Showing 39001 words to 42000 words out of 69452 words

Chapter 14 - BAKAR DAULA BOOK COMPLETE DOCUMENT BY Ameera Adam.txt

Advertisement

04 Jan 2025

6190

bayan wannan?" Ɗan yamutsa fuska ta yi ta ce, "Babu." Mama Uwani cikin wani yanayi ta fara bin ɗakin da kallo, Raihan ta ɗan ja guntun tsaki tana faɗin, "Mama Uwani ki bani wuri bana buƙatar hayaniya."


Mama Uwani ba don ta so ba ta juya jiki a sanyaye ta fice daga ɗakin tana waige, fitarta ke da wuya Mommy na kawo kai tana ganin Mama Uwani ta ce, "Uwani yarinyar ta tashi kuwa?" Mama Uwani cikin ladabi ta ce, "Ta tashi hajiya yanzu na kai mata abin kari." Mommy bata tanka mata ba ta tura ƙofar ɗakin ta shiga, Raihan na gaban mudubi za ta fara shafa mai. Mummy ta kira sunanta tana ci gaba da cewa, "Raihan ba dai yanzu kika ta shi kika yi sallaha ba?" Raihan ta ɓata fuska ta ce, "Haba Mommy wai me kika mayar da ni, ni ba sallah ma zan yi ba period ɗina ya dawo." Fuska ɗauke da damuwa Mommy ta ce, "Period kuma, ina ce yau ko sati biyu ba ki da gamawa ba." Cikin rashin damuwa ta gyaɗa kai tana ci gaba da shafa mai, juyawa Mommy ta yi ta fi ce tana faɗin, "Gaskiya idan ya ci gaba da yi miki wasa dole mu je mu ga likita." Raihan ta tura baki gaba ƙasa-ƙasa da murya tana faɗin, "Kawai don period ɗina ya dawo sai ace sai na je wani Hospital ana zaune ƙalau." Turo ƙofar da aka yi ne ya sa Raihan waigawa a lokacin ta fesa turare tana saka wata doguwar rigar bacci, Mama Uwani ce ta sake shiga hannu ɗauke da kunun gyaɗa ta ajiye, Raihan na ganin haka ta saki murmushi mai sauti ta ce, "Mama Uwani dama kin yi kunu shi ne baki kawo min ba, ai kuwa da na cika cikina sai kin kwashe min tass kin ɗura min kunun nan." Ta ƙarasa magana tana zame towel ɗin jikinta don ita Raihan bata kunyar ko a gaban waye ta cire kayanta ko ta sauya wasu.


Mama Uwani na ganin haka ta fice daga ɗakin, Raihan na cikin saka kaya ta ji kanta na sara mara lokaci ɗaya jini ya fara bin ƙafarta ga wani irin raɗaɗi da jikinta yake yi ta ko'ina, nan take ta yanke jiki ta faɗi a wurin. Wani irin hayaƙi ne ya fara zirarowa ta jikin ƙofa har sai da ya zo gaban Raihan da ke kwance jini ya fara malala daga jikinta, lokaci ɗaya hayaƙin ya rikiɗa zuwa siffar mutum. Kallon kan mudubin Raihan ya yi yana girgiza kai cike da baƙin ciki, ɗaya bayan ɗaya ya fara zuƙewa mayuwan ciki da yake ganinsu da kalar ruwan nan mai yauƙi, kusurwa bangon ɗakin ya kalla ya ce, "Tabbas ba aikin kowa ba ne sai naki Mugaza, na lura kin fara wuce makaɗi da rawa amma ranki sai ya yi mummunan ɓaci." Tun bai rufe baki ba magen nan ta sake ɓullowa ta bango, har sai da ta zo gabansa ta yi girgiza cikin surar wata matashiyar budurwa ta ce, "Ka ga laifina don na nakasta mai shirin tarwatsa farincikina? Ko kana tsammanin zan zura ido ka ɗauko mini kishiya alhalin ka san wannan haramtacciyar al'ada ce a zuri'armu. Wani abin takaici ma ka rasa wacce za ka aura sai bil'adam salon ka ja mini abin kunya cikin ahalina, wallahi ba zan lamunci haka ba kuma wannan somin taɓu ne ka zuba ido ka gani." Tana gama maganar ta sake rikiɗa zuwa mage ta ɓace daga ɗakin, cike da takaici ya kalli gadon Raihan sai kawai ya fara kiran sunan Hidaya. Sai da ya kira sau uku sannan wata matashiyar budurwa ta ratso ta ƙarƙashin ƙasa mai zubin siffar Raihan babu abin da ya bambamta su har kayan jikinta. Wurin abincin Raihan ya nuna mata ya ce, "Ki maye gurbinta kuma bana buƙatar a samu matsala idan ba haka ba har abada ke da biyan buƙatar ƙudurinki."


