Showing 12001 words to 15000 words out of 42346 words

Chapter 5 - DR SAGEER BOOK COMPLETE BY NANA DISO.txt

05 Oct 2025

1224

dake jure akwai da babu itace mace..

    " sageeru kenan yanzu sai zuwa kwana biyu sai a sallameka kenan??

    " Ai na warke anjima karfe 4 akwai wacce zanyiwa cs...

     " Haba sageeru yaushe ka warke din ka hadata da wani likitan sai ya yimata....

     " Mama banga amfanin aikina ba idan bana taimakon talakawa domin wannan matar danake gayamiki satinta daya a asubuti batasan wake kanta ba sai shekaran ko abincin da zataci batada shi ko kudin ganin likita tana cikin halin taimako sosai...

     " Tohm shikenan sageeru Allah yakara budi da takawa da imani ...

     " Ameen mama....

Yasmin ce ke zaune tanacin abinci sai kuwa hajiya cewa tayi kinga har an sallamesu har ya huce asubutin sa...

     " kai amma anya ya warke kuwa??

     " ina wata warkewa? Kawai dai kinsan mutum ne mai taimako...

     " Allah sarki Allah to yakara lafiya..

    " Ameen ... Nikuwa yasmin har yanzu babu tsayayye??

      " Murmushi tayi zuciyarta cike da kunci tace Allah bai tsayar ba,Amma munata addu'a..

   "Hajiya tace ai dama abun na Allah ...Allah yabada nagari ..ameen tace sannan tatashi tayi cikin dakinta da wayarta ke faman ringing...

    " Hello yasmin ykke yusra ce .....
  
   " Banza sai yau kikaga damar kulani to kinkyauta.....

    " wayata aka sacemin shiyasa ankawo kudina ansa wata 5 fa..

     Haba danAllah congrat Allah yasa damu za'ayi...

   " Ameen yasmin DanAllah ki amince da dr sageer ba lallai sai mara mata ba kowa fa da zabinsa da Allah yayi masa ke dai kiyita Addua Allah ya tabbatar muku da Alherinsa...

     " bazaki gani ba yusra bafa wani sona yakeyi ba kawai yaudarata yakeyi...

   " kada ki yanke wannan hukuncin kibashi dama yasmin...kuma kisani wayake auren soyayya yanzu? Malama anayin aureni dan kauna in akwai kauna ai babu wulakanci da tozarci kuma dan a rufawa juna asiri ne, dukiya ba itace aure mai wadatar zuci mai tsoron Allah wanda zai kula dake wannan shine mai sonki...

    " Yasmin ce tace tabbas hakane dan bazan manta maganan malamin mu ba da yace idan kuntashi adduar miji kuce in talakane Allah yabaku mai addini mai kuma sanaa in kuma mai kudine Allah yabaku mai addini mai kuma aiki dashi...

Hakane kawata nagode sai kinjini, sannan suka kashe wayar...

   Dr sageer dake zaune akan kujerar sa yana cin abinci wayarsa ce tafara ringing salama yayi sannan yace wake magana...

     " yasmin cikin rashin kulawa tace nice dama mama tace mekakeso adafa maka??

     " cikin murmushi kamar tana kallon sa yace duk abunda kika dafa ai zanci...

    " yajin naka?

" Naji sauki ai.." Allah yakara lafiya..

    " Ameen nagode my queen Allah ya mallaka min ke a matsayin matata yadda nake sonki Allah kadai zai shaida...

    " Batare da tace komai ba ta kashe wayar cike da murmushi tana fadin kai kasani...

    Hajiya suwaiba ce tashiga cikin part din su mamee ko sallama batayi ba tace tabbas kun nunamin ku makiya nane kunsaka hassada da bakin ciki acikin ranku tayaya zakuyi gaba to sageeru dai bai mutu ba, haruna kuma sharrin ka kai da isa akanku sai kare marasa mutunci kawai...

    " Dukkan su babu wanda yayi magana dan  suna shayenta sosai da sosai...

   
   Abida dake faman kuka tana kaci amanata garba baka kula dani baka sona har yaushe mukai auren zakaci kishiya hatta kusa dabi baka zuwa ...

