Showing 33001 words to 36000 words out of 39246 words
Chapter 12 - YAR FILLO COMPLETE DOCUMENT BY Nabilancy Love π.txt
yanda komai kikace yayi zaiyi mk babu musu.
Da sauri tana fara.a tace "da gaske ?koda nace yasakenine zai saka inna ce masa??
Yagyada kai da murmushinsa yace "kwarraiii ma kuwa
Nan tahau murna tana fadin "aiko dai yaya Abdulhakim kakawo dabara walh haka za.ayi.
Yaji dadi har ckn ransa daya kawo dabara sbd yanajinta tamkar kanwarsa dasuke uwa daya uba daya tun ada shiyasa ma baya son su rabu don bayaso takoma kauye ayanzu khadija tayi kyau tayi haduwar da dole inta shiga cikin yan kauyensu abanbanceta don tayi freash tacika ta goge tazama khadijan birni.
Da wannan dabarar suka rabu
Yana futa Ni,ima datayi shiru tanajinsu ta tashi zaune ahankali takalli dije tace mata "khadija sannu da kokari.
Ashe dama tun asali ba son Abdallah kikieyiba amma kika iya zama dashi lallai na jinjina mk kinzama jaruma yakamata ace anbaki lambar girmamawa dan haka ayanzu nima zanbaki shawarata daki kama mijinki tunda hankalinsa yajuyo kanki kisoshi kamar yadda yake sonki domin kici ribar rayuwarki kada kibari kurabu domin zamanki a birni shine yafi dacewa dake ba zaman kauye ba dan Allah kiyi tunani.
Dije da tayi sakato tanajinta ta kakalo murmushi tace "naji batunki na dauka yar,uwa tosaidai ke kuma awane matsayi kk agunsa ?kinga inhar na amince mas to ke kuma fa ?yazakiyi da son da kk masa kinsan dai baxan juri inga ya wulakantakiba gara kawai komun koma innemi hanyar rabuwarmu dashi yazauna dake ke kkfi dacewa dashi kina sonshi tsakani da Allah kuma ke yar masu kudice gaki yar birni..."kema yar birnin ce khadija.cewar Ni.ima tana dariya.
Dije takama hannun Ni,ima tana cewa "Sister Ni,ima pls mubar wannan zancenma don wani bamai yiwuwa bane .
Ta tashi tafuta tabar Ni,ima tana murmushi da yabon kyawawan halayen ta aranta tabbas samun kishiya kamar Dije sai antona.β¦β¦β¦β¦
*muje zuwa*ππΌ
π *YAR FILLO* π
_Dijen Kauye_
πππππππ
πππππ
πππ
ππ
*True life Story*
*Nabilancy Luv*π
(Auntyn S&S)
PG 110-115
Duk yadda Abdallah yaso yahadu da Dije abu yaci tura taki bari su hadun sbd tasan nufinsa akanta gasashi kawai takeyi dataji muryarsa afalo inta taho take komawa inko tana zaune afalon daya shigo zatayi dabara taje kicin ta hado masa lemo ko ruwa saita zille tagudu dakinsu
Dayawa agidan sunyi zaton ko itanma tana sonshine tunda akan idonsu take masa wannan kyautatawar wanda shi agunsa bakaramin dadin hakan yake jiba
Ko mubina abokiyar sha.awararta tayi zaton ko dijen ta sauko
π
Abdulhakim ne kawai yasan komai
Sai Ni,ima datake kallon dijen kawai a mara wayo domin ta ranfota itama kuma tana ganin rashin wayon dijen tsababa tunda Allah ne yabata dama yakamata ace ta dama lokacinta danji take inama itace dijen,ita yanzu baga yanda Allah yamaisheta ba garin neman gira ta rasa ido garin neman soyayya ta hanyar asiri gashi abu yaja mata jangwan tazama gurguwa kuma samoshin datayi ta hanyar asiri ada yanzu ya karye babu wancan bayanin don yanzu kam Dije ce kadai agabansa ko lowerst baiji sonta kamar yadda yakejin na Dije ba.