Idanunta ne suka ciko da ƙwallah ta ce, "Wuskarbat min kalsusbima wakfit karmu linkasbu muzrabatu fisgatmuha warmi Jalkisu Mu'az." (Don Allah karka yi mini haka, ka san duk duniya babu wanda nake ƙauna kamar Yarima Mu'az.)


Ɗaukan Raihan ya yi da ke kwance ya saɓa a kafaɗa sannan ya kalli jabun Raihan da ke tsaye ya ce, "Dole ki ɗauki ɗabi'a irin ta Raihan hatta yare dole ki ci gaba da irin yarenta ba namu da muka saba yi ba. Na gaya miki idan aka samu matsala ke da Yarima Mu'az har abada." Yana gama maganar ya daki tsakar ɗakin nan take ƙasar wurin ta dare ya faɗa ciki hannunsa ɗauke da Raihan suna shigewa ƙasar wurin ta haɗe ta shafe kamar wani abu bai taɓa faruwa a wurin ba.




SHARE HILIS🌚


Daga yau za ki iya turo kuɗinki don karki bari ayi babu ke🤸🏻‍♀️🤸🏻‍♀️🤸🏻‍♀️


Ummou Aslam Bint Adam🌚
*ZAUJATU JINNUL-ASHIQ*




© *AMEERA ADAM*


Littafin kuɗi ne idan kina buƙata 300 ne ta Account 3090957579 Aisha Adam, First bank. Za ki turo evidence ta wannan lambar 0706 206 2624 Whatsapp only Idan kati ne 300 MTN.


*FIRST CLASS WRITER'S ASSO...*


FREE PAGE 3


Mommy na shigowa ta nufi wurin dianning sai da ta zauna sannan ta kalli wurin da Raihan take zaune ta ce, "Mama Uwani ta ce min kin yi breakfast ko?" Jabun Raihan da ke zaune a kan kujera ta ce, "Eh na yi ɗazu." Mommy na juyawa ta buɗe kular abinci sai ta ga wayam, sake buɗe ɗayar kular ita ma babu komai; haka ta riƙa buɗe kulolin abincin amma sai taunannun ƙashi a ɗan tsorace ta tashi tana faɗin, "Waye ya cinye abincin nan Mama Uwani?" Cikin rashin damuwa Raihan ta ce, "Yanzu na cinye su." A ɗan tsorace mommy ta ce, "Gabaɗaya abincin ke kika cinye har fa da abincin rana na ajiye mana." Raihan ta miƙe ta nufi ɗakinta tana faɗin, "Wanda Mama Uwani ta kaimin bai ishe ni ba shi ya sa." Mommy sororo ta yi jikinta a sanyaye tana bin bayan Raihan da kallo.


Jabun Raihan na shiga ɗaki ta ji Huzaifa na ƙwala mata kira, ta kusurwar bango ta wuce cike da ɗoki don zamanta a cikin gidan jin ta take kamar a kabari take.


Huzaifa da ke tsaye a gaban Raihan ya dubi Jabun Raihan ya ce, "Mugaza ta yi mata rauni zan mayar da ita ga mahaifanta amma zan ci gaba da bata kulawa kamar yadda na kwashe dubban shekaru ina tsaye a kanta. Ki je na sallame ki idan da yuwar wani lokacin na buƙace ki za ki ji ni." Cike da farinciki jabun Raihan ta rikiɗe zuwa siffar wani ƙaton tsuntsu mai ɗauke da manyan fuka-fukai ta ɓace daga wurin, daga wurin da yake ya ɗauki Raihan ya ɗora ta akan gadonta sannan ya ɓace daga wurin.


Bayan shigar jabun Raihan ɗaki ta fara kiran Mama Uwani, cike da girmamawa ta ƙaraso wurin tana faɗin, "Ga ni hajiya."


