Showing 6001 words to 9000 words out of 63876 words

Chapter 3 - JAWAHEER HAUSA NOVELS BY MARYAM OBAM.txt

20 Jan 2025

6921

sai kun dawo sannan akwai kudi a wardrobe din daki na in bakya bukatan taba naki ,yana fadin haka ya wuce.










Karfe hudu dai2 mum ta nufi dakin jawaheer cikin shirinta ganin jawaheer tayi tana zaune tana kallon waya nufanta tayi tana fadin jawaheer kinyi sallah kuwa? Tace mum ina fashin sallah ai, mum tace ok toh maza ki tashi ki shirya zaki raka ni, tace mum kije kawai bana jin fita yau kaina na ciwo, mum tace haba jawaheer fitan nan danke zanyi fah, tace mum ina zamu? Mum tace kedai ki tashi ki shirya ban san dogon zance, bata fuska tayi tare da fadin wlh mum kaina ciwo yake dakin bari gobe mu fita ,mun tace kin san bana son shirme koh maza ki tashi kisa hijab muje, kallon mum tayi tace hijab kuma ina zamu haka? Kodai wani ne ya rasu? Mum tace babu wanda ya rasu kawai wajan da zamu ne bana bukatan ki bini saida hijab, badan taso ba ta shirya tare da saka hijab din, mota suka shiga mum tace jawaheer ta zauna a gaba, hjy hauwa zata zauna a baya ita da mum ,bayan sun shiga driver yaja gidan hjy hauwa suka biya suka dauketa sannan suka nufi islamiyyan, hjy hauwa tace driver yayi parking bayan ya tsaida motan suka fito amma banda jawaheer mum tace jawaheer ki fito mana bude motar tayi ta fito shiga islamiyyan sukayi inda aketa karatu wani office suka shiga suka zauna babu kowa a ciki jim kadan sai ga wani mutum yazo ba wani babba bane amma kana ganinshi kasan mlm ne dan irin shigan da yayi, gaisawa sukayi sannan hjy hauwa tace mlm ga kawata nan sannan ga yarinyar nan sai a sannan jawaheer ta dago ta kalli mlm din, mum tace mlm dan Allah a mata ruqiya domin aljanu ne nake tunanin suka shigeta, jawaheer da sauri ta kalli mum din nata ta fara hawaye tare da tashi tsaye......
























*maryam obam*
[04/01, 14:50] Maryam Obam Group Kd: *JAWAHEER*






*STORY AND WRITEEN BY......*


*MARYAM ALHASSAN DAN'IYA*
*(maryam Obam)*




*🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝*
*{united we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}*


