Showing 36001 words to 39000 words out of 69452 words
Chapter 13 - BAKAR DAULA BOOK COMPLETE DOCUMENT BY Ameera Adam.txt
yake da kawuna huɗu kowanne da surarsa. Akwai kai mai siffar jaki, agwagwa, mage da mai siffar kifi, a kowanne kai akwai manya kahunhuna guda biyu, daga jelar hallitar ɗauke take da tafkeken kan maciji. Yana zuwa ya ɗora shi a gefenta sannan ya ɗaga hannunta ya tura shi ƙarƙashin jikinta kamar yadda uwa take rungume jaririnta. Nesa da su ya koma yana sakin murmushin farinciki a fili ya fara faɗin, "Na jima ina burin haka ban samu dama ba domin gudin abin da zai ɓata miki rai, sai dai a wannan karon dole na ɗau wannan matakin domin haka ne kaɗai sai tseratar da ke daga kaidin Mugaza, idan ba haka ba duk yadda za ta yi sai ta halaka min ku. Ni kuma ba zan juri rabuwa da ke ba wanda ya nemi raba ni da ku zan iya hallaka shi ko wanene, ko da kuwa Mahaifina ne Jingas." Yana gama magana ya ɗaga dutsen da Raihan take kwance da jaririnta, naɗe su ya yi cikin wani kogon dutse sannan ya hura wani kogi da korayen kifayen nan suke ciki, nan take ruwan ya dare Huzaifa ya jefa su ciki ya sake hura ruwan ya haɗe gabaɗaya.
Mommy na daga falo ta fara jiyo muryar Goggo na ƙwala mata kira, da sauri ta nufi wurin da ta ji muryar Goggo tana zuwa ta yi turus ganin Goggo na rarrafe daga ita sai ɗan fatari. Da sauri ta sunkuya tana faɗin, "Goggo lafiya kuwa ko ƙafar ce ta motsa?" Tun bata rufe baki ba Goggo ta ci gaba da faɗin, "Abu ki dubi Allah da ma'aiki ka mayar da ni Albasu wallahi na yafe zaman gidanki, ki maida ni Albasu na mutu cikin aminci tun bata tsaface ni a gidan nan ba." Goggo na maganar hawaye da majina na zuba, a gefe ɗaya fitsari ne ke zuba don Goggo ta yi fitsari daga ɗakin Raihan zuwa babban falo ya kai sau uku.
A ɗan tsorace Mommy ta waiga tana faɗin, "Goggo lafiya kuwa wace ce ta zama matsafiya?" Goggo ta fyace majina da gefen zaninta ta ce, "Wa kuwa kika sani idan ba Rehanu ba. Wallahi yadda na ga tana tsafi ido biyu na ga Annabi haka..." Tun bata ƙarasa maganar ba Mommy ta fara waige tana katseta da sauri cikin ƙasa-ƙasa da murya.
"Goggo don Allah ki daina faɗin haka wallahi Alhaji yana gida kar ya ji abin da kike faɗa, kin san fa baya kawaici a kan yarinyar nan Raihan." Tana rufe baki Inno ta ƙaraso wurin tana faɗin, "Allah ya tonu asirinku, ashe gulmar Ɗana kuke da jikalleta to ahir ɗinku wallahi ke Zinaru ki yi ta kanki arziƙi kika zo ci ba zan miki baƙin ciki ba, gida dai gidan Ɗana ne ba a isa a sawa jikata ido." Goggo takaici ya sake cikata tana ganin kamar gori Inno take yi mata, don haka a zafafe ta ce, "Allah ya sa ni na haifi Abulle har ɗan naki ya aura, magana ce na gama ta yau za a mayar da ni Albasu don wannan sheɗaniyar jikar taki ba za ta sayar da kaina ina ji ina gani ba." Inno na jin haka ta yi zaman ƴan bori daɓar sai kawai ta fashe da kuka, da sauri Mommy ta koma wurinta tana rarrashinta amma fir taƙi yin shiru. Suna nan zaune Alhaji Abdallah ya sauko cikin dakakkiyar shadda ruwan toka da hula baƙa, kayan ba ƙaramin kyau suka yi masa ba. Tun kafin ya ƙaraso Mommy ta fisge ɗankwalinta ta rufawa Goggo, yana ƙarasowa ya ce, "Lafiya dai Inno mai yake faruwa?" Inno na jin haka ta rushe da kuka tana faɗin, "Audullahi ka dubi irin sitirar da ka yi wa Zinaru ita da ƴarta amma da yake sun samu wuri wai cin naman ka suke da ƴarka ɗaya tilo a gidan duniya. Don Allah ko don darajar haihuwa Abulle ai da ɗagawa yarinyar nan ƙafa ina dalili tana uwarta tana cin namanta?" Goggo ta ƙanƙance ido cikin masifa ta ce:
"Audullahi wallahi tun wuri ka san halin da kake ciki, kwarankwatsa dubi Rehanu ta shiga ƙungiyar asiri."
