Showing 24001 words to 27000 words out of 38445 words
Chapter 9 - MAKARANTAR MATSAFA COMPLETE NOVEL By Shamsiya Lauwali Rabo.txt
a yi masa?’ maganar Mama ce ta katse min tunani “ ki tashi kin yi baƙi” gabana ne ya bada rasss.....
[11/12 à 02:37] MRS SADAUKI: *SURUKATA*🪽🪽🪽
Na
*Chamsiya Laouali Rabo*
```{MRS SADAUKI}```💫✍️
*FCWA* ☀️
*SADAUKARWA Ga:*. Shamsiyya Manga, My Namecy 😊
___________________________________
02
“Ba.baaa...ƙi kuma Mama?” na jefo mata tambayar muryata na ɗan rawa ,ƙwanda ta kai min ga kai tana cewa “ munafuka kamar ba ta son auren ,tashi don ubanki ki je suna jiran ki”
Wani kallabi na jawo na ɗora a kaina kafin na fita,a cikin rumfa na gan su a zaune kan kujera sun tsurawa ƙofar ɗakinmu ido.
Dakyar na aro nutsuwa na gaishe su“ ina wuninku?”
“Lafiya lau amaryarmu” suka amsa su duka biyun lokaci guda,a fakaice na ƙare musu kallo suna sanye cikin dogayen kaya amma babu wanda ya ɗora hulla duk da ƙwan fitilarmu bai da wani haske sosai amma hakan bai ɓoye min ganin kamanninsu da Aliyu ba.
“To mu za mu wuce dama mun zo gaishe ki ne,kasancewar ɗazu dandazon mutane yayi yawa ba mu samu muka gan ki ba ” ɗaya ya faɗa ,kafin su miƙe dukkan su.
“To na gode” shine abin da na faɗa ina mai shigewa ɗaki ba tare da jiran sai sun tafi ba ko kuma tunanin yi musu rakiya.
“Har sun tafi?” Mama ta jefo min tambaya,na gyaɗa mata kai ta ce “ mene ne suka kawo miki?”
“Babu komai Mama ” na faɗa a sanyayye.Ta ja tsuki kafin ta ce “ wannan shegen sanyin halin ki bar shi tun yanzu,don gidan yawa za ki je sannan mijinki babban mutum ne wanda kullum cikin yin baƙi yake dole ki yi tunanin zama da shi.Yanzu su baƙin kin basu ruwa ma?”
Cikin na dube ta na ce “ Mama ruwan me za su sha su da ba wani abinci suka ci ba?” ludayin miya ta jefo min aka yi rashin sa'a kuwa ya same ne ga ƙwandar ƙafa,na saki ƙara tare da soma yin hawaye.Nan Mama ta rufe ni da balbalin bala'i da masifa sai da ta yi mai isarta sannan ta yi shiru.
Haka na rakuɓe can jikin gini ina shafar hawaye,ƙafar kuma tuni ta ɗan kumbura tana min zugi. Tausayin kaina ne ya kama ni,ina daga gefe ina kallon ƙannaina suna lesson tare da yin hira jefi-jefi a tsakanin su amma ni tamkar wata mujiya sun maida ni gefe.
‘ Allah ke da magani,da wannan masifar ta Mama ai gara na yi auren na bar mata gidanta ’ na faɗa a zuci kafin na kwanta kan tsohuwar ledar ɗakin sai baccin wahala.
Washegari kamar yadda Mama ta sunnanta mini a kowacce safiya zan miƙe na haɗa wa ƴan makaranta abincin safe haka na tashi tun da sauran duhu na fita zuwa madafa.Dakyar na samu wutar ta kama,na ƙara wanke tukunyar kafin na ɗora kan murhu na zuba ruwa.
Garin ɗan wake na ɗauko na zuba kayan haɗi na kwaɓa,kafin na je na share tsakar gida tasss.Ko da na gama tuni tukunyata ta tafasa,sai da na wanke hannuna sosai kafin na jefa ɗan waken sai kuma na shiga yanka albasa da sauran abubuwan da zan soya mai da shi.
Ba ni na ida aikin ba sai ƙarfe bakwai da wasu mintina,sai na hau kuma wanke kwanuka.Ina nan a zaune ƴaƴan takarda suka fito duk kowacce ta yi wanka ta shirya.
