Showing 33001 words to 36000 words out of 36194 words
Chapter 12 - Ba Kai Nake So Ba Complete Hausa Novel By Fatima Isa Manu.docx
janye Meerah daga rukon da ya mata tana cewa. “ Kai din waye da zaka hana ta farin ciki!!! Shekara goma da babu iyaye ma tana farin ciki sai yanzu zaka hana ta!!! Ce maka akayi kaddara bata kan kowa ne!!!.”
“ Meemah ni kike fadawa wannan kalaman?.”
“ Akan yar uwarta babu abunda bazan yi ba, ba kai ba har wanda zai taba ta.”
Gyada kai yayi yana kallon inda Meerah take a durkushe tana kuka ta hada kai da kafa.
“ Meerah!!!.” Ya furta cikin wani irin yanayi da bazai misaltu ba.
Kasa dago kanta tayi ta cigaba da kuka.
“ Ki daga ido ki fadamin waye ya miki ciki ni zan tsaya miki har a bi miki hakinki.”
Mama ce ta ce. “ Mansoor a bar zancen yanzu.”
Cikin tsawa ya ce. “ Akan me ya sa za’a bar maganar bayan bana bari bane!!! Cikin shege ne fa ke jikinta kuma kice a bar maganar, bazan iya ba.”
Sake fuzgota yayi wanda yasa ta saki kara da karfi, ba tare da ya ankara ba Meemah ta kama damtsan hannun shi tana gantsarawa cizo, da sauri ya saki Meerah wacce ta nufi kasa ta fadi sumammiya.
Da gudu Yasmeen ta nufo inda take tana bubbuga fuskarta, ruwa Mama taje ta dauko mai shanyi tana watsa mata a fuska, kusan sau uku kafin ta sauke Numfashi tana cewa. “ Allah na roke ka ka dauki raina, da wani kuncin gwara mutuwa…”
Rungume ta Meemah tayi tana cewa. “ Ki daina cewa haka.”
Ganin bazai iya control din kansa bane yasa ya fice daga parlon.
Kama ta Yasmeen da Meemah suka yi zuwa dakin su, a bakin gado ta fadi tana sake sakin kuka, suma kukan suka fashe da shi aka rasa wanda zai rarrashe wani.
Kaman wanda aka tsikara ta mike hajijjiya na k’ok’arin yasar da ita, da sauri Meemah ta kama ta tana cewa. “ Ina zaki je kuma.”
Ba ta bata amsa ba ta nufi gurin akwatin ta, da ido kawai suke bin ta, budewa tayi tana ciro wayanta ta kunna , bibbiyu idanunta suke kallo ta danna number da akayi saving da Best Choice.
Yana kwance akan gado yana bacci wayansa ta fara ringing, ba tare da ya duba me kiran ba ya ja yana mannawa a kunne, muryanta ne ya masa amsakuwa tana kuka ta ce. “ Ka cuce ni, bazan taba yafe maka ba duniya da lahira, Allah sai ya sakamin abunda ka min, yanda ka sani zubar kwalla kai ma sai ka zubar In sha Allah.” Ta ida maganar tana sakin kuka.
Tun da ta fara maganar har ta gama bai yi motsi ba, sai da yaji ta kashe wayan kafin ya tashi ya zauna yana sake kira.
Yasmeen ce ta kalle Meerah wacce take kuka ta ce. “ Dama kin san wanda ya miki cikin?.”
Kira ne ya sake shigowa wayan, Meemah tayi sauri ta daga, muryansa har rawa yake gurin cewa. “ Me na miki da zaki min mugun fatan nan?.”
“ Ba ita bace.”
“ Ina me wayan?.” Ya tambaya yana sauka daga kan gadon, sautin kukanta yake ji wanda ba karamin tada masa hankali yayi ba.
“ Meeyah!!! Me ya fayu da ke?.”
“ Tana da ciki ne.” Meemah ta fada tana kashe wayan.
Sakin wayan yayi ya fadi kasa. “ Ciki!!!.” Ya furta a hankali, da sauri ya sauko parlon ya fito compound din yana kiran Alex, duk sai da suka tsorata da yanayin sa.