Mommy ta kalli kulolin kan dianning ta ce, "Mama Uwani yau mun wayi gari da wani abin almara, dubi kulolin nan wai Raihan ta cinye." Da mamaki Mama Uwani ta zaro idanu ta ce, "Hajiya duka ita Uwarɗakin nawa ce ta cinye?" Mommy ta taɓe baki ta ce, "Dama ke ba ta laifi a wurinki ai, yanzu a sake dafa wani abincin bari na haɗa cornflakes." Mama Uwani ta fara tattara kwanukan tana faɗin, "Hajiy ai kowanne laifi kika ɗauko cewa kike ita ce, ni kuma uwarɗakina bata laifi." Tana gama maganar ta kwashe kwanukan ta wuce kitchen da su.


Raihan ba ita ta farka sai bayan azahar, a hankali ta buɗe idonta da suka yi mata nauyi dum! Tana ƙarewa ɗakin nata kallo. Lumshe idonta ta yi saboda yadda ta ji kanta yana sara mata kamar zai tarwatse, yunƙurawa ta yi zata tashi zaune ta ji jikinta ya yi mata wani irin tsami, ƙafarta ta hagu ta ji ta yi mata sanyi kamar ba a jikinta take ba. Da ƙyar ta samu ta fara dafa bango tana jan ƙafar tata da take jin ta yi mata nauyi kamar gungumen icce, tana zuwa falo ta fara yamutsa fuska tana bin ko'ina da kallo, a gefe ɗaya kuma ta fara wani shinshine-shinshine a haukace kamar mahaukaciya sabon kamu, da rarrafe ta fara watsi da kayan fallon cikin wani irin yanayi tana wani irin ƙaraji da gurnani kamar zakanyar da take tsaka da farauta. Ƙarar fashewar kayan ne ya fito da Mommy daga ɗaki a tsorace tana bin wurin da kallo, tana shirin yin magana su Goggo suma suka turo ƙofa suka fito don ganin abin da yake faruwa. Gilas ɗin center table da ta fasa ta fara ɗauka tana wurga musu tana faɗin, "Waye ya ɗauke min ɗana, ɗana ne wallahi duk wanda ya taɓa min shi sai na kashe shi." Inno da Goggo na ganin haka da rarrafe suka juya cikin ɗaki a tsorace, suna shiga suka bankawa ƙofarsu sakata jiki na rawa.


Mommy jiki na karkarwa ta ce, "Raihan lafiyarki kuwa?" Raihan ta sake wurgawa Mommy wata kwalba da sauri ta sa hannu ta kare, kwalbar ta yanketa a hannu jini ya fara zuba, jin ƙarnin jinin mommy ya sa ta fara wurga mata wani mugun kallo tana lasar baki. Ta ci gaba da surutai ba fasali, Mama uwani ta shigo a tsorace tana kallon abin da yake faruwa.


Hanyar kitchen ta nufa tana zuwa a haukace ta fisgo wata ƙatuwar roba wacce take ciki da ɗanyan kifi, tana zuwa falo ta rungumeta da hannuwa biyu tana sauke ajiyar zuciya.




Mommy na shiga ɗaki hankali a tashe ta ɗau waya ta fara kiran Daddy, ba a jima ba ya ɗauka ko jiran cewarsa bata yi ba ta fara faɗin, "Alhaji muna cikin tashin hankali, da alama ciwon Raihan na shekarun baya ne ya dawo sabo don Allah ka yi maza ka zo." Amsa mata ya yi sannan suka yi sallama ya katse wayar a gaggauce, Mommy na daga wurin da take a ɗaki tana jiyo ƙarara fashe-fashen kayan da Raihan take yi. Bayan wani lokaci shiru ne ya biyo baya, jin shirin ya sa Mommy ta miƙe a hankali ta buɗe ƙofar ɗakin. A falo ta hango Raihan zaune rungume da ɗanyun kifi, gabaɗaya ta ɓata jikinta da falon da ruwan kifi ban da ƙarninsa babu abin da yake tashi. Daddy ne ya turo ƙofa ya shigo yana gaba Dr Hamza na biye da shi, sai dai ganin yanayin falon ya sa ya fahimci wannan ciwon nata har ya ninka na baya. Jin sallamar Daddy ya sa ta ɗago da jajayen idanunta tana yi masa wani irin kallo, a haukace ta zaburo kansu tana faɗin, "Kar wanda ya taɓa mini ɗana jinina ne ba zan laminta a raba ni da shi ba." Tana rufe baki ta wurgowa Daddy wata kwalba saura kaɗan ta same shi a fuska ya kauce, Daddy ne ya fara kiran Yunusa mai gadi yana zuwa suka shiga kiciniyar riƙe Raihan sai da ƙyar suka samu nasarar riƙeta Likita ya yi mata allurar bacci, a take bacci ya ɗauketa ta faɗi gefe.


