Showing 9001 words to 12000 words out of 38445 words

Chapter 4 - MAKARANTAR MATSAFA COMPLETE NOVEL By Shamsiya Lauwali Rabo.txt

mana girki”
Ta ce “ a'a na fa warke yanzu zan shiga kitchen“ tana gama faɗa ta miƙe kuwa,ni kuma na ɗauki wayata nan na ci karo da miss call ɗin Uncle Salem ya fi goma duk yayi su ne bayan na kashe kiransa na jiya.Ɓangaren saƙo na duba sai na ga text ɗinsa yana bani haƙuri tare da alƙawarin ba zai sake ba.


Kiransa na yi sai dai sam lambar ba ta shiga,duk sai na ji babu daɗi haka na kunna data na soma yin shat ban ajiye wayar ba sai da na ga ta kusa mutuwa sannan na saka ta caji.Ina shirin shiga wanka na ji ana shelar ana son ganin dukkanin malaman da suka zo a ɗakin meeting da ke cikin makaranta da misalin ƙarfe takwas da rabi .


★Uncle Salem


Cikin kaɗaicin son kasancewa da Nafisa ya soma bijiro mata da sabbin abubuwan da za ta fahimci shi mijinta ne amma da dukkan alamu ya ga sam ita a iya uban kawai ta yi masa matsuguni.Jin ta kashe masa waya yayi tunanin kunya da kuma fushi ne yasa ta datse kiran,hakan yasa yayi ta jera mata su da ya ga ta ƙi ɗauka sai ya tura mata text tare da kashe wayar ya rungume pilow.Zuwa yanzu haƙurinsa da juriyarsa sun yi ƙasa sosai,yana matuƙar son kasancewa da ita a duk cikin sati ranar juma'a da asabar kawai a bai yin azumi duk don kare mutumcinsa.Sau ɗaya tak ya taɓa neman auren wata wacce dama ita ce take haukan sonsa,amma an zo yin auren aka fasa saboda bai da wani asali.


Idonsa sun kaɗa sun yi jajur saboda abu biyu da suka haɗe masa, feeling da kuma fushin Naf wanda a duniya in akwai abin da yake guje ma to bayansa yake shi yasa a kowane lokaci yake yi mata abin da take so.Ko da kuwa iyayenta sun so nuna masa illar gatan da yake yi mata sai ya ce musu har yanzu Naf yarinya ce.Sai dai a jiya da Daddy ya ce masa ya ci a ce ta tare da kuma yadda ya ga surarta cikin doguwar rigar da ta lafe jikinta duk ta fitar da shap ɗinta sai yake ji a ransa eh za ta iya ɗaukar nauyin buƙatarsa.

Juyi yayi ta yi a daren,da ya ga dai sam baccin ba fa zai zo ba sai ya miƙe ya je watso ruwa tare da zama kan dadduma yayi ta lazumi bayan raka'o'i biyu da yayi.Sai daf da asubah ya samu bacci,amma duk da haka ana kiran sallah sai da ya je masjid da ke nan cikin Company ya dawo ya ƙara komawa bacci.Bai farka ba sai wuraren ƙarfe goma na safiya,wani wankan ya sake tare da shirya wa cikin wando tree quater na sojawa da kuma rigarsa t-shirt ita ma ta kakin soja.Bai ɗora hulla ba ya dai saka farin gilashi kafin ya ɗauki key ɗin motarsa ta aiki da kuma wayarsa.Sai da ya fito a hanya ne ya kunna ta,bayan ya shiga mota ne ya ga saƙon cewa Nafisa ta so kiransa amma ba ta same shi ba.Ya ɗan saki murmushi yana jin zuciyarsa ta yi sanyi ko ba komai yana da tabbacin ta sauko daga fushin da take.Kiranta yayi har sau biyu,a na uku ne Inna A'i ta ɗauka ta shaida masa ta fita.



★ƘWARGWAM


Ko da na fito daga wanka tuni Inna A'i ta soya min dankali da kuma ƙwai,na yi zaune na ci na ƙoshi kafin na jawo kayan kwalliyata na shafa mai da turare har da hoda.Bayan nan na zaɓo doguwar riga ta tambaya ƴar côte d'ivoire,sosai ta amshe ni sai na zaɓo hijabi da jaka da kalmi duk waɗanda za su hau da ita.


