Showing 33001 words to 36000 words out of 48065 words
Chapter 12 - ZUCIYATACE HAUSA BOOKS COMPELET BY ESHAAT SMILER.txt
kusadani, da sauri yace Abba my Ammi sai nadawo dariya sukayi dukkansu hardashi Abba yace dan'nemakai kace inagaida ita inanan zuwa anjima Ammi matace yagaida ita yace toh tareda fita.
Koda yaje gidan inna wuro beyi wani da dewaba yabaro gidan Obasanjo complex yashiga, wayoyi yasiya guda uku tareda layinsu dukkan su sanfurdin Tecno ne saidai dayan tafi kyau da tsada kuma touch ce ita sabanin biyun daba touch ba, Bayan yafito sai yanufi wani super market kaya yake tafaman jida irin wanda yasan za'ayi "amfani dasu batareda "andafa ba, Bayan yagama sannana yanufi school Don dauko *SAJEEDAH* alokaci 12:30pm.
Yana isa wasuna fitowa bakin get yasamu guri can gefe yai parking yana kallon dalibai suna tafitowo, can saiya hangota tana tahowa.Cikin nutsuwa take tafiya idanu yatsura mata yanada yadaga ciki "abunda yasa yake kara *SONTA* nutsuwar ta da ibada, ahankali yace Allah kamallaka mani wannan baiwa taka amatsayin matata UWAR yayana domin dai *ZUCIYATA* nasonta.
_*Nikam nace toh" ameen*_
jiyayi wata murya tace *SAJEEDAH ABUBAKAR SADEEQ* *DEEQAR-JEEDART 4ever,* "ahankali yaga yajuya tana dariya dai-dai lokacin dayariyar takarasa guri,itama tana dariya tace ya exam?.. tace Alhamdullah SALMA NASIR yanaku? tace lafiya lau saikuma gobe tace toh Allah yakaimu yakuma bamu sa'a tace ameen, tareda wucewa itama tawuce hon taji agefenta dasauki tajuya dai-dai lokacin da yasauke glass din motar, Murmushi tayi tareda matsawa yabude mata kofa tashiga tareda cewa sannu *yah SEERAJ* yace yauwa me mulki *ZUCIYATA* yakike yakuma exam?..
Murmushi tayi kanta nakasa tace Alhamdullah, yace haka nakeson naji tace yajikin baba?..yace "baba yaji sauki harya yayi wanka yaci abinci yasha magani.Cikin farinciki tace Alhamdullah Allah mungode maka nandai yayi mata batayi "abunda "Dr yace cikin sanyi murya tace toh" Allah yabashi lafiya yace ameen ahaka har suka isa asibitin.
Da sallama suka shiga daki yayinda suka iske baba yana zaune suna fira shida inna, dasauri ta karasa gurinshi fuskarta dauke da Murmushi tace sannu baba yajiki?, shimafuskar shi dauke da murmushi yace dasauki *SAJEEDATU* ya jarabawa? tace Alhamdullah toh"Allah yabada sa'a tace ameen shima *SEERAJ* yagaida shi ya'amsa yana samanshi Albarka, ya tambayi inna yajikin "Sajeed tace ya sauki har yafita yawo, dariya yayi sannan yaciro waya ya baba yabawa inna Sannan yabawa *SAJEEDAH* nata.
Baba yace Allah sarki *SEERAJO* nida banida Lafiya yazanyi dayawa?.. yace baba idan kana bukatar wani'abu kawai kakirani, yace toh "nagode sosai itama inna tayi masa godiya, itakam *SAJEEDAH* tarasa "abunda zata ce,
yace *JEEDAH* muje akwai kaya amota mu shigo dasu, tace to tareda bin bayan shi sunafi tana tayi masa godiya bace mata komai saidai kawai yabude but suka fara kwasan kayan,Wanda saida *SAJEEDAH* taji tsoro saboda gani yawan kayan.
baba yakurawa kayan idanun Sannan yakalli su inna yace kudan bamu guri zamuyi magana sukace toh tareda fita, yamaida kallon shiga *SEERAJ* Wanda yaji gaban shina faduwa saka makon kallon da baba yakeyi masa mai cike da tuhuma Baba yace'?...