Andaura Auren Mubina da Abdulhakim Anyi shagali bana wasa ba wanda aranar aka kaita gidan Abdulhakim din sukuma su Dije a washe gari Suka koma gidansu
Abdallah ne yadebesu amotarsa yakaisu gidan nasa
A wauta ta dije kin kwana tayi asashenta wai ita lallai adakin Ni,imar zata kwana sbd jikinta
Ni,ima tayita mata dariya tace "ho!Allah nagode maka da halin dije na sokonci kekam wai yaushe zakiyi hankali ne ?mace da mijinta tagujeshi maxa tashi ki koma bangarenki donni da kk ganni naxama cikon gida agareku nabar mk Abdallah.
Dije tace "amma dai ko meye har yanzun kina matsayin matarsa kuma kece uwar gida tunda kin girme mini dan haka nabar masa ke yakwana asashinki kuma kidaina cewa ke cikon gida ce matar gida kk kamar kowace macen da take jin ita macen gida ce.
Ni,ima takama baki tana kallon dije kawai mamakinta takeyi ita kokishin mijin batayi toko dan bata sonsa
Tabbas tana zargin ko dijen bata san so bane tunda kamar Abdallah ace ba.a sonsa handsome dashi kyakykyawa me faffadan kirji son kowa kamar yadda wasu matan ke son su sami miji me irin fasalinsa lallai ta jinjinawa dije. ππΌ
Saida dije tayi kwana biyu asashin Ni,ima tana yi mata girki sannan Abdallah yataka mata burki yace mata maza ta koma nata part din yasa me aikin momy ta dawo gun Ni,imar.
Ranta bai soba ta koma bangaren nata amma taci alwashin saita bakanta masa rai don itakam taki jininma yayi mata magana ballan tana ma yakebe da ita tasan kuma damar hakan yakeso
Dayake ackn hutun zangon karshe suke na third term za.ai musu canjin aji zasu shiga jss 3 kwana tayi tana nazari aranta na yanda zata tafi kauyensu domin tunda tazo birni zuwanta daya da sukaje da momy da mubina da Aunty maryam kusan shekara biyu knn tun tana jss one
Tasan inta tambayeshi zataje kauyen nasu baxai barta ba Shiyasa tasamo wata dabara na tafiya batare data fada masa baki da baki ba arubuce zata bar masa sallahu kawai
Ckn dare daya dawo kai tsaye yanufi dakinta yamurda kofar yaji akulle take
Yaciji yatsa kawai yakoma dakinsa domin duk wayon kaxa sai ansha romanya tagama guje gujenta da boye boyenta yasha alwashin saiyasa ahannunsa ya murji "yar roba.
********
Da sassafe tagama shirinta dama toilet dinta ackn dakinta yake tagama shirinta tsaf ta sanya wani swice lace da ddy yadinka musu su uku ita,Ni,ima,Mubina me tsadar gaske ne harda gyalens kwalliyar purple ne ajikinsa dan haka ta bude akwatinta ta dauko wani takalminta plat ne da jakarsa purple sabbine tun na Auranta sai yanzun yai mata amfani sbd ada can batasan toomach ba π
Har gari yagama wayewa bata bude kofar ba abu daya ne take jinsa kudin motar da zatayi xuwa kauyensu batada isassun kudi ahannu abinda yake ahannunta baifi yakaita tasha ba
Tanajinsa yaxo yana kwankwasa mata kofa yana kiran sunanta
"Khadija bude kofar mana.
Ta taso tazo ta tsaya jikin kofar tana fadin "inna bude me zan maka?
