Showing 30001 words to 33000 words out of 38445 words

Chapter 11 - MAKARANTAR MATSAFA COMPLETE NOVEL By Shamsiya Lauwali Rabo.txt

lalle,na ɗaga kai na dube ta kawai ban ce mata komai ba.Sai ta ja tsuki ta fita,Sarah ta matso tana cewa “ ki bar kula ta,so take ta ɓata miki daren aurenki ki kwana da baƙin ciki”

“Mu ga kitson naki ke” na faɗa na yi kamar ban ji me ta ce ba,ta cire hullar kanta na gani.Da na ga kitson sai na ji ina sha'awar ganin gashina a kitse sai dai kuma na yi saurin cire hakan a raina sanin abu ne da ba zai yiyu ba,rabona da kitso tun ina ƙarama shi ma dunƙule biyu ne Mama ke yi min sai ta yi ƴan tsoraye a sama.
Ina nan zaune aka kawo min abinci har da ruwan da zan sha,na tsurawa abincin ido ina kallo yau ce rana ta farko da aka taɓa yi min wannan gatan sai na saki ɗan murmushi tare da jawo kwanon na soma ci .Ina tuna gobe ne fa aurena sai na ji ya fita raina ba don ban jin yunwa ba sai don fargaba.Ƙawayen Mama da da danginta na ta ci gaba da yin hidima kafin ɗaya daga ciki ta kawo min wani tsimi ya fi kalar biyar,ban san na mene ne ba amma dai na yi biyayya na sha sauran kuma ta miƙa min ta ce na dinga sha har ya ƙare sai kuma wasu ƙullinka gari da kwalin madara su ma ta faɗa min yadda zan sha,ɗaya ne ta ware daga cikinsu ta ce “ wannan dole sai bayan sallar magrib za ki sha” kai kawai na gyaɗa tare da amsa.
Bayan fitarta ne na jawo sabuwar ƴar ƙaramar trollyn da na ajiiye domin saka abubuwana,na zube duk magungunan sannan na kwanta ina ta ci gaba da wahalar da kwanyata da tunani iri-iri.Duk gari yayi tsit ba ka jin sautin komai sai na karnuka,tuni kowa ya samu wuri ya kwanta amma ni sam bacci ya ƙauracewa idona.Haka na yi ta juyi ina jin kamar na tashi na fita amma sai na haƙura na ci gaba da bulaye a tunani a haka ban san lokacin da bacci ya ɗauke ni ba.
Washegari hayaniyar mutane ce ta tashe ni tun asubah,kasancewar akwai waɗanda suka kwana gidanmu akwai kuma musulmi daga cikinsu.Daga inda nake kwance nake kallon yadda wata ke yin sallah cike da nutsuwa tana karanto wasu abubuwa da ban san na mene ne ba,har ta kammala ina kallon ta .Na ja ajiyar zuciya,ina sha'awar musulunci suna burge ni musamman in sun yi shigarsu ko ina a rufe.


“Ki tashi ki yi wanka,ki shafa dilka sannan kuma ki turare jikinki da wannan kafin mai lalle ta zo” Mama ta faɗa cike da sanyin murya,na dube ta sai na ga duk ta yi wani iri amma ban tambaye ta dalili ba na tashi na yi yadda ta ce .

Ko da na yi wanka na biyu tuni wacce za ta yi min lalle ta zo,doguwar riga na saka na zo na zauna kan tabarma kafin a soma sai da aka bani kunu mai zafi na sha.


Kusan awa huɗu ana yi min lallen kafin a ida, jefi-jefi muna taɓa hira da mai lallen har muka yi ɗan sabo.
Wuraren ƙarfe ɗaya na rana Abba da abokansa tuni sun taru da kuma dangi Mama maza.Tun a lokacin na soma jin gabana na faɗuwa,ina jin ƙarar cirawar motoci na sunne kai ina jin kamar zuciyata za ta fasa allon ƙirjina ta faɗo.Kamar minti talatin haka sai kuma ga su sun dawo ,wani maroƙi kuwa ya soma shela “ An ɗaura aure ya ɗaru,Aliyu Jafar ya zama mijin Janiki Al Haris ”

Duk da ina cikin tashin hankali bai hana ni maimaita sunan ‘ Al Haris ’ a zuciyata ba,wato sunan mahaifina kenan,don dai shi Abba sunansa ba haka yake ba .