Kamar wanda aka zagi iyayensa haka Alhaji ya ɓata fuska sai da ya haɗiyi yawu mai ɗaci ya ce, "Goggo kin san wa kike faɗa kuwa? Raihan ɗina ce ta shiga ƙungiyar asiri?"
"Ƙarya na yi maka kenan Audullahi?" Goggo ta tambaye shi tana ɗage kai gefe. Shiru ya yi don ya san idan ya buɗe baki a kan Raihan za a iya samun matsala shi kuma yana ganin girman Mahaifiyar matarsa, ba zai so wani abu ya haɗa su ta sanadiyyar Raihan ba. Ganin haka ya sa Mommy ta riƙo hannun Goggo tana cewa, "Goggo ta so mu je ɗaki don Allah." Inno na ganin haka ta fashe da kuka tana faɗin:
"Allah ya fini sanin dalilin da ya sa bai bani ƴa mace ba, amma ya yi mini komai da ya bani Audullahi da ban haihu ba sai na rasa mai kaini ɗaki nima." Tana gama maganar ta kalli Alhaji ta ci gaba da cewa, "Audullahi nima ka kaini ɗaki ba sai an goranta min ba, kuma wallahi aure za ka ƙara don ba za ka zauna da macen da bata ganin mutumcina ba."
Daddy na shirin yin magana suka ji Raihan ta turo ƙofa ta fito fuskarta murtuk babu fara'a, da sauri Goggo ta fara ja baya tana leƙenta. Daddy na ganinta ya saki murmushi ya rungumota yana faɗin, "Barka da fitowa habibtyn daddy." ƙarasowa wurin ta yi ta ce, "Daddy ba dai fita za ka yi ba?" riƙo hannunta ya yi ya ce, "Yanzu ma kuwa don na gama komai."
Fisge hannunta ta yi ta koma kan kujera tana faɗin, "Na faɗa maka gaskiya za ka yarda?" Murmushi ya yi ya ƙarasa wurinta ya ce, "Faɗi babyna."
"Ka haƙura da fita da baƙar mota idan ba haka ba za a samu matsala."
Mommy ta kalle ta tana faɗin, "Raihan me ya sa bakinki baya furta alheri ne? Ke kin san gaibu ne da za ki yanke masa wannan hukuncin." Goggo da ke gefe tana son yin magana tsoro ya hanata. Daddy ya gyara zaman agogonsa yana faɗin, "Baby sai abin da kika ce da wacce kike son da ita." Daga wurin da take ta ce, "Kowacce ka yi niyyar fita da ita amma ban da baƙar." Daga haka sallama ya yi musu Mommy ta wuce raka shi, Raihan na ganin haka ta ƙarasa gaban Goggo ta tsugunna a wurinta tana faɗin, "Wallahi na kuma jin kin danganta ni da ƙungiyar asiri Allah za ki yi mamakina, sai na kaiki Daulatul Jinnul nariy na azabtar da ke." Inno da ke gefe ta karɓe zancen da faɗin, "Wallahi kema kya gaya mata ai ni wallahi ban yafe wannan ƙazafin da ta yi miki ba. Ni dai wannan larabcin da kika yi ne ban san me kika faɗa ba, amma idan za ki tafi da ita don Allah ki kaini na ga yadda Zinaru za ta yabawa aya zaƙinta." Raihan bata bi ta kansu ba ta wuce kan dianning table, saboda yadda yunwa take sasaƙar cikinta don abincin da ta ci babu in da yaje mata. Tana zama ta fara buɗe kulolin da ke wurin nan take ta fara tasa kulolin a gaba, ɗaya bayan ɗaya tana cinyewa, kuloli huɗu ne a wurin amma da zaman ta ko minti biyar bata yi ba ta cinye abincin ciki gabaɗaya, tare da shanye shayin da ke cikin fulas ɗin ta kora da ruwa sannan ta dawo falo ta zauna. Lokacin da ta dawo tuni su Inno sun wuce sashensu don haka basu lura da abin da Jabun Raihan ta aiwatar ba.
