki kamar wata mai jego?"Daddy ya faɗa da shigar sa,Atine ta yamutsa fuska tace "to mi zan yi bayan an nuna ba'a ra'ayin ganina cikin jama'a"da ɗan mamaki yace "kamar ya?su waye ba su ra'ayin ki?"ba tace komi ba juya masa baya dama a kwance ya tarar da ita.
Gadon ya haura yace "kin ga Atinena kiyi haƙuri ki bar fushin nan kin fah kusa zama sarakuwa"cikin jin haushi tace "ah ai ba ka son na zama ɗin tunda ka aura ma wanda bai dace ba yarinyar da tun ta na ƙarama na yiwa Abbasi kamen ta"Daddy yayi murmurshi ya girgiza kai dan kuwa ya san yadda suka yi zaman lafiya ita da Maryam ɗin.
"Ki yi haƙuri dai ai shi ma Abbasin ya samu matar aure yanzu haka maganar da ni ke yi maki shawara na zo mu yi da ke"zumut Atine tayi ta na waro ido farin cikinta ya kasa ɓoyuwa tace "kai haba?yaushe ya faɗa ma haka?"Daddy ya sauke ajiyar zuciya ya zayyane mata komi Atine ta rangaɗa buɗa tace "alhamdullah Abbasi ka gama min komi tunda har ka samo mana babbar yarinya bari na tashi ai zama bai same ni ba"
A can ɓangaren Mahomet kuwa yau wani sabon salo ya fito da shi,yadda ya baiwa Maryam mamaki ya sa tayi saurin tallabo kansa tace "wai miyasa kake semblant kamar marar lafiya?"kallonta yayi sai kuma yayi murmurshi ya cigaba da abinda ya ke,ƴar ƙara ta saki jin zafi ya ziyarceta.
Ƙoƙarin tashi tayi amman Mahomet ya danneta ya cigaba da ƙoƙarin shiga gonar sa sai dai kash Maryam tayi ƙankantar da za ta ɗaukar nauyin sa dakyar ya samu gland ɗin D ɗinsa ya shiga kaɗan.Ta na kuka ta na ƙari haka yayi ta bidirinsa har ya samu nutsuwa,jawota yayi jikinsa ya rungume tsam tare da ja masu bargo.
Balkisu ce durƙushe gaban wani ƙaton mutum baƙi ƙirin da shi,cikin ƙyanƙyashewar zuciya tace "so ni ke a ida maida sa mahaukaci na haƙiƙa ta yadda ba zai sanin shi ɗin wanene ba balle har ya san da wani abu wai shi aure,ban so ko kaɗan ya samu sassauci cikin haukan"ta na gama faɗa boka yayi wata ruɓaɓar dariya nan masororin haƙoransa suka bayyana.
Umarta ta yayi da ta tuɓe babu muso ta cire dukan kayan ta,wasu ruwa ya ɗauko ya yi mata wanka sannan ta maida kayanta.Farin ƙyale ya samu ya saka wani garin magani yace "wannan za ki je mararabar hanya ki turbuɗe wannan kuma na cikin gwangwani cikin kasuwa za ki je ki turbuɗe ina tabbatar maki ki na aiwatarwa zai fara hauka mai digi"cike da murna Balkisu ta karɓa......
[17/02 à 16:18] Mrs SADAUKI 💫: *PAID PAGE 25-26*
*Littafin kuɗi ne ki biya ki karanta hankali kwance ƴar uwa ba tare da kin shiga haƙina ba ki biya 200₦ kacal ki sha karatu in kin shirya kin tuntuɓe Ni ta WhatsApp* +22795045822
MATAN ALBARKA HERBAL MEDICINE
INA KUKE ISASUN MATA MASU AJI MASU DARSJA DA GIRMA MU MATSO KUJI GA GYARA NA MUSSAMN NA ISASUN MATA MASU AJI
INA MAI MATSALAR SAURIN KAWOWAR MAI GIDA KI ZO GA HADIN NE DA KAI ZAKU SAMU QARFI DA ISASHEN RUWA
MAI FAMA DA BUSHEWAR GABA
MAI BUDEWAR GABA
MAI QAIQAYIN GABA
MAI FITAR RUWA BA KAN GADO
INA MAI SO TA MATSE MUNA DA MAIDA TSOHUWA YArinya
Kuma muna gyara amare gyaran da zai shekara a jikin su ina masu jego
Kuma ga naku gadin ISASUN MATA
Muna gyara dukan matasalolin mata na cikiy Dana waje kedai ki tuntubemu a wanna nombar kuma muna wa,azin aure 08163199051
Sign manager c,e o maman shukura
_________________
Dare mahutar bawa,garin maraɗi ya ɗau shiru tsit kake ji.Wasu matasa biyu ne ƴan samari tsakiyar hanya suke haƙa rame bayan sun dawo daga kasuwa Babba ta Maradi sun aiwatar da aikin da Balkisu ta saka su.