Mata biyu ne suka ja ni zuwa banɗaki,kan wata kujerar katako na zauna bayan na cire doguwar rigar jikina kamar yadda suka ce.Haka suka yi min wanka da ruwan lalle,sai a lokacin kuma aka wanke min sumar kaina tasss har da saka min turare.Sai waƙe-waƙe suke har aka gama,sabbin kaya aka saka min haka ma takalmi sannan aka luluɓa min wata dara sabuwa dal aka fito da ni sai guɗa ake ta ko ina.


Ɗakin Mama aka kai ni har kan gadonta,wanda yau ne kawai zan ce na zauna shi.Banda kuka babu abin da nake yi,yayin da ƴan uwanta ke yi min nasiha gefe guda kuma Mama ce hakimce cikin shigar sabbin k
[30/01 08:49] MRS SADAUKI: Free 08


Wani irin abu ne na soma ji yana ratsa ruhina yana shiga,tamkar wacce aka juye wa tunani na wani ɗan lokaci haka na jin kwanyata ta yi wani lummm tare kuma da yin wani sauti kamar an buga ƙwai ga dutse.

Na ware idona a hankali kan SURUKATA wacce take yi min gizo kamar mutum kamar wata halitta.

“ Ƴata Janiki ?” ta kira sunana cikin wani sauti tamkar mai yin raɗa.

Sam ban motsa bakina ba,amma tabbas na ji a jikina na amsa da “ da na'am Mama” sai dai sam wannan ba furicin bakina ba ne,ƙila ruhina!

“Tashi ki je ki kwanta na san kin gaji,Aliyu yi mata rakiya zuwa ɗaki” ta faɗa tana wani murmushi .

Ya amsa da “ to Hajiya Mama” kafin ya miƙe ya ɗauke ni cak ya ɗora kan kafaɗa,sai ya zamana kaina ya sunne ƙasa yana reto.Idona ne suka soma nuna min wasu abubuwan da ke luluɓe a ɓoye a ƙarƙashin jan capet ɗin falon cin abinci,sai dai na kasa tantance na mene ne abu ɗaya na riƙe shine an ƙawata da wurin da jini.


A hankali Aliyu ya kwantar da ni kan bed ɗin,tamkar wata jaririya sabuwar haihuwa haka nake lumshe ido ina kuma ɗan buɗe su da zumar tantance wacce duniya nake sai dai sam na kasa .
Wani bacci mai kamar ido biyu ne na soma yi,gani nan ina gudu cikin daji yayin da wasu mutane masu rabi mutum rabi doki na take min baya a tsiyaci.Sosai nake gudu ina waiwayen su,suna dab da damƙo ni Prince Mahadi yayi min iyaka da su ta hanyar diro wa daga sama kamar wani aljani.A nan take kuma suka yi baya suka gudu,yayin da shi kuma ya jawo ni ya haɗe ni da ƙirjinsa.

Numfashi na yi ta saukewa saboda gudun fanfalaƙin da na yi,ya hura iska kan fuskata kafin ya matso da tasa fuskar dab da tawa kamar zai sumbace ni sai ya min raɗa a kunne “ ki tsaya ki lura da kyau,sannan ki kula da kanki” yana gama faɗa min haka na farka ina haƙi.Abun mamaki har zuwa yanzu ina jin wannan yanayin in mutum yayi gudu,maƙoshina ya bushe ƙamas .Na diro daga gadon,ina fitowa falo na yi kiciɓis da Hajiya Luba.


“Har kin tashi ? Ga ruwa na kawo miki ” ta faɗa cike da kulawa,hannuna har rawa yake na karɓi kofin na shanye ruwan tass ta ƙara tsiyaya min wasu na shanye,sai da na yi kofi huɗu kawai ƙishin ya gushe.


“ Halan kin kwanta da ƙishi ne? Ko kuma mafarkin shan ruwa kika yi?” Hajiya Luba ta yi min tambayar tana wani kafe ni da ido.
Mafarkin da na yi tsaf ya dawo min a kai,amma sai na zaɓi na ɓoye mata na ce “ dama...dama ina da yawan shan ruwa ne”


“Ok to ki kula sosai ba kowane ruwa ne ke maganin ƙishi ba”

“Me kike nufi Hajiya?”

