Showing 9001 words to 12000 words out of 69452 words

Chapter 4 - BAKAR DAULA BOOK COMPLETE DOCUMENT BY Ameera Adam.txt

Advertisement

04 Jan 2025

6132

haɗe da kifa kanta a ƙasa tana ci gaba ta rusa kuka mai cin zuciya. Da ƙarfin gaske suka fisge ta duk irin magiyar da take yi musu bai sa sun saurara mata, saboda sanin kansu ne matuƙar suka saɓa wa umarnin Sarkin Damina tabbas za su tsinci talatarsu a laraba domin na su hukuncin sai ya ninka nata sau dubu.


Suna gab da shiga ɗakin, Mai babbar turaka ta dubi Nalami dogari cikin karayar zuci ta furta, "Ka taimaka ka bar ni ko na taƙi kaɗan ne zan bar musu wasiyyar da ba na son ku buɗe ta har sai bayan babu rayuwata. Jikinsu ne ya yi sanyi duk da kasancewar ba sa daga cikin masu tausayi, ganin tausayi na neman tasiri a zuciyarsu ya sa suka fisge ta da ƙarfin tsiya. Kamar mayunwacin zaki haka Yarima ya kurma wata uwar ƙara haɗe da janyo Mai babbar turaka da ƙarfin tsiya, ganyan da ke maƙale a ƙugunta da ƙirjinta ne ya faɗi gefe Yarima ya haɗe ta da jikinta tare da sauke buƙatarsa a haukaca akanta. Cikin fitar hayyaci ta riƙa ambatar sunan Damina tana tsine masa da aibanta shi da miyagun kalamai marasa daɗin saurare, sai da Yarima ya dawo cikin hayyacinsa ya fahimci Mai babbar turaka ta galabaita. A wahalce ta dubi Yarima yana faɗin, "Yarima mahaifinka ya yi min abin da ba zai taɓa albarka ba, akwai laƙanin da nake son taimakon wannan daular da shi amma yana cikin turakata..." Da sauri Yarima ya tallafo kanta yana faɗin, "Laƙanin me ye kar ki tafi ba ki gaya min ba." Cikin kakari ta furta, "Ka tabbatar da ka yi tozali da sabuwar sarauniyarmu kuma ita ce za ta ɗauko..." Daga haka harshenta ya sarƙe idanunta suka ƙafe ta faɗi matacciya.


Zuwanmu tsibirin keda wuya muka samu dubbannin jama'ar yankinmu sun yi dafifi akan tsiribirin, da yake duk ranar talata da daddare muna taruwa akan tsibirin domin miƙa buƙatunmu ga abar bauta. Mun yi amanna akan duk wanda ya faɗi buƙatarsa a kan tsibirin tabbas buƙatarsa za ta biya. Kasancewar sun lura da halin da nake ciki ya sa suka buɗe min hanya muka wuce don isa ga abar bauta saboda akwai ƙudurin da nake son sanar da ita duba da rikitattun al'amuran da suke baƙuntar rayuwata. Muna gab da ƙarasawa muka riski sautin wakiliyar Abar bauta, ba mu sake tsinkewa daga lamarin ba sai da muka yi tozali da ita ta fito matsayar da ko a tarihin rayuwa ban taɓa jin ta fito harabar wurin ba. Kamar ɗaukewar ruwa sama haka wurin ya yi tsit kowanne ya baje majiyar sauti da maganansa, ko a mafariki ban taɓa tozali da siffar wakiliyar Abar bauta ba sai dai labarin da magaba suke ba mu akan samuwarta da tasirinta ga rayuwarmu.Tun bayan kafuwar yakinmu a tarihin da muka taɓa fuskanta, abar bautar wancen yankin bata taɓa fito wa ba sai a ranar da wani mummunan al'amari ya faru da su wanda sanadin haka ya sa aka kafa tarihi har muka mayar da ranar Talata a matsayin ranar karɓar addu'a kuma ranar biyan buƙata, domin a cikinta ne al'ummar Maharba suka samu ƙarfin iko da nasara akan Baƙar Daular da ke gaba da yankinmu. Sannan mahaifina ya tabbatar min a bisa al'ada duk lokacin da Abar bauta ta bayyana akwai wani mummunan al'amari da zai faru wanda zai hargitsa al'ummarmu. Ban gama dawo wa daga duniyar tunani ba na riski sautinta tana faɗin, "Ya waɗannan al'aumma yau na bayyana kaina ne domin na shaida muku mummunan al'amarin da yake tunkaro mu kwatankwacin mummunar ƙaddarar da ta faru a baya. Kogon bincike ya ƙone ƙurmus! Hasken wutar abar bauta ta ɗauke. Buzun zakin abar bauta ya miƙe yanzu haka yana cen yana fidda aman wuta.


