Showing 3001 words to 6000 words out of 38445 words
Chapter 2 - MAKARANTAR MATSAFA COMPLETE NOVEL By Shamsiya Lauwali Rabo.txt
nake yi,sai shi ma Daddy ya shigo yana tambayar lafiya.Kai kawai na girgiza masa ,ya zo ya kamo hannuna ya ce “ kina ji na Nafisa faɗa min mafarkin me kika yi?” da sauri na janye hannuna daga cikin nasa,na diro daga kan bed na nufi ƙofa.
Sai kuma na yi tsaye ganin Uncle shi kuma zai shigowa gemunsa na ɗigar da ruwa da alamu alwala ce yayi.
Haɓata ya tallabo ta yadda zai iya kallon fuskata da kyau ,tsakiyar idona ya dinga duba yana wani motsa baki kafin ya ce “kin kuwa yi Azkhar yau?”
Idona na soma juyawa ina son kauce kallon nasa da ba ƙaramin takura min suke ba,sam babu daɗi ji nake kamar yana zuƙo raina ne.
“ Kin yi Azkhar na ce?” ya sake tambayata.
Kai na girgiza alamun a'a,don kuwa ban yi saboda tun asubah na samu saƙon cewa sunana ya fito a jerin waɗanda za su je bautar ƙasa wannan zumuɗin ya shagaltar da ni yin Azkhar kamar yadda na saba.
Ya sake ni kafin ya ce “ biyo ni” sai ya juya,haka na take masa baya ina waiwayen su Daddy muka fita zuwa can sashensa da yake waje.
Ɗakin Uncle Salem ciki biyu ne da falo,ɗakinsa guda na bacci guda kuma wanda yake zuba kayan maganin aljanu na ruƙiya.Direct ɗayan ɗakin muka shiga,kaina ne ya juya da na shaƙi warin magani iri-iri yayin da gefen cikina daidai inda aka soke ni ya soma motsi har sai da na danne wurin.
“ Zauna a nan” Uncle ya nuna min wata doguwar kujera,babu muso sai na zauna ɗin.Wata kwalba ya ɗauko tare da zuwa kusa da ni ya zauna kafin ya buɗe ta,tun kafin ya ce min na sha na soma hawaye don ni kaɗai na san irin abin da nake ji a duk lokacin da ya bani ire-iren maganin nan.
Bakina ya taɓe tare da ɗura min maganin,jikina ya ɗauki rawa kafin cikin fitar hayyaci na soma basa labarin mafarkin da na yi tiryen-tiryen.Kwantar da ni yayi yana mai jan doguwar rigar jikina sama,da sauri na rumtse ido lokacin da ya janye hannuna ya ɗora nasa a daidai wurin da ake ta yi min motsi.
Teburin da ke ɗauke da tarkacen da shi kaɗai ya san na mene ne ya jawo,ina ji ina gani da raina Uncle Salem ya soma tsatsaga fatata da reza.Banda wani zaɓi banda hawaye don tuni maganin da ya bani ya kashe min dukkan jijiyoyin jiki sai kaina da ke faman juyi tamkar an jefa ƙwarya a ruwa.
Wata kwalba ya ɗora daidai wurin ya soma tatsar jinina har ƙarar fitarsa kake ji,kamar minti biyu kafin ya cire kwalbar ya ajiye ta kan teburi.Wani magani ya shafa min a daidai ciwon mai bala'in zafi,har sai da raina ya kusa fita kafin da sauri ya cika bakinsa da wasu ruwa ya zo ya fara shayar da ni su.Duk ɗigo ɗaya na ruwan da zan sha to tamkar ana warware azabar da yake jikina ne , wannan yasa nake shan maganin cike da zalamar da ta haifar min da soma shan yawunsa da kuma laɓansa.
Jikin Uncle Salem ne ya ɗauki wata irin rawa jin Naf ɗinsa na sumbatarsa kamar za ta cinye leɓensa,duk wani tsohon feeling nasa da yake faman yin ƙasa da shi a kowacce safiya ya soma taso masa.A daidai gaɓar da ya soma mayar mata da martani kuma tuni bacci ya ɗauke ta,idonsa na fitar da wasu irin hawayen jaraba ya soma sunsunar wuyanta yana jin tamkar ya mayar da ita cikakkiyar mace ko zai samu salamar ruhi.