Muje zuwa
A
๐Zuciyata ce๐
Tareda Alkalamin
โ๐ฝ
๐Lufhat ce๐
๐๐ซ๐๐ซ๐
๐๐ซ๐๐ซ๐
๐๐ซ๐
๐
๐ZUCIYATA CE๐
_Based on true life Story_
๐๐ซ๐๐ซ๐
๐๐ซ๐๐ซ๐
๐๐ซ๐
๐
(Labarin Sarkakkiyar Soyayya)
2โฃ6โฃ
WRITTEN BY
๐ยฉAMEENA UMAR FARUQ๐
OR
๐MEENAT๐
________________________
*_ยฎPEN:WRITERS ASSOCIATION_*
*_PEN THE STRONGEST WEAPON_*
________________________
*_only the exquisite and Whizkid writers are opportune to be pen writers_*
โ๐ฝ
*"SEERAJO* Cikin Dan fargaba yace na'am baba?...tun ranan da Allah yasa nafara ganinka nagane kai din mutumin kirki ne, kuma har zuwa wannan lokaci *ZUCIYATA* "a mutumin kirki take daukar ka, ban taba nasawa a *ZUCIYATA* cewa kai ba mutumin karki bane saidai daga jiya zuwa yau *ZUCIYATA* tafara tsoro tada lamarinka,
Jiya "likita yazo dubani Na tambaye shi kudin maganin nan yakai nawa?.. yafada mani kudin naji tsoro yakamani saka makon jin tsadar magani, yau kuma ga wayoyihar guda uku Wanda na tabbatar da suma tsadaddu ne musamman ma ta *"SAJEEDATU* Sannan kuma ga wayan nan kaya masu yawa shin *SEERAJO* duk inakake samo kudi haka KO" Kanasan kace mani motar daka kejane ake baka kudi masu yawa haka Ummh?..
fada mani *SEERAJO* domin jinka nakeyi ajinina tamkar Dan dana haifa Don hakane banasan ka kasan ce daya daga cikin mutane marasa kirki "arayuwa saboda haka kafada mani ina kake samo kudi masu yawa bayan kudin kada "ake baka?...
Cikin sanyi murya yace don Allah Baba kayi hakuri kaya femani nayi maka laifi, Baba yace a ah *SEERAJO* tunda nake dakai baka taba yimani laifin komai ba, "asalima kullum Cikin kwayautata Mani kakeyi kanayi mani abubuwan dako 'Dan dana haifa iyakar abunda zayayi mani kenan, saboda haka nibakayi mani laifin komai ba idan ma har kayi Mani tona yafe maka Allah yai maka Albarka.
*SEERAJ* ameen baba kamar yadda nafada maka cewa ni direban tabbas nidin direban ne, saidai bana babban mota direbane Na jirgin sama, Cikin mamaki me hadeda tsoro baba yace' direban jirgin sama fakace *SEERAJO?..* yace "eh Baba nan dai yafada masa koshi waya dakuma ainihin aikin da yakeyi,
shikam baba bu abunda yakeyi sai tasbihi tareda kabbara Cikin sanyi murya yace ikon Allah, me tsara lamarinshi yadda duk yagada ma nagode sosai *SEERAJO* duk dai banida bakin dazan yimaka godiya sai bazan fasayi maka Addu'a ba, Allah yasaka ma iyayan kada Alkhairi inarokon Allah ya kyauta ta rayuwarka kamar yadda ka kyauta ta tawa data iyalina.
Ameen Ameen Baba nagode sosai shine abunda *SEERAJ* yaketa fada Cikin farin Cikin domin yanajin dadin Addu'a dababa yakeyi masa, yace baba inasan kabani dama nagyara maka gidanka Da sauri baba yace" Anya *SEERAJO* hidimar nan batayi yawaba?.. yace "a ah Baba batayi ba inajin dadi Addu'a daka keyi mani.
Murmushi baba yayi tareda cewa nima inajin dadi kyautatawar daka keyi mani, Don haka nabaka dama *SEERAJO* Allah yayi maka Albarka yabaka abunda kake Nema na Alkhairi duniya da lahira, yace ameen baba dai-dai lokacin da Sajeed yashiga dakin.