Sanyin da yake busawa a wurin ne ya doki gangar jikinta wanda ya sa ta buɗe idanunta a hankali tana ƙarewa wurin kallo, cikin rashin ƙwarin jiki ta miƙe zaune har lokacin kallon wurin take yi da tsananin mamaki. A hankali wannan jaririyar hallitar ta fara matsowa har sai da ta hau cinyar Raihan, zamanta a cinyarta ya sa ta lura da wurin a zabure ta miƙe tana ƙwalla ƙara haɗe da ja da baya zafin buguwar ya sa hallitar yin can gefe wanda yake nuni da jin zafin da ta yi. Waige-waige ta fara yi tana ambatar sunan mahaifiyarta, kamar daga sama ta riski muryar Mommynta tana faɗin, "Ga ni nan zuwa Raihan."
Tafiya ta fara yi daga wurin da ta fara jin sautin muryar, ta wani lungu ta hango Mommynta ta fito cikin doguwar rigar shadda tana sakar mata murmushi, kallo ɗaya ta yi mata ta ji gabanta ya yu mummunan faɗuwa. Dafa Raihan ta yi tana faɗin, "Kin tashi Raihan?"
Kuka Raihan ta fashe da shi tana faɗin, "Mommy ina ne nan menene wancan abin?" Ta ƙarasa maganar tana nuna wurin da wannan hallitar take rarrafowa a hankali, Mommy ta kalli wurin tana murmushi ta ce, "Taho mu je ki rabu da wancen abin." Har sun fara tafiya Mommy ta kalli Raihan ta ce, "Amma duk wanda zai ce miki ki bishi kar kije wurinsa cutar da ke zai yi ni ce mahaifiyarki babu abin da zan yi miki." Har lokacin Raihan a tsorace take don haka ta kalli yanayin wurin ta ce, "Amma mommy ya aka yi muka zo nan?" A ɗan tsawace ta ce mata:
"Za ki taho ko tambaya ta za ki tsaya yi." Ba musu Raihan ta bi bayan wacce take gani da siffar Mommynta, har sun kusa fita sai gani ta yi Daddynta ya diro da ƙarfin gaske yana faɗin, "Raihan." Da sauri ta waiga wurinsa tana shirin yin magana mai ɗauke da siffar Mommynta ta fara fisgar hannunta tana faɗin, "Karki saurare shi wuce mu je." Da sauri ya ƙaraso wurin rai a ɓace ya fisgi hannun Raihan sannan ya dubi Mai ɗauke da siffar Mommy yana faɗin, "Mugaza ki shiga taitayinki fa, na gaya miki ki fita harkar yarinyar nan ba na son na hukuntaki a kanta amma wallahi idan kika illatata sai na baki mamaki." Lokaci ɗaya ta rikiɗa zuwa wata mummunar hallita mai ɗauke da siffar ƙadangare sai dai kawunanta goma kowanne ɗauke yake da wasu irin manyan harsuna masu kama da kaifin takobi. Da gudu Raihan ta rungume mai ɗauke da siffar mahaifinta tana wani irin kuka tare da faɗin, "Daddy tsoro nake ji." Ilahirin jikinta ban da rawa babu abin da yake yi, rumgume ta ya yi tsam a jikinsa yana shafa bayanta cikin wata irin soyayyarta da take fisgarsa, don karta fahimci wani abu ya sa ya iya riƙe kansa ba tare da kusanceta ba. Wannan abin ba ƙaramin ɓata ran Mugaza ya yi ba, a shammace ta kaiwa Raihan cafka da ɗaya daga cikin harshenta a ƙafa, da sauri Huzaifa ya janyeta amma sai da harshen nata ya samu ƙafarta. Wata uwar ƙara ta ƙwalla sannan ta faɗa jikin Huzaifa wanda yake nuna suma ta yi.
Wata irin mahaukaciyar dariya Mugaza ta fara ƙyaƙyatawa lokaci ɗaya ta murtuke fuska tana faɗin, "Ki je ki da wannan damuwar zan baki rata kafin na sake waiwayo ki." Tana gama maganar ta ɓace daga wurin.