*wattpad @maryam-obam*


*WWW.Maryamobamnovels.com*








https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/










*DEDICATED TO.....*
*Nafisa mrs dan malikin kawo*


















Page 6


















Ta kalli mum tace mum mai hakan ke nufi? Mum kallon aljanu kike min kuka ta saki mai karfi tare da fadin mum nifa lafiya na qalau bani da komai kaman yanda kike tunani kallon mlm din tayi tace mlm ka kalleni dakyau nayi kama damai aljanu ko tabin hankali? Matsowa tayi kusa da mlm ya danyi baya kadan tare da fadin auzubillah karki matso kusa dani haram, mum ta tashi ta rikota tare da fadin zoki zauna jawaheer kwace jikinta tayi daka na mum tace mum bazan iya zama ba, amma inaso mlm ya cire miki zargin da kike min yanzu, kallon mlm tayi da yayi shuru yana kallon ikon Allah, tace mlm mai zaka min ka nuna ma mum dina ni lafiya na qalau, mlm yayi gyaran murya tare da fadin da farko dai ki zauna zanyi miki yan tambayoyi kadan, zama tayi akan kujera tare da kallon mlm tace inaji, mlm yace ya sunanki? Tace jawaheer, kai ya daga alaman yaji yace kina mafarkin ruwa ko wani yana saduwa dake kai ta girgiza alaman a'a, yaci gaba da tambaya kina mafarkin gaki a daji ko kuma ana binki tace a'a, nan dai yaita mata tambayoyi tana bashi amsa harya gama ya dauko wani magani ya bata yace tasha, bata musa ba ta amsa tasha bayan ta shanye tace mlm shikenan? Yace eh an gama, tace mlm bari kaji wani abu kasan miye matsalata? Shuru yayi ba tare da yace mata komai ba tace mlm Allah ya jarabceni dason wani mutum wanda badan nan kasar bane dan kwallon kafa ne nasan zaka iya saninshi sunanshi M samir, mlm a kullum inna kwanta ina ganinshi yana kuka tare da fadamin yana da wata matsala amma idan abun ya fito kar in gujeshi duk wuya in zauna dashi sannan yamin zai aureni duk wuya yace in daure ni tashi ce, ban taba fadama kowa wannan ba kullum sonshi na karuwa a raina duk da a kullum ina kokarin in cireshi a raina amma na kasa, abun kaman kara karuwa yakeyi kullum tun bana iya fadama iyayena harna fara fada musu abunda ke cikin raina dady dina ya fahimceni amma ita mum dina ta kasa itace mahaifiyata ita ya kamata tafi kowa fahimta na tasan wani hali nake ciki ya nake ji, amma mum ta kasa fahimta na saita fara min kallon aljanu da tabin hankali wanda hakan yana batamin rai mum dina tana nesa dani wanda hakan yasa nafi sabawa da dad dina akan mum dina shuru tayi domin kukan da yazo mata lokaci daya, wajan yayi shuru na wajan second biyar sannan taci gaba da fadin kiyi hakuri mum ina fadin hakane dan kisan abunda yake damuna, ban taba soyayya ba sai akan M samir duk da bai san inayi ba, sometimes nakan so incire abun a rai na har inyi kokarin sauraran wasu amma na kasa, tashi tayi tace mlm nasan kai zaka iya fahimta na wlh bana tare da wani cuta illa ciwon so wanda nasan idan ban sami abunda nake soba zai iya zama ajalina, nasha kallo a fina finai irin abubuwan da so yake haifar wa dariya nakeyi ko ince karya ko hauka, domin ina tunanin hakan bazai taba faruwa da gaske ba, ashe ba haka bane, yau gashi abunda nake ma dariya nake ganin karya ne gashi ya faru a kaina har nima ana min kallon mara hankali, ni nasan wannan yana cikin jarabawan rayuwa na, mlm pls make my mum to understand dat i dnt have any jin tana fadin haka ta fita, duka da ido suka bita mum kasa magana tayi mlm yace hjy yarinyarki bata da aljanu kaman yanda kike zargi sannan bana tunanin tana da tabin hankali lafiyanta qalau, kawai tsabar son mutumin nan ne yasa mata take haka which kuma abunda na fahimta kaman bata da kawaye wanda take fada musu matsalanta ku take fadama wa amma dad dinta yana fahimta har yake biye mata amma ke kina nuna mata kaman ta sami tabuwa, kuma ita a nata ganin kune ya kamata kusan wani hali take ciki tunda kune iyayenta, hjy ya kamata ki dinga janta a jiki kina bata shawar wari wanda zata fahimta koda tana firan dan ball din da takeso ki daina nuna mata kyara hakan yakan sa yaro ya tsani kanshi yaga kaman iyayenshi sun tsaneshi yana da kyau ka maida danka abokinka ta yanda zaku dinga bama juna shawara jan yaro a jiki yana sa komai zaiyi saiya fadama iyayenshi sannan nunama yaro kyara yana sa ya dinga boye abubuwa da yawa wanda in ba'ayi wasa ba nan gaba za'ayi dana sani wanda ba'a fata, jikin mum yayi sanyi tace ngd mlm tabbas hakane jawaheer bata da kawa ko daya na tabbata inda tana da kawa da tare zasu dinga shawara rashin kawar ne yasa take fada mana ni kuma sai inki fahimta in dinka mata kallon hauka, mlm kasan ba komai iyaye suke dauka ba amma yanzu da naji maganan ka na fahimci komai yaronka ya fada maka koda shirme ne ka nuna masa kulawa akai, nan suka ma mlm godiya tare da bashi kudi yaki amsa yace dan Allah yayi baya bukatan kudi saida mum tace babu kyau maida hannun kyauta sannan ya amsa suka wuce, a mota suka sami jawaheer tana ta kuka, mum cikin tausayin yar tata suka karasa motar bayan sun shiga mum tace jawaheer kiyi hakuri kibar wannan kukan batai shuru ba har suka sauke hjy hauwa suka wuce bayan sun shiga gida da sauri jawaheer ta shiga gida tana kuka a falo taga dad dinta nufanshi tayi tana sauke ajiyan zuciya, cikin damuwa yake tambayanta mai aka mata? Bata bashi amsa ba sai kukan da take tayi mum ce ta shigo falon ganin dad yace bilkisu mai aka mata haka? Kodai wannan magan ganun naki kike ta fada mata? Hjy bilkisu cikin damuwa tace kayi hakuri da abunda zan fada maka yanzu inaso kamin adalci sannan ka fahimce ni, wlh nayi hakan ne dan ina zargi amma daka baya saina fahimci kuskurena, munje wajan wani mlm ne a islamiya domin ina zargin aljanu jawaheer take dasu, dad yace what? mum tace kayi hakuri ka gama saurara na shuru yayi amma fuskanshi a tamke nan mum ta bashi labarin abunda ya faru, dad baice komai ba sai kama hannun jawaheer da yayi yace tashi kije kiyi wanka kizo kici abinci sannan ki fara shiri jibi zamu tashi zuwa spain bata san lokacin data tashi ba dan murna lokaci daya kuma tace dad r u serious? murmushi yayi tare da fadin yes jawaheer bana daukan abunki da wasa komai naki inaso inyi miki yanda kike so hugging dad dinta tayi tare da furta u r d best dad in d world tana fadin haka ta nufi dakinta.