“Janikiii?” Mama ta ƙwala min kira,jiki na ɓari na tafi a guje don amsa kiran hakan ya tuna min da ciwon ƙafata sai na tsangale ƙafar ina mai raba ta da ƙasa.“ Mama ga ni ?” na faɗa ina yamutsa fuska saboda zugin da ƙafar ke yi min,“ daga nan bakin ƙofa za ki tsaya ?” ina jin haka na san da akwai matsala amma na daure na ida shiga,kamar jira take ta kai min duka tana mai cewa “ da kika girka abinci ubanki ya kawo shi da za ki ce ba za ki zuba musu ba? Har da wani zaginta kina yi mata gorin cewa kin kusa bar musu gidansu”
Ina jin haka sai na ɗaga kai na dubi Ayo don kuwa na tabbata ita ce ta ja min sharri,ina hawaye na fito na shiga madafa na zuba musu abin karyawa na kai musu.
Wanke-wanken da na ƙare cikin kuka kenan,da za su tafi don tsokana har da ce min ta yi “ ƴar aiki mun tafi makaranta” ban kula ta ba sai Sarah ce ta shigar min ta hanyar bangazar ita Ayon.
Bokiti na cika da ruwa na je na yi wanka,ko da na fito sai na tarar da robar da na ajiye ɗan wake a tsakar gida alamu ya ƙare.
” Mama ina nawa?” ita ce tambayar da na yi ko da na shiga ɗaki don yunwa nake ji jiya ban ci komai ba na kwanta,duk da ba mu yi girki ba amma su sun ci wanda aka tarbi baƙi da shi.
“ Ba ki ci ba ne? To ya ida ” ta bani amsa tana mai ci gaba da cin nata wanda ta baɗe da yaji sosai har sai da yawuna suka tsinke.Ban ƙara cewa komai ba na je na buɗe jakar kayana na ɗauko mai na shafa kafin kuma na fita zuwa ƙofar gida.Kan dakali na zauna ina magana ni ɗaya “ Yesu kana dai ganin halin da nake ciki amma ka yi shiru,sai yaushe ne zaka amsa kokena?” sai kuma hawaye suka zubo min,na duƙe kai ina mai ci gaba da kukan haɗi da ɗaukar wata tsumagiya na soma wasa da ita ina yin zane.
Inuwa na gani kai gare ni,da wani mugun sauri na ɗago kai sai muka yi ido huɗu da wani kyakkyawan saurayi.Ya sakar min murmushi kafin ya miƙo min hankici,ban karɓa ba sai farin hannunsa da ƙure da ido ina kallon yadda jijiyoyin hannunsa suka fito sharrr da su tsabar hasken fatarsa.
Kan fuskata ya jefo min hankicin ya kuwa rufe ta ruf,da mugun sauri na lumshe ido tare da buɗe ƙofofin hancina ina shaƙar ƙamshin turaren da ke kan kyakkyawan farin ƙyallen. Can kuma na sa hannu na cire shi daga kan fuskata,sai dai wayam ban ga saurayin ba.Waige-waige na soma ko Allah yasa na gansa sai dai tsit layin yake babu kowa ,na miƙe tsaye ina mai cewa “ to ina kuma ya tafi? Amma ai bai kai ace har yayi nisa ba” sai kuma na maida dubana ga ƙasa inda sawun takalminsa ya fito raɗam har da wasu harufa,kamar wata zarariya haka na soma bin sawun takun takalmin ina tafe ina mamaki har na zo hanyar fita gari.Sai kuma na yi tsaye ba tare da na ƙara taku ɗaya ba,na ce “ cab! Ashe ba ɗan ƙauyen nan ba ne ai wannan da gani ma sai a babban birni” sai kuma na juya zan koma,abin mamaki sai na ga nisan komawa can gida ba kamar tafiyar ba.Sai ma a lokacin na yi da na sanin abin da na yi don da wuya har zuwa wannan lokaci ace Mama ba ta neme ni ba.Na kwashe sama da minti talatin ina tafiya kafin na isa gida,sai na tarar Mama ba ta nan sosai na ji daɗin haka kawai na shige ɗaki tare da kwantawa saboda muguwar gajiyar da na ji ta saukar min.