Da sauri Sajeed yakarasa gurin *SEERAJ* yarike hannun shi tareda cewa *yah SEERAJ* my friend kadawo?.. yace nadawo my friend yajiki?..yace naji sauki *yah SEERAJ* nime kasiyo mani?.. hannun *SEERAJ* yasa akai tareda cewa Oh god my friend ban siyomaka komai ba, baki yaturo yace toh" meyasa?.. yace bakomai namantane amma yanzu fada mani meka keso?..
Yace ummh bicycle (keke) *SEERAJ* dame kuma? yace' da ball, dame kuma?.. yace takalmin but saime kuma? dariya yayi tareda cewa lah yah *SEERAJ* shikenan, Murmushi baba yayi yace Kai Sajeedu duk wannan lissafin *yah SEERAJO* shi kadai?. Murmushi yayi tareda cewa Baba Bari muje nasiyo mashi baba yace tun yanzu?. "eh baba yanzu zamu dawo yace toh" saikun dawo yace toh" tareda kama hannun Sajeed Wanda yaketa murna sukafita.
๐๐๐๐๐
Yau "Ammi batanan take unguwa "Abba yafita masu Aiki ma suna part dinsu, *ZUBEE* ce itakadai zaune a tsaki yar falo tayi wujigawujiga kallo daya zaka yimata kagane batacikin nutsuwarta, kasan cewar kwana biyu bataje school ba saboda yajin aikin da akeyi, Don haka basu samu damar "aikata tsiyar dasuka dababa tunda bawai sun daina bane, saima "abunda yai gaba domin da itada Nusee sunzama tamkar miji da mata Kai KO" miji da mata suna sauwakama kansu.
"Amma banda *ZUBEE* da Nusee domin jisuke kamar zasucinye junansu saboda tsabar masifa, idan sukaje school hostel suke zuwa dayake akwai irin su lalatattu, sai suyita "aikata iskacinsu wani lokaci mako karatun basa tsayawa dauka, toh yanzu kwana biyu da bataje sunyi ba shine takejin ta kamar zata mutu, gawani abu daya da meta shine tunani suran jikin *SAJEEDAH* ko idanuta rufetoh' ita take tunawa.
Nusee ce tashiga falon bako Sallama tamkar wata mahaukaciya, dausari *ZUBEE* tamike tareda Kama hannun ta suka nufi daki ta suna shiga tarufe da key, Sannan suka fara sumbatar junansu saikace wasu tantabaru tareda fatali dakayan jikinsu Sannan suka fada _Duniyar mutanan Annabi "Lud(A S) wayanda ko alahira wutarsu dabance, muddun basu tuba sun daina aikata Ludu da madigoba._ ba'abunda ketashi adakin saisautin nishinsu.
_*Wa'iyazubillahi Allah ka shirya bayinka idan masu shirya wane, idan kuma ba masu shiryuwa bane Allah kaikasan yadda zakayi dasu, UBANGIJI kakare bayinka daga fadawa wannan mummunan dabi'a'Ameen.*_
Sun dauki lokaci suna kazantarsu,Sannan suka saurarawa juna dakyar *ZUBEE* ce tace Bebe meyasa kikazo?.. (kasan cewar tunda ran nanda *SEERAJ* yakamasu sai bata zuwa sai idan bayanan, sai tazo suyita tsiyarsu koku masu hadu can school wanda Ammi sam bata saniba) Nusee tace ke! bebe "aidole nazo kwana biyu da banyi baji nayi kamar zan mutu, jiya mafa saida naje hostel mukayi da Jamima sannan nadanji dadi.
Cikin kishi *ZUBEE* tace kinganiko?.. inda nice dayanzu kinji haushi toh" kitashi kitafi kafin "yah S .P yashigo don, yanagari takarashe maganar dajan tsaki mtww,
_*wai'ita adole taji haushin Nusee tayida Jamima mtswwwww nayi , nace kaji sha sha su sai kace wani abun arziki*._
dasauri Nusee tace toh' yi hakuri bazan sa keyi da'itaba, toh" mu dan karayi sainatafi kafin yah S P din yadawo kinji?.. nandai suka kara lulawa saida sukayi mai isarsu, Sannan sukarabu badan sunsoba Nusee ta tafi gida.