“Babu komai,je ki yi wanka ki fito ki ɗora girkin rana” ta faɗa tare da ficewa.


Can ciki na koma na shiga toilet,bokiti na ajiye tare da buɗe ƙaramin pampo sai na ɗauki soson wanka na zuba sabulu na soma cuɗa jikina.Ina saɓa fuskata da sabulu sai na ji tamkar wani na kallona,da sauri na sa ruwa na wanke fuskar ina gwalar ido.Babu kowa kawai tunanina ne ya bani hakan.A gaggauce na ida na fito,cikin sabbin kayana na lefe na zaɓi doguwar rigar atamfa na saka.Tunani na soma a kan abin da ya rage a ɗakin nan amma sam na kasa tunawa,trollyn da aka zuba min kayan kwalliya na buɗe na shafa mai da turare kafin na fita can kitchen.



Tsaye na yi ina kallon uwar garar da ke cike da store ,ina mamakin duk me ake yi da su har haka kamar mai wani gidan marayu.Ban san me zan dafa ba,kawai sai na yanke shawarar bari na je na tambayi Hajiya .


Yin sallama ba ta cikin tabi'ata,wannan yasa yanzu ma ina isa ɗakinta kawai na kutsa kai.Kusan daskarewa na yi saboda tarar da Hajiya da na yi zaune kan wani tsumma ,kan kafaɗarta kuwa wani tsuntsu ne manyan ido jajaye .

Na ɗan ja da baya da nufin fita,amma sai na ga tsuntsun ya buɗe baki yana magana amma muryar Hajiya Luba ce ke fita.

“Ƴata Janiki,matso mana ki zauna a gefena” ta faɗa .

Jikina ya ɗau kyarma,na ce “ dama abin da za a dafa na zo nem...” ban ida kai ƙarshen maganar ba wannan tsuntsu ya tashi sama bai dira ko ina ba sai tsakiyar kaina.Daga nan kuma ban ƙara sanin abin da ya faru ba sai tashi na yi na gan ni kwance kan gadano,duk yadda na so tuna abubuwan da suka faru kuma na kasa.Abu guda na riƙe na je kitchen zan yi girki amma kuma ban yi ba.


Aka buɗo labule,Aliyu ne ya shigo fuskarsa kamar kullum a murtuƙe.Kakin sojansa ya soma cirewa ni kuma na zuba masa ido ina kallo.A siffa ga namiji har iya namiji sai dai raggo ne a shimfiɗa,ga kuma fitsarin kwance.


Na shagala sosai a kallonsa sam ban ga lokacin da ya zo gabana yayi tsaye ba,sai saukar muryasa da na ji “ ke ba ki san ki gaida mutane ba ?”

“Ka yi haƙuri” na faɗa da sauri,ya ja tsuki kafin ya shiga toilet.Bayan ya fito ne yake cewa “ Hajiya Mama ta ce bayan fitata kin zame jiki kin faɗi a kitchen,shin dama kina da cutar farfaɗiya ne?”


Shiru na yi ina tunanin ‘ to yaushe hakan ya faru ban sani ba? ’

“Ta ya kuwa za ki sani tun da hankalinki ya gushe” ya bani amsar tambayar da na yi wa kaina a zuci,cike da mamaki na ce “ ni fa ban yi magana ba” cikin ido ya kalle ni kafin kuma ya juya ya soma kimtsa wa .


Na dafe kai ina jin can ƙasan zuciyata kamar akwai abin da ba normal ba,amma sam an ƙi bani damar yin tunani ballantana ma na san gaskiyar abin da ke faru.

Daga can bakin ƙofa Binta ta yi sallama,da sauri na tashi na fita.Ta saki ɗan murmushi kafin ta ce “ ku fito lokacin cin abincin dare yayi”

“To ga mu nan” na faɗa tare kuma da zancen ‘ kenan har dare yayi?’

“Mu je” na ji muryarsa tare da wani jan hannuna kamar wata ƙaramar yarinya.
Muna fitowa sai na ga duhun magrib ne kawai ya keto amma kamar wasu kaji wai abincin dare za a ci.
Har muka shiga falon cin abinci bai saki hannuna ba,wannan karon kusa da Hajiya Luba ya zaunar da ni shi kuma ya zauna gefena sai ya zamana sun saka ni tsakiya.



