Showing 18001 words to 21000 words out of 39627 words

Chapter 7 - FATTOMAH BOOK 1 by Nana Meera.txt

20 Dec 2024

2301

Fattomah kyakkyawace ajin farko. Murmushinsa mai kyau ya yi ya ce"me kike yiwa dariya ne?" ta ce"wannan kayan na wane?" waro idanunsa ya yi ya ce"naki mana Fattomah" da sauri ta ce" a ina kasan sunana?" dariya Kamal ya yi ya ce "naji yayanki na faɗa rannan" jinjina kai ta yi sannan tabar wajen hakan yasa shima yabi bayanta.








"Meyasa kake bina ne nida Mommyna muka zo fa" Kalle-Kalle ya shiga yi ya ce"tana ina mu gaisa please" sakar baki Fattum ta yi tana kallon ikon Allah ganin da gaske Mommy ɗin yake nema su gaisa, haɗe rai ta yi tana kallonsa ta ce"nikam please banason abun kunya sai anjima" gaba tayi ya yi saurin biyota hakan yasa ta ƙara tsayawa ya ce"chocolates ɗin naki fa?" "bana so ni wanda na ɗauka sun isheni" girgiza kai ya yi ya ce"ko ki karba ko kuma naje har inda Mommynki take na baki agabanta sai ki zaɓa" Fattum ji tayi kamar ta ɗora hannu aka ta fashe da kuka amma babu dama hakan yasa ta ce"Dan Allah idan ba so kake raina ya ɓaci ba kayi tafiyarka" murmushi ya yi ya ce"ki karɓa shine kawai zai ceceki" dafe kanta ta yi ta ce a shagwaɓe"idan Mommy tazo wajen nan kaida Allah wollah" dariya Kamal ya yi ya ce"kin shirya karɓa?" ganin da gaske ba rabuwa zai yi da'ita ba yasa ta gyaɗa masa kai a hankali, ya yi murmushi ya ce"good gurl". Saida ya biya kudin sannan ya koma ya cigaba da ɗaukan abinda ya kawo shi ita kuma ta koma inda Mommy take tsaye, sai gab da magrib sannan suka baro super market ɗin duk sun gaji saboda yawo, har suka zo gida babu wanda ya ce komai dan duk sunyi laushi....










Sosai Fattomah tayi mamakin irin kayan da Mommy ta siya mata dan ita bata ɗauka sunkai haka yawa ba kayana irin latest ɗin nan kuma unique kana gani kasan kuɗaɗe aka sa aka siyesu, duk yawancinsu ƙananun kaya ne sai abayas only fews ne traditional clothes saida ta gama ganin kayan sannan ta mayar ta ajiye ita kuma ta fito dan zuwa wajen Mommy, banda ƙamshi babu abinda parlon keyi ko'ina very cleaned and tidy, zama tayi kan royal cusion ɗin dake zagaye da parlon ta lumshe idanunta a hankali wata nutsuwa ke saukar mata,






Cikin wani babban gida wanda ya kasance kamar lambu ko'ina iska mai daɗi ke kaɗawa wasu irin kyawawan furarrani ne ke zubowa kamar irin a film ɗin, da sauri Fattomah ta tafi wajen Abbanta wanda yake kallonta yana sakar mata murmushi faɗawa jikinsa ta yi ta fashe da kuka cikin shagwaɓa take cewa"Abbana meyasa ka tafi ka barni?, banajin daɗi Ababana gashi Ammi ma tayi tafiyarta sai ni kaɗai banida kowa Abbana dan Allah kadawo kaji" shafa fuskarta Abba ya yi ya ce"Faɗeematoh rigima, kiyi haƙuri kinji tabbas akwai ƙalubale sosai a rayuwarki amma inason ki kasance mai juriya akowane irin hali kika tsinci kanki kada kiyi ƙasa a gwuiwa, ki zama mai jin magana Faɗeemah domin shine farkon abinda zai haddasa miki matsala cikin rayuwarki ki daina rashin jin magana kome ya faru watarana zai yi ƙarshe kuma kece wacce zaki ci riba ki ƙara haƙuri akan wanda kike dashi Faɗeemah komai ya yi farko zai yi ƙarshe"






"A'a Abbana kada kace haka Please ka dawo wajena dan Allah Abba!!!"