_*ALLAH ya shirya Ameen.*_
๐๐๐๐
Yaukimani kwana biyar kenan da fara aikin gidansu" *SAJEEDAH*,Wanda yayi dai-dai da sati baba daya asibiti yaji sauki a zahiri saidai kuma bamu saniba "abadili, aiki gida kuma yayi nisa kamar yadda *SEERAJ* ya bukaci masu aiki suyi 2 bedrooms flat haka sukayi dayake harkane nanaira harsun kusa gamawa.
*Asibiti*
Da misalin 3:40PM
*SAJEEDAH* ce zaune akan darduma akarkashi bishiyar mangwaro kasan cewar nansu kasaba zama susha iska, jikinta sanye da kayan islamiyya kasan cewar yau "Asabar,hannun tarike dawaya tana Neman layin *SEERAJ* bugu daya ana biyu yadaga.
Cikin sanyayyar muryarta me kashe masa jiki tayi sallama, Cikin muryan bacci ya'amsa tace lah yi hakuri *yah SEERAJ* Nata dakai bacci ko?.juyiyayi "akan tabkeken gadonshi tareda kara manna wayar "akunnanshi, idan shi lumshe yace Ummh ya'akayine *my JEEDAH?..* tace ummh dama zance ne mun shirya, yace toh' bari nayi salla saina taho kinji?..tace toh".
saikuma sukai shuru. can sai tace *yah SEERAJ* yace na'am *my JEEDAH* tace ummh ina *SONKA* da dukkan *ZUCIYATA,* Murmushi yayi mesautin da har saida tajishita cikin wayar, idanu ta lumshe domin jinsauti tayi yashiga jikinta, yace nima ina *SONKI my JEEDAH* da dukkan *ZUCIYATA* fiye da yadda kike sona.
kullum Addu'a nakeyi Allah ya mallaka mani ke amatsayin matata daga ranan, zan nuna maki zallar *KAUNAR* dana keyimaki wanda *ZUCIYATA* ke dauke dashi, nandai yaketa fadamata kalamai SO itama tana fada masa, can yace yanzu duk wannan abunda ake fada mani awayane baza'aiya fadama nishi afiliba, saboda wannan kunyar aini dai kunyar nan tana cutata saitayi tahana *ZUCIYA* tafada mani abunda takeji game daniko?..
aizan kamata sai nayi maganin ta, dariya tayi tace Kai *yah SEERAJ* ina zaka ganta?..yace auni dana ganta tun ran da nafara ganin ki, dariya tayi tareda cewa toh'shikenan saikazo yace Ok sannan takashe wayar. sai tafara buga game awaya tadauki tsawan wani lokaci tana buga gamedin, can saiga Sajeed shima sanye dakayan makaranta yace' Aunty *JEEDAH* nashiriya.
"Agogon wayarta kalla yanuna mata 3:50pm tace toh" je kayi sallah nima yanzu zanyi kafin *yah SEERAJ* yazosai mutafi yace toh"tareda bin hanyar masallace,yayinda ita kuma ta tashi tanufi daki domin can take yin sallarta.
๐๐๐๐๐
"Ayau jumma'a wanda yayi dai-dai da kwanan Baba goma sha biyu a' asibiti,yaji sauki yaki kyau abun shi idan kaganshi baka cewa yana dauke da ciwon koda, harma za'a sallameshi gobe. kuma "a yaune su *SAJEEDAH* sukayi hutu kasan cewar sun gama jarabawa tun shekaranji ya.
"Aikin gida kuwa tuni angama shi duk wani kayan more rayuwa *SEERAJ* yasamusu, jiyama yasa almajirai sukayi saukar kur'ani "agidan shiga kawai yarage.
"Ahankali yake tuki sanye yake cikin farar shaddatayi masa kyau,dayake shirin daya keyi kenan duk Ranan jumma'a *SAJEEDAH* ce zaune agefen shi daga school yadaukota.