Su na gama saka farin ƙyalen cikin rame suka maida ƙasa suka rufe,ɗaya daga cikin su ya kira layin Balkisu "Hajiya an gama aiki saura biya"can ɗayan ɓangaren Balkisu tayi ƙasa murya tace "Mumuni ka tabbatar kun yi komi yadda ya kamata?"wanda ta kira da Mumini ya ja tsuki yace "wlh wani sa'in yawan tambayar rainin hankalin da kike min ta ɓaƙanta rai,ke da kika riga kika san akan kuɗi babu abinda ba zan iya ba"Balkisu tayi ajiyar zuciya tace "to gobe in Allah ya kai mu zan je can na biya ku kuɗin ku"ƙit ta kashe kiran tace "ai wlh da na bari wata banza ta amfana da shi gwara a ida haukata ka mtws banza kawai"
A can ɓangaren Mahomet kuwa cikin barci ya fara jin ana kiransa,sai kuma ya ji kamar ana yi masa dariya.
A hargitse ya farka daidai nan ya ga giftawar gawa cikin likafanin ta fari sol,tsabar tsoro da firgici ya saka sa yin ihu ya na cewa "wayyo Allah"ai kuwa gawar nan ta nufo sa yayi saurin faɗuwa ita kuma ta rufta kansa kawai sai ya tashi zaune ya na ƙyalƙyacewa da dariya.
Ƙyalƙyace-ƙyalcen sa ya tayar da Maryam daga barci,hasken ɗakin ta kunna sai kuwa ta ga Mahomet zaune ya na yin wani abu da hannu kamar mai rabon abinci ya na yi ya na dariya.
Da sauri ta diro daga kan gadon ta dafa sa tace "Mahomet miy..."ba ta samu damar idawa ba saboda gigitacen marin da ya ɗauke ta da shi ya fiddo ido ya na zarar su kafin yace "miyasa za ki taka sa ?ko baki ganin laɓuɓu gaban ki?"da sauri Maryam tayi baya zuciyarta na dukan tamanin-tamanin tsabar tashin hankali.
Ƙofa ta nufa da sauri ya miƙe ya maidota,wani marin ya kuma kai mata yace "wato ba za ki bayar da haƙuri ba?"baki na rawa tace "ku yi haƙuri"Mahomet ya tuntsire da dariya yace "hegiya taji tsoro hhhh"sai kuma ya game fuska ya na yi mata wani irin kallo wanda yasa ta sakin fitsari a wando.
"Laaa !pampo ruwa"ya faɗa tare da duƙawa zai shan fitsarinta da ya fara gangarawa da ƙasa,da sauri ta janyesa sa ta na cewa "kar ka sha fitsari ne,najasa ce"
Kamar mai hankali sai ya ɗago daga durƙushin da yayi yace "Ni ne najasa?"ya ɗaga hannu zai kuma marinta ta ruga a guje ta buɗe ƙofa shi ma ya take mata baya.
Ihu Maryam ta shiga yi wanda ƙarage ko ina,da sauri Daddy wanda ya ke ɗakin Ammi ya fito kallon yadda Maryam ke taka step bibiyu Mahomet na take mata baya sai kuma ƙyarƙyarta dariya ya ke ya sa gaban Daddy faɗuwa da sauri shi ma ya yo ƙasa sai dai ko kafin ya iso tuni Mahomet ya fara jibgar Maryam ita kuwa sai ihu ta ke ta na kiran sunan duk wanda ya zo bakinta.