Da gudu Alex ya iso gurin nashi. “ Ka kama mana flight yanzu zuwa nigeria 🇳🇬.” Ya fada a rikice.
“ Sir sai dai gobe da safe amma yanzu fa 12 o’clock na dare fa.”
“ Koma ya zakayi kayi gobe da safe na ganni a guyin ta.” Da haka ya juya ya koma ciki yana daukar wayansa ya sake kiranta amma bata dauka ba.
Daura kanta tayi akan kafar Meemah tana cigaba da kuka wanda ya zuba mata headache, a haka barcin wahala ya dauke ta.
Yasmeen ce ta taso tazo suka kama ta ta hau kan gado, mantaleto Yasmeen ta mikawa Meemah ta shafa mata a gurin da Mansoor ya kumbura mata hannun.
Tana barcin amma tana bata fuska alamun hannun ciwo yake mata sosai, hawaye ne ya zubo daga idanun Meemah na tausayin yar uwarta ta, share mata Yasmeen tayi tana girgiza mata kai.
Tun kafin ka shigo dakin kake jin sautin ihun su, Sumy ce da Zuby suke madigo sai Luby da take kwance tsirarar uwarta wani gardi na sex da ita, hannu ya kai yana cafko nonuwan Sumy wanda suke tsaye Zuby na caka hannu a gabarta.
Da sauri ya cire daga jikin Luby ya koma gaban Sumy ya fara bugawa kamar jaki, ihu take tana sake taya shi, hannu Zuby ta kai tana shafa jikin shi, murmushi ya mata yana kissing nata.
Tashi Lubna tayi tana cewa. “ Guy’s nifa ina ga lokacin warewa na yayi, nasan Dad zai dawo yanzu kuma idan bana gida zai ci ubana ne.”
Tashi Zuby tayi tana cewa. “ Nifa ban dandana ki ba Luby.” Ta yi maganar tana shafa breast nata.
“ Zamuyi waya kawai bari na tafi.”
“ Beb ko na sauke ki ne?.” Cewar wannan gardin da yake kwance ko kunya babu ya baza capacity shi a waje.
“ No need basai ka kaini ba Gaza.” Da haka ta saka kayanta ta zuba uban hijabi ta fita daga hotel din, direct gurin da aka tana da domin motoci ta nufa tana budewa ta shiga, a 360 ta fice da gudu daga hotel din.
A dakin kuwa Sumy ce ta dubi Zuby tana cewa. “ Ki sallami wannan guy din mun gama na yau.” Bude jakar dake kan bedside tayi tana ciro bandir din dubu guda biyu ta mika mishi.
Karba yayi yana tashi tsaye ya saka kayan shi yayi gaba, ko ba komai ya tashi da Dubu dari biyu.
“ Ina ga muma fa mu tafi ko ya kika ce?.” Zuby ta fada tana kallon Sumy.
“ Ok muje to.” Da haka suka fito sun wani buga manyan hijabai kamar mutanen kwarai.
*WASHE GARI*
Jirgin safe Alyan ya biyo shi da Alex, karfe 10 ya musu a Nigeria suka sauka a ABJ, or ready anyi masa bucking din flight zuwa Kaduna, ko zama bai yi ba suka hau jirgin su ya tashi sai KD.
Kwata yau ko fitowa daga daki bata yi ba, tun da ta tashi akan sallaya take har alfijir ya fito, Meemah ce ta sake shigowa a karo na ba adadi tana cewa. “ Kar ki cutar da abunda yake cikin ki Meerah, be san komai ba ki tausaya masa ki tashi ko kadan ne kici abincin.”
“ Bazan ci ba Meemah ku barni kawai.” Ta fada hawaye na zuba daga idanunta.
Yasmeen ce ta shigo tana cewa. “ Meerah ki tausayawa abunda yake cikin ki dan Allah ki fito muci abinci.”
“ Ku dena ba kanku wahala dan zubar da cikin zanyi.”
Muryansa suka ji ya daki cikin kunnen su. “ Wani cikin za ki zubay….