"Sai zakiyimin wani abin ne zaki bude?nifa mijinkine khadija bai kamata kiringa min haka ba yakamata boyen kankin nan da kkyi yazo karshe inada bukatarki _plz open the door my wife_
tayi murmushi kawai domin ko me zaice bazata bude dinba duk dadin bakinsa ayau
Tace "zan bude maka kofa amma saika gaya min abinda yake tafe dakai.
"Kudin cefane nazo nabaki tunda naga bakida komai a kicin.
Taji wani sanyi aranta kudin motar zuwa kauye yasamu.
"Ka ajiyemin akan table katafi inka dawo mahadu da dadaddare.
Yazaci da gasken take zasu hadun da daren saikawai yace mata "to zan ajiyr mk amma kiyimin alqawarin da daren bazaki kulle kofa ba.
Ckn wani salon murya da batasan tana da itaba ta yaudara tace "naji na amince nayi maka alqawari zanbude maka kofa harma mukawana tare.
Har ckn ransa yaji dadin kalaminta kuma ya yarda da ita.
Yajuya asanyaye ya ajiye mata dubu biyar yafice
Saida tajiyo tashin motarsa yafuta sannan ta fito ta dauki kudin ta saka ackn jakarta ta zatgawa karenta igiya ko ni,ima bata yiwa sallamaba don batason asan ta tafin ma
Me gadi ne yaga futarta yayi mata adawo lfy
Tana zuwa tasha saura mutum daya amotar da zata hau ta zuwa kauyan nasu tuni tana shiga mota ta daga sai kauyen Marina..β¦β¦β¦β¦
*Auntyn Sayyada da Shahida ce*ππΌπ *YAR FILLO* π
_Dijen Kauye_
πππππππ
πππππ
ππππ
πππ
*True Life Story*
*Nabilancy Luv* π
(Auntyn S&S)
PG 115-120
Addaji Tana tsakar gida saijin Sallamar Dije taji tashigo janye da akwati ahannunta
Addaji da murnarta ta tareta tana fadin "maraba maraba da yan birni on njab'b'aama b'oy.
Dije tayi murmushi tace " addaji sannu da gida.
"Yawwa dije Gorko maa accii ma na? _Tare kike da mijin naki_?
Dije ta girgiza
_Toye Abdallah woni?_ Ina Abdallahn yake?
A sanyaye Tace" _o wurtake jam_
Addaji ta kura mata ido taga kamar akwai damuwa atattare da ita saita gyara zama tace mata "Dije ko akwai damuwa ne?
Dije ta girgiza kanta tace "babu wata damuwa Addaji kawai dai nazo ganin gidane
"Da amincewar mijinki?
Addaji ta watso mata wannan tambayar.
Tayi dim!baxata fadi gaskiyaba sbd Addaji zata iya hadata da kawunnanta su korata ba shiri itakam tana son ta huta na kwanaki don tayi kewar kauyen nan nasu.
Asanyaye dije tace "eh!dama shiyace nazo nayi kwana biyu zaizo yadaukeni.
Murmushi Addaji tayi tace "Allah sarki yakyauta ya kika baro mutan gidan?
"Lafiya suke Sunce agaidaki.
"Ina amsawa, tashi kikai kayan ciki kizo ga abinci can a madafi kizuba kici.
"To Addajina. Dije tafada tana mikewa da fara.a akan fuskarta
Tunda tazo take cikin Nishadi tawuni aranar tana sharar baccinta hankali kwance saidai mafarkin datayi yadaga mata hankali sosai ganin wai gata da Abdallah suna nitso a swimming pool yana suna wanka
daganan bayan sun gama wankan sai gasu a lambu azaune takwantar da kanta ajikinsa yana bata tufa abaki
Abin yadaure mata kai data farka wato ma dan shirmen mafarki har wani soyayya aka nuna mata tanayi da Abdallah ack
Taja tsaki tana fadin "Allah kaimin tsari dayin soyayya dashi.
*******
A can birni kuwa hankalin Abdallah tashi yayi matuqa ganin yadawo baiga dije agidan ba yaduba kowane sashi harna ni,ima bata nan
Ni,ima da mai aikinta sukace yau dai kam basuji motsin taba.