Kallon mum dad yayi yace bilkisu na rasa mai yasa gaba daya kika canza bakya jin duk maganan dana fada miki, yanxu kinji dai abunda mlm din yace Allah yasa ki dauka kiyi amfani dashi, tace kayi hakuri insha Allah komai ya wuce sannan wannan abunda ya sami jawaheer na jarabawa zan kara dagewa wajan roqan Allah akan ya zaba mata mafi alkhairi a rayuwa, yace yauwa ko kefa, dan murmushi tayi tare da fadin kasan ita daya ce yarinya ta mace duk wannan abunda kaga inayi duk sonta yaja hakan tunda babu mai so yaga nashi ya shiga wani hali, dad yace hakane sai muyi ta addu'a sannan tare na mana visa harda ke zamu tafi jibi da khalil mum tace tafiyan family ne kenan gaba daya dariya dad yayi yace mun dade bamuyi irin tafiyan nan ba gaba dayan mu, tunda muka dawo daka saudiya bamu kara fita mu duka ba naso muje harda umar babban dansu kenan, amma yace shima zaiyi tafiya, mum tace Allah ya taimaka, ya amsa da ameen...... Toh jawaheer za'a spain koya zata kaya???






















*maryam obam*
[06/01, 01:05] Maryam Obam Group Kd: *JAWAHEER*






*STORY AND WRITEEN BY......*


*MARYAM ALHASSAN DAN'IYA*
*(maryam Obam)*




*🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝*
*{united we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}*


*wattpad @maryam-obam*


*WWW.Maryamobamnovels.com*








https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/










*DEDICATED TO.....*


*Nafisa mrs dan malikin kawo*


















Page 7






















Jawaheer shiri take sosai domin tafiya spain ko abinci bata iya samu taci dan murna sai dad yayi dagaske take ci, kaman yanda dad yace jibi zasu tafi hakan ta faru domin dai rana bata karya inji masu iya magana, yau jirginsu ya daga zuwa kasar spain.....








