Showing 3001 words to 6000 words out of 48065 words

Chapter 2 - ZUCIYATACE HAUSA BOOKS COMPELET BY ESHAAT SMILER.txt

23 Jan 2025

3927

kihada masa" ruwan wanka sannan kizo kikai masa" abinci, *ZUBEE* tace toh" tareda mikewa tanufi shashin, nasa.


Ko sallama batayiba kawai ta kutsa Kai cikin dakin,



Yadaga Kai ya kalleta cikin (takaici shiga masa datayi daki ba sallama) yace keh!" bakida hankali ne dazaki shigo min daki ba sallama,
Cikin daure fuska yace waima tsaya maiki kazoyi dakina?...




Batace komai ba saidai ta tsurama kirjinsa ido, wanda yake cike da lallausan kashi bakikkir sai shekeki yaketa famanyi,
(kasan cewar yariga ya balle botur din rigarsa).




Ganin "inda take" kallo "ajikisa yasa yai Saurin Kama bakin rigarsa yarike gam, tareda da watsa mata harara yace keh! wai mene haka "Ina magana kinyi mani shuru?... sai wani kallona kike sai kace baki taba ganinaba.


Taturo baki gaba tace toh" ai "Ammice tace' nazo nahada maka ruwan wanka,


Yasake watsa mata harara yace oh" saboda ga kuturu ko?... kibari sai kifara hadawa kanki tukun Na sannan ki hadama wani, zakifata min adaki kosai na bata miki rai tukun Na?...


tace yah p...Da sauri yace dalla fita mun daki,
Juyawa tayi tafita sumu-sumu,


Da sauri yaje yarufe kofarsa tareda yin kwaf yace wawuyar yarinya kawai, sannan yacire rigarsa yadauki towel yashiga toilet domin yayi wanka.


Nasandai mai karatu zaiso yasan,

Wanene pilot *S* *A* *SaRDAUNA*
Wato Seeraj Abbas Sardauna shine asalin sunan sa, Amma abokansa suna kiransa da S A Sardauna,


Alhaji Abbas Sale Harka shine cikakken sunan Mahaifinsa, kafin yazama Sardaunan Minna, asalinsa bafullacen gwadan ne iyayansa Da kakanisa Duk yancan kauyan gwadane, Alhaji Sale Harka shine mahaifin Alhaji Abbas Sardauna Alhaji Sale yakasance hamshakin mai "Arzikine wadda yagada wurin iyayansa, Irin dukiyar Nance tada tsarkakkiyar wacce babu kazanta aciki, (ba irin dukiyar nan tayanzu ba wace kaida ganin wata dukiyar kasan bata Allah bace, Allah ya kyauta Amin)


Alhaji Sale Harka yakasace hamshakin Dan kasuwa, Wanda yake gudanar Da kasuwanci gari-gari




Tun bayan rasuwar kakaninsa da "iyayansa ganin kowa nasa yakare sai yaji gaba daya kauyan gwadan yafita "aransa,


Saboda haka Sai yadawo cikin garin Minna anan Basso yake zaune tareda iyalansa matarsa mai sunan Hajiya Amina amma suna kiranta "inna wuro sai yaransa guda biyu Alhaji Abbas Da Kuma Haj Rabi'atu,
(Kar mai karatu yaji itana kiran su Alh Abbas Da Hajiya Rabi'atu yayi mmk toh"ba abun mmk bane sunje makka so uku)


Alhaji sale Harka yacigaba da gudanar Da kasuwancinsa cikin kwanciyar hankali kamar yanda yasaba, kwatsam Ranan wata Laraban da iyalansa bazasu taba mantawa da itaba,




domin kuwa Cikin dare ciwon Kai mai tsanani Yakama Alhaji Sale Harka, hankalin "iyalansa yai matukar tashi ganin yadda yake shan wahala,


Da sauri Abbas yaje yafito da mota suka nufi asibiti saidai kash!! ,Kafin duk sukaiga isa Asibiti Allah yadauki ran Alhaji sale Harka (Allahu Akbar rai bakon duniya Allah kasa mucika Da imani ka kuma bamu ikon tashi da imani Amin)


DA sauri Abbas yaja birki ya tsaya saka makon jin abunda "Inna wuro take fada, wato innalillahi'wa'inna'ilaihinraju'una, yau maizan gani ni Ameenatu? Alhaji Mutuwa zakai kabarni,sai kuma tafashe da kuka maiban tausayi Hajiya Rabi'at kukan take Hakanan Alhaji Abbas yajuya kan motar zuwa gida yana kuka yana driving tabbas sunyi babban rashi.