Ina shirin fita ita ma Inna A'i ta fito daga kitchen hannunta riƙe da kwanon miya na jiya,ta ce “ ashe ba ki ci abincin nan ba dubi yadda duk yayi tsutsotsi ya lalace”

Na dubi cikin kwanon na ga babu kyawun gani manyan tsutsotsi ne ke ta yawo suna shige da fice cikin ragowar naman kajin.Da mamaki na ce “ amma kuma abincin har ya isa lalacewa haka?”

“ Ni ma haka na ce,ko ƙila zafi” Inna A'i ta faɗa .
Na ce “ kawai ki zubar ki wanke kwanukan sai ki mayar musu ,ga key nan in za ki fita ki rufe ɗakin na tafi sai na dawo”
“Allah ya tsare hanya”

Na ce Amen ina mai yin addu'ar fita daga gida.Kamar yadda ƴan magana ke cewa in ka yi boko to ƙauyancinka ragage ne hakan yasa duk da ban san ko ina na makarantar ba haka na dinga karanta duk wani allon sanarwa da na gani har na dace da ɗakin meeting.


Da isa ta sai na tarar duk kamar ma kowa ya zo ni ake jira,sallama na yi tare da samun wuri na zauna kusa da wata wacce na ga tana sanye da hijabi saɓanin sauran matan da ke wurin duk sun ci uban ado an ɗora mayafi.
Babu jimawa kuwa manyan namu suka suka shigo,duk muka miƙe tsaye don nuna girmamawa kafin mu zauna.


Ɗaya daga cikinsu ne ya soma yin magana ,su biyar ne huɗu maza sai mace ɗaya.
“Yawwa da farko muna yi wa baƙin malaman School Ƙwargwam Barka da zuwa,kamar yadda kuka sani duk faɗin garin nan wannan ita ce kawai makarantar da ake koya karatun boko da sauransu...” sai yayi wani murmushi wanda yake ɓoye wata manufa kafin ya ci gaba da cewa “ Ƙauyen Ƙwargwam na zagaye da ƙauyukan maƙota guda huɗu,shine a tsakiya sannan dukkan sauran ƙauyukan nan a wannan makaranta tamu mai farin jini suke zuwa ɗaukar darasi.Kar dai na cika ku da surutu,ina son waɗanda za su koyawa ƴan sakandari su koma layin nan duk su zauna” ya nuna wani layi,nan duk wasu daga cikinmu suka ware kansu nan ne na fahimci wato ba iya primary ba ce kenan school ɗin.

Kamar kuwa ya karanci tunanina sai ya ce “ makarantar ta kashi gida uku ne,da farko Sakandari sai ya nuna layin malaman kafin ya ce wannan shi ne Principal ɗinku ku da ɗalibanku,ƴan primary kuma ga naku shugaban headmaster sai ya nuna mutumen nan na jiya da ya kawo min abinci shi kuwa har da yin wani murmushi.Ina so duk ku basu girmansu,ni kuma mai yin magana ni vice headmaster,wannan kuma vice principal ya nuna ɗayan namiji ,daga ƙarshe sai wannan kuma ita ce Grand Maa mai makarantar ce ofishinta shine dogon nan mai jan penti in kuna da wata matsala ko wani abu da ya shige muku duhu ita ce za ku je ku yi wa magana” bayan duk ya gama nasa jawaban su ma ɗaya bayan ɗaya suka yi nasu kafin su faɗa mana fatansu da kuma tsarin makarantar wanda tun da nake ban taɓa jin irinsu ba amma haka na ja bakina na yi shuru.


Bayan an gama meeting sai wasu matasa suka shigo suka soma rabon coffe mai shegen ƙamshi.Ana bani na karɓa ina kallon ruwan coffe ɗin waɗanda a tsakiya aka shatin zuciya,na dubi na maƙwabciyata na ga ita ma nata haka yake.


Na yi shuru ina tunanin ko sai yaushe zan fara soyayya oho.
“Madam Nafisa ” Muryar headmaster ta katse min tunanin na ɗago muka haɗa ido,ya sakar min murmushi kafin ya ɗaga kofin hannunsa kamar yadda Turawa ke yi mai nufin Bismillah.
Na ɗan murmusa kafin na soma kurɓa ina ganin lokacin da ya saki murmushi ,a baki coffe ɗin har ya fi daɗi kan kyawunsa a ido.