Amma mai gadi yabashi tabbacin yaga futarta da akwati ahannu.
Yagarxaya gidan momy ko can ta nufa amma abin mamaki sai momy tace masa batazo ba
Momy ma fada tahaushi dayi "banyarda dakai ba Abdallah da alama akwai abinda kayi mata yasa tabar gidanka batare daka saniba.walh duk inda kasan zaka samota kaje kanemota kafin ranka yabaci domin inhar dady yaji ranka ne zai baci maza kaje kanemo "yar mutane inkuma ba hakaba mu iyayanka muje munemo ta
Hankali atashe yafuta yasuri mota yahau titi yana ta kalle kallen hanya ko Allah zaisa yaganta ahanyar
Gidan Aunty maryam ma yaje amma tace masa itama batazoba tabbas abin yadaga masa hankali har dare yana yawwon nemanta ko da yaiwa Abdulhakim wayama ko taje gun mubina shima ce masa yayi batazo musuba
Sai dare daya dawo gidansu dady yasashi gaba da fada yace masa "Da alama ko kauye ta tafi ta gaji da abinda kake matane.Abu danake mata na takurawa agidana kawai saidai ko can din ta tafi abinta.
Dady yace "dolenka kayi sammako gobe katafi can kauyen kataho a ita inkayi mata lefi kuma kabata hkr cewa tace wannan sbd baka isa ka wulakanta khadija ina raye ba.
Haka yakoma gida sukuku dashi apart din dijen yakwana yana tunaninta sai ayanzun ma yakarajin wata azababbiyar kaunar khadijan tabbas inya sami zuciyar khadija zataga soyayya tsantsa sai ya mantar da ita irin tsanar datayi masa don yasan kome tayi ayanzu laifin sane.
Ya kudurta aransa duk rintsi duk wahala bazai yarda yarabu da khadijaba zaiyi juriya yai hkr da ita na duk abinda zata nuna masa na qiyayya har Allah yasa wataran tasoshi
Washe gari ko karyawa baiyiba yai wanka yanufi kauyen marina don taho da khadija
Yana tafe ahanya Abdulhakim yakirashi yake tambayarsa ya maganar khadijan anganta kuwa?
Abdallah yace "gani dai ahanyar kauyensu zanje naduba kotana can mutaho tare don dady yace kada inyarda intaho kafata kafarta.
Abdulhakim yace masa "to Allah yasa tana can din domin nakikkira wayarta naji akashe ko matsalar network ne.
Abdallah yace "may be hakanne.plz my bros katayani addu.a Allah yasa tana can din
"To amin dan,uwa Allah yakiyaye.
"Amin. Sukai da juna sallama yakashe
Agidan gonarsu yasauka saida yahuta da kusan awa biyu kana yanufi gidansu Dije wanda saida kwatance ma yaje gareshi don zuwansa daya bazai iya sake kai kansaba again
Yasa yaro yai masa sallama da masu gidan
Koda yaro yasanarwa Addaji bako na sallama awaje da sauri ta leka
Tana ganinshi tahau fara.a don koda bata taba ganin saba tasan shine mijin dijen don tariga tasan Abdulhakim farin sani shine dai dama bata taba ganiba
Har kasa ya durkusa yagaidata tareda gabatar da kansa gareta
Tace "lale maraba shigo daga soro mana.
Taje da saurinta tadauko masa tabarma ta shinfida azauren yashiga yaxauna
Takawo masa fura da nono tadamu tasha sukari
Yau saiga Abdallah dashan fura harda santi mutumin da ada yakewa Abdulhakim kallon kaxami yanashan furar yan kauye kawai don wulakanci bawai don yaga wata kaxanta atattare da dijenba
Yaita baxa ido yaga ta inda dijen zata bayyana
Sai can addajin ta dawo tace masa "kayi hkrfa taje gidan kawunta ne tun dazu amma nasan yanzu tana kan hanya.