Washagari "akai jana'idarsa aka kaisa gidansa Na gaskiya, Hakanan ruwa ta cigaba datafiya,


Yayinda Alhaji Abbas ya cigaba da kula da mahaifiyarsa da kanwarsa, yana kuma juya dukiyar mahaifinsa Cikin lokaci kankani Alhaji Abbas yazama shahararran Dan Business, lntenational Business yakeyi kuma abun yakar besa sosai saboda haka yaisuna sosai "acikin gida Nigeria,


"A wannan lokacin kuma tuni "Anjima dayima Hajiya Rabi'atu aure, tana zaune a unguwar
Mai tumbi damijinta.


*******************
Wata Rana Alhaji Abbas yaji labarin wani shahararran business man, "a Jordan "anyce yana bada kaya "akan farashi maisauki sunan mutumi Alhaji Seerajo,


koda Alhaji Abbas ya isa Jordan baisamu ganin Alhaji Seerajo ba, kasan cewar Alhaji Seerajo shahararran Dan business ne wani lokaci yana wuyargani Toh" dama yanada ya'ya uku duk mata kuma duk yasasu aharkar business din, saboda haka sai kawai Alhaji Seerajo ya hada Alhaji Abbas da babbar yarsa mai suna Raihana don sugudanar da business din,


haduwar farko Da Alhaji Abbas yayi Da Raihana yaji takwanta masa "arai, don haka bayan sun gama cinikin kayan,
Alhaji Abbas baiyi nauyin bakiba gurin fada mata cewa yana sonta ba,
Toh" Itama anata bangaren taji yakwan mata arai,


Toh"bayan takoma gida sai tafadama mahaifinta" abunda Alhaji Abbas yace gameda ita, Alhaji Seerajo ya tambayeta tana sonsa tace eh' yayi murna sosai dajin haka Amma Yace Raihana tabari zayasa aimasa bincike Akansa
Tace toh".


Alhaji Seerajo yasa kayi masa bincike "akan "Alhaji Abbas ankuma tabbatar masa cewa shi Mutumin kwaraine,


Saboda haka
Bayan kwana biyu sai Alhaji Seerajo yakira, Alhaji Abbas Yace masa yabasa Raihana don haka sai ya turo magaba tansa,




Ba'a dauki wani lokaci ba akai bikin Alhaji Abbas Da Hajiya Raihana aka kawota Nigeria, Alhaji Abbas yaso yahada Raihana da mahaifiyarsa "inna wuro, toh" sai "ita "inna wuron tace "a ah yaje yasata "adaya daga cikin gidajensa ita kam yabarta nan bosso, tareda masu aikinta saboda tafi sabawa danan din,
Toh" dama yanada wani gida "a tunga kuma duk Cikin gidajensa wanna yafi yatsari da kyau don haka sai kawai yakaita can,


Sukaci gaba dazama Cikin So DA kaunar juna, har Allah ya azirtasu DA Haihuwar Da namiji kyakkyawa dashi' Wanda za'a iya cewa yayi gadon kyaune ta Uwa Da Uba,


"Akasa masa sunan mahaifin Raihana wato *SEERAJO* yataso Cikin So dakaurar iyayansa, sunyi masa tarbiyya mai kyau, arzikin da suke dashi baisa sunbar
Sa ya lalaceba, tunda a wannan lokacin'ma tuni anba Alh Abbas Sardaunan Minna arziki kuma yakara habbaka sosai.