A firgice na farka jin sautin muryar Mama tana zagina tare da jefo min tambayar da ta hantsila hanjin cikina “ ina abincin da na ce ki yi kafin na dawo?”
Ido na shiga zarowa saboda ni na kasa tuna lokacin da muka yi da ita na yi girki,ga ƴan makaranta kuma sun yi tsaye sun zubo min ido da alamu sun kwaso yunwa.
“ Don ubanki ba magana nake yi miki ba? Ina dambun da na ce ki yi?” Mama ta faɗa tana zuba min dundu a baya,cikin azaba na ce “ yana madafa cikin tukunya” a yadda na yi maganar cikin haƙiƙanin gaskiya ƙila shi ya saka Mama fita,ni kuwa da na san ban yi komai ba sai na ƙara tsurewa na zauna zaman jiran ta dawo na karɓi hukunci.
“ Ke Ayo kika ce ba ta girka komai ba,je ki madafa ki zuba kan babban kwano a ci gaba ɗaya” Mama ta faɗa bayan ta dawo ɗakin.Sam ban yarda da abin da ta ce ba sai da Ayo ta shigo da dambu yana ƙamshi,duk suka kewaya suka soma ci suna santin yayi daɗi.Ni kuwa ido na tsura musu tare da yin saƙo ina ta son tuna lokacin da na yi dambun,“ Janiki ina kika samu kifi?” tambayar Mama ta katse min tunani,murya na ɗan rawa na ce “ Abba ne ya aiko da shi”
Cike da masifa ta ce “ don baƙin hali irin naki shine kuma kika saka shi a miyar dambu?”
“Na rage saura yana madafa” na sake sharo wata ƙarya ba tare da na san dalili ba,da wani irin sauri Ayo ta miƙe ta je ta ɗauko Kifin nan kuma suka shiga ci ban sani ba daɗin kifin ne ya shagaltar da su suka kasa ganewa kifi ƙwaya ɗaya sai ci suke ya ƙi ƙare wa ko yaya.
Amma ni kam na lura da hakan,sai ya zamana tsakanin ƙaryar da nake yi tana zama gaskiya da kuma wannan abin al'ajabi wanne ya kamata na fi jin tsoro......
[13/12 à 08:05] MRS SADAUKI: *SURUKATA*🪽🪽🪽
Na
*Chamsiya Laouali Rabo*
```{MRS SADAUKI}```💫✍️
*FCWA* ☀️
*SADAUKARWA Ga:*. Shamsiyya Manga, My Namecy 😊
___________________________________
03
Abu dai kamar a mafarki ya tabbata gaskiya ne duk abubuwan nan da ke faruwa.Bayan sun ci sun ƙoshi suka ture Kifin wanda har yanzu kamar yadda Ayo ta ɗauko shi yake ko kaɗan bai ragu ba,“ ga shi nan ki ci ba don halinki ba” cewar Mama tana watso min mugun kallo.
Dakyar na iya ɗaga ƙafa na je na ɗauki kwanon da kifin yake ciki na fita can tsakar gida,kasa ci na yi sai aukin tunani da na fara.
‘ To duk wannan wa ya ajiye shi? Ko dai saurayin ɗazu? To in haka ne wane ne shi? Ko aljani?’ sai kuma na waro ido a take kuma na ji wani tsoro ya mamaye ni.
Ƙugin da cikina yayi shi ya fargar da ni da yunwar da ke ƙumshe da shi tun safe ban ci komai ba.Haka kawai na ji ban iya cin abin da ban san waye ya ajiye shi ba.Can madafa na kai na ajiye shi sannan na fita zuwa maƙwabta gun ƙawata Rahila,na kuwa yi sa'a ummarta ba ta gidan don sosai ta tsani ƙawancen namu duba da yadda na zama mujiya a cikin ƙauyen babu mai ƙaunar ya raɓe ni.
“ Laaa! Wai ke ce? Yanzu kuwa nake shirin zuwa gidanku na kai miki ɗan malele da na yi” Rahila ta faɗa cikin fara'a.Na saki murmushi na ce “ kamar kuwa kin san tun safe ban ci komai ba”
Nan take yanayin fuskarta ya canza ta ce “ ba ku yi abincin ba ne ko kuwa yau ma hana miki suka yi?”