Su jawaheer an sauka a kasar spain tunda suka sauka ta lumshe ido tana jin wani irin nishadi tare da farin ciki sai take ganin kaman gata ga M samir nan, wata katuwar mota ce taxo ta daukesu da kayansu wani gida suka nufa gidan sama, bayan sun karasa gidan suka shiga komai na gidan an rufe da farin kyalle saboda kura cirewa sukayi suka zauna a kujeran falon, hjy bilkisu ta kalli mijin nata tace wannan gidan fah nadai san baka da gida a kasar nan, murmushi yayi tare da fadin saboda jawaheer na siya, munyi waya da ambassador akan ina son gida a kasar nan shine ya hadani da wani kin san shi yana asibiti, toh wannan gidan ma mutumin yace nayi sa'a harta yan kasar sun kasa siyan gidan dan yayi kudi da yawa, mum tace ah lallai kam ai dole dan gidan ya hadu gskya duk da banga ko ina ba, jawaheer ta tashi tare da fadin bari inga gidan khalil shima binta yayi nan sukai ta zagaya gidan wanda yasha kayan more rayuwa ga gidan kato a kalla dakuna sun kai bakwai a gidan, mum tace ma dad naga su turawa basa irin gida haka babba, yin katon gida sai balarawa, dad yace suma yanzu turawan sun fara, jawaheer ce ta fito daka wani daki tana fadin dad ni wannan ne dakina na riga na zaba, dad yace ok dear duk inda ya miki nan zaki dauka, khalil yace dad ya kamata a bata daki a kasa ne, kafin dad yayi magana ta amshe da fadin sai kace namiji zan zauna a kasa dad shi zai zauna a kasa ya dinga gadi yaga masu shiga da fita, khalil yace ni din zan zama mai gadin nufota yayi da nufin ya kamota ta fara gudu shima yana binta dad da mum dai dariya sukayi mum tace kuna jin karfin jikinku ne sai yasa kuke ta wannan gudun, saida suka gaji dan kansu suka zauna suna maida numfashi, dad waya yayi aka kawo musu abinci tare da masu aiki biyu turawa duk ta hanyar mutumin da ambassador ya hadasu dashi, saida suka huta sannan alhaji jibrin mai dala ya shirya dan zuwa duba ambassador a asibiti, harda su mum da jawaheer jawaheer tayi shigan riga da wando sai tasa boyfriend jacket akai mai tsawo tare da yafa karamin gyale a kanta ta nada shi kaman hijab, duk da batai makeup ba tayi kyau sosai, cikin wata sabuwar jeep suka shiga nan driver yaja su suka nufi hspt din, kafin su shiga dakin da ambassador yake saida aka basu wani kaya suka daura akan nasu domin haka ka'idan asibitin yake, bayan sun shiga suka sami ambassador yana jin jiki duk da yana dauriya amma kana kallonshi kasan ciwo nacin shi, alhaji jibrin mai dala yace sannu ambassador ya jikin ya amsa da fadin da sauki alhmdlh, nan suma su jawaheer suka gaidashi ya amsa da fadin jikin alhamdlh, alh jibrin yace dama haka kake jin jiki? Ambassador yace ai jiki yayi sauki ma sosai akan da, cikin tausayi alh jibrin yake kara fadin Allah ya kara ma lfya, ambassador yace ameen, amma lfya kuwa PA dina yace kana ta kira cikin damuwa? Alh jibrin yace ah a ka barshi kawai inka warke mayi magana, ambassador yace haba haba ka fadi mana kai ka sani koh zan tashi, alh jibrin yace zaka tashi mana insha Allah, dama akan maganan dan kwallon kafa din nanne M samir wlh kaga yarinya ta ga tanan ya nuna jawaheer wacce tayi tsuru tana sauraransu, ita take son ganinshi, ta hanamu sukuni, ambassador yayi shuru yana ji har alhji jibrin ya gama sannan ya sauke ajiyan zuciya tare da fadin babban magana, alh jibrin yace kaman ya? Ambassador yace gsky ganin M samir yana da matukar wuya kaman a nigeria ne talaka yace yana son ganin shugaban kasa kaga hakan bamai yuhuwa bane a garesa, inaga kaman ma wannan zaifi sauki, domin M samir yana daya daka cikin matasa masu kudin duniya ganinshi zaiyi matukar wuya dama wani ne daka cikin yan kwallon dana hadasu, sai dai ta ganshi in za suyi wasa a cikin fili, jawaheer fita tayi da sauri tana kuka tare da fadin shikenan bazata sami ganin M samir ba shikenan burinta da mafarkinta zai zama karya kenan mota ta shiga ta zauna tana ta rusgan kuka driver din da aka hadasu yana ta kallonta ta mirror cikin tausayi, gashi babu daman ya tambayeta ko lfya,










