Showing 9001 words to 12000 words out of 41148 words

Chapter 4 - KABEER COMPLETE Book Complete Document by Amina Yakubu.txt

28 Dec 2024

5164

rarrashi na daidai nan rahama ta shigo da gudu tazo ta fisgoni ta hankadani na fadi ta fara balai aidama nasan dole haka saita faru wanan Dan bazan kyaun nata dole ya rudeka aikai ba waliyi bane ni gaskiya ka dauke ta daga gdn nan idan ba haka ba wallahi saina fadawa dad dinka abinda yake faruwa ta karasa mgnr cikin kuka. Kama hannunta yayi suka tafi part dinsu yanata aikin rarrashi dakyar ta hakura.


Washe gari
Da wuri ya shirya saida ya kara rokonta akan don Allah ta rike amanata kafin ya dawo, idan ya dawo zai daukeni daga gdn, ni kuma ya bani hakuri akan nacigaba da jure duk irin wulakancin da zatayi min kafin ya dawo nace to. Yayi mana sallama ya tafi aunty rahama harda kuka wai zatayi missing dinsa, da kyar ya lallabata yayi shiru sanan ya wuce.


10pm
Aunty rahama ce zaune a falo ita da wata cousin dinta hadiya suna zaune suna hira dake kawarta ce dama shiyasa ta kirata tayin kwana. Lbri take bata akaina ita tarasa yanda zatayi dani, kuma ga dukkan alama mijinta sona yake, Amma yanzu na bude wuta nace bazan zauna da ita ba yace idan ya dawo zai dauke ta daga gdn nan. Kaji shirme, aike dama sokuwa ce wani lkcn ina kike tunanin zai kaita idan ya dauke ta? Gida zaije ya kama mata suci karansu ba babbaka, kinga shikenan ya sami gdn Hutu. Nidai idan zaki bi shawarata muje ki koreta adaren nan idan ya dawo ya Tatar bata nan, kai kinaso ya bata min kenan, zai Iya sakina fa akan wanan yarinyar, dalla manta dashi tsakanin mace da miji sai Allah sai kiyi amfani da kissa ki mantar dashi, duk fadan da zaiyi kice bakisan lkcn data fita ba. Dariya tasa suka tafa wanan shawara tayi muje mu sameta. Ina kwance harna fara bacci sainaji muryarsu sama sama, na tashi na bude musu kofa suka shigo hadiya ce ta fara cewa lalle saken naki yayi yawa haka ya gyara mata daki kamar wata matar shi sanan rahama tace ke aysha inaso ki hada komatsanki a Daren nan kifar gdn nan idan kuma ba haka ba zanyiwa mahaifan elbash waya na fada musu ke karuwarsa ce ya kawo ki kike zaune, kuma nayi imani idan dad dinshi yaji saiya kusan tsine mishi, kuma dole kibar gdn Sbd haka ki zafi daya ko ki tafi batare da kin jawo masa fishin iyayensa ba, ko kuma suzo su koreki a wulakance cikin shesshekar kuka nace karki fada musu zan tafi, mikewa nayi na tattara kayana na fice muna tafe tare har mukazo inda zamu rabu, sanan nace don Allah ina Neman alfarma kiyi hakuri nabar motata anan sabd bana Iya long journey da mota, idan kk bar mota nayi aikin banza kenan, Sbd zaki dawo daukar motarki wata ran. Karki damu koda nazo bazan cigaba da zama daku ba, kuma nayi miki alkawari bazan taba fadawa mijinki ke kika Koran ba, nagode da zaman da mukayi dani,kuma don Allah ki yafe min sabd kin shiga tashin hankali a dalilna. Naja trolley na na fice daga gdn, garin yayi duhu banda kukan karnuka ba abinda ake ji ga hadari ya hado sai walkiya ake, tafiya nake Amma bansan Inda zan dosa ba addua nake Allah ya dauki raina na huta Sbd rayuwata bata da sauran amfani ni bakowa bace face annoba, Yessss annoba ce ni sabd duk inda naje guduna ake nayi zurfi a tunani har nahau kan titi ban Sani ba.