Dakyar ya rareashi kansa ya janye daga jikinta,daɓas ya zauna yana duban yadda take baccin wahala . Ƙonannen jinin mai tattare da guba yayi baƙi ƙirin a cikin kwalba,sai ya ɗauke shi ya je ya zubar toilet ya wanke kwalbar.
Sai da ya je ya sake wata alwala sannan ya nufi masjid,a can ya samu Daddy bayan sun yi sallar sun fito ne Uncle Salem ya dubi abokin nasa ya ce “ Abdul Hameed ban san me yasa ka zaɓi ka ɓoye min rufaffen sirrin Nafisa ba,amma hakan bai da wani amfani don kusan na fahimci matsalar junun da ke jikinta ya samo asali ne daga can tushe ba wai gamo ta yi da su ba”
Cak Daddy ya tsaya yana kallonsa, Uncle Salem ya jinjina masa kai ya ce “ tabbas ko yau sun ziyarce ta,saboda sakacin addu'ar da ba ta yi ba”
Daddy ya ce “ mu je can gida zan yi ma bayani” haka suka wuce suka isa,a keɓaɓen falon Daddy duk suka zauna tare da yin shuru Uncle Salem ya matsu ya ji labarin yayin da shi kuma Daddy ya rasa ta ina zai soma.Can ya nisa tare da furzar da huci kafin ya ce “ to da farko dai kamar yadda na faɗa ma ni ɗana ga sarauniya Ayodele Ayush,kafin zuwan Musulunci a Victoria Falls suna bautar ababen bauta iri-iri ,yin tsafi kuma sai ya zama adon garin.Sai dai sannu a hankali duk komai ya canza saboda yadda mahaifina sarki Ameer ya taka muhimmiyar rawa ganin ya kawar da duk wani fasadi sai dai kash zuwana duniya kuma aka tsiro da wasu sabbin canfi wai alamomi sun nuna za a sake yin maimaici wato daga cikin tsatsona za a samu wacce za ta jagoranci mulkin ƙasar.Amma tabbas ni ba magajin sarki ba ne,sosai na ji tsoro da jin haka don tamkar karatu haka ake biya min maganar nan har na mallaki hankalin kaina”
Uncle Salem yayi saurin katse shi da cewa “ haba aboki ta ya za ka yarda da wani canfi?”
Daddy yayi murmushi wanda ya fi kuka ciwo kafin ya ce “ dole na yarda mana,duba da tun ina ɗan shekara ashirin a duniya na ajiye iyali saboda yadda kullum nake kasa bacci ina harin neman abokiyar rayuwa wacce zan jefar wa da ƙwan haihuwar shugabar gobe ko zan samu sukuni ”
Uncle Salem ya ce “ kana nufin wai Naf?”
Daddy ya jinjina kai ya ce “aboki tun lokacin da na yi aure zan ce ma wannan larurar da ka san ni da ita ta mugun feeling ta kau,shi ma tun a daren farkonmu.Sannan kana dai ganin yadda lamarin aurena ya kasance a sirrance sai daga baya iyayena suka sani,har bisa yanzu sarki fushi yake da ni saboda na ƙi yarda na zauna a can Victoria Falls ni kuma ina gujewa Nafisa ƙalubalen da za ta fuskanta ne in ta zama shugaba”
“To amma mene yake baka tabbacin cewa hakan za ta kasance?” Uncle Salem ya tambaya .
Daddy ya ce “ saboda kama take da wata goggon Mamana ita ce mace ta biyu da ta mulki Victoria,to yadda ka ga Nafisa ita ma haka take kai kace tsaga kara ne aka yi.Hakan kuma babbar matsala ce domin zai iya kasancewa ita ta dawo duniyar nan a gangar jikin Nafisa ”
“ Wai ko sarauniya Deborat?” Uncle Salem ya tambaya,don kuwa ita ɗin ba ɓoyayya ba ce a duniyar nan duk kusan labarinta ya karaɗe ƙasashen duniya saboda shahararta wurin iya yin tsafi,sai dai ko kafin Daddy ya ce wani abu tuni tv ɗin da ke manne jikin bango ta soma yin wata tsaga “ƙiiiii!” kafin kuma ta faɗo ga ƙasa ,sai iska kuma mai ƙarfi wacce ta haifar da fashewa ƙwan lantarki ji kake ɗuuu haskensa ya ɗauke sai labulaye suka soma tashi sama suna wulwulwul....