Tun *SEERAJ* yana primary school yakeda burin son zama Pilot, toh" bayan yagama karatunsa na Secondary sai kawai ya tattara ya koma Jordan, don yacigaba da karatusa acan, duk dacewa Alhaji Abbas bai so hakaba Dayaso yasashi Cikin business dinsa, toh" Amma yazaiyi tunda yaga dan'nasa burinsa kenan nason yazama pilot saboda haka sai be hanash tafiya ba,


Shiko *SEERAJ* koda yaje Jordan bai tsaya wasa ba, yamaida hankalisa sosai akan karatun dayajeyi, da taimakon Allah Dana kakansa Alhaji Seerajo ya kammala karatun sa, ya kumafito cikakke matukin jirgin sama tareda wasu yan Nigeria abun gwanin sha'awa, kuma abun mamaki duk acikinsu shine me Kara min shekarun, tunda alokacin shekarasa Ashirin da biyar,


ganin kwazansa yasa kamfani jiragen sama Na Jordan taso taukar shi' "Aiki,


Yace a ah subari yaje yafa yima kasar sa tukun'na,


Hakanan suka dawo gida Nigeria cike da nasarori, inda bincike yanuna cewa,
*SEERAJO ABBAS* *SARDAUNA,* shine Mutum Na farko a Nigeria daya fito kwararran PILOT kuma mafi karancin Shekaru,


nutsuwarsa DA kwarewarsa akan "aikinsa ne yasa cikin dan kankani lokaci yaisuna yazama shahararran matukin jirgin sama "anan Nigeria,


Wanda "ake matukar jidashi "a gida Nigeria. kai ba gida Nigeria kadai ba harda kasashen ketare, shekara uku yayi yana Aiki "anan gida Najeriya sannan yakoma Jordan, "inda yanzu haka yana Aiki neda kamfanin Jiragen sama Na Jordan,

yanzu ma yazo hutune shinefa suka nemi alfarma, yadauko masu hajjata
*SEERAJ* *ABBAS SARDAUNA KENAN*,


Wacece *ZUBEE* wato Zubaida Bashir, shine cikakke Sunan" ta Amma kawayanta suna kiranta *ZUBEE Bash,* ta kasance diya ga Alh Bashir Da Haj Fati, yaranta biyar uku mata biyu maza *ZUBEE* ce babba sannan Bashir Amma suna kiransa Abba saboda sunan babansu yaci
Sai Habeeba, Fa'iz" sannan Auta Fa'iza.
Haji Fati DA Haji Raihana Aminan junane sosai,


Alh Bashir ma'aikaci gwamnatine Wanda yake DA matsayi babba agwamnati, yana zaune a unguwan barikin sale Alh Bashir yawa data iyalinsa sosai ba'abunda suka nema kukarasa,


Haj Fati irin matan nan ne dabasa tsawa tawa yayansu" sannan kuma basason "a tsawata masu,"idan sunyi ba dai-daiba.


Shiyasa *ZUBEE* ta tashi Sangartatta ba'abunda ta iya amatsayinta Na ya mace komai saidai masu Aiki suyi mata hatta dasu undis dinta masu aiki ke wane mata, tun batayi wato ba Haj Raihana take daukar ta tajeda ita gidanta takwa biyu saboda tana matukar kaunar *ZUBEE* KO" don bata da yara dayawa ne oho" har *ZUBEE* tayi wayo tana zuwa dakan ta.


*ZUBEE* tagama primary da secondary school yanzu haka tana C O E ne, Zubee da *SEERAJ* dasuna shiri sosai wanda ita ke kirasa "yah S P duk da yanajin haushin rashin komai din da bata'iya ba tunda wani lokaci hatta DA ruwan Lipton idan yace tada famasa sai tace ita bata iyaba ,


toh" rashin shirin nasu yasamo "asaline tun zuwanta C o e, ta haduda bad friend sai taduki wata muguwar da'bi'a "tanayi ba tare da kowa yasani ba, wato Lasbiyan saidai kuma kuma duk Abunda kakeyi wata Rana sai asirinka yatonu.