Da gudu yake tafiya ya dawo daga wajen meeting, da motoci guda biyu kawai ya fita shi yake tuka motar da Kansa, dayar kuma body guards dinsa ne aciki be Ankara ba kawai yaji ya bige mutun cikin tsananin tashin hankalin ya fito ya dauke ta da gudu yasa a mota suka nufi asibiti


Maman Aysha
[9/17, 20:34] Amina Yakubu: πŸ“πŸ“πŸ“KABEERπŸ“πŸ“
6⃣5βƒ£βž–7⃣0⃣


Gudu yake kamar zai tashi sama, tun kafin ya kara ya sanar da family doctor nsu abinda ya faru, direct asibitin ya nufa, kafin ya karaso nurse din ta hada emergency bed, suna zuwa ya dauko ta da gudu ya shiga ciki, da sauri nurses suka karbeta suka Dora ta akan gadon, vital sign aka fara dauka sanan sukayi elevating bed din aka samata oxygen, akayi setting din cannula aka samata dextrose saline Sbd likita yace hypoglycemia ne, sun dauki blood sample na pcv da blood group, sanan akayi mata wasu allurai. Duk bayan 15 minute ake Chekiang vital sign din har suka dawo normal, pcv din nata da aka duba 28% sai doctor yace basai an kara jini ba. Duk wani emergency care an bata saidai har yanzu bata farfado ba cikin tashin hankali Mr kabeer yace don Allah Dr Abdul ka temakeni kar yarinyar nan ta mutu plisss, yace karka damu nayi mata scanning ko tasamu internal injury, Amma naga every thing is Norma so karka damu insha Allah zata farfado. Kallon guards dinsa yayi yace ina ganin Ku tafi gd ni anan zan kwana, daya daga cikin su me suna rabiu yace haba yallabai kai ka tafi ka huta ni saina kwana da ita, ba matsala rabiu kuje kawai Sbd idan na koma ma fargaba bazata barni nayi bacci ba, to shikenan yallabai saida safe Allah ya kara rufa asiri yace amin.
Dakin da aka kwantar ta special room ne gado guda daya ne a dakin, sai kujera 3 siter, sai TV plasma da reciever sai kuma karamin fridge. Motarsa ya koma yasa wasu substaff maza suka goge jinin daya zuba akayi dis infecting wajen da sprit, sanan ya bude boot din motarsa ya dauko sabuwar jallabiya fara Sol ya koma dakin da Aysha take ya shiga ya rufe da key sanan ya shiga toilet ya cire suit din jikinshi yayi wanka, dake toilet din is very neet, sanan ya saka jallabiyar, ya fito ya kunna A/c dakin, ya kwanta akan kujera. Juyawa yayi ya kalli gadon da take sai yaji yanaso yaga fuskarta Sbd acikin duhu ya kadeta, kuma tunda suka shigo asibitin be kalleta ba. A hankali ya karasa bakin gadon yana dubawa ya ganta .amaki ya kamashi a knli ya furta Aisha Ahamad TURAKI ita na buge dama? To ina zata da tsohon Daren nan? Kuma ina motarta ta fito a kafa? Fuskarta ya zubawa ido yana kallo, a zuciyarsa yace tana da kyau sai rashin kunya, tsaki yayi ya koma ya kwanta.


Washe gari
Da asuba ya tashi yayi sallah, yayi addua sosai akan Allah ya bata lpy. Har nurse din ta shigo medication bata farka ba. Wajen 8:30am doctor ya shigo ya kara dubata yayi mata RBS yaga ya dawo normal, cikin damuwa Mr kabeer yace yanzu ya zanyi doctor karka damu any time zata Iya farfadowa. To shikenan Allah ya temakeni ma nasan iyayenta bari na kirasu na sanar dasu abinda yake faruwa, Dr Abdul yace OK, bari. naje office yace to. Wayarsa ya dauko ya fara dialing bayan anyi picking ya gaishe shi cikin girmamawa sanan ya fara masa bayanin abinda ya faru, saida ya bari ya gama sanan yace OK indai magnar Aysha kake to ba yata bace amma ni na riketa tun tana jaririya, kuma yanzu na koreta Sbd kin bin umarnina da tayi, kuma ni yau Kasan wata hudu kenan ban sata a idona ba. Idan kaga zaka temaka mata to, idan kaga bazaka temaka mata ba shikenan, nidai bani ba ita. Besan lkcn daya kashe wayar ba sabd tsananin mamaki ya kara maimaita mgnr a zuciyarsa bashi ya haifeta ba? Taki bin umarninsa? Kuma bashi ba ita? To meke faruwa da Aysha ne? Matsawa jikin gadon yayi har yanzu tana nan a yadda ya barta nan take yaji tausayinta ya kamashi