Daddy ya jawo rigar Mahomet a harzuƙe ya juyo ya yiwa Daddy wata irin bangazar tsiya wacce ta saka shi faɗuwa daidai nan Abbasi ya fito ya na "Innalillahi wa'inna iley raji'un"da ɗan ƙarfi cak Mahomet ya tsaya kafin ya faɗi bisa gwiwoyinsa kamar raƙumi.
Karatu Abbasi ya fara kawai sai ya faɗi kwance ya na kallonsu da ido kamar irin mutumen nan da yayi aiki ya galabaita,Ammi da Inna ma duk sun fito direct gun Maryam suka nufa wacce hancinta ke zubar da jini.
Ruwan sanyi Ammi ta ɗauko ta wanke mata fuskarta nan jinin ya tsaya ashe dama haɓo ne,jikin Inna ta shige ta fashe da kuka.
Ammi ma tuni ta fara hawaye, Abbasi ne kawai mai jarumtar dan Daddy lokacin da ya faɗi bisa hannunsa na hagu ya sauka tuni ya samu gocewa.
Inna ta ja Maryam suka koma part ɗin ta ,Ammi ta je kusan Daddy yayinda Abbasi ke ta aikin yiwa Mahomet karatu.
Washegari
Haka gidan ya tashi jungum tuni an yi ma Daddy ɗori Maryam ma an gasa mata jikinta, Mahomet kuma ya na can cikin ɗaki a kulle sai zage-zage ya ke.
Hajiya Atine sai sake jajatan lamarin ta ke, Bilkisu baki kawai ta taɓe dan dama can ba ta shiga harakar kowa.
Misalin sha ɗayan rana Malam Sabi'u da Dr suka nufi ɗakin da aka rufe Mahomet,ana buɗewa ya zaburo Malam Sabi'u ya watsa masa wasu ruwa kawai sai ya nutsu.
Jininsa Dr ya zuƙa cikin wata ƴar kwalba kafin ya fice ya bar Malam Sabi'u wanda ya riƙe kan Mahomet ya fara karatu.Jujuya kai ya fara ya na son cire hannun malam daga kansa da sauri Abbasi wanda ya laɓe bayan ƙofa ya zo ya riƙe hannuwansa shi ma da ayoyin Allah ga bakinsa.
An ɗauki plus de 30mns amman aljannun da ke kansa sun ƙi yin magana har sai da malam ya haɗa gumi,bakin Mahomet ya taɓe ya zuba masa wani magani nan yayi birkiɗa da ƙasa a ƙarshe barci ya ɗauke sa.
Malam Sabi'u ya girgiza kai yace "manyan sheɗanu ne sun ƙi yin magana ka ga ma barci suka sa shi wanda kuma zai iya kai safiyar gobe bai farka ba"cike da tausayin ɗan uwan na sa Abbasi ya takewa malam baya ya na mai ɗaga kiran Farida da ya shigo wayar shi.
"Allo Abbasss lafiya tun jiya ni ke kiran wayar ka ba ka ɗauka?"cewar Farida , Abbasi ya nisa yace "ina lafiya yayana ne ciwon sa ya motsa kuma babban tashin hankali hauka ya ke na gaske fiye da kullum"Farida ta dafe kai tace "Allah sawaƙa to,nima ga ni nan ina jinyar ƙawata ina ga ita ma ciwon haukan ne ya kamata"da sauri Abbasi yace "subahanallah kar dai ace Hawa ɗin ki?"Farida tace "ita fah kai dai bari rabon ayi jiya mu ka tafi STM mijinta ya turo mata saƙo mun zata abun kirki ne ashe takardar sakinta ce ya saka a enveloppe ya turo mata ,mu na cikin mota ta buɗe saƙon ta na ganin miye a ciki ta buɗe marfin mota ta faɗo yanzu haka ta samu kariya a hannu banda ciwon da taji a kai"salalami Abbasi ya shiga yi tare da jajanta mata.