Yace "ba komai inna.
Addaji tace "ko akwai matsala ne?
Ya girgiza kai da sauri "a,a babu wata matsala inna kawai dai nazo mukoma ne dama kwana daya nace tayi.
Ta gyada kai sai sannan takara yarda da Dijen
Yana nan zaune harna tsahon awa guda
Yanata latse latsen wayarsa saijin sallamarta yayi da siririyar muryat gwanin dadi
Tana shigowa zauren taja tunga tana kallonsa
Kamar zata koma taji amma saiya mike da sauri yakamota cikin zauren yahadata da jikinsa abango yana fadin "Da izinin wa kika taho ?
Ta hade rai "walh koka sakeni ko inmaka ihun barawo.
Ya kyalkyale da dariya yace "kin dade bakiyiba dan Allah maza kiyi.
Walh kina ihu nima zanyi ince kinmin sata kingudo kauye.
Ta kura masa ido da wautarta tace "kambu me na satar maka?walh kowa yasanni akauyen nan niba barauniya bace.
Yadangwale mata baki yace "to aigashi kinfara acan birni kinsatomin zuciya kingudo kauye dan haka walh yau me rabani dake sai Allah.
Tayi yinkurin tureshi da karfin tsiya amma takasa
Yace "walh yau kafata kafarki nama gayawa innarki naxo tafiya dake kuma dady yabani sako cewar inhar kika wuce yau baki dawo gidana ba to bashi bake kuma ayanzu hakan kintaho kinbar momy ckn damuwa don ta zaci ko bata kikayi.
Su dije ba wuya anxuru tuni ta gaskata zancensa jikinta yai sanyi tace "to nji zantaho amma baxan tafi dakai ba nikadai nazo nikadai zankoma amma ba yauba gaskiya dan Saina huta
Yace "nikuma yau inbaki tafi dani ba anan gidan zankwana kuma adakinki akan katifarki khadija.
Ta gwalo ido tace "sbd hauka.?
Ya daga gira yace "aiso nake innuna mk cewar akan sonki na haukace.
Tayi kas da kanta tace "nikuma akan kinka na haukace Abdallah.
Amaimakon yaji haushima sai wani dadi yaji dayaji ta ambaci sunanshi donji yai tafi kowa iya ambatar sunan
yakai bakinsa nata zai tsotsi dan lebenta tuni ta goce da sauri tana harararsa tace "mufa akauyen nan ba.a iskanci irin wannan kada agani asani awaka gaskiya kada kasake walh zanyi Allah ya isa.. π
Su dije manya
Shi abinma dariya yabashi domin yai tsammanin yanzu dije tasan komai tunda tawaye abirni tayi karatu to amma ya alakanta abin da sokonci tunda ita yar farice kuma hali dai zanen dutsene.
"Zaki taho yanzu mukoma gida ko inbuga dadi ingaya masa.?
Tayi masa shiru domin baxata iya yiwa maganar dadi foli ba
Wayarsa ce tadau ruri yaduba yaga Abdulhakim ne
Yana dagawa yace da Abdul din "Dan,uwa gani ga khadija Amma ta bujire wai baxata biyoniba.
Abdulhakim yace bani ita
Ya mikawa dijen ta karba tana zobara dan bakinta me kama da minti
"Hello khadijan Abdallah.! Yafada da zolaya
Tace"niba tashi bace.
Abdulhakim yai dry yace "to ta waye inba tashin ba?
"Tame rabo mana.
Yakyalkyale da dariyar keta yace "to aishine me rabon.haba khadija kinga yanda Allah yayi da dan,uwana dan Allah kitausaya masa kibiyoshi ku dawo tare jiya baiyi baccin arxikiba yana sonki khadija ni shaidane kuma inbaki taho yauba dady baxaiji dadi ba haka nima zanyi fushi dake ga mubina ma kinbarta adamuwa ya kk so muyi knn.?