Na ce “ bani da na ci na ƙoshi na baki labari” ba ta musa ba haka miƙo min shi cikin kwanon mai murfi,na buɗe tare da zauna wa na soma ci .
“Akwai sauran yajin ne ki ƙara min?” na tambaya,ta je ta kawo min kafin ta ce “ wane labari ne za ki bani?” ban ɓoye mata ba na labarta mata batun ɗan waken da Mama ta hana min har zuwa aljanin saurayin yau da kuma abubuwan mamakin da suka faru.
Rahila ta ce “ ki ce gamo kika yi da aljani na ƙwarai,kin san da cewa ita ma Asabe ta taɓa ganin wani ɗan albarka har ya taimake ta ?”
Na waro ido na ce “ wai kuma aljani da gaske?”
Maimakon ta bani amsa sai ta canza zancen da “ jiya wai bushe-bushen mene ne aka ta yi gidanku? Na so na leƙa amma Umma ta hana”
Nan take na ji abincin ya fita raina,na fidda hannuna tare da sunne kai.“ Mene ne wai?” Rahila ta tambaya da sauri.
Dakyar na bata amsa da “ aure za su yi min da ɗan hajiya Luba aminiyar Mama”
“Wai Luba ƴar bori ?”
Na gyaɗa mata kai kawai,Rahila ta wani ƙara gyara zama ta ce “ cab! Wane daga ciki to? Ai na ga duk suna da aure”
“Aliyu” na bata amsa .
“Innalillahi wa'inna ileyhi raji'un!” ta furta tare da yin shiru,sanin wannan furicin musulmi ba su yinsa ne sai in wani mummunan abu ya faru na yi saurin ɗago kaina na dube ta.Hawaye na gani tanƙam a idonta,hankalina sai ya ƙara tashi na shiga tambayar ta “ Rahila lafiya?”
“Janiki har ƙiyayyar da Mama ke yi miki ta kai haka da har ta yarda ta aura miki mahaukaci?” ta yi furicin hawaye na silalo mata.
Na daki ƙirji na ce “ mahaukaci kuma?”
Ta jinjina kai ta ce “ wane ne bai san Aliyu nada taɓin hankali ba? Tun bayan dawowarsa daga mission ya haukace an ce wai ƙarar alburushi ce ta taɓa masa kwanya,amma wai a hakan Mama ke son haɗa ki da shi?”
Jikina ne ya hau rawa kamar wacce aka zubawa ruwan ƙanƙara har sai da Rahila ta riƙe ni gam,“ na shiga uku Janikiii?” ta furta cike da tashin hankali.Da sauri kuma na ture ta tare da miƙewa tsaye ko hannu ban wanke ba na fita a guje zuwa gidanmu .
Cak na tsaya ganin Hajiya Luba zaune dirshen kan tabarma ita da Mama suna tsara yadda bikin zai tafi har da zanen kayan katakai.
“Ke lafiya don ubanki kika wani shigo a firgice kamar mai figar ruwa?” Mama ce da wannan furicin ,hakan ya bai wa Hajiya Luba damar ɗagowa ta dube ni.
“ Ƴata Janiki ƙaraso ki duba da kanki ki zaɓi kalar gadon da za a yi miki ” shine abin da ta ce ,kamar mahaukaciya haka na ƙara kwasa a guje na fita a tsiyace.Gudu nake ban tsaya ba sai da na kai bayan gari sannan na samu wuri na zauna na haɗe kai da gwiwa na soma kuka kamar raina zai fita.
Tsawon lokaci ina a haka kafin na ji tsayuwar mutum a kaina,ban wani damu ba na ci gaba da kukana.
“ Ke ba ki gajiya da kuka?” na tsinkayo sautin muryarsa,da wani mugun sauri na ɗago na dube shi .Saurayin ɗazu da safe ne,yayi wanka ya sauya kaya sai baza ƙamshi yake.
Ruwa ya miƙo min a gora ya ce “ ungo wanke fuskarki sai ki goge ta da wannan ” ya haɗo min har da sabon hankici.Kamar wacce ya yi wa asiri haka na karɓa na buɗe murfin gorar,ina soma wanke fuskata sai na ji duk wata damuwata ta gushe.Na lumshe ido ina mai ci gaba da watsa ruwan da nake jin su tamkar ruwan tsarki da father na Coci ke bamu labari.
