Showing 27001 words to 30000 words out of 42346 words

Chapter 10 - DR SAGEER BOOK COMPLETE BY NANA DISO.txt

05 Oct 2025

1223

tanajinta duk bakin ciki ya isheta...

    Part din yasmin ta shiga taganta da doguwar rigar atampha ke menene haka?.

    Dallah jiki canja 'yan kanti ake sawa da dadda irin body hug dinnan atampha ai sai da rana..kuma ki kula wallahi kada kisake ki bawa kishiyar ki fuska ta raina ki ke karma kidinga sakar mata fuska...

   Tohm yaya Aisha.." kuma kidinga likawa gida damutanen nan sun samana uwa agaba ke wai har da maryam azagen mama ni har fada tayimin akan nayi musu magana....

   " Ai mama bataso ayimusu komai narasa dalili wallahi...

    " ke ni bari natafi mijina yana jirana sai munyi waya..

    Tohm..

Yana dawowa yasmin tasa riga da siket sun kamata gasu daman roba da taji dr yace yana palour din kasa yana ki ranta...

    Tana zuwa tace sannu da dawowa yasu mama?

    " Duk suna gaishe ku..

Ya K'alli ramlat yace maganar me kikace za'ayi??

  " Eh naga kamar batasan almajirai ne suke mana gyaran gida ba har dak'in ka...

     " yasmin ce tawani kada ido tare da daga dan yatsa tace no fa babu wanda zai gyaramin dakin miji wallahi ni zangyara abu na..

    " Kinga malama tun kafin kizo gidan nan akeyin haka...

    " yasmin tace yanzun kuma sai gashi nazo ba kuma babu wanda zai gyaramin dakin mijina ni zan gyara nasamu lada ...

     " mtseww sai kiyita yi...

    " Zantayi ai tunda neman aljannata nazo yi ba wasa ba...

    Dr sageer ne yace ya'isa haka ke ramlat kina sawa ayi miki ranar girkin ki kekuma yasmin sai kiyi ranar naki girkin...

   " Tohm tace sannan tatashi tabar musu gurin tana shiga tasamu guri ta zauna bayan wasu 'yan lokuta yashigo wanka yayi sanna ya kwanta tunda yashigo yasmin taga kamar ba'a yadda yafita ya dawo ba...

    " kwanciya yayi ya jingina da gadon... " yasmin kuma fita tayi tazubo masa lemon kwakwa sannan tasa key adakin tarage fitila zama tayi kusa dashi tace ga lemo na markada maka?

     " bazan iya shaba yasmin ki shanye ke... " batace komai ba ta ajiye tayi gefe da kanta...  " haba sweetheart menene haka kuma kinsan amfanin kwakwa dai kuma kinga bakiyi tsarki ba idan nasha sha'awa ce zata dameni kada naje nayi barna adaren nan...

    " Kwanciya tayi agefen kirjinsa wani irin kamshi ya shaga ga dukiyar fulanin ta duk sun ciko cikjn sanyin rai tace to meke damunka mijina..

    " Nan yabata labarin khalil har kudin aikinsa da za'ayi masa...

  " haba my doctor kanafa da arzukin biya masa danAllah ka biyamasa shi shi taimako ai baya karar da arzuki kuma dum sharrin dayayi aikaga kansa ya koma yanzu please ka biya masa...

     " tabbas maganganun ki hakane inshaaAllahu zan biya matata inaji dake! Wayarsa ta gani ramlat tana kiransa sauri tayi tafara kissing dinsa Sai da ta tabbatar ta katse ta sakeshi.. " cikin wata rarraunar murya yace ina sonki dake zan zauna yasmin, kina raina dan ke nagina soyayyata na shaida da halinki, idan nayi fushi ki rarrashine, idan gani ga ki sai naji ina cikin farin ciki, sonki yana cikin jikina, kisa ranki ni naki ne har abada bazaki bar gidana ba...

  " dariya tayi tace farin ciki kai ne mai bani, kai kazamo muradi na, siyasa tayi ta kashe wayar, ya rungume matarsa har bacci ya kwashe ta yayi mata addua sannan shima ya kwanta....

   Ramlat ce ke faman zageyi wallahi sai nayi maganin yar iskar yarinyar nan sai na koya mata hankali shima harda kashemin waya aikuwa wallahi zai gane kuransa...
Hello rabia gobe kizo akwai matsala..." tohm ramlat sannan tasa dariya lokacin da zan kashe miki aure yazo hahaha....