"Akwai watarana *SEERAJ* yadawo gida sai bai iso kowa ba Amma sai ya ga dakin da *"ZUBEE* take abude, don haka sai yanufi dakin yana kwala mata kira har ya isa bakin kofar dakin Amma baiji ta amsa ba,


har yajuya zaya tafi sashin sa don "atunani sa barci takeyi, sai yace "ita wannan sarauniyar raggayen harda rufe kofama bazata" "iyayi ba mashiririciya kawai yai kwaf,


Bari Na rufomata" kofar yasa hannusa daninyar yajawo kofar kenan,sai yaji wani irin nishi DA sauri yanura kofar don a tunani sa *ZUBEE* ce' batada Lafiya saidai "Abunda yagani ne yasa yaisaurin jawo kofar Da karfi,


Yayin da yai mutuwar tsaye domin kuwa *ZUBEE* yagani "itada kawar Nusee tsirara suna aikata masha'a",(wa'iyazubilah) sai salati *SEERAJ* yake ta faman zubawa yakai kusan minti biyar "a tsaye sai zufa yake Amma har zuwa wannan lokacin basu"fito ba,


hakan ne yanuna masa cewa wato ma basu"san yagansu" ba, don haka sai kawai yafara bugun kofar Da iyakacin karfi sa yana fadin Dan Ubanku kufito kona shigo na illata yarinya Ashe Ku yan'iskane?...


DA sauri suka Saki junansu tare da durowa daga gadon sai maida nunfashi suke, yayinda kowace tafara rarumar kayanta tana sawa,


Bayan "sunsa kayan sai sukayi tsaye cirko-cirko suna" kallon juna, itakan *ZUBEE* kirjinta sai dukan tara-tara yake, itako Nusee ba Abunda yada meta "asalima haushin *SEERAJ* taji, kawai suna tsaka dajin dadinsu yazo yakatse masu,


Nusee ta kalli *ZUBEE* tare DA yin kasa da murya tace amma "yah P S din'na ya kwafsa, mana wallahi KO release Mutum baiyiba tsaki taja mtsww.


shikam *SEERAJ* jinsu shuru yasashi kuma buga kofar da karfi, yace' baza kufito ba sai nashigo na karya yarinya?....,


sum-sum suka fito *ZUBEE* tana gaba Nusee na biye Da ita" cikin zafin nama *SEERAJ* ya finciko *ZUBEE* ya shara mata Mari yasake shara mata sannan ya tureta tafada kan'kushi,


Nusee zata gudu ya finciko ta itama yashara mata mari hada duka,
yace tabar gidan nan yanzu-yanzu kuma idan yakara gani kafarta "a gidan nan saiya karya ta,
Aiko Nusee a 360 tabar gidan.


Tundaga wannan lokacin sai *SEERAJ* yafita Harka Zubee saboda wani irin haushinta yakeji.




Bayan faruwar haka Da kwana biyu, da misalin karfe goma Na Safiyar Lahadi kasan cewar ba'aiki don haka *SEERAJ* yana gida, suna zaune a parlor shida Ammi suna kallo,


Sai ganin *ZUBEE'* sukai Jaye DA troling bag dinta, Ammi ta kalleta tace ke! kuma Lafiya "Ina zakije da bag?.. *ZUBEE* tace gida zantafi Ammi tazaro ido tace shine zaki tafida bag din kayan ki duk? tace "eh tace hala anyi miki wani abune"? da sauri ta kalli *SEERAJ* Wanda hankalin sa yana gurin kallo, tace a a" abunda akai Mani zanje nedai na kwana biyu.


Ammi tace toh" shikenan da motarki Zakitafi? tace "eh, toh" kice Ina gaida "Haji Fati, tace' toh" taja troling tare Da cewa "yah P S sai "anjima, ba tare da ya kalleta ba yace mujima dayawa.


Bayan *ZUBEE'* tafita sai Ammi tace My young pilot, yace' na'am my Ammi tace wata alfarma nakeso "kai mani?..


Yai murmushi tare da kama hannuta yarike yace' My Ammi, "ai tsakanin Na Da ke" babu "alfarma saidai Umarni,


Saboda haka ki" bani Umarni kawai sai nikuma Nacika miki shi" muddun be sabama "addin Muslim ba.