Cike da tausayi Huzaifa da ke ɗauke siffar Daddy ya shimfiɗar da Raihan, a daidai wannan lokacin jaririn hallitar nan ya ƙaraso wurin ya kwantar da kansa a jikinta. Hannu biyu Huzaifa ya sa ya ɗago jaririn idanunsa ɗauke da ƙwallah ya ce, "Mahaifiyarka na fuskantar ƙalubalen rayuwa, amma daga yanzu zan tsaya mata tsayin daka don kare martaba da ƙimarta." Yana gama maganar ya sake ɗora mata shi a kanta yana motsa baki, lokaci ɗaya jaririn hallitar ya ɓace.
Yana ganin ɓacewarsa ya kalli Raihan da ke kwance ya ce, "Daga yau za ka kasance tare da Mahaifiyarka ko baby komai za ka riƙa ankarar da ni kamar yadda ka ankarar da ni kafin Mugaza ta cimma ƙuduri a kanta."
Share hilis🌚
Ummou Aslam Bint Adam🌚
[11/5, 3:26 PM] Mai Agogo: *ZAUJATU JINNUL-ASHIQ*
© *AMEERA ADAM*
Littafin kuɗi ne idan kina buƙata 300 ne ta Account 3090957579 Aisha Adam, First bank. Za ki turo evidence ta wannan lambar 0706 206 2624 Whatsapp only Idan kati ne 300 MTN.
*FIRST CLASS WRITER'S ASSO...*
https://chat.whatsapp.com/J0qrgC0rXNQ57u50VzeewR
FREE PAGE 1
Girma da nauyin cikin da ke jikinta kamar an kifa ƙwarya, bai hanata gudun da take yi na ceton rai ba. Gudu take zabgawa saboda miyagun hallitun da ta yi tozali da su, masu kawo mata farmaki da zimmar cafkar tsohon cikin da ya yi tsini tamkar zai fashe.
Zuwanta bakin wata bishiyar kuka mai duhun gaske ya bata damar tsugunnawa cikin haki, saboda ji take kamar bayanta zai ɓalle gida biyu saboda azaba, ajiyar zuciya take saukewa akai-akai kamar wacce ta shekara tana matsanancin gudu a tsakiyar rani. Dafe bayanta ta yi wani irin azabar ciwon baya da mara ya sarƙeta kamar ana tsaga marar tata da kaifaffiyar aska. Sannu a hankali ta waiga bayanta don ganin mummunar halittar da ke bibiyarta kamar yanda inuwar mutum take bibiyarsa. Kukan jarirai ne ya fara yi mata amsa kuwwa kamar saukar aradu a tsakiyar ka! Ta ko ina take jin sautin kukan na su kamar kunnuwanta za su tawatse.
Kuka haɗe da dariya ne suke ta shi a cikin dajin, zuwa can ta hango inuwar wata hallita na tunkaro ta, matsananciyar guguwa ce ke tashi bishiyoyi na kaɗawa da ƙarfa yanda kasan za su jijjigo daga jikin jijiyoyinsu.
Cikin wani irin gwamamman yare ta riski muryar inuwar tana cewa, "Sai kin halaka ke da abin da yake cikinki, kin zama halakakkiya keda tsiron da ke cikinki." Ba ta yi aune ba ta fara jin abu na bin ƙafarta zuu! A daidai lokacin da ta ji wani irin nishi ya taso mata.
Durƙushewa ta yi a wurin tana murƙususu, nan take wani irin kukan Jarirai mai haɗe da kukan Jaki ya fara karaɗe lungu da saƙon da ke cikin dajin tamkar zai tsage gida biyu. Sannu a hankali Jarirai suka fara rarrafowa suna zageta kamar ana zagaye wainar gero. Duk da halin da take ciki bai hanata yunƙurin tashi domin tseratar da rayuwarta ba, amma ina! Haihuwa ta tunkarota gadan-gadan nan take jaririn ya faɗo.
Sannu a hankali ya rinƙa bin duk wurin da jini ya zuba yana lasa shi da sauran 'yan uwansa Jarirai, tamkar waɗanɗa suke da'irar ƙungiyar asiri. Raihan da ke durƙushe da sauri ta zabura kamar wacce aka ɗanawa ruwan dalma, tana yunƙurin tashi nan take mabiyiya ta faɗo. Kamar yanda Kura take ƙishirwar nama haka suka afkawa Mabiyyar kafin wani lokaci tuni suka gama da ita.