Ina buɗe ido yanzu ma wayam ban gansa ba,“ to ko dai aljanin ne kamar yadda Rahila ta ce?” na tambayi kaina a fili kafin na miƙe na kama hanyar gida.
Kiciɓis muka yi da Hajiya Luba a ƙofar gida,ta dubi fuskata kafin kuma ta maida idonta ƙurrr kan hankicin hannuna.Yadda ta ƙure shi da kallo yasa ni ma na kai dubana,sai na ga a tsakiyarsa an zana masa wani hatimin masarauta.
Da sauri na jimƙe shi ina mai cewa “ har za ki tafi?” ta sakar min murmushi ta ce “ eh ai mun gama zaɓen komai” sai kuma ta raɓa gefena ta wuce .Na bi ta da kallon mamaki,sai na ga ta waigo muka haɗa ido da sauri na shige cikin gida.
“ Tun da kin dawo daga yawon gantalin sai ki zo ki fidda masara a ruwa ki je ki kai niƙa,yau tuwon laushi za a yi” Mama ta faɗa tana mai ci gaba da ƙirga kuɗin hannunta,na kuma yi imanin cewa Hajiya Luba ce ta bata.
Sai da na je can ɗaki na adana hankicina biyu har da na ɗazu kafin na zo na soma aikin da aka sani.Bayan na fidda masarar na je na kai niƙa na dawo sannan na hura wuta,na ɗora tukunyata sannan na soma tankaɗe garin.
Haka na yi aikin ni ɗaya ko ijin wuta babu wanda yayi min har na gama,na je na yi wanka .
Ana kiran sallar magrib Abba ya shigo a gajiye ,ni ɗaya kawai na gaishe shi ya amsa kafin ya ce “ ki kai min ruwan wanka”
“Toh Abba” na faɗa tare da fita na kai masa,kayan da ya cire kuma na ɗauko na fito da su don na wanke Mama ta tsayar da ni.
“ Me za ki yi musu?”
“Wankewa zan yi” na bata amsa.
“Kin manta gobe Lahadi? To ki ajiye su zuwa gobe da safe sai ki haɗa da na yaran duk ki wanke”
“Amma Mama gobe akwai zuwa Coci” na faɗa murya na ɗan rawa don ban son yin abun da za ta hana ni zuwa wurin bautar Ubangiji.
“Gara da kika tuna min Kirista ta ƙwarai ai ni kin san bani sallah sai ke”
Da sauri na sunne kai saboda a duniya ina tsoron mugun kallon Mama,na gwammaci ta dake ni a kansa.Haka ina ji ina gani na mayar da kayan,da kowa ya fara cin abinci ni kasa ci na yi saboda tunani biyu na
[30/01 08:49] MRS SADAUKI: Sati guda currr Mama ta ɗauka tana azabtar da ni da yunwa,ba wai ba ta bani abincin ba ne a'a sau ɗaya tal nake da damar cin abinci a wuni a maimakon sau uku.Kuma wanda ake bani ɗin ba wani ba ne,ƙarin haushi kuma ni ce ke girka musu abincin wani sa'in ma ita Mamar sai na yi mata nata daban saboda juna biyun da ya bayyana gare ta mai kwaɗayi.
Yau ta kama asabar,gobe kuma ranar zuwa coci in na tuna da goben zan kai wa abin bautar tamu kokena a ɗakinsa har wani sanyi nake ji yana ratsa ni.
Tun wuri na yi dukkan ayyukana har da wankin kayan ƴan gidan,sannan na yi musu girki.Ina zaune gefe ina kallon su suna cin girkin rana,shinkafa da miya ce na yi musu sai ƙamshin kifi take.
“ Ko a zuba miki tun yanzu?” Mama ta jefo min tambayar,na jinjina kai alamun eh.Sai ta ɗauri wani ƙaramin faranti ta zuba min tare da turo shi gabana tana zagina “ don ubanki gobe ma ki sake yi min laifi,azabar da zan yi miki sai ta fi wannan.Kuma ki bar kallona da shegun idanun naki masu kama da na aljanun ruwa ”
Ban ce mata komai ba na ɗauki abincin na fara hannu baka hannu akushi,ko minti biyu cikkake ban ɗauka ba na cinye kuma