Maman Aysha
[9/18, 12:50] Amina Yakubu: πŸ“πŸ“πŸ“KABEERπŸ“πŸ“
7⃣0βƒ£βž–7⃣5⃣


Ya Dade yana kallonta , sanan ya fita zuwa office din Dr Abdul, doctor inaso naje gd nayi wanka, so don Allah wa zaka bani ya zauna da ita kafin na dawo? Zan yiwa nurse luba magna, to shikenan, cikin muryar damuwa yace amma Doctor ina tsoron kar wani Abu ya sameta, tun jiya fa rabonta da abinci, ai da tausayi. Dariya doctor yayi, Mr kabeer ko itace amaryar tamu ne? Naga ka damu da yarinyar sosai, aa wallahi kawai dai INA tausayinta ne, to karka damu zata dawo normal very soon, is alright bari naje na dawo, to shikenan saika dawo. Diriver shi ya aika gdn mum dinshi aka karbo masa break fast yayi wanka yaci abinci sanan ya Dan kwanta sabd jiya beyi baccin kirki ba, duk bayan yan mintuna yana kiran Dr Abdul yaji ko ta farfado, amma har yanzu shiru.


6 hours later
Zaune yake office din doctor cikin tsananin tashin hakli yake cewa Dr Abdul karfa yarinyar nan ta mutu baka sani ba, ace mutun tun jiya har yanzu fata farfado ba? Kafin yayi mgn phone dinsa ta fara kuka yana picking yace ta farfado? alhamdulilla muje Mr kabeer patient dinka ta farfado, da sauri suka shiga dakin likita ya karayi min wasu allurai, sanan yace a bani abinci naci nidai binsu kawai nake da kallo adon gari kawai na gane acikin su to me me yasa aka kawoni nan? Me yahadanida adon gari? Nan take brain dina ta karantomin abubuwan da suka faru, bansan lkcn da nasaki wani irin kuka ba adon gari ne ya kama hannuna ya rakani toilet, ya bani sabon brush da MacLean nayi brush, sanan ya had amin ruwa ya fita nayi wanka, kafin na fito naga ya ajiyemin lotion da perfume da kuma wata shegir bul gown blue damayafinta ya fice, shafa man nayi sanan na dauki rigar nasa na fesa turare. Saida jikin sa ya bashi na gama shirya wa sanan ya shigo dakin dauke da yan ubansun food wormers ya dauki plates ya zubamin abincin da kansa yace na karba naci mamaki ne da kuma tambayoyi fal cikin zuciyata, saidai bazan Iya tambaya ba. Hadadden abinci ne Amma inayin loma biyu naji bazan Iya Ciba kawai sauna ajiye plate din wani irin kallo ya watsa min da bazan Iya fassara abinda yake nufi ba, sanan cikin wata unique voice dinsa yace ko bazaki Iya ci ba nazo na baki? Ya salam kawai na furta a zuciyata, wanan golden voice dinfa kodan mostly idan mun hadu da fada muke rabuwa shiyasa bansan voice dinsa ba, can't you answer me? Naji daddadar muryar shi ta daki kunnena, bani da apatite ne na bashi amsa a kasalance, OK Amma da kin daure kinci ko kadan ne, Sbd kusan 24hours kenan bakici komai ba, idan kuma akwai abinda kike sha'awa ki fada na sayo miki yanzu, nace ba komai nagode.


