Showing 45001 words to 48000 words out of 48065 words

Chapter 16 - ZUCIYATACE HAUSA BOOKS COMPELET BY ESHAAT SMILER.txt

23 Jan 2025

3497

kudin haka?.. inji cewar *SAGEER* kenan wanda tun lokacin da *"SEERAJ* yakira shi yafada masa yadda zayayi dakudin yake mamaki ganin betaba yin hakaba shine, yakudiri aniyar saiyaga wanda za'aba wayan nan kudin haka, don haka ne bayan yakaima megadi saiyakoma gefe ya labe cikin motar shi don yaga wanda zayazo karban kudin shine yaga *SAJEEDAH* take takarba.


Cikin daga murya yace' toh" Uban meza kiyi da kudin?.. cikin tsoro tace Ummh! dama.. tsawa yada kamata tareda mika mata hannun yace bani, dasauri tace don Allah kayi hakuri abincinmu yakare shine zamu siya,da karfi yace Zaki bani kosai nayi ball dake?..dasauri tamika masa idanun ta kuwa tuni yafara siyayar hawaye, yakarba yana harararta tareda ciro waya daga aljihun wandonsa yakira layin *SEERAJ.*


Yace kai yanzu dama wannan kuchakar za'aba wannan makudan kudin?..cikin bacin rai yace "eh itaza'aba sai akace me?..yace sai'akace baza'a bayarba, wani Uban ashar *SEERAJ* yawatso masada larabci KO" *SAGEER* yaji abunda yace?.. kobaijiba "Oho sannan yace dan 'iska kudin ka komawa?..


yace kudin Kane amma bazan bayarba kuma yanzu zanje nafada ma "Ammi cewar baka rabuda wannan kuchakar yarinyar ba, yafadi yana hararanta kasan cewar tana nan tsaye bata wuce ba dayake taji dawanda yake Waya, cikin matsananci bacin rai *SEERAJ* yace idan kasake kiranta kuchakar sai munyi bura'Ubada kai idan nadawo, sannan kasan Allah idan baka bata kudin nan ba sainayi maka abunda Harka mutu bazaka manta dashiba, kuma idan kafada ma my "Ammi Allah ya'isa banyafe ba tunda yanzu kazama mugun mumafuki da'iska kawai yakashe wayar.


Baki *SAGEER* yasaki cikin mamaki yayinda yabi wayar hannun shida kallon tabbas yasa iskancin *SEERAJ* yana iya'aikata abunda yafada, tsaki yaja mtswwwww! sannan yad'ago ya watsa mata harara tareda cewa dalla gafara barki kiba cemani agurin nan kafin nayi ball dake.


Dasauri takarba tareda bari gurin da dan gudunta bin bayanta yayida harara, yace yan'iska sai suyita baka-baka acikin hijab kamar mutanan kwarai "ashe yan'iska ne yayi tsaki mtsww, tareda nufar inda motar shi take yashiga yaja yatafi yanata jininin magana.


Tsayawa tayi tana maida numfashi tace mugu dan'bakinciki rijiya tabayar guga zata hana, mtsww tayi tareda cewa haka kawai ban masa komai ba yabi duk yatsaneni, wayar tace tayi kara dasauri tadaga takai kunnanta kamar zatayi kuka tace *yah SEERAJ* "abokin ka mugune nan tafada masa abunda yaimata shuru yayi yana sauraranta gabadaya ransa yagama baci, cikin kwantar da murya yace kiyi hakuri kinji?. *my JEEDAH*


ni narasa yadda 'akai S A Nasko yazama haka amma nasan watarana sai tayida nasanin abunda duk yayi, yanzu yabani kudin?..tace "eh yace "OK kijeku siya duk abunda kuke bukata tace toh" *yah SEERAJ* mung... yace banace banaso ba?.. cikin muryar shagwaba tace toh" Sowee! Murmushi yayi tareda cewa I only Love u *my JEEDAH* tace D same two u my *yah SEERAJ* yace thanks ki gaida mani "Inna da "Jeed tace toh" sannan yakashe wayar.