Tayi murmushi tace be sabama "addini ba, saida are sure zakayi Mani KO"me nace? yace yes my Ammi am sure zanyi makishi insha'Allahu .tace toh" sonake ka auri *ZUBEE,*




Wani iri zufane yaji yajikasa cikin lokaci kan-kani tamkar yahadiyi Karin kunama, "a hankali ya daga Kai ya kalleta Da idunun sa dasukai jajir yace...?






Kubiyoni
.


A




馃挊 ZUCIYA TA CE 馃挊
Tare




Alkalamin




鉁嶐煆�




馃挊 LUFHAT CE馃挊
[8:26AM, 2/20/2018] 鈥�+234 902 288 0912鈥�: 馃挊馃洬馃挊馃洬馃挊
馃挊馃洬馃挊馃洬馃挊
馃挊馃洬馃挊
馃挊


馃挊ZUCIYATA CE馃挊
_Based on true life story_
馃挊馃洬馃挊馃洬馃挊
馃挊馃洬馃挊馃洬馃挊
馃挊馃洬馃挊
馃挊


(Labarin Sarkakkiyar Soyayya)


3鈨�


WRITEN BY


馃挊AMEENAT UMAR FARUQ馃挊
OR
馃挊(MEENAT)馃挊




*WANNAN PAGE* *DIN*
*DOMIN KUNE* *YAN'UWA RABIN* *JIKINA,*
*AWWAL(baban walida)*
*KHADIJAT (Aunty)*
*AISHAT (Maman* *Fadila)*
*BALKISU (Maman jafar)*
*MUSTAPA (Musty)*
*ALKASIM (Malam)*
*SALISU (Kawu)*
*IBRAHIM (Himu)*
*MUSA (Daddy*
*ABDUL-QADEER(kure)*
*NASEER(Man Nas) HABIBA AND*
*FIDDAUSI (Last Born) Allah yakara mana dankon ZUMINCI Ameen*






-----------------------------------------
*_庐PEN WRITERS ASSOCIATION_*


*_PEN:THE STRONGEST WEAPON_*
----------------------------------------






*_only the exquisite and whizkid writers are opportune to be writers_*






鉁嶐煆�






My Ammi! Sai kuma ya sunku yar dakanshi kasa, ko" kadan *SEERAJ* be taba tsammanin abunda Ammi zata ce masa kenan ba.


"a ransa ko" fadi yake meyasa my Ammi zatayi masa haka? meyasa zatace ya auri *"ZUBEE*
alhalin bai taba jin *son* *"ZUBEE* da aure acikin zuciyar sa ba KO" dai-dai da kwayar zarra ba,


Shin meyasa my Ammi tayi tunanin *"ZUBEE* tazama abokiyar rayuwar sa? *ZUBEE* da halayyarta tabi'arta kwata-kwata basuyi masa ba,


Sai tambayoyi yaketa zubawa kansa" Amma kuma yakasa bakan'nasa amsa, can wata zuciya tace masa tabbas *"ZUBEE* batada da Halayyar kwarai Amma kuma dole ka aureta"KO" don farin Cikin my Ammi.


"Itakam Ammi dataga yayi shuru sai tafara tunani KO"
bazaya iya auran *"ZUBEE* ba?..


Ganin haka yasa sai "ta kwantar da murya kasa tayi kalar tausayi, tareda kallon sa" tace my young pilot baza Kai Mani wannan alfarman ba KO"?


"A hankalin yadaga Kai ya kalleta" tareda yin wani irin murmushi Wanda kana ganinsa kasan Na dole ne,


Yace' My Ammi I already told do you tsakanin mu babu alfarma ba sai dai Umarni KO?..


Ta gyeda Kai alamar "eh yace toh" kin bani Umarni nikuma Zan cika maki shi insha'Allahu, Zan "auri *"ZUBEE* "indai hakan shine farin Cikin ki I will married her for your sake.