2 hours later
Tare suka shigo shida Dr Abdul da Suleiman PA doctor ya kalleni yace ya jikin? Da sauki, Allah ya kara sauki nace amin, na sallame ki zaku tafi gd yanzu akwai drugs din Dana rubuta zai baki ki tabbatar kina sha kinji ko nace to, shikenan yallabai zaku Iya tafiya to nagode doctor, zaki Iya tashi ko na taimaka miki? Zan Iya, to saukko muje ina fara tgy naji jiri yana kwasata, na tafi zan fadi da gudu ya rikeni aidama nasan bazaki Iya ba shiyasa na tambayeki, tallafoni yayi muka karasa har bakin mota ya bude min na shiga sanan ya zagaya ta daya bangaran ya zauna Suleiman PA ya zauna a gaba, driver ya tashi motar muka fita daga asibitin gabana banda faduwa ba abinda yake, Sbd ina tsoro kar ya maida ni gida phone dinsa ce ta fara kuka yana dauka yace hlo Yaya Salma kin wuni lpy? Lpy kalau Broz, ga babynka ta dameni da rigima wai yau tru out baka kirata ba, ayya bani ita hlo my baby stop crying, ko kinaso nima nayi kuka? Aa na daina, yauwa gud girl, to uncle yaushe zakazo very soon zaka sayomin ice cream? Har chocolate zan kawo miki, thanks uncle bazan kara kuka ba yawwa gud girl saina zo bawa mamanki, hlo my sis nayi missing dinku da yawa wallahi may na shigo abj next WK, I miss you too Broz, OK saika zo dama inason ganin ka nayi maka budurwa idan kazo mayi mgnr, wata yar iskar dariya yayi yace gud nyt. Driver ne ya juyo yace yallabai ina zamu? Kaimu gd, muna zuwa ya matsa remote katon gate din ya bude muka shiga, shi ya temaka min muka shiga har cikin gdn fadar kyau da tsarayuwar gdn bazai yiyyu anan ba, nidai nace Allah ya yi mana arziki na halal. Wani daki ya shiga dani na zauna a bakin gado sanan ya kalleni me kike shawa akawo miki kici? Nayi shiru, Aysha dake nake magana fa wayyo Allah nace a zuciyata mutumin nan yana Neman kashe ni da unique voice dinsa Ashe wasu irin qualities yake dauke dasu shiyasa yan mata suke manne masa? Can't you answer me? A firgice nace ice cream, wani shu'umin kallo ya watsamin ice cream abinci ne? Mostly idan nasha da cake shikenan ba saina ci abinci ba, fita yayi ya kawo min da cake din ya fice, nima ina gama saha na kwanta