Sai satar kallon shi takeyi aranta ko tajinjina kyau irin na *SEERAJ* mutum saikace dan'larabawa,
_*nikam nace toh ai shine lol*_
Murmushi yayi kasan cewar yana kallonta ta madubin motar, juyowa yayi ya kalleta yace ki kalleni da kyau domin nidin naki ne, dasauri tarufe idanu tana dariya tajikunya yakamata tanasatar kallon shi.
Baki yaturo kamar karamin yaro cikin sigar shagwaba yace kwalliyar Jumma'ar ma da nayi nasan batayi kyau bane shiyasa ma kodan yabawa ba'ayiba, dasauri tace lah *yah SEERAJ* kayi kyau sosai yace really?.tace yesss yace toh" kawo goron jumma'a, tace toh'meka keso?.dai-dai lokacin da yayi fakin "a harabar "asibitin tareda kashe motar, sannan yajuyo yazuba mata lumsassu idanun shi yace *ZUCIYARKI* nakesonki mallaka mani kamar yadda namallaka makitawa.
Kanta yana kasa tana wasa daya tsunta tace Ai *ZUCIYATA* ta kace *yah SEERAJ* yace toh" godiya nakeyi *my JEEDAH,* Sannan su kafito direct guri inna suka nufa datake zaune Kar kashi bishiya tana shan'isa, su kagaida ita sannan sukanufi dakinda Baba yake bayan su gaida shi sai *SAJEEDAH* tafito takoma gurin inna tabar *SEERAJ* shida baba suna fira.
*SEERAJ* yace baba'angamafa gyaran gidan baba yace madallah, kaganshi nanma "awaya nadauko kagani, yafara nunamasa baba yana kallo yanasa mashi Albarka, Bayan yagama nuna mashi sai yace nagode *SEERAJO* Allah yayimaka albarka saikuma yafashe dakuka cikin tsoro *SEERAJ* yace'?..
Muje zuwa
A
๐Zuciyata ce๐
Tareda Alkalamin
โ๐ฝ
๐Lufhat ce๐
๐๐ซ๐๐ซ๐
๐๐ซ๐๐ซ๐
๐๐ซ๐
๐
๐ZUCIYATA CE๐
_Based on true life Story_
๐๐ซ๐๐ซ๐
๐๐ซ๐๐ซ๐
๐๐ซ๐
๐
(Labarin Sarkakkiyar Soyayya)
2โฃ8โฃ
WRITTEN BY
๐ยฉAMEENA UMAR FARUQ๐
OR
๐MEENAT๐
________________________
*_ยฎPEN:WRITERS ASSOCIATION_*
*_PEN THE STRONGEST WEAPON_*
________________________
*_only the exquisite and Whizkid writers are opportune to be pen writers_*
โ๐ฝ
"Karya kake wlh kasan inada abunda bakada shi yanzu haka daga gidana nake nagama cin medadi, nasha medadi dasanyi inahutawa acikin a c, Wanda Kai baka dashi, kaga koda ganan za kagane tafiyar badaya bace kodayake naga take takenka saboda kaga muna makota saikana ganin, dani dakai dayane shine har kake ta wani "aikawa nazo kuma kasan nafi karfinka, toh" gani nazo sai kafada Mani dalilin kirana daka keyi Saboda haka Ina sauraran ka?..
Murmushi baba yayi Alh Siddi kenan aiduk wannan abun daka lissafa bawai kai kabaws kankaba kyautane Allah yabaka bakuma waidan kafi kowa bane a ah kawai dai ganin damanshi ne Wanda kuma idan yaga dama sai ya kwace yabawan.... Dasauri yace toh" Dan bakin ciki banji bakin kaba kajiko?,
Baba yace bana bakin ciki daka duk tsawon zamana dakai ban taba bakinciki da abunda Allah yabaka ba don haka kar kayi tunanin ko'ina bakin ciki da arzikin ka, Mtsww yayi tsaki tareda cewa idanma zakayi kayi nidai kafada Mani abunda yasa kakirani Saboda inada abunyi kanaji KO?..
*SEERAJ* kam idan ransa yayi dubu toh" yabaci yayinda yaji wani irin tsanar Alh Siddi ya darsu a *ZUCIYAR* shi, har yanafadi aranshi shikam tunda yake be taba ganin Mutum jahili kuma matara mutunci irin Alh Siddi ba, maganar baba ne takatsewa *SEERAJ* zance zucin dayake inda yake cewa Alh Siddi.