Assalamu alaikum!!!

   *ALLAH YA RABAMU DA  HASSADA... DA WULAKANTA MUTUM DA KUMA FASIQANCI YARABAMU DA KARYA ALLAH KATSAREMU SHARRIN ABUNKI...BAMU SHARRI ALLAH YATSARE MU DA MASU SHARRI*

   _Ina gaisuwa da jinjina gareki kuyi hakuri da shiruna da kukaji ubangiji Allah yabiya muku bukatun ku na alheri_

    *Endless lurv ...oll your comment make me happy...soyayyar da kukeyiwa wanga littafi bazata faduba but still ina godiya..*

   ~ *I can't stop saying..please avoid all the grammatical And spelling errors..*~*

  *Ina Kuma fatan kuna amfanuwa da abunda nake rubuta??..* (Abunda muke ba daidai Allah yayafe mana) Ameen
_
   *Please do vote comment and like your vote and comments give me more courage to continue writing my story...and it helps me to write better...#TEAM...DS....DS LOVERS*_

*Urs Nana diso*

Deejarh berver

http//:deejarhberver.wordpress.com

Email:kabba43@yahoo.com

Gmail:nanadiso100@gmail.com   

Wattpad:NEIRNAHDISO

  
[11/6, 1:45 PM] Aysha Galadima: 70-75

*_DOCTOR_*
        _*SAGEER*_

_NA NANA DISO_

      http://deejarhberver.wordpress.com

   © *HASKE WRITER'S ASSOCIATION*

Tun asuba bayan dr sageer yafita yasmin ta gyara dak'in sannan taje ta gyara nasa daga nan bata tsaya ko'ina ba sai kitchen nan tagara feraye dankali tana cikin soyawa taji an rungume ta ta baya murmushi tayi sannan tace har ka dawo..

    " sumbatar ta yayi ta gefe yace nadawo my swewtheart me zan tayaki dashi..

   " haha tohm kayi mana blending din kankanar nan sai kisa a jug, angama cikin kan kanin lokaci yagama sannan yadawo kusa da'ita nagana my queen!..

    " Amma fa najidadi wallahi kaje kayi wanka tukun kafin nakarasa...

    " No! Ai ni ke zakiyimin.. " zaro ido waje tayi tace aini ba'a koyamin yiwa manya wanka ba sai yara kanana.....
   
  " bata rai yayi yace aini jaririnki ne sai yadda kika sarrafa ni oya yisauri inajiranki...

     " shagwabe masa tayi tace ni Allah ban iya ba kaje kawai kayi abunka..

   " ransa ne ya baci batare da yace komai ba ya fita ya nufi dak'insa tabbas yana mutukar bukatar yasmin ga soyayyar ta dake dawainiya dashi nan ya kwanta a kan gado yakasa tashi...

   Yasmin nata maganar ta amma taji shiru tana juyawa taga bata ganshi ba nan tace tabbas tasan baiji dadi ba tana karasa farfesun sannan ta huce zuwa dak'inta wanka tayi tasaka wata doguwar riga duk ta matseta duk shape dinta yafito nan tashafa hoda sannan tasa pink lipstick tayi kyau sosai....

  Ramlat ce tafito ga cikinta yayi nauyi dariya tayi taga anshirya dinning nan ta zauna ta zuba tafaraci..

   " sallama yasmin tayiwa dr yana kwance ahankali ya amsa cikin mamaki tace au bakayi wanka bane??

   " Banza yayi mata har ta karaso kusa dashi gaba daya shaawar ta ta lullubesa baisan lokacin daya kamo ta ba kissing dinta yafara kota'ina duk yakusa zauce wa, da sauri tayi baya tace lafiyarka kuwa??

     Yasmin kada kisa na hauka ce please kibani hakkina yasmin please..

    Mamaki ne duk ya cikata yadda taga duk yafita hayyacinsa cikin sanyin murya tace banyi tsarki ba fa...

    " zan baki magani kisha ya dauke please ina mutukar sonki yasmin please yakara kallon shigar datayi yayi mata mutukar kyau...

   " Shiru kawai tayi masa dan ita wallhi bazata sha magani ba can tayi siyasa tace kada ka makara a office please ka tashi kayi wanka...