Da mamaki Mommy take kallonta ta ce"Fattum kedawa?" A firgice ta buɗe idanunta tana zazzaresu, kallonta Mommy ta yi ganin yanda take haɗa gumi dukda AC dake faman aiki cikin parlon ita kuwa Fattomah ta kasa gane abinda yake shirin faruwa da'ita ashe daman mafarki take ba gaskiya bane?, da gaske Abba ya mutu kuma bazai dawo ba?, mene ne abinda Abba ke ƙoƙarin faɗa mata???, rasa abinda zata yi yasa kawai ta fashe da kuka tana riƙe kanta wanda take jin yana mata wani irin ciwo. Zama Mommy tayi gefenta ta dafata ta ce"Fattomah lafiya meya faru?" kasa magana Fattum ta yi sai kukanta data cigaba, rungumeta Mommy tayi ta ce"dan Allah ki yi hakuri ki daina wannan kukan karki zo kina rashin lafiya kinji kiyi shiru" sosai Fattomah tasha kukanta kafin daga bisani tayi shiru ta koma sauke ajiyar zuciya har bacci ɓarawo ya yi gaba da'ita.






A hankali ta tura ƙofar bedroom ɗin ta shiga tana ɗan Kalle-Kalle, zaune ta ganshi kan kujerar dake gefen gadon da alama ya yi nisa cikin duniyar tunani dan bai ma san ta shigo ba, zama Ayrah ta yi kan gadon a hankali ta ce"Doctor!" ko kallonta bai yiba wanda ya sake tabbar mata dacewa tunanin yake har sannan sauke idanunta ƙasa tayi cikin sanyin murya ta ce"Doctor dan Allah ka daina wannan tunanin da kake please" ganin har sannan bai juyo ba yasa ta miƙe ta ƙarasa inda yake, saida ta taɓa shi sannan ya kalleta aɗan firgice ya ce"Ayrah lafiya?" numfasawa ta yi ta ce" ka tashi mu ci abinci please" gyaɗa mata kai ya yi ya ce"I'm coming" girgiza kai ta yi ta ce"kawai ka tashi muje idan ba haka ba zama zaka sake yi" murmushi ya yi sannan ya kama hannunta suka fita daga ɗakin.






Banda kuka babu abinda Fattomah keyi ta ruƙunƙume Mommy sai kuka take kamar ranta zai fita ita kanta Mommy ƙarfin hali kawai take dan tana matuƙar jin Fattomah aranta, ganin abun nasu ba mai ƙarewa bane yasa Daddy yazo ya janyeta daga jikinta yana kallon Fattomah ya ce"ya isa haka dear zaki dinga zuwa you don't need to worry kinji"tana kuka ta ce"Daddy ku tafi dani" murmushi ya yi ya ce"shikenan next week Imad zai kawo ki kinji" kallon Imadudden ya yi ya ce"please ka kula da'ita yanda ya kamata tym to tym kana kawota"Okay kawai Imad ya ce sannan ya yi gaba, kallonta Jawaad ya yi ya ce"ki yi shuru mu tafi gida" gyaɗa masa kai tayi sannan ta bar wajen su Mommy akan idanunsu jirginsu Mommy ya tashi zuwa garin Abuja, wani sabon kukan taji yana neman kwace mata Jawaad ya riƙe hannunta suka fara tafiya, back seat ya buɗe mata ta shiga sannan ya shiga gaba Imad ya yiwa motar key bakinsa ɗauke da Bismillah suka bar Airport ɗin, a hankali ya gangara gefen hanya ya yi parking da mamaki Jawaad ya kalleshi kafin ya yi magana ya juya yana kallon Fattomah ya ce"whether you keep quiet or get out okay?" a hankali ta fara rage sautin kukan nata tsaki ya yi sannan ya ci-gaba da tafiya batareda ya sake cewa komai ba.








*Ameenatou I Ibraheem#*
*Nanameera ce#*






*Like nd share*




*Juma'at Mubarak to oll muslims Allah ya haɗamu da Alkhairan cikinta🤲🤲*
[5/13, 9:29 PM] Nanameera: *FATTOMAH*




MIKIYA WRITERS ASSOCIATION.






*Ameenatou I Ibrahim*
*Nanameera ce*






PAGE 23-24.