Maman Aysha
[9/18, 14:31] Amina Yakubu: πŸ“πŸ“πŸ“KABEERπŸ“πŸ“
7⃣5βƒ£βž–8⃣0⃣
Ban farka ba sai asuba, ina tashi nayi alwala nayi sallah dake yasa an shigo min da trolley na saina bude na dauko alkur'ani na fara karatu daga yussabihu zuwa kasa, a massalacin gdnsa yayi sallah dake akwai liman yana biyansa duk wata so har makotan gdnsa ma suna zuwa sallah massalacin. Yana shiga falon yaji kira'arta me dadin gaske tana tashi kawai saiya samu waje a falon ya zauna yana bin surar da take a hankali dake shima ya sauke. Haka yaita bin duk surar da take karantawa har saida nakai suratul nazi'at, kawai sai kuka yaci karfina nan take na fara addua ya Allah kafi kowa sanin halin da nake ciki bani D's kowa, Allah kafi kowa sanin ba wani mutun da zan Iya nunawa a matsayin Dan Uwana na jini, ya Allah ka Sani tunda nazo duniya banji dimin da yakeji agun mahaifiyarsa ba, idan har iyayena sunada rai ya Allah kai gaggawar hadani dasu, idan kuma basa raye kayi gaggwar daukar raina na bisu inda suka tafi kuka sosai nake da har nakasa control din kaina. Ji nayi an rukoni, ina daugowa muka hada ido dashi Aysha me yasameki? Ko jikin ne? Nace aa, to fadamin me ya faru? Nace ba komai are you sure ba abinda yake damunki nace eh, to karna kara jin kukanki kinji? Nace to. Yana fita naje nayi wanka nasa wasu Riga da siket na atamfa, pink and white ne kalar atamfar saina dauki hijabi pink nasa, na dauki hand bag dina daya hannun kuma naja trolley din na fice daga dakin a falo na sameshi ya zabga uban tagumi nace ni zanje na tafi, nagode da temakon da kayimin Allah ya saka maka da gdn aljanna. Harna juya na fara tafy naji yace Aysha tsaya, cak na tsaya ba tare da najuyo ba wane irin sauri kike zaki tafi baki karya ba? Daga tafiya na dawo ne ko gd banje ba ka bugeni, so nasan yanzu hankalin yan gdnmu dole a tashe yake, yess I see, hanklinsu yana tashe Amma ko media basu bada cikiyarki ba yau kwana biyu? Zo ki zauna akwai mgnr da nake so dake, banyi musu ba naje na zauna, sanan ya dubeni yace baki mamaki ba dana taho dake gdn, instead of na wuce dake gdnku? Yaci gaba da magana washegarin ranar da abin ya faru na kira dad dinki nayi mishi bayanin cewa na bugeki da mota kina asibiti unconsciousness, me makon ya tausaya yanda kowanne uba yakewa dansa idan Abu ya faru, saiya jefeni da wasu maganganu da nake son jin amsarsu daga gareki, Aysha zan tambayeki bana son kimin karya, Sbd ba mutumin dana tsana irin munafiki, makaryaci da kuma me cin amana, so pliss I want you to tell me d truth. Tambayata ta farko wane irin umarni dad dinki ya baki kika ki yi? Yace rabonsa dake kusan wata hudu kenan, a gdn wa kike bayan kin bar gdnsa? Sanan daga ina kike lokcn dana kadeki? Cikin nutsuwa na fara bashi lbri tun daga ranar da deputy governor yace yana sona, korata da daddy yayi, zama agdn elbash aikin dana fara da kuma korata da matar elbash tayi Wanda shine sanadiyar fitowata harka kade ni. Saida ya zubda hawaye don tausayi sanan yace kin tabbata lbrn da kika fadamin gasky ne? Nace eh, yace to karki damu naji duk adduar da kikayi dazu bazan boye miki ba da natsaneki Sbd rashin kunyar da ki kayimin, da kuma tozartani da kikayi a media, Amma yanzu na hakura kuma zan temaka miki, zan baki daya daga cikin gdajena ki zauna, zan nemo miki wata tsohuwa data tafa aiki a gdnmu mutuniyar kirki ce Ku zauna tare, sanan zan daukeki aiki a matsayin sakatariya ta, Amma inaso ki tsare mutuncin kanki. Insha Allah zanyi nagode Allah ya saka da alkairi, amin, idan yaso Monday saiki fara fita


Maman Aysha
[10/14, 9:52 PM] Chopy: [9/20, 10:13] Amina Yakubu: πŸ“πŸ“πŸ“KABEERπŸ“πŸ“
8⃣0βƒ£βž–8⃣5⃣


A ranar yaje gwamai ya dauko baba mero, ya direct gdn daya bamu mu zauna a lamido crecent ya wuce da ita ya sami almajirai suka tayata gyarn gdn, sanan yaje mall dinshi ya iyo mana provision, duk wani Abu da Kasan ana bukata a gd adon gari ya sayo mana, har detergents saida ya siyo, ya sayo mana gas cooker da cylinder saida ya tabbatar komai yayi normal sanan ya dawo gd. Ni kuwa tunda ya fita nake bacci ban farka ba sai after 3 toilet na shiga nayi wanka nayi alwala INA sallah naji motsin shigowarsa, bayan na idar nayi addua saina fita a dinning na same shi har yayi wanka yasa wasu shegun blue shirt da black jeans saida na Dan rusuna nace ina wuni? Ba tare daya kalleni ba yace lpy INA gajiya, ya jikin? Nace da sauki hankalinsa gabadaya akan phone dinsa yake, shiyasa na sami damar kare masa kallo

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login