Haka su dad suka shigo motar suka sameta tana ta rusgan kuka, nan dad ya fara aikin rarrashi amma kaman kara zugata yake dan haka ya barta in sunje gida ya rarrasheta dakyau, koda suka isa gida fita tayi tana kukan dukansu suna tausaya mata musamman dad, zata wuce daki khalil ya rikota yana fadin haba lil sis mai yasa zaki sa kanki cikin damuwa haka? Cikin kuka tace bakaji abunda ambassador yace ba tunda ambassador bazai iya hadani dashi ba bana tunanin zan iya ganinshi tako wani hanya, shikenan komai nawa ya tsaya, bazan sami cikan burina ba bros ina son M samir a kullum da burin ganinshi nake kwana nake tashi indai ganinshi zaiyi wuya har haka kenan mafarki na ya zama karya..... Kasa tayi tana kuka cikin tausayi dad ya matso kusa da ita yace jawaheer kiyi hakuri insha Allah na miki alkawarin ganinshi tako wace hanya, kai ta girgiza tare da fadin dad baka ji abunda ambassador yace ba gwara in koma nigeria in nemi ganin shugaban qasa zaifi min sauki akan ince ina son ganin M samir, dad bana tunanin zanyi tsawon rai domin duka tunani na da jini na yana tafiya da M samir a kullum, zuciyata tana bugawa da tunaninshi dad in har ganinshi zai zama wahala a gareni miye amfanin rayuwa na? Ganin kowa yayi shuru yana kallonta yasa ta danyi murmushi wanda ake cewa yafi kuka ciwo tace dad nasan kuna min kallon rashin hankali ko wani abu makamancin haka, nasan koda kai bakamin mum tana min, amma abunda nake son ku fahimta shifa so ba karya bane wlh da ana cire abu a rai da tun tuni na cire shi na huta amma Allah ne yasa min sonshi wanda nasan shine kaddarata Allah yamin komai na rayuwa ban rasa komai ba komai nake so ina samu amma abu daya ya gagareni samu shine farin ciki na wato M samir, na yarda Allah baya bama bawa komai dole saiya jarabceka, wasu Allah kan basu dukiya da komai sai ya hanasu haiyuwa wasu kuma sai suzo a talaka abinci ma dakyar suke samu amma sai Allah ya azurtasu da haiyuwa lallai babu yanda Allah bayayi lumshe ido tayi wanda ya kada yayi ja, tace dad bana son zama a kasar nan inaso mubar nan da gaggawa nasan bazan iya cire M samir ba amma zan koma kasata inje inyi ta jinyar zuciyata har lokacin mutuwa na yayi...... Hmmm muje zuwa






















*maryam obam*
[08/01, 17:32] Maryam Obam Group Kd: *JAWAHEER*






*STORY AND WRITEEN BY......*


*MARYAM ALHASSAN DAN'IYA*
*(maryam Obam)*




*🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝*
*{united we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}*


*wattpad @maryam-obam*


*WWW.Maryamobamnovels.com*








https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation/










*DEDICATED TO.....*


*Nafisa mrs dan malikin kawo*


















Page 8


















Shuru tayi tana kuka.. Mum ta matso kusa da ita tare da rungumota tace kiyi hakuri jawaheer tun farko abunda nake so ki fahimta kenan amma yanzu alhmdlh tunda kin fahimta, ba komai bawa yake soba yake samu a rayuwa duk kudinka duk gatanka akwai abunda yafi karfinka, sannan Allah yakan jarabci bayinsa ta hanya da dama idan kayi hakuri sai ya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login