[25/01 10:35] MRS SADAUKI: *MAKARANTAR MATSAFA*☠️
```LoVe aNd HoRrOr story```👽
By
Chamsiya Laouali Rabo
{MRS SADAUKI💫✍️}
*SADAUKARWA :* Ga dukkan Malaman makaranta.
*FCWA*☀️
________________________
04
A cikin duhun ɗakin ne Daddy da Uncle Salem suka hango wata mace sanye da fararen kaya wanda ko tantama babu likafani ne.A tsaye take jikin window sam ƙafafunta ba su taɓa ƙasa ba sai wani lilo suke kamar wacce aka rataye,farin gashin kanta kuwa sai yin sama yake iska na naɗa shi.
Cikin muryarta wacce kana ji ka san ba ta ɗan adam ba ce ta soma yin magana,“ ko kai ko abokinka babu wanda ya isa ya dakatar da ni daga yunƙurin da nake,Yarima Abdul Hameed ban sani ba ko ka san cewa sunan Deborat ya haramta ga duk wanda yayi hijira ya bar gidansu domin guje abubuwan da allolinmu za su zartar,ka sani cewa Nafisa jaruma ce ba mu zaɓe ta ba sai da sanin za ta iya.Sannan ka godewa Allah da ya kasance aikin alkhairi ne za ta gudanar ba wai na cutar da al'umma ba,sannan kai kuma da kake ta ƙoƙarin dakatar da mu ziyartar ta ka sani akwai lokacin da maganinka ba zai yi aiki a jikinta ba don haka gara ka baiwa kanka lafiya ka bar matarka ta yi aikinta yadda ya kamata.A tunaninka hatta auren naku ba mu sani ba? Mun sani sarai saboda kai ne za ka yi jinyarta a lokacin da ta kammala aikinta na farautar azzalumai ” tana gama faɗa kawai ta bi ta window ta fita yayin da kuma komai ya dawo normal hatta hasken ƙwan lantarki rasss ya koma yana yi .
Daddy da Uncle Salem sai suka fara ƴar kallon-kallon ba tare da sun cewa juna komai ba.
Can Daddy ya kasa yin shuru ya ce “ aboki ka yarda da fatalwa?”
“ Na yarda mana saboda ni ma ita ce ta raine ni” Uncle Salem ya basa amsa .
“ Ban gane ba”
“ Eh kamar yadda na faɗa ma ni kaina ban san iyayena ba domin a titi aka tsince ni to Inna Delu ta raine ni ta bani dukkan tarbiyya da kuma kulawa ta uwa,sai bayan na mallaki hankalin kaina ne ta sanar da ni ita wace ce saboda za ta koma makwancinta“
Daddy ya ce “ wai kana nufin dama Inna fatalwa ce?”
“ Eh sosai ! Bari na je na duba na ga ko Naf ta tashi” ya faɗa tare da miƙewa ya fita ,hankalinsa da tunaninsa na kan fatalwar Deborat wacce kusan duk dare Inna Delu na yi masa gatanarta.
Ko da ya shiga ɗaki ya tarar Nafisa na ta yin baccin gajiya ,ya dubi agogo ya ga lokaci sai tafiya yake ga shi kuma ba ta yi sallah ba.Sam bai son ya tashe ta amma sanin sallar asar ma nada ƙurarren lokaci yasa ya soma shafar fuskarta da tafin hannunsa mai taushi da sanyi.
Cikin bacci na soma jin sanyi na ratsa min kumatu,ga taushi kamar auduga.A hankali na ware idona na sauke su kan kyakkyawar fuskarsa,ban ida warkatsewa ba ya ce “ lokacin sallah Naf”
Jin ya ambaci sallah na yi saurin tashi hankali tashe don na tsani na makara,ya ɗan ja da baya yana mai ci gaba da kallona kafin kuma ya fita.Ni ma fitowa na yi na wuce can sashenmu sai da na fara gabatar da sallar sannan na yi wanka na saka riga doguwa marar hannu na ɗaura kallabinta sannan na fita.