Kallonsa Jawaad ya yi bayan ya tsaya da driving ɗin ya ce"zuwa gobe zan shigo in sha Allah" gyaɗa masa kai Imad ya yi, murmushi ya yi yana kallon Fattomah ya ce"sai da safe dear" kallonsa kawai tayi amma bata ce komai ba ya juya ya sauka daga motar, sosai gaban Fattum ya shiga faduwa ganin ya rage daga ita sai Imad cikin motar shi kuwa ko nuna alamar yasan da mutum bai yiba ya cigaba da driving ɗinsa har suka ƙarasa gida. Kashe motar ya yi ya fice daga ciki hakane yasa itama ta fito tana bin bayansa kamar wata mara gaskiya, a babban parlon gidan wanda yasha kayan alatu kala-kala ta ganshi tsaye yana magana da Salma wacce itama take tsaye jikin kujera da mamaki ta kalli Fattomah sai kuma ta kalleshi ta ce" baƙuwarmu har ta iso?" kamar bazai magana ba sai kuma ya ce"kaita wannan apartment ɗin"okay ta ce sannan takalli Fattomah ta ce"muje Fattum" bin bayanta Fattomah ta yi bata sake yarda ta kalleshi ba. Tsaki ya yi sannan ya haura samansa, sosai apartment ɗin ya tafi da imanin Fattomah dan ya yi matukar haɗuwa kana gani kasan gidan manya ne, kallonta Salma ta yi ta ce"nan ne ɗakinki akwai komai cikinsa including kitchen idan kina son dafa wani abun okay?" gyaɗa mata kai Fattum ta yi sannan ta juya ta fita ajiyar zuciya Fattum ta sauke sannan ta shige cikin bedroom ɗin dan kwanciya ta huta.










Tuntsirewa ya yi da dariya yana kallonsa ya ce"to kai yanzu ina zaka sake samunta?" murmushi Kamal ya yi ya ce"inada numbernta kuma ko ba haka ba ni nasan zamu sake haɗuwa da Fattomah saboda ita ɗin ta kasance mallakina ce kaga dolene mu kasance tare nasan zan sake ganin kayata" girgiza kai Saleem ya yi ya ce"sannunka romeo kace tama zama taka?" jinjina masa kai ya yi Saleem ya ce"Alhamdulillah finally dai Aboki zai yi aure Allah ka nuna mana lokacin nan ai ka zaunu"murmushi kawai Kamal ya yi bai ce komai ba. A hankali take sakkowa daga stairs ɗin tana ɗan Kalle-Kalle gudun kada ta haɗu da Imad har ta ƙaraso parlon, babu kowa cikinsa ko ina ya yi shiru gwanin daɗin zama, kamar wacce aka yiwa dole haka ta samu kanta da zama kan kujerar tana kallon wata drama da ake haskawa Mbc 3 ƙaunarta da cartoon yasa hankalinta duk ya tafi da ganinsa wanda hakan yasa har batasan sanda ya shigo cikin parlon ba, jin kamar mutum akanta yasa ta juya dan ganin waye a mugun tsorace ta mike daga wajen tana mutstsuke idanu, wani banzan kallo Imad ya watsa mata sannan ya ce"get out!!" yanda ya faɗi maganar ne ya sanya taji jikinta na ɓari ganin kamar bata gane abinda yake faɗa yasa ya daka mata tsawa ya ce"ba dake nake magana ba shashasha kawai!!" fashewa tayi da kuka ta tafi da gudu tabar parlon tsaki Imad ya yi ya ce"aikin banza kawai zanyi maganinki ne soon" yana gama faɗin hakan ya juya yana kallon tv ɗin tsaki ya yi ya ce"yarinya ko wahala".














Kuka ta dunga yi ita daman tasan wannan zaman babu abinda zai ƙara mata sai wahala bazata iya zama da wannan mutumin ba ko kaɗan bashida mutunci, tunawa dasu Mommy ya sanya ta sake fashewa da wani irin kuka tabbas tasan ta shiga uku zamanta anan, haka ta dinga kukan nan ƙasan carpet har bacci ɓarawo ya saceta. Wani kallo ya yiwa Jawaad amma bai ce komai ba Jawaad ya ce"gaskiya na faɗa wlh dole sai kana sanyaya zuciyarka saboda yarinya ce ƙarama batada wayo idan da zaka jata jikinka ka nuna mata soyayya wlh duk abinda kace tayi shine zata yi amma indai zaka dinga nuna baka sonta tofah zata dameka ne gwara kayi tunani" murmushi Imad ya yi irin na rainin hankalin nan ya ce"idan ta fasa rashin hankalin, what do you think?, zan rabu da'ita ta ɓatamin rai ne?, wlh duk sanda ta yi min laifi sai na hukuntata i most punish her saboda haka ruwanta ne ta shiga hankalinta ruwanta ne tayi rashinsa nidai ina nan kan matsayata" shuru Jawaad ya yi yana tausayin Fattomah cikin ransa fatansa ɗaya yarinyar tayi masa biyayya domin duk abinda Imadudden ya ce tofah yana iya aikatashi batareda ya yi duban wani abu ba, cikin sigar lallashi ya ce"Allah ya baku ikon zama lafiya shine kawai abinda zan ce maka, yanzu yaushe zaka koma America?" tsaki ya yi ya ce"ina naga tafiya America yanzu ai dole sai nan da 3months idan ta koma wajen Daddy" Jawaad ya ce"please ka kiramin ita zamu gaisa" harararsa ya yi ya ce"ba'a gidan nan ba ka bari ta koma hannun magabatanta please" tuntsirewa da dariya Jawaad ya yi ya ce"ai kaima magabacinta ne yanzu malam ko bakada labari?" "Allah ya kiyaye" tashi suka yi atare Jawaad ya ce"dan Allah ka kirawo min ita" wani kallo ya yi masa ya ce"bakasan hanya bane?" murmushi ya yi ya ce"ai naga mutum da iyalinsa" kwafa Imad ya yi sannan ya bar parlon.