๐Ÿ’˜๐Ÿ’˜๐Ÿ’˜๐Ÿ’˜
Yaune su *SAJEEDAH* zasu tafi nijer kasan cewar tunjiya Kawu Labaran ya'iso sunfito cikin shirinsu tsaf Sajeed yace" Inna yanzu ba dake zamu tafi ba?.. Murmushi tayi Wanda ga dukkan alama nakarfin hali ne, tace Sajeedu kenan aini inayin takaba kuma wanda yakeyi takaba baya zuwa ko'ina yace toh" idan kin gama Zaki iskomu can ko?.. tace a ah kuda zakuyi sati biyu kudawo aiba saina bikuba...yace' toh"innamu sai mun dawo tace toh"kudawo Lafiya Allah yakiyaye hanya *SAJEEDAH* tace Ameen inna damun isa zankira ki tace toh" har bakin kofar gida tarakasu tana tsaye tana hangosu harsuka shiga mato suka tafi dayake da mota yazo tareda drive shi yaja suka dauki hanya toh mukam saimuce Allah yakiyaye hanya.




"Ahankali inna takoma gida cikeda kewan ya'ya'nta tareda Addu'ar Allah yadawo mata dasu lafiya, takalli Binta dake zaune tace kitashi kidora karin kumallo tace toh" tareda tashi tanufi kicindin(Binta diyar wata yar uwan Inna ce shekaru ta duk basu wuce sha hudu amma tanada garin jiki) tazota taya Inna zama ne kafin su *SAJEEDAH* sudawo.




Dayake sunyi sammako saboda haka sundan isa dawuri saidai kam, su *SAJEEDAH* sungaji likis Saboda basu taba tafiya me dankaran nisa hakaba, Sajeed ma barci yake tayi abunsa inda *SAJEEDAH* taga sun nufa ya matukar bata mamaki.


domin kuwa gari guda tagani watoh wani dankareren Estes's ne dagidaje suke birjik aciki, direct gidan Kawu Labaran suka nufa matar shi mesuna Haj Safara'u tarbesu kasan cewarta macece mekirki, dakanta takai masu ruwan wanka bayan sunyi wanka sun shirya sai takawo masu abinci mejida lafiya, sukaci suna gamawa takira "Inna da *"SEERAJ* tafada musu cewa sun isa lafiya,Sajeed Kam tuniyai barci itakam *SAJEEDAH* takasa barci .


sai mamaki take tareda tambayar kanta waidama yan'uwan babansu masu kudi haka?... neshine, sukabarsu cikin wahala Wanda sanadin rashi yasa ciwo tayiwa babansu mummunan illah dayasa yabar duniya.


Kawai sai tafashe da kuka Na tausayin tuno wahala da babansu yasha ahankali takeyin kukan,Haji Safara'u ce tafito daga part din Kawu zata wuce nata saitaji sheshshekar kuka tada kinda *SAJEEDAH* suke, don haka sai tashiga dakin canta hangota tana kuka dasher takarasa kusa da'ita tazauna tareda cewa subhanallahi *SAJEEDATU* meyasa meki?..,


Cikin kuka tace bakomai tace haba waya zakice bakomai gashi naisko kina kuka Ummh fada mani meke damunki?.. Kodai bakiji dadin zuwa gurin mu bane?.. tace a ah tace toh" menene yasaki kuka?...ahankali *SAJEEDAH* tafada mata abunda yasa ta kuka harda taimakon da *SEERAJ* yayi masu duk saida tafada mata.


itama Haj Safara'u kukan take natausayin halin dasuka shiga,ta share hawaye tareda sharema *SAJEEDAH* sannan tace kiyi shuru zanbaki labari, amma saikin yimani alkawari duk abunda kikaji bazaki fadawa kowa ba, sannan kuma bazaki nunawa kawunki komai ba ke bashi kadaiba dukkan su"?...


cikin sanyi murya *SAJEEDAH* tace insha'allahu zanyi duk abunda kikace" Haj Safara'u tace toh" inazuwa kofar dakintaje tarufe sannan tadawo tace ki saurareni tace toh"ahankali tafara bata labari kamar haka.


๐Ÿ’˜๐Ÿ’˜***๐Ÿ’˜๐Ÿ’˜
"Alh Ado manomi shine sunan kakan ku shahararra manomine dayai suna anan kasar nijer, Alh Ado Mutum neda Allah ya'azurtashi danoma Wanda ta dalilin noma yatara arziki meyawa, da matarshi daya mesuna Hajara da gabaya yakaro wata matar mesuna "Hauwa duk dacewa "Hajara bataso yakara auren ba kuma alokacin tanada yara hudu duk maza "Sammani Labaran "Sulemai da lsah, haka akaizama tsakani Hauwa da Hajara badadi domin Hajara tasani Hauwa sosai.