A yau na tsaya a gabanku domin na tabbatar muku da bala'in da yake tunkaro rayuwarku, ga taron rundunar baƙar inuwa tana tunkaro mu don haka ya zama wajibi mu haɗa ƙarfi da ƙarfe mu sake tserartar da yakinmu domin gujewa abin da ya faru ɗaruruwan shekarun da suka gabata, a zahiri dukkan alamun da suka bayyana a baya sune suke sake bayyana a wannan lokacin domin yanzu haka tazarar da ke tsakaninmu da wannan baƙin yaƙin bai fi taƙi kaɗan ba. Ina jin tsoron kada farmakin Baƙar Daula ya wanzu a gare mu duk da muna da tsarin da ko tsuntsu ba za su iya gani da idanunsu ba matuƙar ya kasance ɗaya daga cikin ahalinmu na Maharba." Ras! Na ji gabana ya faɗi musamman da na tuna Kandala bata daga cikin zuri'ar Maharba, hasalima tsarinmu ya katange da ita." Ina tsoron kar wani mummunan al'amari ya faru da ita. Hankali a tashe na furta, "Ba zan bari ba Kandala! Ba zan taɓa bari a cutar da ke ba tun da kaina na ɗauki alƙawarin kulawa da rayuwarki. Zalincin baƙar Daula ba zai taɓa ɗarsuwa a kanki ba koda zan rasa rayuwata tun da ni ce sillar salwantar iyayen da suka haifo ki don haka zan bada jini da ruhina akan ki.


*Ummou Aslam Bint Adam*🌚
[11/25, 7:00 AM] Ameera Adam🌚: *BAƘAR DAULA*




©AMEERA ADAM


FIRST CLASS WRITER'S ASSO...

Tsokaci: Ƙirƙirarran labari ne bai faru a gaske ba, ban rubuta don cin zarafin kowacce ƙabila ko yanki ba. Daga sunayen garuruwa zuwa na abin bauta duk ƙirƙirarru ne, kuma ban lamunce a sauya min littafi ta kowacce siga ba tare da izinina ba.⚠️


4




*KU MATSO KU TAHO*💃🏼


Wannan labarin salonsa na daban ne💃🏼 cike yake da sarƙaƙiya da tsananin ban tausayi😰 ku dai kar ku bari a yi babu ku.🏂


Littafin kuɗi ne idan kina buƙata 400 ne ta Account 3090957579 Aisha Adam, First bank. Za ki turo evidence ta wannan lambar 0706 206 2624 Idan kati ne MTN. Idan kika bari na kammala cmplt 700 ne.


Idan kin san kin sayi ɗaya daga cikin litattafan nan *AN YA BAIWA? KO DUBU JIKAR MAI CARBI KO ZAUJATU JINNUL-ASHIQ* za ki biya 300 wannan ragin na waɗanda suka sayi wannan littafan nan ne kaɗai.💃🏼


Na ɗaga hannuwa riƙe da takobi da kwari da baka na salaƙe na sunkuyar da kai ina miƙa gaisuwa da kirari cau cau cau cau, sai ni Ameera 'yar Alhaji Adamu Amiriyan Mamanta, uwar Aslam da Ayman Amanar Oganta turmi sha daka 🥰
Wiiiiiiihuuuuuuhuuuu mace mai kamar maza ko cikin maza sai an duba domin wuya ake yi wa lissafi daɗi sai an jinkirta. Allah dai ya biya wuya a ƙofar Na'isa, wuya a ƙofar Kabuga wuya a ƙofar Nasarawa wuya a doka wuya, wuya a ƙofar kansakali mun buga a dajin Jemagu mun buga a dajin Falgore ko dajin Sambisa albarka. Sai ni ƴar Kanawan dabo amanar mutanen Rigana, idan ka ga matsoraci ko rago a Rugana baƙo ne domin jarumi ba'a nuna masa hanya, sa'a dai 'yar gaban goshin *FIRST CLASS WRITER'S* Amanar Marubuta La'ilaha'illahu. Sai ni ta hannun Matar Habibu ni ce dai ƙawar Mum Amnash amanar Masoyanta, cau cau cau cau makaranta ku matso ku ji wannan kafcan don idan kika bari aka yi babu ke an barki a baya. Domin duk wacce ta bari aka yi wannan tafiyar babu ita ta fita daga cikin jaruman mata masu aji.🌚