    " ciremin rigar to.." a hankali ta fara kokarin cirewa tana matsowa kusa dashi zata balle botul din yakara sumbatar ta... " cikin murmushi tana hararar sa tace nifa kada kaceremin bakina gaskiya... " Hahaha naga na wane bakin ai ko nacereshi babu komai...

   " wanka yashiga yana fitowa yasa kayansa sannan suka sauko daga sama nan suka tadda ramlat tanata cin abinci yasmin daman ta fahimta don taji haushi tayi hakan aikuwa sai tayi dariya tace mai ciki ai gwara dakika fito..

     " Dr sageer ne yace yajikin naki?  Kallonsa tayi tace da sauki abincin yadanyi yaji please arage cika yaji..

     " yasmin ce tace na manta ai sorry za'arage kinsan ku bakomai kukejin taste din ba..

       " ramlat kallon ta tayi ta dallah mata harara tace anjima zanje gida..

    " yasmin ce tace maje tare na gaida momy... "ramlat ce tace kije kiyi mai??

    " Opps sorry namanta ma mijina baison yawan fita in kinje kya gaisheta yana ganawa ya sumbace ramlat agoshi yace kina bukatar wani abunne? " eh katawomana da abarba da pear...

     " yaamin ce tatashi ya rakashi har bakin motarsa sannan tace Allah yatsaremin kai mijina yakareka kakula da kanka please...

     " ki kularmin ke ma da kanki please kiyi wanka kuma danAllah sweetheart kinji...

    " murmushi tayi ta koma cikin gida bai tafiba sai bayan tashiga ciki...

     " Zanyi maganinki da kaina sai kin bar gidan nan cewar ramlat munafuka kawai matseya ciya...

    " yasmin ce tayi gaba ko kallonta batayi ba sannan ta shige part dinta...

   Baffa ke zaune yana cin tuwo, mama ce tace khalil fa ba lafiya bakaje kayi musu sannu ba...

     " subhnallahi bansaniba amma zan lika in nagama...

    " Mamee ce ke faman masifa haba alhaji haruna mutuwar zuciyarka tayi yawa ko abinci bamu dashi nifa nagaji...

    " To ya kikeso nayi kowa yaki daukata sana'a...

     " Aikuwa bazaiyihu ba ehee..

     Sallamar baffa ce ta katse su babu wanda ya amsa masa dakin inna yashiga tace sannu da zuwa yauwa ina yini ya mai jiki kuma?

       " jiki alhamdulilahi ai yaron arzuki sageeru ya biya kudin aiki sai dai Allah yabiyasa...

    To mashaa Allah ga dubu dare kyayi jinyarsa...
  "  Allah yasaka da alheri...

   Inna ta nuna alhaji isa tace ahaka zaka mutu da bakin ciki wallahi wannan danuwan naku yayi gaba ku kuma alhakin sa bai kama ku ba...

   Bayan yafito alhaji isa yace bani ko dubu biyu ne danAllah...

   " Dallah matsa ficeka bazan baka ba wallhi nagayamaka banza mai mutacciyar zuciya...

    " DanAllah dan annabi ki taimaka biyar bani dashi haba matata...

    " Ga hamsin nan akan taga sai ka dauka...

    Yau tana girkin ramlat tana zaune suna waya da rabia tana gayamata irin rashin mutuncin da zatayi wa yasmin sai gab da magriba ta dafa indomie...

   " yasmin kuwa bayan tayi wankanta tayi cake sannan  sannan tayi lemon kwakwa da dabino...

    Dr sageer yana dawowa dakin ramlat yafara shiga sannan yace kunci abincin ko?

     " ai yasmin tace bataci ga naka nan kan dinning..

   " Me zaci to idan bataci abinci ba bari nayi wanka sai na sakko...

     " bayan yayi wanka ya huce dak'in yasmin sallah yatarar tanayi sannan yaje yakarasa wani aikinsa a computer daga nan kuma ya koma tana zaune tasa wani half gown tayi mata kyau sannu da zuwa..

   " to me zakaci kikace bazaki ci abinci ba ..

    " kaga cake nayi kuma nayi lemo shiyasa.. " zama kusa da'ita yayi yace muji cikin to.. " dariya tayi tace Allah na koshi..

   Jan bakin nan naki yayi kyau sosai kafin tayi magana yasa bakinsa anata janye kanta tayi tace bafa girki na bani...