*SAHIBAR JAJIRTATTU✍🏼*
27 - 28 *💅BA KAI NAKE SO BA💅*
_The story is all about love, romantic, sacrifice, heartbreak and destiny_
*STORY & WRITTEN*
*BY*
*FATIMA ISA MANU💐*
*( DR TEEMAH)🦋🕊*
*SAHIBAR JAJIRTATTU✍🏼*
Masu neman littafin *BA KAI NAKE SO BA* daga farko tare da sauran littafina zaku iya following channel ɗi na dan samu👇https://whatsapp.com/channel/0029Vaf6CpQDuMRYD1FMD92T
Open this link to join my WhatsApp Group: https://chat.whatsapp.com/IKUcfCN5rPQ9o0CaBtB2qP
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
(J.W.A)
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️*
*DIAMOND 💎 STAR ⭐*
*LADIES🧝♀️🧝♀️🧝♀️*
*(We stand together)*
🤝🤝🤝🤝
*GARGADI*
Wannan littafin ƙagaggen labari ne, ban yarda wani ko wata ya sauya min shi ba ta kowace siga, sannan kuma ban amince a dauramin shi a youtube ba tare da izini na ba.
*BISMILLAHI RAHAMANIN RAHIM 🙏💫*
*BOOK ONE*
*FREE PAGE 27 & 28*
Alhamdulillah!!!!! na kammala book one🤗 ga masu buk’atar su cigaba da karanta littafin *BA KAI NAKE SO BA* Book two dari biyar ne ~N~ 500, amma zanyi discount ga mutane goma da zasu fara biya da farko, zasu iya biyan dari hudu ~N~ 400🫠🫠🫠, dan haka ku hanzarta kar wannan damar ya wuce ku🤗😘😘😘. Za’a iya biya via 9031176727 Fatima Isa Opay, idan mutum ya turo da kudin sai ya yi screenshot ya turo mini da evidence of payment ta WhatsApp number ta 09027308227 SAHIBAR JAJIRTATTU ko DR TEEMAH.
Kar ku bari wannan labarin ayi sa ba tare da ku ba❤️🌹🫠 Yan Nijer kuma su min magana.
*BOOK TWO zai fara zuwa ne 28th April In Sha Allah kar ku bari ayi baku🤗🤗🤗*
**************************
Muryansa suka ji ya daki cikin kunnen su. “ Wani cikin za ki zubay?.” A tsorace ta mike daga kan sallayan tana kallon shi, Meemah da Yasmeen da suke bakin kofa ne suka matsa da sauri, dan babu wanda yayi tunanin mutum zai shigo.
Yana sanye ciki jallabiya coffee colour, fuskarsa a hade ya nufo inda take, da sauri ta fara yin baya baya tana kallon shi.
“ Wani cikin za ki zubay Meeyah?.” Ya ida fada fuska a hade.
“ Cikin shegen zan zubar.” Ta fada tana kallon kwayar idanunsa.
“ Kay ki kuskuya dan sai kin biyani.” Kau da kai tayi tana rufe hanci da tafin hannunta, da mamaki ya ce. “ Wayi nake yi?.”
Meemah da suka zama yan kallo ne ta ce. “ Bata son kamshin turaren ka ne.”
Matsawa yayi yana cewa. “ Ina saykan da na baki?.”
Hararan shi tayi tana jan tsaki, cikin tsawa ya ce. “ Ina tambayan ki kina yaina min hankali!!!.”
Saurin cewa tayi. “ Na ajiye ne.”
Kama hannunta yayi yana janta da sauri Meemah ta tare gaban shi tana cewa. “ Banaso ta sake kuka a rayuwarta, dan Allah ka barta haka munsan ba zamu iya kara da kai ba, ka yi hakuri ka fita daga rayuwarta.”
Kallon ta yayi na second yana cewa. “ Naji.” Da haka ya fito hannunsa rike da nata.
Mansoor da Mama ne suka fito daga parlon, da mamaki Mansoor yake kallon su, kamar me koyan magana ya furta. “ Bobo me nake gani? Yaushe ka shigo kasar?.”