Gudun kada Abar bauta ta fahimci abin da nake faɗa ya sa Mahaifina ya damƙi hannuna mara ciwon sannan ya yi min raɗa a kunne da cewar, "Ɗaure bakinki ya fi miki alheri akan mummunan fushin da abar bauta za ta yi da ke." Idanuwana na ɗago ina kallonsa, har ƙwayar idona ta ciko da ƙwallah sai na haɗiye abina don na tuna gargaɗin da mahaifina ya yi min akan zubar ƙwallata. Muryata na rawa na furta, "Ina gudun abin da zai faru da Kandala don ka san tsarinmu ba zai taɓa tasiri a tattare da ita ba. Ta kasance bata daga jinin Maharba da mafarauta, idan baka manta ba da bakinka ka gaya min Abar bauta ta tsarkake iya zuri'ar wannan yankin namu ne kawai, ka na ganin idan wani abu ya faru da Kandala zunubi da munanan abubuwa ba za su ƙaru a kaina ba duba da abubuwan da suke faruwa da ni? Na yi sanadiyar mutuwar iyayenta, kuma tun da dokar dajin na lashi aniyar kare haƙƙinta kamar yadda iyayenta za su kula da ita. Don Allah kada ka dakatar da ni saboda ina tausayin rayuwarta, ta rasa iyayenta a yankinmu, ta rasa zuri'arta a yankinmu, ta rasa budurcinta a yankinmu shin wannan kaɗai bai isa ya sa a tausayawa rayuwarta ba?" Jikin mahaifina ne ya yi sanyi tamkar wanda aka zare wa laka, ya dube ni haɗe da sauke ajiyar zuciya sannan ya furta, "Shi kenan Kyauta! Abar bauta ta kawar da muguwar rana a kan ki, za ta shiga lamuranki ba za ta da mu kunya ba albarkacin tsafi da farauta." Jin daɗin kalamansa ya sa na sakar masa murmushi a daidai lokacin na ji Abar bauta ta sake cewa, "A daren yau zuwa gobe za a katange yankin nan daga baƙar guguwar da ta taso mana. Ya zama wajibi a zubar da jini ga rauhanai don su sake dafa mana akan sha'anin rayuwarmu, wannan shi ne abin da zan iya sanar da ku don na taimaka muku. Idan kuka bijirewa umarnina zan iya sauya sheƙa daga wannan yankin zuwa wani na kafa daulata, munanan abubuwa za su yi ta faruwa a kan ku haɗe da farmakai daga sauran ƙasashe musamman Baƙar Daular da kullin burinta ta shafe tarihin Maharba a faɗin duniya." Cikin aminta da kalaman abar bauta da ba ta yarda ya sa muka amsa mata da faɗin, "Uwar gijiya abar bauta ta dafa mana ta shafe matsalolinmu, mun dogara da ke don haka ke ce mai yaye mana damuwa da ba mu waraka a kowanne lokaci. Mun ji mun amince za mu yi abin da kika ce domin mu ma su bin umarninki ne, mun dogara da tsafi da sihiri sune madogarar abar bauta ita kuma ita ce madogararmu a koyaushe."