    " jikinsa yana rawa yace danAllah yasmin please yakara kamota kan gado ya cillata nan yafara sarrafata yana kokarin cire botul dinta ta gartsa masa cizo tayi sauri ta miki tayi bandaki aguje ta rufe tana haki...

   " yasmin yasmin danAllah ki bude ki taimaka kada na mutu danAllah...

   " Bafa girki na bani ba, wannan ai cin amana ne...

    " ki tsaya kiga sai na bude kofar bari na dakko daya mukullin...

      " yana fita tafito tasaka sakata aduk ko fofin sannan ta saka mukulli...

     " yana dawowa duk hankalin sa atashi yafara bude kofofin sai dayazo ta karshe sannan ta bude tana kan gado tana kuka danAllah kabari doctor please babu kyau wallahi ba girki na bani....

   " kallon ta kawai yakeyi yana kokarin nufota yasmin kibarni kada nasamu matsala ita dai tana ta kallonsa yana kokarin tabata sai ya wadi kada sumamme....

   ASSALAMU ALAIKUM

LAFIYA UWAR JIKI BABU MAI FUSHI DAKE...

   _Ina gaisuwa da jinjina gareki kuyi hakuri da shiruna da kukaji ubangiji Allah yabiya muku bukatun ku na alheri_

    *soyayyar da kukeyiwa wanga littafi bazata faduba but still ina godiya..*

   ~ *I can't stop saying..please avoid all the grammatical And spelling errors..*~*

  *Ina Kuma fatan kuna amfanuwa da abunda nake rubuta??..* (Abunda muke ba daidai Allah yayafe mana) Ameen
_
   *Please do vote comment and like your vote and comments give me more courage to continue writing my story...and it helps me to write better...#TEAM...DS....DS LOVERS*_

*Urs Nana diso*


http//:deejarhberver.wordpress.com

Email:kabba43@yahoo.com

Gmail:nanadiso100@gmail.com   

Wattpad:NEIRNAHDISO

  
[11/6, 1:45 PM] Aysha Galadima: 75-78

  *DOCTOR*
           *SAGEER*

_NA NANA DISO_

      http://nanadisoo.blogspot.com

   © *HASKE WRITER'S ASSOCIATION*

     Yasmin ce ki kokarin kallon inda dr ya wadi nan ta gigice cikin rudewa ta sakko tana jijjiga shi tare da fadin danAllah katashi mijina wallhi badan na bata maka bani ba kuka takeyi sosai da sosai, cikin hanzari ta kirawo dr khalifa bugu daya ya dauka yace lafiya  yasmin naji kina kuka??

     " Dr zai mutu danAllah kataimaki ne.." Lokacin yace me yafaru cikin kuka tagaya masa shiru yadanyi na lokaci sannan yace gaskiya yasmin baki kyauta ba mijinki ne fa kuma kinsan bashida cikakkiyar lafiya kuma kinsan illar sha'awa kuwa? To takansa mutum cikin hauka mutum yafi mahaukaci zaucewa idan ta motsa masa..

   " Nasan nayi kuskure wallahi amma ni banyi tunanin abun zai kai haka ba, yanzu yazanyi ya tashi...

  " karki damu nan da 1hours zai miki amma ki dakko ruwan sanyin kina danna masa jikinsa...

    " cikin hanzari ta kashe wayar sannan ta dakko towel da ruwa tayi yadda akace mata sannan tafito dan tasan ramlat sai tafito kiransa..

    " Ramlat ce ta dallawa yasmin harara ke kin manta girkina ne? Banson ni iskanci yaza"ayi ki janye shi??

    " Yariga yayi bacci bansaniba ko ciccibo miki shi zanyi sannan ta shiga dakinta tasaka key...

  Ramlat ce tace lallai yarinyar nan sai na koya mata hankali wallhi zakigani sannan ta koma part dinta...

     " zama tayi agefensa tana ta kallon sa har ya bude idonsa da yayi jajir dashi jiyowa yayi yana kallonta cikin damuwa tace sannu yaya..

    Ko kara kallonta baiyi ba sannan ya fita dakin sa yashiga wasu magunguna yasha sannan yasamu yayi wanka yasmin ce hankalin ta atashe ta biyosa dak'in kafin takaro cikin wata irin tsawa yace fitar min a dak'i...

     " hawaye ne yafara wanke mata fuska amma haka ta hakura tafita tana zuwa dak'in ta wada kangado sai kuka ahaka bacci ya kamani...