Kan kujera suka ɗorata Likitan ya fita yana yi wa Daddy bayani.


"Wato Alhaji da alama ciwon yarinyar nan ya dawo sabo, domin idan har abin da mahaifiyarta ta faɗa ne za mu iya cewa ya ninku a kan na da, saboda a da tana surutai kawai idan abin ya tashi, amma a wannan karon tana nuna kifi a matsayin ɗan cikinta. Akwai issue mai girma a game da lamarin ciwonta, za mu yi bincike mai zurfi a kai, sannan kar a riƙa wasa da magungunanta ta riƙa sha akai-akai." Jikin Daddy a sanyaye ya miƙawa Dr Hamza hannu yana faɗin, "Na gode sosai Dr don Allah a yi wani abu kai, ka san ina matuƙar son Raihan ba zan iya jure rashinta." Dr Hamza ya jinjina kai ya ce, "Insha Allah Alhaji kuma a ci gaba da addu'a everything will be successfully." Daga haka suka yi sallama da Likita. Yana komawa ciki tuni ma'aikatan gidan suka shiga hada-hadar gyaran falon, kusa da ita ya je ya zauna ya zura mata ido, hannu ya ɗora a kan goshinta zuciyarsa babu daɗi ya ce, "Wish you quick recovery dear, me ya sa al'amuranki basa zuwa da sauƙi why? Allah ya baki lafiya my baby." Mommy na ƙarasowa wurin ta dubi Alhaji cikin damuwa ta ce, "Habibi ni kam wata shawara gare ni." Bai furta mata komai ba ya ɗago yana kallonta ya yi mata alamar yana sauraronta. Jingina ta yi da bango ta ce, "Gani nake yi mai zai hana ciwon yarinyar nan a haɗa shi da na islamic chemist ko akwai shafar aljanu a ciki..." Tun bata dire zancenta ya buga mata tsawa da cewar, "Ba na son na ƙara jin kin danganta min Raihan da wani jinsin bayan bil'adam, idan ba haka ba ranki zai yi mummunan ɓaci. Me ye wani islamic chemist malaman da kaje wurinsu sai dai su fara yi maka turare da hayaƙi, da sun samu wuri za su fara yi maka maula. Idan ba za ki taya ni mu nema mata magani ba don Allah ki cire hannunki daga cikin maganar, ni kaɗai na isa na nema mata lafiya." Ran mommy ba ƙaramin ɓaci ya yi ba, amma babu yadda ta iya haka ta ja bakinta ta tsuke don ta san akan wannan maganar sai su haura sama su faɗo. Daddy ne ya cicciɓi Raihan zai kaita ɗaki da sauri Mommy ta nuna masa ɗakinta tana faɗin, "Ka kaita Toilet ɗina zan gyara mata jikinta a can sai ta kwanta." Bai tanka mata ba ya wuce ya kaita ɗakin Mommy don har lokacin fushi yake yi.


Mommy da kanta ta gyara Raihan ta kwantar da ita a kan gadonta, zama ta yi a gefe tana kallon ƴartata cike da tausayawa. Idanunta ne suka ciko da ƙwalla, ta sharce ƙwallah ta furta, "Wannan ita ce kalar tamu ƙaddarar, Allah ya baki lafiya Raihan."