Kasa kallon Aminin nasa yayi yana nufan hanyar fita da ita, da sauri Mansoor ya rike dayan hannun nata yana kallon shi, jan ta Alyan yayi shi ma Mansoor ya ja ta, kuka ta fara tana cewa. “ Ni ku barni.”
Ba tare da ya kalle Amininsa din ba ya ce. “ Man ka bayta babu yuwanka da ita.”
“ Alyan wai me kake nufi ne?.” Mansoor ya fada yana jan Meeran, da karfi ya janye ta daga hannun Mansoor din ta fado jikinsa yasa hannu daya ya kankame ta a kirjinsa, idanunsa sunyi ja yake cewa. “ Man banaso mu samu matsala da kai, saboda haka ka fita daga maganan nan.”
“ Ke nan kasan wanda ya mata cikin?.” Cewar Mansoor yana isowa daf da shi har hucin numfashin su yana haduwa.
“ Ina yuwanka da wanda ya mata cikin? Ai tun da ba kai bane shi ke nan.”
Ganin abun yanaso ya zama masifa ne a tsakanin su yasa Mama cewa. “ Kuyi hakuri ku bar yarinyar nan dan Allah.”
Hannu Mansoor ya kai zai kama Meerah, da sauri Alyan ya komar da ita ta bayan shi yana kallon Aminin nasa cikin ido. “ Alyan kai ka mata ciki ke nan?.”
“ Sai akayi ya idan ni ne na mata?.”
Cikin zafin nama ya cukumo gabar jallabiyan Alyan din yana furta. “ Ka cuce ni Alyan.”
“ Kai ka cuce kan ka.”
Dunkule hannunsa yayi yana kai masa naushi a baki, a razane Meerah ta saki ihu tana ja baya ganin lokaci daya bakin Alyan ya fashe, shi ma naushi ya kai masa a bakin nasa.
Ihu su Yasmeen suka saka ganin karamin abu ya zama babba, abun ka da fadan samari naushi kawai suke kaiwa junan su, da gudu Meerah ta shiga tsakanin su tana kama Alyan tana cewa. “ Kar ku rabu ta sanadiya ta dan Allah.” Kankame ta yayi da hannu daya yana kallon shi, huci Mansoor yake yana kallon shi shima.
Mama ce ta rike Mansoor tana cewa. “ Akan mace kuke fada, shekaru ashirin da tara ba kuyi fada ba sai yau, yau din ma akan mace? Wallahi kun bani kunya.”
“ Akan Meeyah babu abunda ba zan yi ba.” Nunashi yake da yatsa yana cewa. “ Akan ta hay kai bazan bayi ba.”
K’ok’arin kwace kansa yake daga rukon da Mama ta masa tana cewa. “ Mazinaci kawai.”
“ Ka kiya ni da komai zan amsa, naji akan ta ni mazinaci ne, akanta ni wawa ne, sannan akan ni mahaukaci ne!!!.” Ya karashe fadin hakan cikin daga murya.
Kuka take tana k’ok’arin kwace kanta daga jikinsa, cikin takaici Mansoor ya ke cewa. “ Ka yiwa yarinya ciki dan kana ganin kana da kudi.”
“ Idan nayi din sai me, ni nayi mata ciki kuma zata haiho shi duniya sannan ya taka a gaban idanunka, ka bishi da kallo dan babu abunda ka isa ka masa.”
Fuzge hannunsa daga rukon da Mama ta masa yayi yana sake kai masa naushi a baki.
Shi ma kai masa yazo yi Meerah tayi saurin rikewa tana kallon kwayar idanunsa ta furta. “ Kar kayi dan Allah, ka tafi kawai banason fadan kun nan.”
Tallafo fuskarta yayi da tafin hannunsa yana cewa. “ Naji zan tafi amma dake zamu tafi.” Hawaye ne ya zubo daga idanunta yayi sauri goge mata yana kallon Mansoor ya ce. “ Daga yau ke da kuka kun yaba hanya In Sha Allah Mrs Alyan.”
Hannunta ya kama ya nufa hanyar fita da ita, Mansoor na shirin bin su Mama ta rike shi tana girgiza masa kai. “ Amma Mama a gaban mu zai tafi da ita.”