    " Garba ne yace ai ko jaki yanason kulawa da hutu ballantana ne mutum, menene bana yimiki acikin gidan nan menene bana baki tundaga kan ruwa har reza?  Bakya tsafta kwata kwata dubi dakinki sai kace na mahaukaciya naga har tsintsiya sai na siyo?? Bakya kitso akan kari bakya dan kunshin nan da mata sukeyi ke harma irin style dinkinnan bakyayi wanda zan kalleki naji sha'awar ki komai ina baki har kudi kaya abinci komai akwai ayimin naji dadi ne baza'ayi ba ba? Dan haka aure babu fashi, karatun Alkur'ani tunda muke agidannan banga kinayi ba to uban me kikeso nayi miki??

    " Kuka tasaka tace inshaa Allahu zangyara har sallah ma zantsayar inshaa Allahu kayi hakuri sannan ta durkasa...

    " bakomai abida ni ina kaunarki shiyasa natsaya ina gayamiki gaskiya...

   " zangyara inshaa Allahu mijina...

    Ramlat ce ta fito daga wanka tana amsa waya nan dr sageer ya shigo jakarsa kawai ya ajiye sannan ya rungumeta my brstr kullum kyau kiketa karati sannan ya sumbaci bakinta...

    " shiru tayi sannan tace wane irin so kakeyimin dr?

   " kara rungumeta yayi sannan yace wanda bazai fadu ba...

    " Nan tafara sakashi fita hayyacin sa tabbas mijinta daya tamkar dubu ne samun mai hakuri irinsa sai an tona...

   " Nan suka shiga wata duniyar cike da soyayya da farantawa juna...

   Da safe baffa ya shirya zai tafi kasuwa sai yasmin tace baffa kudin wayar anjima zanje nasiyo...

    " Auta kenan gwara da kika tunamin sai kisiya biyu ke da maryam ko??

   " Hajiya suwaiba ce tace wannan marasa mutuncin kaima dai narasa irin ka dakake jin tausayin su Alhalin su basuji naka ba...

    " baffa ne yace haba babbar yaya ai komai rubewar hannu baka yanke ka yarba...

    " Sallamar dr sageer ce ta katsesu nan suka gaggaisa sannan ya zauna yasmin dake barandar tsakar gida tana gyara wasu abubuwan ta ...

   " mama ina yasmin ta shiga ne ko tana makaranta?..." aa tana can baranda kaje ku gaisa mana...

    " Ita dai hajiya suwaiba takasa cewa komai sai adduar Allah yasa ta amince...

     Amincin Allah ya tabbata ga sarauniyar sarakai hasken zuciyata...

    " Dagowa tayi ta kalleshi nan idonsa yakara rikita ta ta, can tace katashi lafiya...

    " lafiya kalou ina mamakin kin yarda dakikayi da maganata yasmin kuma ke kanki kinsan bazan yaudareki ba...

    " Shiru tayi sannan tace idan ma ka yaudare ni ai kaikaga zaka iya domin shi alhaki kwuikuyo ne ai...

   " yasmin kalli cikin idona magiya nake ki kauna ce ne danAllah!!! Banda ke bazan yabi kowacce 'ya ba kinsani..  tabbas tun kina karama nasa kaki acikin zuciyata.. kinsan zafin soyayya tunda kinyi kuma kinsan wahalar ta..yasmin dita mai kyan hali ga kuma kyan halitta kwayar idonk'i yana riketar dani har na k'asa dauk'e idanuwa na akanta......

    Shiru tayi sannan tace danAllah doctor ka rufamin Asiri ka hakura da soyayyar mu...please sannan ta goge hawayenta...

     " Tabbas yasmin idan kika yimin haka baki kyauta ba kuma zaki sakani halin da yafi nada...DanAllah ki taimaka min sannan ya zauna ...yau zakiji labari na

   Sunana sageer...

Assalamu alaikum

    Naga Sak'onin ku nagode Allah yasakada alheri...kuyi hakuri da shiru na da kukeji..lurv u oll
  
   _I can't stop apologized for the  spelling and grammar mistake's_

     *How was the page???*

    _Please do vote comments and like my story really need your comments and vote#TEAM....DS

*Urs Nana diso*

Deejarh berver

http//:deejarhberver.wordpress.com

Email:kabba43@yahoo.com

Gmail:nanadiso100@gmail.com 

Wattpad:NEIRNAHDISO

  
[11/6, 1:45 PM] Aysha Galadima: 30-35

*_DOCTOR_*
        _*SAGEER*_

_NA NANA DISO_

      http://deejarhberver.wordpress.com

   © *HASKE WRITER'S ASSOCIATION*

  Yanayin da momy ta tarar dashi ko motsi bayayi nan takira mai gadi ya taimaka mata suka nufi asubuti directly emergency sukayi nan akayi dak'in dashi sannan babban amininsa wato dr khalifa yashiga domin ya dubasa...