"Ahaka har Allah yaba Hauwa ciki tahaifi namiji akasa masa "Abubakar itakuma Hajara tasake haihuwar mace akasamata "Fatima, haka rayuwa tamika yarasun girma Sosai saidai dai "Hajara da yaranta basu kaunar Hauwa da 'danta shikuma "Alh "Ado irin mutanan nan neda gidansu ba rashin ciba rashin sha dukiyace gatanan Allah yahore, saidai basudamu da abun iyalain sukeyi don haka "Abubakar yasha wuya agurin yan'uwansa.


Wata ranasai akawayi gari Alh Ado Allah yakarbi ransa, ba ciwo bakomai hankalin iyali shi yatashisosai saida basuda yadda zasuyi tunda kwanan shi yakare, hakan sukai hakuri saidai kuma wani abun al'ajabi shine ranan da duk Alh "Ado yacika kwana'arba'in da rasuwa ranan kuma "Hauwa tace ga garinku nan, tabbas "Abubakar yashiga tashin hankali, saidai kuma babu yadda da'iya da abunda Allah yashirya, hakanan ba yacigaba da fuskatar baya jinda dinsu ko kadan,.


Dadai yagaji da'abunda suke masa kawai sai yabar nijar, yayindasu kuma suka raba gado kasan cewar Alh "Ado yanada manya-manyan gonaki guda uku, don haka saisuka siyar daya tareda kayan gona suka raba kudin kowa yatashi da naira miliyan goma sha biyu harda Abubakar din, saidai nashi rabawa sukayi yayinda ko wannan su yakara miliyan biyu amma shi Labaran miliyan hudu ya dauka saboda shidin duk yafisu fitina.


dayar gonar kuma shine nan sukayi ginin gidajansu duk aciki suke zaune da iyalaisu yayida dukkasu sunada ya'ya', "Alh Sammani nekawai Allah bai bashi haihuwa Kawunki Labaran yara hudu mata uku namiji daya, shi kuma kawunki "Sule yanada biyar duk mata shikuma kawunki lsah yanada hudu mace daya uku maza, ita kuma gwaggonki Fati tanada biyu duk mata kuma duk zakigansu" insha'allahu.


daya kuma gonar suka cigaba dayin nomo akwai watarana dababa ku yazo shida innarku lokacin ana goyonki', abunda akai masa" banji dadi ba saidai ba yadda zanyi basubashi dukiyar shiba' suka kuma yimasa walakanci, shine ya tattara yakoma najeriya bai koma dawowa ba saidai mukaji rasuwashi.


wannan nan shine labarin yanzu abunda nakeso dake shine karki taba nuna masu kinji wannan Labarin kinjiko?,.. mata gyada sannan kiyi hakuri da duk wani abuda sukayiwa babanku sannan kiyita Addu'a a kwana atashi zasuba kudukiyar mahaifinku, kinji ko?..tashare hawaye tareda cewa nagode insha'allahu zanyi yadda kikace, tace yauwa 'yata yanzu kikwanta kihuta gobe za'akaiki gidajan kawun'nanki kigaidasu tace toh tareda kwantawa ita kuma tajamasu kofa tafita.


Washegari bayan su *SAJEEDAH* sun karya kumallo autar Haj Safara'u mesuna Zarah takaisu gida-gidasuna gaida yan'uwa,satinsu biyu kusan kullum saisunyi wayada lnna da *SEERAJ.*


๐Ÿ’˜******๐Ÿ’˜
Najeriya
kamar yadda Ammi tace kar *SEERAJ* yadawo sai ana saura kwana biyu bikinsu" da *ZUBEE* haka akayi, kasan cewar gobe salallai jibi daurin aure, don haka ya'iso misalin karfe goma nadare saidai ran nan nashin abace kasan cewar yau kusan fiyeda sati daya kenan yana kiran layin *SAJEEDAH* amma be samunta,don haka ya kudirin aniyar gobe dasafe zayaje gidansu" ya tambayi inna ko" lafiya sanna yafada musu zancen wannan jarababben auren nan da'akasa shiyi dole.