“ Halaliyar sa ce idan ma ya tafi da ita babu ruwanka.” Cewar Mama tana jawo shi parlon.
Yasmeen da Meemah suka rungume junan su suna kuka.
Mota ya bud’e ya saka ta yana zagayawa ya shiga, da gudu ya ja motan suka bar unguwan, kuka sosai take duk ta cika masa kunne, parking yayi a gefen hanya yana kallon ta.
“ Wai me hakan ne?.”
“ Ni ka mayar dani.”
“ Bazan mayay ba.”
Kuka ta cigaba da yi kamar ranta zai fita, mantar da ita yayi ya cigaba da driving.
A get one ya tsaya akayi scanning din motan, ya nufa get two aka duba, bude masa get akayi kowa na mamakin motan dan sun san mai motan baya kasar.
A Parking space ya tsaya, kallon ta yayi yana cewa. “ Kukan nan ya isa.”
Ba tare da ta dago kai ba ta ce. “ Har kana da bakin da zaka ce min kukan ya isa bayan kai ne silan kukan, ko ka manta cikin shege ne fa a jikina.”
Tauna lebe yayi yana bude murfin motan ya fito, zagayowa yayi ya bude mata yana saka hannu ya kama ta, dago da kai tayi tana kallon shi, kafin ta fito.
Kallon compound din take tana sake kallon shi, hanyar da zai sadaka da parlon ya nufa yana rike da hannunta. “ Ina ne ka kawo ni?.”
Bai bata amsa ba ya tura kofan parlon, tana biye da shi a baya suka shigo tsakiyar parlon, kallon ko ina take da ido tana tunanin nan kuma ina ya kawo ta, takun takalmi taji hakan yasa ta daga kai da sauri tana kallon mai saukowar, da sauri ta sake buya a bayan shi.
Kallon shi Ammy take fuskarta dauke da mamaki da al-ajabi musamman da tasan baya kasar, bata tabbatar ba sai da ta bude baki ta ce. “ Babana!!.”
Sunkuyar da kansa yayi murya a kasa ya furta. “ Ammy.”
Jin haka ya tabbatar mata da shi ne, da sauri ta sauko daga upstairs din ta iso din yake tana cewa. “ Babana ya na ganka a nan?.”
Shuru yayi bai ce komai ba, sai ma sunkuyar da kai din da yake ta yi, idanunta ne suka sauka akan bakinsa wanda ya fashe da jini a wajen, da sauri tasa hannu tana dago da fuskarsa ta furta. “ Subhanallah me yake faruwa ne wai? Kayi wani laifi ne ko me?.”
Nan ma shuru ya yi zuciyarsa sai harba uku-uku yake.
“ Alyan me ya faru?.” Ta kuma tambayarsa.
Laylerh da fitowar ta kenan taji Ammy na tambayarsa, dama ta shirya ne zata je gidan su Yasmeen, ita ma cike da mamaki ta kira sunan shi. “ Yaya?.” Kafin ta karaso gurin.
Cike da damuwa Ammy ta kuma cewa. “ Alyan banason irin haka ka fito fili ka sanar dani halin da kake ciki.”
A hankali ya dago kai yana kallon Mahaifiyarsa din, kamar mai koyan magana ya fara cewa. “ Ammy… dama…. Akwai…” Shuru yayi yana kallon ta.
“ Alyan ka fadamin me yake faruwa zan taya ka yakin.”
Numfashi ya sauke yana matsawa gefe, da sauri Laylerh ta furta. “ Meerah!!!.”
Kallon ta Ammy take tana sake kallon Alyan din, alamun bayani take son ji.
Da sauri ya kama hannun Ammy yana cewa. “ Ammy kiyi hakuyi, banyi dan na bata miki yai bane, amma… amma nasan cewa ke din uwa ce kuma zaki fahimce ni.”
“ Bangane ba, wace ce ita?.” Cewar Ammy tana sake kallon Meerah wacce ta sunkuyar da kai hawaye na bin kumatun ta.
“ Ammy In-law dinki ce ita.”
Kallon mahaukaci ta bishi da shi tana cewa. “ A taya