Yunwa nake ji hakan yasa direct kitchen na shiga,Ammy ce da A'i mai aiki ke ta faman yin girki da dukkan alamu yau sarautar ta Daddy ta motsa shi yasa Ammy ke aikin da kanta.
“Yunwa nake ji” na faɗa kamar zan yi kuka,A'i ta yi dariya ta ce “ oh shagwaɓarki Nafisa ko auta albarka ”
Ammy ta ce “ bar ni da ita dai ta ci gaba da sakalcin in ta je can ƙauyen ai na ga wacce za ta yi wa”
Kamar wacce suka yi wa allurar zaburar wa kuwa haka na wani kwanto jikin A'i mai aiki wacce nake kira da Inna na ce “ ai tare da Innarmu zan tafi ita za ta dinga kula da ni,kafin na dawo ta yi min girki mai daɗi” A'i ta washe baki don sosai take jin daɗin yadda Nafisa ta ɗauke ta tamkar Kakarta sam ba ta nuna cewa ita ke ƙasa gare ta,haka kuma ita ce ta raine ta tun tana cikin tsumman goyo ko aiki za ta yi haka take goye ta in kuma ka ga sun rabu to Uncle Salem ne ke gidan.
“ Ki ma cire wannan a ranki don Inna A'i ba za ta bi ki ba” cewar Ammy tana mai zuba min kunun gyaɗa a kofi.
Na ce “ wai Innarmu ba za ki je ba?”
A'i ta ce “ ke wasa take yi miki fa,tuni ai na haɗa komatsaina na ƙulle a buhu” cike da jin daɗi na ɗauki kofin kunun gyaɗana na fito falo na zauna,tv na kunna na saka horror film ina kallo ina sha sam ban jin tsoron abubuwan da ake nunawa wani sa'in ma ji nake tamkar ƴan uwana ne.
Ƙamshin turarensa ne ya fara yi min maraba kafin shi ya shigo,na ɗaga kai ina kallonsa .Sanye yake cikin kakin soja sun yi bala'in yi masa kyau sai dai ya aske gemunsa da sajensa,da sauri na ajiye kofin hannuna ina turo baki ina kallonsa tuni kuwa ya fahimci dalili don tun ina yarinya nake faɗa masa ina son saje,sannan Inna A'i ta taɓa faɗa min ranar farko da na fara ganin Uncle Salem ya cire sage da gemu haka na yi ta kuka ina ɓata fuska sannan kuma na ƙi yarda da shi .
Da sauri na miƙe zan bar wurin yayi saurin kamo tsintsiyar hannuna yana mai cewa “ oyaaa Naf ɗin Uncle kar ki yi fushi zo ki shanyen kununki ki zo mu je na yi miki shopping ” jin ya ambaci shopping yasa na juyo don na san duk cikin shirye-shiryen tafiyata ne.
Na sake turo baki a karo na biyu kafin na ce “amma shine ka aske ...” yayi wani murmushi mai sauti yana cewa “ zai fito ai,kin ga kar ki yi fushi da Uncle ɗinki” sai ya zaunar da ni tare da ɗaukar kofin ya ci gaba da bani kunun har na shanye kafin ya ce “ je ki canza kaya ki zo mu wuce”
Da murna na koma ɗakina,sai dai ban canza kayan ba kawai dai na zumbulo dogon hijabi har ƙasa.Ina fitowa Uncle Salem ya matso kusa da ni kafin ya ce “ ki canza kaya Naf ” da mamaki na dube shi,ko ta ya aka yi ya gane ban canza ba.
Na marairaice fuska na ce “ Please mu tafi kar dare yayi” ya ɓata rai yana kallon ƙirjina,sai na turo baki na koma ɗaki na je gaban madubi na yi tsaye ashe rabon a yi ne ya kai ni don kuwa ina tsaka da tantance yadda saka hijabin bai ɓoye ainihin shap ɗin jikina ba sai na hango wata farar mata tana saka min abubuwa a jaka,ta yi zaune daram kan gadona.Na waiga da sauri sai na ga wayam,ina maida dubana kan madubi daidai nan ta bi ta window ta fice.Da mugun sauri na je bakin windown sai na gan ta a buɗe alhalin kullum a rufe take ban barinta a buɗe .