Bayan mun gama sha ne aka rabawa kowa ajin da zai koya ,sai kuma duk muka miƙe Grand Maa sai ƙara jadadda mana take gobe tun ƙarfe bakwai na safe kowane malami ya tsaya bakin ƙofar ajinsa.

Muna fitowa na cewa wacce muka zauna kusa da juna,“mene ne sunanki?”
“Adama,ke kuma fa?”
“Ni kuma Nafisa”na bata amsa nan muka so yin masayen lambobi sai dai ni na bar wayata can gida tana caji a dole ni na bata tawa na ce sai ta ɗago min hannu.

Ina zuwa bakin ƙofar ɗakina sai na tarar da shi a rufe.Sai na zauna kan ƴar matakalar da aka yi bakin ƙofa na tsaya jiran Inna A'i don babu tantama gidan headmaster ta je.Ni kaɗai ce a wurin amma haka nake jin ana magana kusa da ni irin sosai ɗin nan,da na waiga ko ina kuma babu wanda na gani.Shuru na yi ina tunanin ko dai kunnuwana ne amma abin mamaki sai na ji ana dariya,da sauri na dubi inda sautin ke fitowa wani ɗan rame na gani irin na gidan tururuwa tabbas a ciki nake jiyo sautin amma sai aka yi tsit na wani lokaci.

Ni kuwa da son jin ƙwaƙwaf na duƙa tare da kai kunnena ƙasa ina saurara,ƙafafun mutum na gani tsaye kusa da ni.Da sauri na tashi sai na ga headmaster ne,yayi min kallon nan nasa kafin ya ce “me kike yi haka a waje?”
Na ƙaƙalo murmushin yaƙe na ce “na zo na tarar Innarmu ba ta nan ne shine na tsaya jira har ta dawo”
“Kuma kin yarda za ta dawo ɗin?” ya jefo min tambayar wata iri,ni kuma da yake ba wani damuwa na yi ba na ce masa “ eh za ta dawo ai ita ce za ta zauna da ni har mu koma”
“Hum!” ya ja wani ƙyaci kafin yasa key ya buɗe min ɗaki,na yi masa godiya tare da shigewa ciki.

Har zan shiga wanka na soma jin ƙaurin ƙonewar abinci,da sauri na shiga kitchen na kashe gas ɗin .Bayan na yi wanka na fito na yi mamakin da ban ga Inna A'i ta dawo ba,wayata na cire a caji na duba sai na ga Uncle ya kira ni sai na mayar masa ya ɗauka.Muka fara gaisawa kafin na ce “ Uncle ina ne za ka je na ji kamar kana driving?”
“Wurinki mana ko ba ki so?”
Cike da murna na ce “ wai Uncle da gaske?“
“ Na taɓa yi miki ƙarya? Ke dai kawai ki shirya tarbena don na kusa zuwa sai an na iso” yana gama faɗa ya kashe,ni kuma cike da zumuɗi na miƙe na soma gyara ɗakin na shiga kitchen na fara duba abubuwan da duk muka zo da su na haɗa masa lemun zoɓo na jona ƴar ƙaramar frigine ɗin da ke nan a kitchen na saka.

Haka na zauna na yi ta yin abubuwan da na san yana so kafin isowarsa.Aikin da na duƙufa shi ya mantar da ni wani cewa Inna A'i ta fita,haka na wuni ni ɗaya sai dab magrib ne Uncle Salem ya kira ni ga shi ya iso ni na je na tarbo shi can fara isa makaranta.Gidan gaba na shiga ya tuƙo motar yayi parking nata daidai ɗakina,nasa sabon key ɗin da headmaster ya bani na buɗe sannan muka shiga .A gajiye yake wannan yasa ya soma shiga wanka,ko da ya fito tuni an soma kiran sallah da sauri na ɗauke idona ganin ya fito babu riga daga shi sai farin towel ya ɗaura a ƙugu.
A ɗan daburce na ce “ Uncle ga kayan buɗa bakinka”
Bai ce komai ba sai gefen katifa da ya zauna haka nan ya ƙi saka kayan,da kansa ya zuba zoɓon don dai ni ba zan juri kallonsa a haka ba na shige toilet na ɗauro alwala .