Tace "to zanbiyoshi mu taho amma badan halin saba sbd kai da dady kawai.
"Eh munji mungode da hakan.
Abdallah jin hakan datace saiyayi murmushi ya lumshe ido yabudesu tar akanta ta miko masa wayar tace "ga wayarka kabarni inshiga ciki to.
Yakarba yamatsa ta wuce
Yace mata "kifito yanzu da kayanki kada mubata lokaci
Tayi masa banxa harda dan harararsa ta gefe
Dariya kawai yai mata
Tayiwa addaji sallama ta fito
Addaji bata fahimci komai ba ita dadima abin yai mata naganin mijin dijen yabiyota ckn so da kauna.
Gashi taga dijen ta canza tayi mugun kyau zaton addajin ma ko cikine da dijen
Suna tafe amota babu wanda yace da dan,uwansa kanzil
Waka yasaka ta soyayya ta balarabiya Nancy agram me kwantar da zuciya da sanyin dadi
Bini bini yakalleta yaga dai fuskarta ba fara.a bai sake takalar taba dai har bacci yadauketa yaita kallon kyakykyawar fuskrta yaji kamar yashafo fuskar amma yana tsoron abinda zai biyo baya
Godiya yaitaiwa Allah day mallaka masa khadija me kyau amatsayin mata fatansa kuma Allah yasaka sonsa ackn zuciyarta
Horn din dayakewa me gadine yatasheta abacci tafahimci sun iso datagansu akofar gidan Abdallan
Sashinta ta wuce kawai ko akwatinma shiya biyota dashi
Toilet ta shige ta watsa ruwa taje takwanta agado daga ita sai "yar bes da dogon wando fela
Yatsura mata idanu daya shigo dakin takalleshi taja tsaki kawai
Ya zauna agefen gadon yace "khadija nazo muyi muhimmiyar magana kitashi zaune.
Tace "nikuma ayanzu bacci nakeji ba.
Yace "duk baccin da kikasha amota?
"Bai ishe niba. Tafada atakaice
Yace "to dama nazo mk da kokon barata ne akan soyayyarki da Allah yajarrabceni kitaimaka kimance komai daya faru abaya ki karbi soyayyata ki amsheni amatsayin mijinki ina ckn wani hali ni mabuqacine nadaina halayena nashan giya a neman mata harga Allah bazan sake ba kece zaki taimakeni kimantar dani plz.
Yakama yatsunta na hannu
Ta kwace hannun nata tana fadin "aiba ni kadai bace matarka da zata taimaka mata kaje ga ni,ima can dama itake taimakon naka ai.
Ya marairaice mata yana fadin "ni,ima tabar mk ni tun kafin ki tafi tafadi hakan kuma kinga alamar banda akwai dangantaka atsakanina da ita da tuni na sallameta gida na abinda tayi abaya.to amma tunda baxaki tallafeni ba shikenan na hkr zanjira har zuwa lokacin dia zuciyarki zata huce tasoni dan kanta.
yana gama fadin hakan yatashi Yafuta abinsa ko waigenta baiyiba
Tabi bayansa da kallo
Yakamata ta tausaya masa hakan amma inta tuna wasu abubuwan takanji gara ta rama don yayi mata azaba abaya
Ba laifi ta wani bangaren yana burgeta domin yanada fasalin da za.a soshi dogone jayent kyakykyawa fari me saje da dogon hanci gashi da faffadan kirji ya iya kallo amma baxata iya furta tana sonshiba koda zuciyarta ta kamu
Ta tashi tashige kicin ta duba bau komai ciki sai indomie duk da taginsheta don cimarta ce dama amma haka ta dafa ta fito ta zauna tafara ci
Wayarta dake kan table tadau ruri ta dauko ta duba saitag ashe mubina ce
Tasan maganar tafiyarta kauye zatayi mata