Da ido kawai Hajiya Luba ta dube ni amma abun mamaki sai na ji sautin muryarta tamkar da baki ne ta yi maganar.
“Ki buɗe kwanon abincin ki bai wa kowa umarnin ci” shine abin da idon nata suka faɗa min.


A hankali na kai hannuna tare da buɗe ƙaton murfin,nan tururi da ƙamshin naman kaji ya cika wurin da kuma na wainar shinkafa.Na aro murmushi na yaɓawa fuskata mai cike da mamaki na ce “ kowa ya ci ya ji dadaɗan girkin da na yi mana,fatan za ku ji daɗinsa sosai”

Duk suka yi murmushi kuwa kafin a soma ci,ni ma cike da zumuɗi na soma ci saboda yunwa da na kwaso.Bayan mun gama ci Hajiya Luba ta ƙara bani wani umarnin na kawo jus,haka na miƙe na fita zuwa ɗakinta.

Da na shiga ɗakin duhu ne da shi ɗif,sai dai abun mamaki duhun bai hana ni ganin komai na ciki ba tamkar safiya.Ban wani damu ba tun da ni dai burina shine na ɗauko abin da aka aiko ni don shi,wannan yasa jus ɗin kawai na ɗauka na koma can haka na rarraba wa kowa kafin na koma wurina na zauna na sha.

Muna gama sha aka kira sallah,sai duk suka fita wannan karon har da Aliyu.Ni kuwa tamkar wacce aka riƙewa mazaunai haka nake ji sam ban yi ƙoƙarin tashi ba ma.


“Ungo ki sha” Hajiya Luba ta faɗa tana miƙo min kofin nan na ɗazu,na karɓa na shanye tass kamar jira kuwa ake sai na soma jin duk abubuwan da ni ɗazu sai dai na yanzu na ga wani banbanci shine yadda kawai na kwanta shanɗam kam capet.

Ba bacci nake ba,haka kuma ba zan ce idona biyu ba .A takaice dai ina tsakanin duniyoyin biyu,ina kallon lokacin da Hajiya Luba ta miƙe tsaye ta soma zagaye ni tana faɗar wasu ɗalasimai kafin kamar almara ta soma yi wa ruhina magana.


“Fito zuwa gare ni,zo ka yi min hidima ,lokaci yayi da nake ta faman jira” ta faɗa tare nuna tsakiyar ƙirjina,tamkar yadda ƙasa ke tsagewa haka na soma ganin gangar jikina na buɗewa kafin wani abu mai kama da inuwa ya fito,wanda ba komai ne shi ba sai ruhina.....



Littafina na kuɗi ne,ki ɗaure ki biya 500 Hajiya via
2670215530
ZULFAU YAHAYA
Ecobank

DM +22795045822
[24/12 à 08:16] MRS SADAUKI: My book is only 500 via
2670215530
ZULFAU YAHAYA
Ecobank

DM +22795045822



Free 09


Tamkar a mafarki dai ruhina ya fita daga gangar jikina ya je gaban SURUKATA ya zube,yatsan hannunta ta tsaga nan jini ya soma tsirta haka ta soma shayar da ruhina shi na wani lokaci kafin kuma ta basa umarnin ya je ya koma inda ya fito.
Yadda in mutum ya suma in an zuba masa ruwa yake zabura haɗi da jan numfashi da ƙarfi,to ni ma hakan ce ta faru da ni bayan ruhina ya dawo cikin gangar jikina.

“Ƴata Janiki kin tashi?” Hajiya Luba ta faɗa ,wacce a yanzu na gan ta zaune kusa da ni.Kai na gyaɗa mata ba tare da na ce komai ba,don ji na yi kamar na rasa tunanina.

Ta saki murmushi ta ce “ tashi ki je ɗakinki zan aiko miki da magani domin magance ciwonki” ba tare da na san wane ciwo take nufi ba na tashi na fita zuwa ɗakina.