    Mumy dake faman sintiri da salati abunda yafi tsaya mata ina ramlat tashiga?? Aikin tatafi mijinta na wannan halin?? Cikin kankanin lokaci takira dady nan yakaraso yanata salati da fadin sai ya sabawa ramlat...

     " mumy ce ta kalli Dady idonta cike da hawaye tace to yanzu yaya zamu sanar da mahaifansa??

     " Tun ahanya nakirawo baffa dan shine mai sauki kuma sai yafi fahimtar abun cikin sauki....

    Baffa dake faman sauri mama tace ina zakaji ne??

    Au namanta bangaya miki ba sageeru ne babu lafiya rai ahannun Allah suna can asubuti...

     " Innalilahi kuma yasmin tacemin jikin da dan sauki kaga yanzu yayi tsanani to innakarasa aiki matawo ko??

     " tohm bari nasanar da alhaji haruna da isa ko??

      " Toh a sanar dasu kuwa kasan dai halinsu dama dai ka kyalesu ko??

    " Ai shi zama da mutum sai kayi hakuri ballantana hakkin maqotak'a...

    Yana fitowa daga part dinsa yatarar dasu harda su maryam bilal da mamee zasu fita babu wanda ya k'alli shi sannan ya dubesu yace sageeru babu lafiya ankwantar dashi asubuti...

     " Alhaji haruna ne yace wannan matsalarka ce, Alhaji isa kuma yace ai da mutuwa yayi kaga sai muci gado ko??

    " mamee data tamutse fuska tace ku dayake wahaltawa ai sai kuje kuyi jinyarsa sannan suka fita...

    " Dai dai lokacin da zai shiga mota hajiya suwaiba tashigo nan yace mata tatawo suje asubuti, Akan hanyarsu tatafiya tace kaddai ciwon sageeru ne ya tashi???

    " Eh hajiya shine abundai sai addua... " D'ana bai samu macen kwarai ba ina tabbatar ita zata karasa shi...

     " Baffa ne yace hajiya kamar yaya?? " Nan ta kwashi labarin duk abunda ramlat take masa ayadda aka bata labari...

      " kidaina kuka Allah yana sani dashi kuma za'a daidaita su inshaa Allahu...

      " kallon baffa datayi tace babu yarinyar dakake ganin za'a hadasu??

     " Shiru yayi yace kina nufin yakara aure wai?? Haba hajiya abu abun asannu tukunna...

     Suna karasawa asubutin sukayi gurinsu nam suka gaisa dasu mumy sannan likita yafito yace ina mahaifansa??

   " Gamu cewar baffa daga nan suka bisa office shi da hajiya kallonsu yayi yace kunsan yanada ciwon zuciya ko??

     " Kwarai kuwa cewar hajiya... " To yanzu dai jikin nasa Alhamdulilahi zai farka nan da 10hours inshaa Allah amma inasu ku lura kukuma kula sosai akwai matsala atare dashi...

      " Kamar ta tunani saka abu arai da damuwa gakuma yunwa har ulcer takamashi yana da kyau alura da lafiyarsa..

      " Inshaa Allahu za'ayi...

Brstr ramlat da ita da rabi suke hira nan ramlat tace kawata cikine fa dani???

    " Wani bakin ciki ne ya tokari mata wuya wato har ramlat tasamu jindadi da mijinta tabbas tasan abunda zatayi...

     " Dake fa nake magana brstr rabia??

  " Nan da nan kwallar bakin ciki ta cika idonta nan ta goge hawayen ta tace ina tausaya miki ramlat ace ashekarunki kin haihu? Mijinki zai gujeki daga nan yafarayi miki wulakanci daga karshe kuma sai kishiya...

    " Ramlat ce tace anya kuwa kinsan yadda dr yakeson haihuwa kuwa?

     " Tohm shikenan zakiga yanason haihu akan idonki zai wulakanta ki kuma babu yadda zakiyi kuma acikin manyan mata ma kallon raini zasu dinga yimiki kina babbar hajiya araina ki...

   " wallahi hakane yanzu yaza'ayi to??