Raihan ta jima tana bacci sai bayan wani lokaci sannan ta tashi, ɗingisawa ta ci gaba da yi har ta fito zuwa falo. A lokacin an gyara falon sai ƙamshin turare yake. A zaune ta hango Mommy Mama Uwani na zaune a ƙasa tana matsawa Mommy ƙafa, cike da farinciki Mama Uwani ta ce, "Uwar ɗakina kin tashi?" Kafin Raihan ta yi magana Mommy ta furta, "Barka da tashi My Princess." A ɗingishe ta ƙaraso wurin cikin damuwa mommy ta ce, "Me ya samu ƙafar taki?" Raihan ta yamutsa fuska ta ce, "Wallahi haka kawai na ta yi min nauyi. Mommy kamar mun je wani wurin ko? Ko dai mafarki na yi ne?" Mommy a tunaninta lokacin da ciwon Raihan ya tashi take nufi, ita kuma Raihan tana son tuna zuwanta Duniyar su Huzaifa amma kanta ya yi nauyi ta manta. Mama Uwani ta kafeta da ido sannan ta ce, "Uwar ɗakina sannu kin ji, ai ke kin zama ƙadagaren bakin tulu a karki a kar tulu a barki ki ɓata ruwa." Raihan ta ce, "Yauwa Mama Uwani, don Allah haɗo min ruwan tea." Ta yi maganar cikin jin daɗin kanbabawar da Mama Uwani ta yi mata, Nan take Mama Uwani ta tashi ta nufi hanyar kitchen. A hankali Goggo ta turo ƙofa ta fito falo, don tun lokacin da ciwon Raihan ya tashi da suka shige ɗaki babu wacce ta fito a cikinsu, kallo ɗaya za ka yi wa Goggo ka tabbatar da tsoro ya mamaye zuciyarta amma sai ta dake ta fara yashe baki tana faɗin, "Rehanu hutawa ake yi." Raihan ta taɓe baki ta ce, "Ni kam ko karatu ne wallahi Goggo ya ci ki haddace sunana, kullin sai na ce miki ba sunana Rehanu ba amma ina miyar kuka ta toshe ko'ina." Mommy ta ɓata fuska ta ce, "Gidanku Raihan." Goggo da ta lura Raihan ta dawo cikin hayyacinta, ta yi mata daƙuwa ta ce, "Gata a zaune ita kika gayawa haka." Goggo ta nemi wuri ta zauna tana faɗin, "Abu kunna mini wannan shirin da suke na ƙasashen labarawa ko idanuna sa ƙara ƙarfi." Inno ta ƙaraso wurin tana faɗin, "Allah ya sani ba za mu kalli masu jajayen kunne ba, ni dai ki kai mini shirinsu wannan yaron Adamu zango da Ali Nuhu, ki saka mana sangaya mu kallah." Mama Uwani ce ta ƙaraso da kofin shayi ta taimakawa Raihan suka wuce ɗaki, don ƙafarta sosai ta yi mata nauyi ɗingisawa take yi.


Shigar su ɗaki keda wuya, Mama Hasiya ƙanwar Daddy ta yi sallama cikin falon. Fara'a ɗauke a fuskarta ta shiga cikin falon. Mommy da murmushi ta tarbi Mama Hasiya tana faɗin, "Mai gidan da ba awo ba cefane, ba waya ba labari." Mama Hasiya ta zame mayafin jikinta tana faɗin, "Mutum da gidansa wacce waya zai yi." Mommy ta saki murmushi tana faɗin, "Barka da zuwa wai da yamman nan kike tafe." Mama Hasiya ta ajiye jakar hannunta tana faɗin, "Wallahi dole ce ta kawo ni, kin san Hubbi ya yi tafiya ƙafar Dubai to sun yi waya da DR John wai yau zai shigo gari so kin san matsalar hospital ɗin Dr John idan kana son ganinsa sai dare." Mommy ta sauya fuska cikin yanayin damuwa ta ce, "Allah ya sa a dace wai wancen karon ba ya ce ƙasa da six months komai zai iya faruwa ba? Ya ce za ki iya samu ciki a kowanne lokaci." Mama Hasiya ta jinjina kai ta ce, "To kin ga dai shiru, lamarin rashin haihuwar nan ba ƙaramin damuna yake yi ba. Tun hubbi bai fara damuwa ba yanzu na fuskanci abin ya fara damunsa, shekara sama da goma sha biyar ba haihuwa an ya ina da rabon ganin ƙwaina a duniya kuwa?" Mama Hasiya ta yi maganar idanunta na cikowa da ƙwallah. Cikin sigar lallashi Mommy ta dubi Mama Hasiya tana faɗin, "Komai kika ga ya faru da bawa da sanin Allah, ba a nan take ba. Komai fa lokaci ne mutane da dama akwai waɗanda suka fiki daɗewa kuma Allah ya kawo musu mafita, mu ci gaba da addu'a komai ya yi farko

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login