Kallonta Imad ya yi ganin yanda take bacci a ƙasa duk ta takure jikinta, tsaki ya yi sannan ya sanya ƙafarsa ya ɗan shureta, a mugun firgice ta farka saboda daman cikin tsoro ta yi kukan, wani shegen kallo ya watsa mata sanda suka haɗa ido ya sa ta sauke idanunta ƙasa




"Tashi ki fita"


Abinda Imad ya furta kenan sannan ya yi waje, miƙewa tayi tana ɗan turo bakinta itama ta fita wajen. Da sauri ta ƙarasa wajensa tana murmushi ta ce"yaya Jawaad" mirmushin shima ya mayar mata sanda ta zauna gefensa ya ce"Fattomah" kwaɓe fuskarta ta yi ta ce a shagwaɓe"yaya Jawaad ka tafi dani gida please nan babu daɗi" shafa kanta ya yi ya ce"Ayyah sorry dear ki bari kin kusa dawowa gidana forever" Fattomah bata gane abinda yake nufi ba ta ce"kawai mu tafi yau yaya" murmushi Jawaad ya yi yana kallon Imad wanda ya haɗe rai ko kallonsu bai yiba, cikin sigar rarrashi Jawaad ya ce"kiyi haƙuri ki zauna anan in sha Allah kina gama exams zan tafi dake amma yanzu kiyi haƙuri" raurau tayi da idanu ta ce"Allah yaya kayi alƙawari?" gyada mata kai ya yi ya ce"yeh! amma yanzu ki shirya gobe ki tafi makaranta" jinjina masa kai ta yi ta ce"toh yaya kai zaka zo ka tafi dani?" waro idanunsa ya yi yana murmushi ya ce" Fattum rigima to driver zai kai ki" haɗe rai tayi ta ce"toh ni bazani baaaaa" yanda tayi maganar cikeda shagwaɓa yasa ya yi dariyar da bai shirya ba, wani kallo Imadudden ya watsa musu da ya sanya tayi ƙasa da kanta shi kuwa Jawaad murmushi ya yi ya mike yana kallonta ya ce"saida safe dear ki shirya da wuri kinji" jinjina masa kai tayi ya ce"good gurl Allah ya yi miki albarka" murmushinta mai kyau ta yi ta ce"Ameen yayana" kallon Imad wanda yake danna wayarsa ya yi ya ce"saida safe Footballer" can ciki ya ce"good night dear, Allah ya tashemu lpy" Ameen Jawaad ya ce sannan ya juya ya fita. Miƙewa ta yi ta shige ciki yabi bayanta da wata uwar harara ni kuwa nace abanza 😂😂.












Da sassafe ta tashi ta shirya saboda abinda yaya Jawaad ya ce mata, bayan ta ɗauko school bag ɗinta ta sakko ƙasa dan tafiya makarantar, tsayawa ta yi dalilin Imad data gani tsaye jikin dinning table hannunsa rikeda mug na tea, a ɗan duburbarce ta ce"ina kwana?" idan table ɗin dake gaban Imad ya yi magana to Imad ma ya yi magana ganin haka yasa ta sunkuyar da kanta bata ce komai ba amma tana tsaye dan batasan wane wanda zai kaita makarantar ba. Kusan 5mins tana nan tsaye shikuma har sannan bashida niyyar gama abinda yake ko kuma kulata, fashewa Fattomah ta yi da kuka da ƙarfi, da sauri Imad ya juyo ya kalleta dan ganin abinda aka yimata






Tsabar baƙin ciki ji ya yi kamar ya jawota ya yi mata duka, a matuƙar fusace ya ƙaraso gabanta yana kallonta ƙirjinsa sai ɗagawa yake dan idan da Abinda ya tsana a rayuwarsa bai shige kuka ba ya tsani yaga ana kuka musamman yanzu da take masa kukan na rashin dalili, cikin wata shaky voice ya daka mata tsawa ya ce".