Farin cikine me tsanani yarufe Ammi Wanda yasata rungumesa" ba tareda kulada halinda yake" ciki ba, tace nagode! nagode!! nagode!! my young pilot Allah yabaka Wanda zai saka" farin Ciki kamar yanda kasani,


Ta mike tana cewa bari nakira "Haj Fati nafada mata wannan abun farin Ciki kafin Abbin ka yadawo.
Bin bayan ta yai da kallo har saida tashiga daki,


Sannan yarufe idosa" tareda sa hannun sa" a dai-dai gurin da zuciyar sa take bugawa, yace my "Ammi *"ZUBEE* zata mallakeni a matsayin mijin "auran ta kamar yadda kike San hakan ya kasance, saidai Am sorry to say "my Ammi *ZUCIYATA CE* "Zubee bazata taba mallakar taba, saboda *ZUCIYATA* banata bane domin inaji ajikina ma mallakiyar *ZUCIYATA* na nan tafe,
A hankali yamike jiki ba kwari yanufi daki.


馃挊馃洬馃挊馃洬馃挊
. 馃挊馃洬馃挊
馃挊
Cikin lokaci kan-kani magana ta watsu acikin dangi kowa yai farin ciki musamman ma iyayan yara mata wato Ammi DA Haj Fati,


suma iyayan maza sunyi farinciki kwarai da gaske kasan cewar akwai fahimtar juna sosai tsakanin Alh Abbas Sardauna da Alh Bashir,


Haka abun yake "abangaren *"ZUBEE*sosai take farinciki itakam dama arayuwar ta babu mutumin da yake birgeta irin Seeraj
toh" sai Kuma gasi zai zama mijinta,


murna "takeyi sosai KO" bakomai itakam taciri tuta Mutum kamar *"SEERAJ* ga kyau ga ilimi kudi matsayi, yanzu fa shine young pilot of All Africa Kai! "ai itakam ta tserema sa'a,


Duk da cewa yanzu bata jin wani feeling Da namiji saboda lesbian din datake wa'iyazubilah,(Allah ya shiryamu Amin) amma kam tana jin farin cikin dazata zama matarsa"

Saidai wani lokaci kuma idan ta tuna daganin da *SEERAJ* ya tabayi masu" itada kawarta "Nusee sai taji tsoro yaka mata,saboda tundaga wannan lokacine tafahimci yana jin haushinta sosai,


Ba'a dauki wani lokaci ba akai baikon Seeraj Da *ZUBEE* shi Kuma buki sai tagama C O E din ta,


Akwana atashi bawuya agurin Allah gashi yanzu sauran one year *"ZUBEE* ta gama karatun ta sai Ashe bikin wannan kenan.


*CIGABAN LABARIN*
*******//****//******
A hankali yafito daga toilet din yana daure da towel "akugun sa, hannun sa Kuma rike da wani karamin towel din yana goge lallausan kashin kasan,
Cikin nutsuwa ya karasa
Gaban dressing mirror yai tsaye yana karema kansa kallo ya dauki kusan 5mint, sannan yafara shafe shafensa," goganan shafa can fesa nan saidai yadauki tsawon wani lokaci sannan yagama,


Wedrof yanufa yabude wata ash din jallabiya mai gajeran hannu yadauko yasa,


Agogon dake man'ne jikin bangon daki ya kalla yanuna masa 9:40AM,yaja dan gajeren tsaki mtsww tareda cewa I want eating something sannan yanufi hanyar fita,


A parlor ya iske Ammi tana kallo zama yai kusada ita tareda cewa sannu da hutawa my Ammi,


Murmushi tayi sannan tace yauwa sannu da hanya kana bukatar wani abun'ne?


Murmushi yai shima tareda Shafa lallausan kashin kansa yace my Ammi yinwa nakeji akwai abinci ?


Tace sosai ma kuwa "ai already nayi maka favorite food kin ka,


da sauri yace my Ammi sakwara? tace yes ni nai maka shi da kaina l know baka iyan ci abincin kowa sai nawa shiyasa nai maka"


yanan akicin bari *"ZUBEE* takawo maka sai tafara kwalama Zubee kira, " Zubee! "Zubee!! "Zubee!!! daga can ta amsa ma'am Ammi gani nan zuwa,


tace Ammi gani, yauwa tafi kici kidauko wa yayanki abinci sa" tace toh"

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login