A falo na tarar da Aliyu yana waya da dukkan alamu kuma da Ogansa ne duba da yadda yake magana cikin ladabi.Har zan wuce bedroom amma yayi min alama da hannu a kan na je.Sam jikina bai da wani ƙwari tamkar zan faɗi haka na je na tsaya a gabansa,ya jawo ni tare da ɗora ni kan cinyarsa.Yana waya yana yawo da hannunsa a jikina can ya ajiye kafin ya maido hankalinsa gare ni,wani irin kallo yake min kamar mai son ya isar min da wani saƙo.Ina ganin ya matso fuskarsa gare ni na yi saurin lumshe ido,ai kuwa abin da na yi tsammani ne.Sumbata na yayi ta yi haɗi da romance ,ba tare da neman izini ba kwatsam aka shigo ɗakin.Da sauri na zabura na tashi ina raba ido,ita kuwa Hajiya Luba kicin-kicin ta yi da rai tana wani kallonmu kamar ta ritsa kwarto.


“Hajiya Mama ko da abin da kike buƙata?” Aliyu ya faɗa a kunyace ba tare da ya tashi ba.

“Sai in ina buƙatar wani abu zan shigo ɗakinka Aliyu? Tun yaushe ka yi min iyaka da shigowa ba tare da na sani ba?” Hajiya Luba ta faɗa ,amon muryarta na fitar da hucin baƙin ciki.


“Ki yi haƙuri Hajiya ba haka nake nufi ba,dama ai ko ba ki shigo ba yanzu zan je na sanar da ke zan je mission jibi ” Aliyu ya faɗa .


“Ai ban ga alamun za ka je ba ɗin,ke kuma uwar me kike jira da kika yi min tsaye ko banda ikon yin magana da ɗana sai a gabanki?” wannan karon sosai fushinta ya fito,jikina na rawa na nufi bedroom ba tare da na ce mata komai ba.


Kan gado na zauna ina haƙi kamar wacce ta yi gudu,wani abu nake ji tamkar zan faɗi.Dukkan jikina ya ɗauki rawa,murya na ɗan rawa na ce “ Aliyuuu!” da ƙarfi na yi maganar ta yadda zai ji.

Ai kuwa ya shigo a guje yana cewa “ me aka yi?”

“Zan faɗi jiri nake ji” na faɗa tare da tashi tsaye ,yayi saurin tallabo ni .Hajiya Luba ta shigo tana cewa “ dama maganinta na zo kawo mata ungo ka bata ta sha” ta faɗa tare da miƙa masa wata kwalba,Aliyu ya zaunar ni sannan ya dangwalo maganin da yatsansa ya saka a bakina kamar ƙyaftawar ido haka na ji komai ya dawo normal.Na ja wata ajiyar zuciya,cike da tausaya wa Hajiya Luba ta matso kusa da ni tana mai cewa “ ki kwanta ki huta Ƴata Janiki, Allah ya baki lafiya.Ki riƙe maganin nan wurinki duk lokacin da kika ji wannan yanayi to ki dangwale shi da yatsa ki sha za ki samu sauƙi”


“ Na gode sosai Mama ” na furta cike da jin daɗi.
“Aliyu ina ga ya kamata a ɗaukar wa da Janiki ƴar aiki wacce za ta kula da ita da kuma yi mata hidima,ciwon nan nata bai son yawan motsi da zirga-zirga ”


“To Hajiya Mama ” ya furta kafin ya miƙa min kwalbar maganin.A tare suka fita shi da ita,ni kuma na kwanta kan gadona tare da rungume kwalbar a ƙirji.

Na saki wani murmushi na ce “ wai Janiki ce za a ɗaukar wa ƴar aiki, na gode abun bauta da ka nuna min ranar da zan yi farin ciki” sai kuma na yi shiru na koma zancen zuci ‘ to yanzu a haka zan zauna da Aliyu ba tare da mun mori rayuwar aurenmu ba? Ko ya san bai da lafiya? Ƙila kuma shi wannan saurin inzalin bai ɗauke shi matsala ba don ban ga ya nuna alamun damuwa ba’ sai kuma na ji tausayin kaina.


Ina nan kwance ya shigo, trolly ya jawo ya soma zuba kayansa yana yi yana waiwayena har ya gama ya zo yayi tsaye kai gare ni ya tsura min ido.Duk sai na ji na tsargu,ga kuma wani tsoronsa da ya dirar min lokaci guda.

“Ki tashi ki yi wanka ki canza kayan nan zuwa na bacci ” ya faɗa yana furzar da huci.Ba tare da na ce masa komai ba na sauko,har zan wuce amma

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login