Fuskar abar bauta ce ta fasalta irin farincikin da ta yi da mu, don haka ta ɗaga hannunta sama ta wara ƴan yatsunta nan take wani mulmulallan haske ya dira a kai. Ta dube mu ta sake kallon haske sannan ta furta, "Albarkacin tsafi da sihiri, albarka da tabbata a gare ku ya ku wannan zuri'a ta mafarauta masu albarka. Shin akwai mai son a bincika gobensa don sanin abin da zai faru da shi? Akwai mai ciwo mu warkar da shi? Ko akwai mai son mu ninka nasara da tsaririn tsafinsa don ya gagari kowanne rauhani a dajin farauta?" Tun bata rufe baki ba mahaifina ya ɗaga hannu sama, kasancewar mahaifina sarkin Maharbin yankinmu ya sa mutanen garinmu suke matuƙar ba shi girma domin mutum ne mai adalci da son talakawansa. Ganin mahaifina ya yi magana ya sa alummar da ke wurin suka fara kai masa gaisuwa cikin girmamawa, "Sarki ya zo mutuwa ta zo, mutuwa mai kai ƴan maza ƙasa ko da son rai ko babu. Abar bauta ta riga da ta buɗa maka kwarankwatsa dubu sai ka gama lafiya amanar ƙauran garin Dume, amana ta kai mana amana ta kai maka mun baka amana ka ba mu gaskiya ko sun ƙi ko sun so sai mun bar wuya a dajin Gagarar maza. Sa'a dai maza sa'a dai uban dawa wuya mai sa ƙarar kwana ga ƙananun maharba uban dawa sai ya kai labari ko da daɗi ko babu." Sunkuyar da kai Mahaifina ya yi alamar gaisuwar tana kai masa sannan ya ɗago ya amsa musu da cewar, "Dawa dai mazaje! Ba kyau ba daɗi, idan wuya ta yi wuya yaro ke guduwa ya bar babansa. Kwarankwatsa dubu ranar Talata mai zuwa sai na kai hallitun dawa dubu biyar da ɗoriya ɗan butar uwa, Abar bauta ta buɗe mana dai." A hankali muka riƙa takawa har kan tudun tsira sannan mahaifina ya tura ni daga gabansa kaɗan ya fara yi mata magana."Abar bauta ta yafe min kada ta yi fushi da ni a yau ma na sake dawowa da 'yata Kyauta domin ta shiga lamuranta. Ɓoyayyun al'amura na sake bayyana a tattare da ita, don haka na sake dawowa da ita don na ji ko akwai wani taimako da Abar bauta za ta yi domin Kyauta ta rinƙa rayuwa kamar kowa." Daga can duhu-duhun wurin da mutane ke tsaitsaye na hango wani matashin saurayi yana ƙara kutso kai sakamakon jin bayanin da Mahaifina ya yi, muna haɗa ido ya sakar mini murmushin da ban san dalilinsa ba, sai dai abin da ya ɗaure min kai ba kasafai na cika tozali da matashin ba sai a ranaku makamantan waɗannan da muke kai wa Abar bauta kukanmu.Hasali ko kaɗan ba ya daga cikin zuri'armu domin gabaɗaya mun san kanmu waɗanda suke rayuwa a yankin. Ina cikin wannan tunanin na riski muryarta tana faɗin, "Akwai ɓoyayyun lammura game da Kyauta don haka nake gagara bincika abin da yake damunta, a duk lokacin da na bincika gobenta ba na samun biyan buƙatata. A duk faɗin yankin nan babu wanda zan bincika rayuwarsa ta gaba na samu tangarda sai Kyauta, ina mai yi maka albishir da cewa ita ɗin ta musamman ce don haka waɗansu abubuwa suke baƙuntar rayuwarta. Babban abin da za mu saka a gaba shi ne, mu mayar da hankali wurin zagaye garin nan domin idan muka zagaye gari na yi ammana da tsafi da sihiri babu abin da za same mu." Wurin ne ya yi tsit muna sauraron ci gaban bayanin da abar bauta take. Sai da ta sake hawa can ƙololuwar samman tsauninta sannan ta ci gaba da cewa, "Albarkacin ranar talata da nasarorin da ke cikinta muna miƙa wuya ga alƙaluman tsafi akan zan sanar da talakawa su nemi waɗannan kayan tsarin su aiwatar da shi domin neman warakar su. Da farko za ku saro kan wani ƙasurgumin kumurcin maciji da ke Dajin Bawaya, sai ku kawo min na jiƙa shi da ruwan sihiri haɗe da tumfafiya, idan ya kwana ɗaya a jiƙe sai a dake kan macijin ku samo mana ruwan kogin haladu a wanke idon matasan makafi a haɗa da ƙasar kabarin Jarumi Baushe uban Yaɗiya, idan kuka yi haka ku kawo min na haɗa sauran mahaɗin da kaina. Zan baku shi ku je ku zagaye garin nan da shi kuma duk abin da za ku gani kada baki ya furta ko zuciya ta tsorata, duka waɗannan abubuwan za a same su ne a cikin ƙasa da kwana biyu." Duk da zuciyoyinmu sun fara karaya bai hana mun amsawa abar bauta ba, tana gama jawabin ta dafa raunin da ke jikina haɗe da ɗaura min wata baƙar fata wacce da alama ta baƙar wahainiya ce. Nan take raunin jikina ya warke wani ƙarfi ya ratsa ni tamkar wani abu bai taɓa faruwa da ni ba, daga haka ta sallame mu sannan kowa ya watse gidansa.