Inna ce zaune a tsaki yar falon hankalinta tashe yau ki mani kwanatara kenan tana kiran layin *"SAJEEDAH* bata samu, shikuma layin Kawu Labaran tana karira amma baya dauka don haka hankalin ta duk yatashi, kasan cewar yausati su" uku da kwanan biyu.


cikin sanyin murya tace Binta karakiran layin nan nakawun su" Sajeedu kisakar yadda za'aji, tace toh tareda sake kira cikin sa'a koya dauka saita mikewa inna bayan sun gaisa itace Ina ta kiran layin tabana samu ko lafiya?..kai kuma ko nakira baka dauka, yace ayya bana kusada wayar ne "itakuma wayar tace yafadi Inna tace allah sarki dama nace ne yaushe zasu dawo?..


Wani irin murmushi yayi yace ayya aiba zasu dawoba *SAJEEDATU* ma aure za'ai mata da yaron gurina Nasir,Cikin tashin hankali inna tace?..




_Aha turkashi_




Muje zuwa




A




๐Ÿ’˜Zuciyata ce๐Ÿ’˜




๐Ÿ’˜Lufhat ce๐Ÿ’˜
[11:02PM, 4/6/2018] โ€ช+234 902 288 0912โ€ฌ: ๐Ÿ’˜๐Ÿ›ซ๐Ÿ’˜๐Ÿ›ซ๐Ÿ’˜
๐Ÿ’˜๐Ÿ›ซ๐Ÿ’˜๐Ÿ›ซ๐Ÿ’˜
๐Ÿ’˜๐Ÿ›ซ๐Ÿ’˜
๐Ÿ’˜


๐Ÿ’˜ZUCIYATA CE๐Ÿ’˜


_Based on true life Story_
๐Ÿ’˜๐Ÿ›ซ๐Ÿ’˜๐Ÿ›ซ๐Ÿ’˜
๐Ÿ’˜๐Ÿ›ซ๐Ÿ’˜๐Ÿ›ซ๐Ÿ’˜
๐Ÿ’˜๐Ÿ›ซ๐Ÿ’˜
๐Ÿ’˜


(Labarin Sarkakkiyar Soyayya)

3โƒฃ7โƒฃ

WRITTEN BY


๐Ÿ’˜ยฉAMEENA UMAR FARUQ๐Ÿ’˜
OR
๐Ÿ’˜MEENAT๐Ÿ’˜


________________________


*_ยฎPEN:WRITERS ASSOCIATION_*


*_PEN THE STRONGEST WEAPON_*
________________________


*_only the exquisite and Whizkid writers are opportune to be pen writers_*






โœ๐Ÿฝ




"Au me?..yace aure fa cikin tashin hankali tace' innalillahiwa'inna'ilaihirraji'un, yace meye haka Saratu sai kace nafada miki mugun'abu?...zufa ta share natashin hankali tareda cewa "a ah yaya naga dai ba haka mukai dakaiba inace cewa kai sati biyu zasuyi sudawo ko?.. bama wannan ba aiba babanta yayi mata miji tunkafin yabar duniya kaga idan mukatada alkawari aiba'mu kyauta bako?.. tunda ya tabbatar mani dacewa KO" bayan ba ransa ayi auran tada wannan yaro daya kyautata mana arayuwa,


yace ayya aiduk abunda yaimaku baidaifi dan'uwanta bako?.. Sannan aiba yadda za'ayai Abubakar ya aurar da ita batare da saninmu ba Saboda bayada yan'uwan dasuka fimu don haka kinga ko yanada rai mune masu aurar da'ita toh" ballantana yanzu da bayada rai kinga mune yazama dole muzaba mata miji don haka kiba shi wannan yaron hakuri Anyi mata miji dan'uwanta. Kuka tafashe dashi tareda cewa don Allah yaya Labaran karkuyi Mani haka Ku taimakeyi nafita kunyar wannan yaro tareda cikawa mahaifinta burinshi Wanda yakeso yacika KO" bayan ba ransa don Allah yaya kuyi hakuri takarashe cikin matsananci kuka,


yace ayya Saratu saidai kam kiyi hakuri amma aure tsakanin *"SAJEEDATU* da "Nasi bafashi yana kai nan yakashe wayar.
Wani irin kuka Inna tasaki meban tausayi tareda cewa "Oh ni Saratu Allah ka taimakeni kashiga tsakanina dawayan nan bayi naka, kuka Inna takeyi sosai yayinda Binta take bata hakuri.