   Khalil an salamo shi daga asubuti yakoma baki yarame yayi kamar ya mutu inna ke kusa dashi tana sannu ba dan halin ka shigen son duniyar tsiya gashinan ka hadu da wanda yakusa kaika lahira...

     " wallahi inna bazan kara yin komai ba danAllah ki yafemin wallhi nasan nayi kuskure...

    Kadai nemi yafiyar Allah batawa ba..

Alhaji haruna yana fita yatarar da wasu mutane suna jiransa har zai koma cikin gida suka rikoshi daman munzo ne akan bashin da kukaci a kamfani na million 30 ashekarun ba munzo ku bada kudin...

    Hankalin sa ne yatashi dan shi ya manta ma sunci, zara ido yafarayi yana rantse rantse zasu kawo musu karshen watannan...

    " okay sukace sannan ya shiga ciki yana zuwa yadinga kwallawa isa kira to munshiga cikin bala'i isa mun shiga cikin masifa banki sunzo karbar gidansu...

    " inna ce tace Allah yakara muku ai daman duk wanda ya dauki duniya da zafi to zaiga ta kuwa...

     " motar khalil zamu siyar sai a harhada musu kudin ko..

    Eh hakane kam, ko kuma musai karamin kudi mu barmusu su kwace gida hahaha kaga munsa baffa cikin tashin hankali shine baida inda zaije...

    " yauwa d'an uwa kayi tunani mai kyau sosai da sosaima haka za'ayi kuma maganar yan fashin da mukace zamu tura masafa?

     " ai munyi magana dasu yau zasuzo nace su kwashe masa komai da komai kar su barmasa komai...

     Mamee ce tace kai amma kunyi tunani mai kyau wallahi...

     Mama ke faman dariya labarin da baffa yake bata, wane satin zamu koma sabon gidanmu inshaa Allah..

   " kace har ka gama? Mashaa Allah naji dadi Allah toh yakaimu da rai da lafiya ..

    Yasmin tana tashi da safe sallah tayi sannan tatafi tayi wanka taje kitchen taga har andafa ruwan tea dankali da kwai ta soya sannan ta huce dinning table ramlat sai kallonta takeyi itakan ta kayan nata sunyi mata kyau zama tayi suna jiransa ya sakko basu jima ba sai gashi ya sakko kusa da ramlat yatafi yace am sorry matata nasan nayi miki laifi jiya bakijini ba banjin dadi ne da wuri na kwanta..

   " murmushi tayi tace ai bazan iya fushi da kai ba mijina..

   " to me kika dafa mana tea na kokarta nayi waccan kuma tayi dankali da kwai..

    " To zubamin tea din kawai shi zansha...

   " Yasmin kuwa zuciyarta kamar tafashi amma shiru tayi tana kallonsu....
  
   " Shikuma sai satar kallon ta yakeyi wayar ta ce tafara ringing tashi tayi ta dakko nan da nan dr yafara gigicewa irin shigar datayi bashiri kuwa ya dauke kansa..

   " hello yusra kina lpya cewar yasmin?

    " lafiya kalou nake ke jibi kamuna fa nida dr khalifa..

    " Toh zankiraki Allah yakaimu....

     " Dr sageer ne ke shafa cikin ramlat yana fadin baby na yakusa fitowa...

     " zanje wankin kai kaji?

      " banza yayi mata sai da takara maimaitawa yace bazakijeba..

     " ramlat ce tayi wata bazawarar dariya...

    " tashi yayi zaitafi ya sumbaci ramlat yasmin tace bakaci dankali da kwai ba...

   " Bazan ci ba..

" biyoshi tayi zata rakashi yace koma bana bukata...

  " ramlat ce tasaka dariya miji ba sonka yake ba sai naniki masa akeyi..

     " yasmin ce tace ai ko yanzu kasuwa tatashi dankoli yace riba..tahau sama..

  Anty rabia ta kira tace ta turomata mai kunshi da kitso tace tohm shikenan zan turomiki da'ita anjima...

   
  Da daddare gurin karfe tara su baffa sukaji an hauro musu cikin gigicewa da addua suka tashi su bakwai ne suka danno cikin dakin sa babban su ne cikin tsawa yace kudi kudi ko mu kasheka...

     " baffa ne yace ko nawa kukeso zan baku kukwantar da hankalin ku amma kuma

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login