    " ki tashi muje azubar shine kawai mafita...

     " To wanne asubutin zamuje??

      " Babban asubuti zamuje akwai kawata acikin asubutin ai... "  awanne bangare take?? " tana bangaren emergency...

     " Okay tashi muje sannan suka huce zuwa asubutin ...

   Yasmin dake k'an gado tana tunanin irin kalaman dr sageer tabbas namijin mazaje ne mijin da kowacce mace ke fatan ta samu wani murmushi tayi sannan tace ya Allah karabani da auren da ba soyayya...

     " yasmin zanje asubuti kafin nadawo ki dora abinci...

   " Mama wane babu lafiya?? " Sageeru mana ...
  
    " Shiru tayi sannan tace tohm Allah yabashi lafiya sannan taje tayi alwala nan tayi sallah tare da addua Allah yabashi lafiya..

    Su ramlat suna sauka tace rabia mijina fa babu lafiya muyi sauri ji nakeyi kamar wani abu zaifaru...

    Ke kinfiya matsala wallahi aikin banza zo muje suna shiga sai kuwa sukayi karo da dady nan yakifa mata mari sau biyu da sauri baffa yace haba alhaji menene haka???

    Dan ubanki mijinki bai baki daman fitaba kike fita ?? Sai yanzu kikaga damar zuwa??

  Gabanta ne yayi mummunan faduwa sannan tace wallahi ...

    " mumy ce tace kada kice komai munafuka...

    Rabia ce ta salallaba tayi sauri tafita bata tsaya ko'ina ba si motarta cike da dariya hahaha har iyayenki sai nasaka sun tsinemiki hahaha taja motarta tatafi....

Ramlat ce ke kuka tana fadin nashiga uku ina mijina yake??

     Mumy ce ta dakatar da ita mijinki din uban wa mara tarbiya??

     " hajiya ce tace haba mumy ai bahaka ake ba har yanzu fa yarinya ce ramlat kiyi mata ahankali kikasani ko wane case din takeyi mai mahimmanci...

    " mumy ce tace wane irin case ne daya huce cutar mijinta eh??

    Haka sukayi jugum jugum mumy tace ramlat bazata zauna dashi ba mama ce zata zauna ....

    " Har karfe tara shiru har ya huce 20hours har yanzu bai farka ba...

     " hajiyar sageeru ce tayi cikin dakin nasa ta zauna akusa dashi inbanda kuka da addua babu abunda takeyi...

   Yasmin dake zaune a palour tarasa menene yake mata dadi, tun dazu sai tunanin dr sageer takeyi cikin yanayin kunci tace why my heart nan hankalinta yakara tashi taga har goma basu dawo ba abinci ta zuba sannan ta nufi hanyar fita tare da rufe kofar su tana kokarin fita bilal yace uwar gantali inakuma za'aje??

     " Gidan uban da ka aikine sannan ta bude kofa tafita nan tasamu mota tahuce asubutin...

     Lokacin data isa gaba dayansu sunyi jugum jugum tana karasawa dakin taga hajiya tanata kuka... cikin tashin hankali tace hajiya lafiya shiru tayi mata sai alamar kuka...

     " a tunanin ta mutuwa yayi cikin tashin hankali ta matsa kusa da gadonsa tana kuka hannunsa ta ruki tace ya sageer please karka mutu danAllah karka barmu tana wani kuka mai cike da tashin hankali...

  " A hankali ya bude idonsa kalmar da tazo bakinsa shine yasmin...yasmin..yasmin....zaki aure ne???

   " batasan lokacin data miki sannan tayi waje ba tana kuka nan dukk'an su suka tashi sukayi hanyar ciki ba kowa yana kallonsa yana Alhamdulilhi ramlat ce ta matsa gurinsa tana kuka...

" likitane yashigo sannan yakara yimasa allura..

   " Alokacin hajiya suwaiba ta miki tabi yasmin...

Assalamu alaikum!!!

       *Please and please kuyimin afuwa da yawan shuruna da kukeji,Allah yasaka muku da Alheri ina ganin sakon ninku....Nana diso love u so much....*

  
   _I can't stop apologized for the  spelling and grammar mistake's_

     *How was the page???*

    _Please do vote comments and like my story really need your comments and vote#TEAM....DS

Wato haqiqar haquri shi ne bãwa ya gudãnar da rãyuwarsa a lõkacin musiba/balã'i kamar yadda yake gudãnar da rãyuwar lõkacin zaman lãfiya !