*Ameenatou ce#*
*Nanameera ce#*








*Like nd share*[5/13, 9:30 PM] Nanameera: *FATTOMAH*


*MIKIYA WRITERS ASSOCIATION*




Ameenatou Nanameera




PAGE 25-26.






"Uban me aka yi miki?" yanda ya yi maganar afusace yasa ta ɗan yi baya tana kare fuskanta gudun kada ya kai mata duka, kwafa ya yi sannan ya ce"akwai ubanda ki ke jira anan?" turo ƙaramin bakinta wanda yasha lip gloss kamar ba school zata tafi ba tayi ta ce aciki-ciki "koba kuɗin makaranta zaka bani ba" wani banzan kallo Imad ya watsa mata sannan ya yi wani killer smile, juyowa ya yi gaba ɗaya yana sake ƙare mata kallo ya ce cikin rainin hankali ya ce"wane ya kawo ki gidan nan?" kallonsa Fattum ta yi sai kuma ta ɗauke kai tana zumɓura baki, murmushi Imaad ya yi ya ce"I'm asking you" can ƙasa ta ce"kai ne" ya ce"wane ya siya miki kaya sanda za kizo gidan nan?" asanyaye ta kalleshi sai kuma ta sauke idanunta ƙasa ta ce"Daddy ne" murmushi ya yi for the second time ya ce"da gaske?"gyaɗa masa kai ta yi ya ce"kuma amma shine bai haɗa miki da kudin makaranta ba?, ki ce Daddy baison kije da kuɗi makaranta" da Mamaki Fattomah take kallonshi dan har sannan bata fahimci abinda yake nufi ba. Lura da hakan yasa Imad ya ce"ki huce ki tafi dan ni bazan iya baki wani kuɗin makaranta ba tunda ba ni ne na sanya kiba kuma ba zamana kike ba saboda haka wuce daga nan" tunda ya fara magana Fattum take kallonsa with mouth agape yama za'ayi ta tafi makaranta babu kuɗi ai abinda bazai yiwu ba kenan, ganin har sannan tana tsaye ko motsawa ba tayi ba yasa ya ce"ba kiji abinda na ce miki ba?" cikeda shagwaɓa ta ce"ni wllh bazan tafi babu kuɗin makaranta ba to me zan siya??" baki buɗe Imad yake kalllonta har takai ƙarshen maganartata sannan ya ce"keee, I'm play with you?, kinga alamun Ina yi miki wasa???" shuru Fattomah ta yi dan ita ko kaɗan bai bata tsoro ba kuma yanda ta faɗa bazata tafi ba dole sai ya bata kuɗin school kamar yanda aka saba bata. Jinjina kansa ya yi sannan ya ce"Malama bar wajen nan ko ranki ya ɓaci" ƙin tafiya tayi ta tsaya tana kafeshi da manya manyan idanunta masu matuƙar ɗaukan hankali, riƙe ƙugunsa ya yi da hannayensa yana sake jinjina gaddama irin tata amma duk iya gaddamarta bata ko kawo ɗan yatsan sa ba. Agogon dake aiki jikin bangon ɗaki ta kalla wajen ƙarfe 7:45am kuma tasan Indai 8:00am tayi tofah baza'a barta ta shiga ba kamar zata yi kuka ta ce"dan Allah kabani wlh zanji yunwa kuma ba'a tashinmu sai la'asar" ko kallonta Imad bai yiba ya haye sama wanda hakan ke tabbatar mata da cewa bazai bata ba.








Waje Fattomah ta yi tana fita taga drivern da zai kaita makarantar already ita yake jira shiga motar ta yi sannan suka bar gidan, saida taga sunyi nisa sannan ta fashe da wani irin kuka, kallonta drivern ya dinga yi ta jikin mudubi har suka isa makarantar tasu. Yana sauketa ta shige makarantar bata ko kalleshi ba, kasancewar ranar Monday ne yasa tana shiga

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login