Da zan fito sai da na ɗan ziro kai don ganin ko ya saka riga sai dai karaf muka haɗa ido da shi,yana nan kuma a inda na barsa.Ya sakar min murmushi yayin da ni kuma na fito cike da kunya,kaina sunkuye na ɗauki dadduma na soma yin sallah ko kafin na gama ya canza kaya ,a nan ɗaki shi ma yayi sallah gefena kan nasa daddumar.

Hannuna ya kamo da nake ta yin Azkhar ɗin yamma da ban samu na yi bayan sallar asar ba.Wani irin sanyi ne nake ji yana ratsa ni ga tuwon tafin hannunsa sai wani matse min nawa yake .

“ An gama yi wa Uncle ɗin fushi?” ya tambaye ni yana murmushi mai sauti.
Na ce “ ni ban yi fushi ba”
“ Kalle ni” ya faɗa ,a hankali na dube shi ɗin idonmu ya sarƙe cikin na juna ina son kawar da kai amma tamkar wacce ya yi wa dabaibayi na kasa.A hankali na soma sauke ajiyar zuciya ,tsawon lokaci muna a haka kafin ya buƙaci in zuba abin da na dafa mu ci.Jiki duk a sanyaye na zuba muna ci muna aukin kallon juna har muka gama,ana kiran sallar isha'i na miƙe don gabatarwa amma ya katse ni “je ki yi ɗahara ki sake alwala”

Ban musa masa ba don ba ya daga cikin halayena yin gardama a gare shi.Da mamakina kuwa da na shiga toilet alwalata ta karye iya ɗan kusanci da muka samu kawai,amma sam ban kawo shi wai don wannan niyyar yasa ya ce na je na sake alwala shi yasa ko da na fito ban wani ji kunyarsa ba na haye dadduma,shi ma sai da ya sake yin wata alwala kafin ya yi sallah.


Hira muka soma yana tambaya ta meeting ina basa amsa cike da sakewar fuska kafin na soma jin cikina na yin ciwo,tun ina daurewa har na kasa.
“ Je ki kwanta” cewar Uncle ,ina cije leɓe na haye katifa tare da yin rairan ina duban sama dafe da cikina.

Jakar da ya zo da ita ya buɗe sannan ya ɗauko wasu kwalabe yayi wani haɗi cikin kofi ,kafin ya cika bakinsa da ruwan ya zo ya ɗora shi kan nawa.Na buɗe bakina na dinga haɗiye ruwan maganin a hankali ina lumshe idona har na shanye duka,ina jin yadda Uncle ya soma tsotsar lips ɗina amma banda wani ƙarfin hana shi dukkan jikina ya saki kwanyata ma tamkar ta rabu biyu tunanina yana gushewa yana dawo wa kamar wani network.

Wani irin zazzaɓi ne nake jin yana rufe ni a sunnu,na ware idona a hankali kamar na jariri sabon haihuwa ina kallon Uncle da ya gama tsotse min baki.So nake na faɗa masa ina jin sanyi amma babu bakin magana,tashi na ga yayi yasa key ya rufe ƙofar sai a lokacin ne kuma Inna A'i ta faɗo min a rai.

Jakar kayana ya buɗe ya je ya ɗauko kayan baccina,irin rigar nan mai buɗewa ya saka min bayan ya zare ta jikina sai rumtse ido nake don ko bra ban saka ba saboda muddin ba fita zan yi ba takura min take.Shi ma irin rigar ya saka sai dai bai ƙulle tashi ba,ina ganin ya kashe hasken ɗaki ya kunna wutar ƴar ƙaramar waya sai ya ɗauko ƙaton blanket ya rufe ni kafin shi ma ya shigo ciki.Hannuna mai sanye da zobe ya kamo ya riƙe kafin yayi min rumfa da ƙirjinsa mai cike da yalwa gashi ta kwanta sai santsi take.