Dõmin Allah SWT bã ya qar'bar wani abun daga wajen bãwa; fãce sai dan ya bãwan yayi haquri, haqurin kuma ya sanya Allah SWT ya so bãwan kamar yadda Allah SWT ya fad'a cewa:
(( Kuma Allah Yana son mãsu haquri )).

Bisa ga haka idan Allah SWT Yana son bãwa sai ya zã'bar masa abin da yafi alheri gare shi da ma duk abin da zai zama maslaha a gare shi, don haka sai bãwa ya yarda da hakan.

*Urs Nana diso*

Deejarh berver

http//:deejarhberver.wordpress.com

Email:kabba43@yahoo.com

Gmail:nanadiso100@gmail.com

Wattpad:NEIRNAHDISO

  
[11/6, 1:45 PM] Aysha Galadima: 45-50

*_DOCTOR_*
        _*SAGEER*_

_NA NANA DISO_

      http://deejarhberver.wordpress.com

   © *HASKE WRITER'S ASSOCIATION*

Dago k'anta tayi sannan ta k'alli yadda ya rike hannun ta, cikin kuzari ta zare hannun ta sannan tace lok'aci fa yana kurewa?

     " batare da yace mata komai ba ya cigaba da driving sai da yaje daidai kofar jami'ar sannan yatsaya...

     " jiyowa tayi tace nagode... " har tayi gaba sannan yace yasmin?

    " Cikin nutsuwa ta karaso har inda yake sannan tace Naam!

     " cikin daure fuska kada taki gayamasa yace karfe nawa zaki tashi???

     " sai lokacin da malamar tazo nayi mata submitting ai...

     " Okay to kikula da kanki bye bye..." wata harara tayi sannan tace tuntuni bai taba cewa in kula da kaina ba sai yanzu...

    

  Wallahi mamee dr son yasmin yakeyi Allah bazan yarda ba sau dai ni ya aure ne...

  " ke ki kwantar da hankalin ki indai nice bai isa ya aure yasmin ba tabbijan ki kwantar da hankalin ki nasan me zanyi...

     " Maryam ce tace yauwa mamee ta ai yasmin da mai gadi ta dace wallahi...

     " Alhaji haruna ne yace ai sageeru sai nasa yan fashi sun nakasa shi ina tambayar sa bashin kudi sai cewa yayi kowa zai bashi kudi amma banda ne ai wannan raini ne zaici ubansa....

    " lallai wuyansa yayi kauri Daman ai shi dan Adam butulu ne...

   Barister ramlat dake zaune a office dinta duk cikin yanayin damuwa, irin rashin kulawa da dr yake mata har yafara taba mata zuciya tana cikin tunani sai ga rabia ta shigo....

    " ke dai sai kinsawa kanki hawan jini baki da tunani sai na namiji to sai kiyi tayi su hada miki hawan jini ai ki rabu dashi nahada ki da sugar dady wanda sukafi miji ki komai....

     " me kike Nufi rabia?

Dallah ina nufin maza mana ki rabu da dr nahada ki da wasu ku shakata akwai wani sabon Alhaji da aka hadani dashi sai na barmiki shi...

    " Allah yakiyaye wallahi ai ni bana zina ingayamiki ko shekara nawa dr zaiyi baya kulani bazan bi maza ba...

   " kinga kar kigayamin babu dadi kikasan irin shi matan dayake kula? Ya dirka miki cikk yabarki da sha'awar sa kuma yayi ficewar sa dan love dinnan bai nunamiki shine zaki dinga fiffiga akansa??

     " aa rabia komai fa lefe nane abubuwa nawa nakeyi baya kulanani yayi hakuri dani sai yanzu zanje haushi, ciki kuma kinsan babu maganin da ban shaba yake barewa ke duk ba wannan ke damuna ba aure da zai kara...

   " ke kikasani malama ainaga nakya daukar shawarata sai kiyi abund kikaga shine daidai...

    Mtsww ke fa rabia matsalata dake fushi dallah kigayamin zan dauka...

    " kinsan namiji ba'ayi masa sanyi in kin koma ki yimasa rashin mutunci kikuma yimasa kashidi ke in san samune ki gudu gida zakiga ya janyi ko kefa yanzu kikayi magana me kyau ni bari natafi sai gobe...

   Okay bye

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login