"Anyini Lafiya?.. yace gazahiri kagani, Murmushi baba yayi toh" dama nacene akiramani kaina rokeka gafara kilana tabayi maka wani laifi ban sani ba, nida bakayi Mani komai ba idanma kayi Mani toh" nayafe maka. Yace yo tonidama laifin mezanyi maka don haka Allah yayafe mana bakidaya, baba Yace toh Ameen nagode.
Sannan kuma amatsayin ka namakocina Inason kazama shaida ni Abubakar nabawa *SEERAJO* gashi nan auren *SAJEEDATU* Kobay...Cikin masifa Alh Siddi yace toh" same don zaka bada auren yarka saina sani Ko-ko salon kace nai mata kaya dakiko?.. toh" karkaji dawai bazanyi ba kaji KO?..yarka kuma duk Wanda zakaba kaba ba'abunda yadameni ehe fuuu yasa Kai zaifita Da sauri baba yace toh" Alh Siddi nagode datasowa "asauka Lafiya Mtswwwww! yayi tareda banko kofa gafffff.
Shikam *SEERAJ* baki yasaki yana kallon baba aranshi kuwa fadi yake shin baba wani irin mutun ne haka,?.. wata iriyar *ZUCIYACE* Allah yai masa?.. itakam *SAJEEDAH* hawaye neke tamalala afuskarta, na bakin cikin "abunda Alh Siddi yakeyiwa BABASU kuma ba wannan bane nafarko dama yasaba,
akwai wani lokaci daya tabayi masa irin wannan cin mutunci zatayi magana, baban yace kul karta kuskura tasa baki idan manya suna magana aiba'irin tarbiyar dayayi mata kenan ba, shiyasa tundaga wannan lokacin KO "Alh Siddi yana fadawa baba maganganun nacin mutunci bata cewa komai saidai tayi kukata tashare hawaye.
Zumbur *SEERAJ* yamiki yazabi Alh Siddi Baba yarike hannun shi, da sauri juyowa yayi yakalli Baba yayinda baba yake girgiza mashi kai alamar a ah, domin yafahimci abunda yakeshiri zuwaya aikata, yace baba kabar ni naje Na fadawa mutumin nan koda kalma dayace, konaji sanyi a *ZUCIYATA kaji?..*
Baba yace "a ah *SEERAJO* idankayi haka "aibaka kyauta ba domin shindi babban ne agareka, Saboda haka kayi hakuri ka kyale "shi kasan mutane kowada irin halin shi, komawa yayi ya zauna tareda rintse idanun shi, wani irn bacin rai yakeji tareda jin tsanar Alh Siddi a *ZUCAYAR SHI.*
"Ahankali *SAJEEDAH* tamike tafita daga dakin tana share hawaye da hijab dinta, da Inna da Baba sukabi bayan tada kallon, "ahankali yabude idanu tareda zubasu inda *SAJEEDAH* take zaune saidai be gantaba, da sauri yace baba Ina *JEEDAH* yace tafita waje, zumbur yamike yabita. bin bayanshi baba yayi da kallon Murmushi yayi tareda rufe idanu yanaji ajikinsa KO" yanzu yabar duniya *SEERAJO* zaya kula mashi da *SAJEEDATU.*
Inna ce tace toh"shin BABAN Sajeedu kafasan cewa ciwo bamu tuwa bane KO?..Murmushi yayi yace nasani mana Saratu, tace toh" nifa bangane wannan maganganun daka keyi ba?.. gashi sai sawa kake ana kiran mutane harda, wannan mutumin da be dauki Dan Adam da DARAJA ba,
Don Allah nidai kabari tafadi ranta "abace Murmushi yayi tareda cewa toh" Saratu nabari.
tsaye yaganta bakin kofa idonta rufe cikin bacin rai yace shiyasa natsani wancan banzan mut.. dasauri tabude idanu tareda cewa "a ah *yah SEERAJ* karka zageshi Cikin mamaki yace saboda me?..tace Saboda shidin baban Besty nane, tsaki yayi mtswwwww! yace kar