Balkisu gaban mahaifiyarta ta na shaida mata abinda ya faru da Mahomet daren jiya "tatasss!"kake ji ta wanketa da mari ta na cewa "ashe ba ki da hankali Balkisu?ta yaya za ki yanke ɗanyen aiki ba tare da tambayar izini na ba?fansa za mu ɗauka ta hanyar gurgunta rayuwar Issufu ba wai ɗan sa ba da bai san komi ba"Balkisu na kuka ta ce "to ai ni Ɗan ni ke so ba uban ba miyasa ba ki bar ni na auri Mahomet a madadin Alhaji Issufu?" Mama ta juya baya tace "ba za ki gane ba labarin na da tsayi sosai"
★★★ *ASALIN LABARIN...*
"Yusuf ya kake gani in mun shiga siyasa?"cewar Mahmud ya na mai ɗaukar tufa🍏 ya guntsura,wanda aka kira da Yusuf yayi murmurshi yace "Mahmud ban ƙi ta taka ba sai dai ni a yanzu ba ni da burin da ya wuce uwar ɗakina ta samu ciki yanzu wajen shekaru shidda da aure ko ɓatan wata ba ta taɓa yi ba"Mahmud ya jinjina kai yace "haka ne amman ni ba ka tunanin ko auren banda ai gwara kai ka na da matar ga shi kuma har ka fara neman wani auren na biyu"ƙarar fashewar glass ya saka su duk juyowa su na kallonta ido taf hawaye ta dubi mijin nata tace "yanzu Alhaji har ka fara neman aure saboda rashin haihuwa ta?babu komi Allah ba mu zaman lafiya"ta na gama faɗa za ta juya da sauri Mahmud yace "haba Ammi miye haka dan Allah?a wannan zamanin ai kishiya tamkar yayi ce dan Allah kar ki ɓata ran ki"hawayenta ta goge tace "mai sunan Ɗana ta yaya ba zan yi fushi ba za'a kawo min kishiya babu sanarwa balle har a bani damar shiryawa ko so kake a kawo amarya ta fi Ammin ka?"ta ida zancen cikin sigar zolaya ta na murmurshi wanda ya saka Alhaji jin sanyi a ransa dan dama can yayi farin sani ita mace ce mai sauƙin kai.
Makaranta guda suka yi dukan su uku a aji ɗaya,sunan Ammi ya samo asali ne ranar da Mahmud ya ji ta na cewa in shaa Allah sunan ɗanta na farko Mahmud sai kuma ya zamana babban abokinsa Yusuf ya kasance mijinta.
Bayan kwana biyu da yin wannan zance sai kuwa aka fara maganar kawo amarya,duk rawar ƙafar da Alhaji ke yi Ammi kawar da kai tayi har Allah ya sa amarya Atine ta shigo gidan.
Zaman lafiya suka fara yi da farko,sai dai bayan wata biyu kacal zaman ya sauya sakamakon samun cikin da Atine ta yi shikenan ta fitini Ammi da gori.
Ammi na zaune ta cikin abinci Atine ta fito ta na toshe hanci "ke miye wannan duk ya cika mana gida da ƙauri?"Ammi ba ta tanka ta ba ta cigaba da cin abincin ta,dungure mata kai tayi tace "ke ba da ke na ke ba?"Atine ta faɗa cikin ɗaga murya a hasale Ammi ta tashi ta sharara mata mari Alhaji wanda ya ke daf da shigowa yayi saurin kutso kai kawai sai Atine ta dafe ciki ta na kuka.
Idon Alhaji sun rufe duk da ya ji ƙarar ta mari ce amman yadda Atine ta dafe ciki ya sa ya kai hannu ga Ammi wanda kuma shi ne karon farko tun da ya aureta.
Cikin kuka Ammi tace "Allah nayi imani kai ke badawa kai ke hanawa ya Rabbil Izzati Allah na roƙe ka nima ka ban haihuwa dan alfarmar Manzon Allah SAW"....