Wannan karon yana ɗora bakinsa kan nawa ji na yi kamar ya jona ni ga lantarki,tuni na ji duk jijiyoyin jikina sun dawo aiki.Na ƙanƙame shi gam ina yin numfashi da sauri-sauri,yayin da shi kuma ya ci gaba da shan yawuna kafin ya soma shayar da ni nasa can kuma ya cire bakinsa ya mayar da shi daidai kunnena yana cewa “faɗa min wa ya baku abinci jiya?”
Dukkan jikina rawa yake saboda sabon yanayin da na tsinki kaina,na tallabo bayansa da kyau na ƙanƙame shi ina jin lokacin da igiyar rigata ta since ƙirjinmu ya mannu da na juna sai na ji kamar raina zai fita tsabar shock.Murya na rawa na ce “ headmaster ne!” ina gama basa amsa ya ƙara lalubo bakina wannan karon har da romance yana yawo da hannunsa a duk sassan jikina.Ni dai duk abin kamar a mafarki nake jinsa ba zahiri ba saboda tunanina ba zaune yake daram ba,ban san lokacin da na yi bacci ba bugun ƙofa ne ya tashe ni.Na ware idona a hankali sai na ga Uncle a tsaye bakin ƙofa yana murza key,yana gama buɗe wa sai Inna A'i a tsaye kamar wacce aka fiddo daga rame.......


My book is only 500 via

2670215530
ZULFAU YAHAYA
Ecobank

DM +22795045822

Zuwa page 10 zan gama free page in sha Allah,za ki iya yin payment ɗinki tun yanzu.
[26/01 17:59] MRS SADAUKI: *MAKARANTAR MATSAFA*☠️


```LoVe aNd HoRrOr story```👽


By
Chamsiya Laouali Rabo
{MRS SADAUKI💫✍️}

*SADAUKARWA :* Ga dukkan Malaman makaranta.


*FCWA*☀️

________________________


08

Da wani irin sauri na gyara rigar baccina wacce na tuna sosai Uncle ne ya saka min ita .Na miƙe tsaye ina mai ci gaba da kallon Inna A'i wacce ta shigo ƙafafunta fututu kamar wacce aka fiddo daga kabari.Tana shigowa Uncle ya maida ƙofa ya rufe,sannan ya je ya zauna kan dadduma hannunsa riƙe da ƙaramar casbi.

“ Innarmu daga ina kike?” na samu kaina da tambaya.
Sai ta dubi Uncle Salem,ni ma sai na dubi bangaren da yake ina mai tambayar kaina ‘shi wannan a nan ɗakin ya kwana ko me?’ a nan take kuma kwanyata ta soma kawo min gogagen kilishen abubuwan da suka faruwa sai dai ba su fita sosai ba dishi-dishi ne ban ida tantance taƙamaimai abin da ya faru ba a tsakaninmu.


“ Bari har na yi wanka Nafisa, lokacin sallah ma ya gabato ” Inna A'i ta faɗa tare da nufar toilet.
Yadda na ji idonsa na yawo a jikina yasa na kai dubana gare shi,sai na ga ashe cinyoyina ne yake kallo bai ƙyaftawa.Duk sai na ji babu daɗi don dai bai saba yi min haka ba,na je na ɗauki hijabina na saka na yi tsaye har sai da Inna A'i ta fito daga wankan sannan na shiga saboda fitsarin da nake ji ya matse ni.



Wani irin tsoro ne ya kama ni ganin ina yin fitsari baƙi ƙirin da shi tamkar wani Lipton .Wani kuka ne ya ƙwace min tare da tashi ina yarfa hannu,ban san ta ya aka yi har Uncle ɗin ya ji kukan ba sai gani na yi ya shigo toilet ɗin sam kuma a wannan matakin da nake cikin tsoro ban ga aibun shigowarsa ba .


Wani irin sihirtacen kallo yayi min a tsakiyar idona da suke tsiyayar da hawaye kafin ya ce “ ki yi wankan tsarki ki fito, wannan dattin ciwon cikin da kika yi ne jiya ko kin manta har magani na baki?” yayi maganar yana jan ruwa fitsarin ya wuce,sai a lokacin na ji kunya tare da gyaɗa masa kai alamun na yarda.

Murmushi ya sakar min kafin ya fita,sai a lokacin na cire rigar baccin da hijabi.Wankan tsarkin na yi kamar yadda ya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login