Sannu a hankali na rinƙa waige-waige don ganin na lalaubo matashin da nake ɗora zargi a kansa, amma sai haƙana ya gagara cim ma ruwa. Na neme shi sama da ƙasa na rasa! Dama na san za a rina wai an saci zanin mahaukaciya. A duk lokacin da na yi tozali da shi haka ce take faruwa don haka nake tunanin yana tattare da mummunar manufa game da yankinmu. Saboda na tabbata banza ba ta kai zomo kasuwa, kuma tamkar wanda yake wa rufa ido ban taɓa ji wani ya yi magana ko ƙorafi akansa ba. Kasancewar ba a ranar na saba ganin hallitun da ƴan uwana ba sa iya ganinsu ba ya sa na ja bakina na yi shiru, amma haka kawai jikina ya ba ni ziyararsa a gare mu ba alheri ba ce.


Matashin saurayin na barin wurin kai tsaye ya bi ta wata ɓarauniyar hanya da ke ƙarƙashin ƙasa, cike da fargaba ya rinƙa falfala gudu don yana tsoron tonuwar asirinsa musamman da ya tuna irin kallon zargin da Kyauta take yi masa. Sai da ya yi gudu mai nisa sannan ya isa wurin wasu rundunar dakarun mayaƙa, haki yake yi kamar ransa zai fita sannan ya sanar da su duk abin da ya ji game da yankin su Kyauta sannan ya ɗora da cewa, "Matsala dai ɗaya ce kamar yadda na gaya muku a baya, duk lokacin da na shiga yankin nan ba na iya ganin kowacce halita da idona face manyan dabbobi da ƙanana. Da taimkon Shugaba Usaina ta ba ni wani laƙani shi ne nake iya ganin yarinya ɗaya da idanuna kuma nake iya jin sautin abin bautarsu, ita ma a yadda na lura tana ganina sai dai ina tsoron kar asirinmu ya tonu." Shugaban Dakarun ne ya bushe da dariyar ƙeta sannan ya furta, "Ka gama aikinka don haka za ka iya tafiya ga Daularmu mai albarka, na tabbata idan muka kai wa Sarki wannan zuri'a ta Maharba sai ya yi mana ƙarin girma ya ɗaukaka darajarmu.


Runtse idonsa matashin ya yi tare da faɗin, "Shugaba Usaina! Shugaba Usaina." Nan take wani haske ya mamaye wurin babu jimawa ya ɓace ɓat. Gurfane yake a gabanta yana sauraron abin da za ta faɗa, sanin faɗin rai da izzarta ya sa ya ƙagara har ya ɗago don a tunaninsa ko ta bar wurin bai sani ba. Suna haɗa ido ya sauke kansa ƙa sa cikin girmamawa ya furta, "Sha kundum ta dafawa aikinki." Miƙewa ta yi ta fara taku ɗaiɗai ta rinƙa zagaye shi sannan ta furta, "Na saurari bayaninka don haka ina mai umartarka da ka iya bakinka idan ba haka ba sai na fisge rai daga gangar jikinka. Tabbas Boka mai zamani ya yi gaskiya Sha kundum ta sake bayyana a wannan yankin da kake min leƙen asiri sai dai babbar matsalar da har yau ya gagara bayyanar da suffar yarinyar. In dai ina numfashi Sarki Damina ba zai taɓa samun cikar burinsa na jininsa ya gaji karagar mulkinsa ba, na yi rantsuwa da abar bauta sai dai zuri'arsa ta ƙare a wahale yana

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login