Washegari tunda misalin karfe goma nasafe *SEERAJ* yafito dashirin nazuwa gidansu *SAJEEDAH,* sanye yake cikin wata dakakkiyar shadda fara yayi kyau sosai sai kamshi yake zubawa saidai kuma fuskar nan tashi kam aba annuri sai kace be taba dariya ba, ta falon Ammi yabiyo Saboda yanasan yagaida ita kafin yafita,


Saidai falon cike yake da yammatan Amarya sai firasuke wucesu yayi tamkar basan Allah yayi ruwan tsiyar su agurin ba, aikam yana shiga dakin Ammi sukafara gulmarsa, wata daga cikin su take wow gaskiya *ZUBEE* kinyidace wannan hamson guy haka gaskiya yanada kyau.


wata kuma ta amsa da cewa sosai ma kuwa saidai naga kamar yanada jinkai?..da sauri Nusee tace sosai dama ita mugun haushin *SEERAJ* takeji, don haka ne tayi saurin amshe maganar harda cewa kodan yaga yanada kyau ne gakuma naira data zauna kota'ina shiyasa yake wani jijida kai itadai, *ZUBEE* duk dacewa bata wani son auren amma taji dadi da'aketa koda mijin da zata aura koba komai ta tseremasa'a.


Bayan yagaida Ammi tareda gwaggon shi Rabi' sai yace my Ammi zanje gurin *SAGEER* tace toh" saika dawo har zayafita, saiga Nana autar gwaggo Rabi' dasauri hannun tarikeda roba lallai ne aciki cikin zolaya kasan cewar tasan yatsani lalle amma saboda tsokana, tace yah P S lallefa nazo samaka naga kuma kamar zaka fita ko?..tafadi tana yin dariya, harara yawatsa mata tareda cewa toh" basai kizo ki sama nidin ba tunda bakida hankali ne, baki ta turo tareda cewa toh' ainaga ba'asa maka bane kuma gaka ango shine nace Bari nazo Nash..


harara yasake watsa mata wanda yasatayi shuru sannan yakalli Ammi, yace my Ammi idan NaNa tashafa mani wannan kazantar idan namareta sai hakorin ta guda yacire, idanu NaNa ta zaro, yayinda Ammi tayi dariya tace baban Jordan kenan yaza'ai kana Ango kace bakasan lalle ummh ?... yace "eh banaso, gwaggo Rabi dake dariya tace kyalesu 'dana sunsani sarai bakason lalle shine NaNa da she ganta ka harda wani daukowa zata Shafa maka wuce abunka katafi kaji?...yace idan baki bani hanya nafita ba saina begeki agurin nan dasauri ta matsa tana dariya, yana fita tace sarkin masifa kowani Ango yana farinciki amma ban dashi, gwaggo Rabi tace idan yakamani aizakiyi bayani tace Ai Ammi zata checheni KO?.. tace kwarai kuwa 'yata.


Koda yafita gidan su *SAGEER* yanufa daga waje ya tsaya yakira shida waya yace yana jiranshi yafito yanzu nan, mota yashiga yana cewa Ango kasha kamshi laraban Jordan saukar yaushe?... baibashi amsa basai daikawai yatada mota, yace ah mlm Ina zamune haka?... yace gidansu" *my JEEDAH* dasauri yace what!?..yace "eh nazone na daukeka kaga inda zani saboda kaji dadin fadawa my "Ammi tunda kaidin kazama mugun mumafuki, tsaki yaja mtswwwww! tareda cewa amma dai kacuceni *SEERAJ* yace ranan muguwar ka nafada maka,


Harsuka isaba wanda yasake yiwa dan'uwansa magana, bayan yakashe motar yafito sai *SAGEER* ya watsa masa harara tareda cewa' toh" nidai Ina nan cikin mota ba'inda zanyi "ehee, shima hararar ya watsa masa tareda bashi amsa dacewa aisuba munafukai bane don haka basu gayyar mumafuki a gidansu" sannan yarufe kofar yanufi gidan.