“ Naf wai har yanzu ba ki shirya ba?” na ji muryar Uncle Salem a bayana,na juyo da sauri ina cewa “ yanzu zan shirya“ sai kuma na ga yana buɗe ƙofofin hancinsa ya ce “ wannan wai ƙamshin mene ne kamar na Gawa?”
Da ido na tsure shi ina kallo jin ya ambaci gawa,a zuci na ce ‘ kenan dai da gaske ne abin da idona ya gane min? Ko ɗaya daga cikin fatalen da ake cewa sun shigo duniyarmu ne?’
“ Ki yi sauri ina jiran ki a mota” ya faɗa tare da fita.Kayan atamfa na saka kafin na ɗora hijabi sama,sai da na je na shaidawa Ammy kafin na fita can tsakar gida inda yake jirana.Bayan motar na shiga na zauna kusa da shi,waya na tarar yana yi sai da ya bai wa direba umarni sannan ya soma tuƙa mu.
Sai da muka hau titi sosai kafin ya kashe wayar wacce duk rabinta turanci ne da kuma sunayen makaman yaƙi.Na ɗaga kai na dube shi daidai shi ma ya dubo ni,sai muka haɗa ido hannuna ya kamo yana murmushi ban san dalilin da yasa ni ya hana ni na dinga riƙe hannunsa amma shi in ya yi niyya haka yake kamo ni.
“ Faɗa min me da me kike son saya?” ya tambaye ni yana ɗan matsa hannuna,ko kaɗan ban jin wani abu na daban saboda a matsayin uba na ɗauke shi.Na langwaɓar da kai na ce “ Chocolat da kuma teddy babba,sai turare da kuma ƙumbar kanti,da lipstick,da uhmm yawwa da sabuwar waya Uncle Please ” na ƙarashe tare da ciro ƙafafuna na yo sama da su tare da ɗora su kan nasa,ina jin lokacin da ya ja wani numfashi kafin ya ce “zobe fa?” ya tambaye ni saboda yadda ya san ina son zobe sai dai duk in ya siya min ban san ya ake yana ɓata ba.Na saki ɗan murmushi kafin na ce “ na hannunka nake so” sai na soma ƙoƙarin zare wani zobensa mai shegen kyawu da sauri ya dakatar da ni yana mai cewa “ zan saya miki wani dai”
Na turo baki na ce “ Uncle wannan zoben dai kamar a tare aka haife ku ko kuma wani ɗanka sam ba ka son rabuwa da shi,ina ga ma ka fi sonsa fiye da Niii!” na ɗan ja ƙarshen ban shirya ba saboda yadda ya kafe ne da rikatatun idonsa masu matuƙar kaifi .
“ Shi zoben?” ya tambaye ni cikin wata irin murya,ban iya cewa komai ba sai kai da na ɗaga masa alamar eh.A gabana ya cire zoben daga babban yatsansa na tsakiya sai ya kamo hannuna na hagu ya zura min shi a yatsana na biyu,a hankali yayi ta shafar zoben yana kallon tsakiyar idona har ya gama daidaita shi,sam tunanin ta ya aka yi zoben da shi kansa a babban yatsa kawai ya tsaya masa amma ni kuma a yatsa na biyu? Wannan tunanin sam bai shigo kwanyata ba sai na shiga yin murna har da wani rungume shi, Uncle Salem ya ƙara jan ajiyar zuciya a karo na biyu.
Muna isa Mall ɗin ya ja ni izuwa ciki,ana ganinsa da kakin soja duk a soma basa girmansa,ɗaya daga cikin ma'aikatan wurin aka haɗa ni da ita muka je tana nuna min kaya masu kyau sam ban san Uncle yayi tafiyarsa ba sai da muka sauko ƙasa ina ta baza ido amma ban gansa ba.Idona ya ciko da hawaye har zan tambayar mai kula da shiga da fita sai ga shi ya shigo ,ya sakar min murmushi kafin ya ce “ zo ki zaɓi wayar kafin a kira sallah” ya wani kama