Kamar haɗin baki haka suka waiwayi wurin da take tsaye, tamkar 'ya'yan Birrai haka suka fara tsalle suna ɗane jikinta har Allah ya basu nasarar hawa jikinta. Lokaci ɗaya suka fara lasar jikinta, ihu take kurmawa kamar zautacciya amma babu ɗaya daga cikinsu da ya yi alamun dakatawa. Daga can ƙafarta ta hango Jaririn da ya fito daga jikinta yana bin jinin ƙafarta yana lasa. A haukace ta ƙwalla ƙara tana ambatar sunan Mahaifiyarta kamar wacce ake zare wa rai.
Firgigit ta farka daga bacci tana sauke ajiyar zuciya kamar wacce ta ci gasar tseren gudu, jikinta rawa yake kamar mazari, ta haɗa gumi sharkaf kamar wacce take gaban maƙera.
"Barka da tashi ranki shi daɗe." Ba ta yi aune ba ta ji kalaman Mama Uwani a tsakiyar kanta. Da sauri ta ɗago ta kalle ta har lokacin jikinta rawa yake, sai da ta jingina da bangon gadon ta lumshe ido tana sauke ajiyar zuciya ta ce, "Yauwa Mama Uwani."
"Kina buƙatar wani abu?"
Girgiza mata kai ta yi tana murza idanu, hamma ta yi haɗe da miƙa sannan ta dubi Mama Uwani tana faɗin, "Mama Uwani ki haɗa min Tea kafin na fito." Cike da girmamawa Mama Uwani ya russuna tana faɗin, "An gama shalelen Uwani, gabanki gata bayanki gata. Duk abin da kika faɗa haka za a yi uwar ɗakina." Tana gama maganar ta fice daga ɗakin, Raihan miƙewa ta yi tana ɗan waƙe-waƙenta sannan ta faɗa toilet don ɗaura alwalar sallar asuba. Sai dai rana ta buɗe sosai wacce take nuni da gari ya waye tangararan don ƙarfe tara har da kwata a lokacin.
Sai dai har lokacin mafarkin da ta yi bai gama sakin jikinta, wani abin da ya bata mamaki bai wuce zuwan period ɗin ta ba alhalin ba lokacin zuwansa ba ne.
Mama Uwani tana fita bayan Raihan ta shiga toilet wata baƙar mage ce ta ratso daga bangon kusurwar ɗakin, idanunta jawur suke kamar gauta ga ƙarshen jelarta wani tafkeken kan maciji ne ban da sheƙi babu abin da yake yi. Kalle-kalle ta fara yi tana shine-shine sannan ta fara girgiza cikin wani irin yanayi, lokaci ɗaya ta fara rikiɗa zuwa kaloli daban-daban. Sai da ta rikiɗa zuwa kaloli sama da goma sannan ta dawo kalarta ta farko, ta buga tsalle zuwa kan gadon da Raihan ta tashi wanda har ya ɗan fara ɓaci da jini. Tana hawa kai ta fara lasa sai da ta siɗe shi tas sannan ta sauko cikin takun ƙasaita tana kalle-kalle, a hankali ta taka zuwa kan mudubin Raihan da ke cike da kayan shafe-shafe da turarruka kala-kala.
Girgiza ta yi lokaci ɗaya ta rike zuwa wata mummunar hallita mai siffar dorinar ruwa da ranƙwalelen ƙaho a goshinta, a hankali ta fara zuƙe mayuka da tururrukan da ke cikin kwalabe da robobinsu, nan take komai ya zama wayam babu komai a ciki. Wani irin ruwa ta shiga ɗurawa mai yauƙi sai da ta gama cika su sannan ta hura iska suka dawo tamkar mayuka da turarrrukan da ke ciki da farko. Mama Uwani ce ta tunkaro ƙofar da sauri wannan hallitar ta sake rikiɗewa zuwa mage wannan karon jelar rabuwa ta yi gida biyu dukkansu ɗauke da kan maciji. Tana jin alamun buɗe ƙofa da sauri ta ratse ta jikin bango ta ɓace daga ɗakin, sai dai takaicinta ɗaya da bata samu ta ƙarasa cimma abin da yake tafe da ita ba.
Mama Uwani jere kayan abincin Raihan ta fara yi, a daidai lokacin Raihan ta fito ɗaure da towel. Da murmushi Mama Uwani ta riƙo hannunta tana faɗin, "Ƴar gatan Uwani me kike buƙata