[19/02 à 13:19] Mrs SADAUKI 💫: *PAID PAGE 27-28*
*Littafin kuɗi ne ki biya ki karanta hankali kwance ƴar uwa ba tare da kin shiga haƙina ba ki biya 200₦ kacal ki sha karatu in kin shirya kin tuntuɓe Ni ta WhatsApp* +22795045822
MATAN ALBARKA HERBAL MEDICINE
INA KUKE ISASUN MATA MASU AJI MASU DARSJA DA GIRMA MU MATSO KUJI GA GYARA NA MUSSAMN NA ISASUN MATA MASU AJI
INA MAI MATSALAR SAURIN KAWOWAR MAI GIDA KI ZO GA HADIN NE DA KAI ZAKU SAMU QARFI DA ISASHEN RUWA
MAI FAMA DA BUSHEWAR GABA
MAI BUDEWAR GABA
MAI QAIQAYIN GABA
MAI FITAR RUWA BA KAN GADO
INA MAI SO TA MATSE MUNA DA MAIDA TSOHUWA YArinya
Kuma muna gyara amare gyaran da zai shekara a jikin su ina masu jego
Kuma ga naku gadin ISASUN MATA
Muna gyara dukan matasalolin mata na cikiy Dana waje kedai ki tuntubemu a wanna nombar kuma muna wa,azin aure 08163199051
Sign manager c,e o maman shukura
______________________
Tunda aka shiga da Atine ɗakin haihuwa Alhaji ke zarya ya rasa ƙugun zama,can sai ga nurs ta fito hankali tashe ta na cewa "da matsala Alhaji ka zo ka sa hannu a yi mata aiki a fito da jinjirin nan in ba haka ba za'a iya rasa su dukan biyun azo babu Uwar ba Ɗan"jiki na ɓari Alhaji ya sa hannu aka shigar da Atine.
Babu jimawa aka fito mata da baby boy,nan fah Alhaji ya shiga murna duk da ko an tabbatar masa da an juye mahaifar Atine saboda ta samu matsala.
Ammi da murna ta rungume Ɗan ta na shafar kansa a can ƙasan zuciyarta kuwa addu'a ta ke Allah ya bata haihuwa ita ma ta ga jininta.
Goggon Atine wacce har da ita aka yi rakiya ta karɓe jinjirin ta na cewa "bari a kaisa gun mahaifiyar shi ya ji guminta,tun ɗazu ta farfaɗo amman kin wani riƙe sa sai kace ke kika yi mata wahalar naƙudai"
Ammi tayi murmurshi tace "a'a ita tayi kayarta ban ce ni nayi ba"ta faɗa ta na mai miƙa mata babyn "ah to ina ce dai cikinta ne aka fasa ba na ki ba"cewar goggo Ammi tayi kamar ba ta ji ta ba.
Tun da aka yi haihuwar nan habaici kawai dangin Atine ke yadawa Ammi ba ta tanka su sai dai ta shige ɗaki tayi kuka har ta gode ma Allah,ana haka aka yi biki yaro ya ci sunan Abbas amman uwar shi ta mayar da shi Abbasi.
Tun haihuwar Abbasi Alhaji ya ɗauki son duniya ya ɗora masa musamman da shikaɗai ne Allah ya basa,Atine an samu abinda ake so kullum ta na maƙale da Alhaji su na yiwa yaron su wasa.
Abbasi na da wata tara ya fara tafiya ya iywa nan ɓanar sa ta ƙaru sunan Daddy kawai ya iya.
"Ɗan so zo na baka wainar ƙwai zo dawo kar ka fita"Atine ke faɗa ta na yiwa Abbasi magana wanda sai ƙiriniya ya ke sai yayi kamar zai tafi gun Daddy sai kuma ya nufi hanyar fita,dakyar ta samu ta kamo sa ta zaunar da shi sannan ta buɗe kwanon wainar ƙwan iskanta ya bugi hancin Ammi da gudu ta nufi toilet ɗin falo ta shiga kelaya amai.
Dukkansu bayanta suka bi da kallo kafin Daddy ya mara mata baya ganin ta jima ba ta fito ba,ƙugunta ya riƙe ya na ɗan bubuga bayanta har sai da ta gama ya taimaka mata ta wanke fuska da baki ya kamota zuwa falo.
Hanci ta toshe ta na girgiza kai,ɗakinta ya kaita kafin ya ɗauki waya ya kira Mahmud bugu biyu ya ɗaga ya na cewa "aboki yanzu ni ke shirin kiran ka na shaida maka an ɗaga ranar bikin an maido shi nan da wata uku"Daddy yace "kuma dai shine kuma ka yarda?"Mahmud yace "to ya zan yi tunda amaryar ta zamana ƴar rigima" Daddy yayi murmurshi mai sauti yace "to Allah kai mu ya sa alkhairi zuwa wannan lokaci Ammi ɗin ka ta ɗau nauyi ba za ayi hidimar biki da ita ba"Mahmud yace "kai haba?kar