Innace zaune shuru tana tunanin maganganun da "kawu labaran yafada mata jiya Wanda yasa takasa samun sukuni aranta, "ahankali tafurta haba wannan wani irin rashin adalci ne ?..haka insha'allahu bazaku taba samun narasa akanmu ba, kuma da izinin Allah indai harni Saratu da Abubakar ta hanyar sunnar ma'aiki mukahaifi *SAJEEDATU* toh" KO" insha'Allahu batada mijin daya wuce *"SEERAJO* da'izin Allah, Sallamar Wanda tajine yasa taji gabanta yafadi kadan.


ta'amsa dai-dai lokacin da yashiga falon fuskarta sake tace a ah lale maraba sannu dazuwa *SEERAJO,* saukar yaushe agarin?.. zamayayi akan kafet cikin jin kunya yace yau sannu Inna jiya nadawo, tace Allah sarki kadawo lafiya? yace lafiya lau Inna na sameku lafiya?..tace lafiya lau yasu "Haj?.., yace suna lafiya daga nan kuma sai sukayi shuru kowa da abunda yake sakawa aranshi.


Can yace Inna dama nazo nafada maki wata magana ne saidai don Allah Inna karkiyi wa maganar tawa mummunan fahimta kinji?..gabanta ne yafadi kadan amma kuma sai tayi murmushi tace haba *SEERAJO* aiduk maganar dazaka fadi bazan taba yimata mummunan fahimta ba Saboda haka kafadi maganar insha'allahu zanyi maka kyakkyawa fahimta, nan yafada mata komai gameda auren shida *"ZUBEE* tundaga farko harkar she.


Tabbas taji badadi aranta saidai kuma haka Allah ya kaddaraz sannan shidin ai mijin mace hudu ne don haka aiba'abun damuwa bane, jin tayi shuru yasa cikin sanyin murya yace Inna don Allah kiyi hakuri nayi biyayyane ga Ammi amma badan raina yanaso ba, kuma aure nada *"ZUBEE* bashi zaya hanani auren *"SAJEEDAH* insha'Allahu domin itace Zabin *ZUCIYATA.*


Murmushi tayi tace haba *SEERAJO* Ai wannan ba'abunda muwa bane don haka karka damu kanka, sannan kuma aikai din mijin mace hudune ko bayan ita yayar Sajeedun zaka iya kara auran wasu, Allah yabada zaman lafiya, sannan Inaso kazama Mutum me biyayya ga'iyayanka kajiko?..kanshi nakasa yace toh"Inna nagode sosai dakika fahimceni, sannan Inna yaufiyeda sati daya inata kiran layin *JEEDAH* bansamu ba yace toh" KO" lafiya?..cikin karfi hali tace lafiya lau wai wayar tace yafadi shiyasa ba'samunta yace ayya toh idan akwai layin da'ake samun ta abani tace toh"tareda mika masa wayarta tace ka duba akwai layin Kawu ta Labaran saika dauka, yakarba yacire lambar bai dadeba yayimata sallama yatafi.


๐Ÿ’˜๐Ÿ’˜***๐Ÿ’˜๐Ÿ’˜
Nijer
*SAJEEDAH* ce zaune afalo ita kadai kasan cewar Haj "Safara'u batanan itakuma "Zarah daga firasunyi barci itada "Sajeed shiyasa tafi toh" falo tazauna, yanzu kam tafara ga jiya da nijar, saboda abubuwan dake faruwa wayanda sunfarayi matayawa wayarta dagatasa chaji suje gidan kawu "Sammani sudawo anneme Waya ko" kasa ko" sama Ba'a ganiba,


sannan gawani irin nace mata da yaya Nasir yayi ran nan ma cewa yayi Waishi sonta yake, tab tafurta tareda cewa nikam aita *yah SEERAJ* ce, toh" me mazanyi dashi wanda kwata kwata 'da bi'unsa basu yimaniba mutun saimeneman mata gakuma shaye- shaye, shikuma "kawu yace satin nanzamu koma gida gashi har yau kwana uku da satin tawu ce amma bece mana komai ba,


Ni abunda mayafi damuna makaranta da'a nakoma sannan yanzu haka

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login