Showing 3001 words to 6000 words out of 33266 words

Chapter 2 - YAN UBANCI COMPLET BOOK By Maman Afrah.doc

ne basu da wani banbanci, dan ko d'inki Ishalle za ta yiwa Hindatu to tare take musu da Ikilima kai ko da wani abu ne na ci za ta baiwa Hindatu to tare za ta raba musu da Ikilima ,wanda ba haka bane a b'angaren Kande dan ko Hindatu tana tsaye tana kallon abu suna ci ita da Ikilima to Kande na zata tab'a baiwa Hindatu ba ko da kuwa Hindatun za take kuka amma Kande ba za ta tab'a Hindatu abun ba.


Wata ranar asabar ne da yammaci Ishalle tana hura wuta domin ita ce da girki,bayan ta hura wutar ta koma can kan tabarmar da take zaune tana goga d'anyar kub'ewa ,Hindatu name gefenta a zaune tana wasan k'asa Kande kwa tana d'akinta ita da Ikilima kawai sai ganin Ikilima Ishalle ta yi ta fito hannunta a b'oye a bayanta murmushi Ishallen ta yi ta ce

"Ikilima zo ki yi wasa ke da y'ar uwarki mana"

"Ni ba zan yi wasa da ita ba kuma ni ba y'ar uwata bace kuma Ummata ta ce kar in so ta in tsaneta" Ikilima ta ce tana kumbura baki irin na maras kunya.

"To ai shikenan tun da baya zaki yi wasan ba"

"Ni kwa Ummina ta ce in ke son ki kuma ke y'ar uwata ce komai na samu in ke sammiki "Hindatu ta fad'a tana yiwa Ikilima murmushi.

"Ke ni bana sonki "Ikilima ta ce tana harar Hindatun.

Ummi Ishalle ce ta d'ago kai ta kalli Ikilima domin ji ta yi maganar ta tab'ata ta duk da cewa a lokacin Ikilima tana da shekara tara amma hakan bai hana Ummi Ishalle ta ji zafin maganar ba, sannan kuma da ta dubi fuskar Ikilima sai ta ga tarbiyar b'ata rai alamar da gaske take.Kau da kai ta yi gefe ta tashi ta sanya silifas d'inta za ta je ta iza wuta.

"Kema fa ba uwata bace sabo da ba ke ki ka haifeni ba" Ikilima ta fad'a tana murgud'a baki.
Tsayawa Ummi Ishalle ta yi da fifita wutar ta tsaya tana kallon Ikilima yadda take magana kamar wata uwar mata duk wani manyance yarinya k'arama ta iya sabo da koya mata da uwarta ke yi.juyawa ta yi ta k'ara itace ta duba tukunyarta juyowar da za ta yi kawai sai jin k'aran duka ta yi zaro idanu Ummi Ishalle ta yi ganin wata murd'igegiyar bulala a hannun Ikilima da ta zabgawa Hindatu a kan ta,kafin Ummi Ishalle ta k'araso Ikilima ta kuma zabga mata a gadon baya nan take Hindatun ta fad'i k'asa tana kuka da murza wurin dukan.

"Ke Ikilima wannan wane irin duka ne me ma ta miki da zaki daketa da wannan bulalar? "Ummi Ishalle ta ce tana k'arasowa wurin.

"An duka d'in kuma ai ba sai ta mini wani abu ba tun da ni ce gaba da ita ,kuma ita ba y'ar d'akinmu ba ce"

Ummi Ishalle bata kuma bi ta kan Ikilima ma ba sai ta nufi kan Hindatu ta d'aga ta, sosai yarinyar ke kuka har shid'ewa take jijjigata Ummi Ishalle ta shiga yi tana lallashinta kama rigar Hindatun ta yi ta d'aga abinka da farar fata har wurin ya yi jajawur ga bird'in nan ya fito wata k'wallar tausayin y'ar tata ne ya taru a idanunta haka kawai bata ji ba bata gani na an duketa dukan da ko ita da ta haifeta bata tab'a mata ba.

"Kin min dai -dai ikily haka nake sonki ai duk wanda yace ya ci tuwo da mu to wallahi miya ya shahara, ba dai kin had'a Y'AN UBANCI da y'ata ba to kwa wallahi kin had'a kan ki da jaraba dan ki sa a ranki cewa baki ga komai ba dan yanzu aka fara kuma ba, a gama barbad'a wai an ba gozoma tuwo a hannu ta ce ba, a gama haihuwar ba ai"Umma Kande da ta fito daga d'aki ta fad'a tana kama hannun Ikilima ta rik'e.

Baki sake Ummi ta tsaya tana kallonta mamaki gaba d'aya ya gama lullub'eta duk da ta san halin Kande amma yau abin ya d'aure mata kai kasa cinye abin da ya zo ranta ta yi ta ce.

"Haba ke kwa Ummar Ikilima bai kamata ace kina yin haka ba ai ,kalli bayan yarinyar nan ki ga bird'in da Ikilima ta mata kuma ki ce ta kyauta? " Ummi Ishalle ta k'arasa fad'a tana nuna mata Bayan na Hindatu.

mtssss ta ja wani wawan tsaki sannan ta ce " hmmm lallai Ishalle ki ke ki iya shege to bari ki ji in fad'a miki gaba tsakanin Ikilima da Hindatu yanzu aka soma ko kuma ma in ce ba, a soma ba dan wallahi babu afuwa babu ragawa a tsakanin mu da ku, yadda ki ke kishiyata to Hindatu tafi kishiya a wurin Ikilima, kuma in dai dukane baki ga komai ba dan gaba tafi baya yawa dan abin da za ta mata nan gaba sai yafi wannan dan ki sani ma yanzu ma ni na turo ta ke hatta bulalar ma ni na bata" ta fad'a tana turo d'ankwalinta gaban goshi.

Ummi Ishalle da ta sanya hannu a hab'arta tana bin Umma Kande da kallo ta sauke sansanyar ajiyar zuciya ta ce
"Allah kyauta to Allah kuma ya baki hak'uri"

"Wuhuhu da hak'urin ta mutu sadakar nawa kike ka samu"

"Ni dai na san Hindatu ba komai take yiwa Ikilima ba,amma dai duk da haka zata k'ara kiyayewa da shiga harkarta "Ummi Ishalle ta ce tana kama Hindatu ta d'agata tsaye.

"Hehehehe ai dole a kira akuyar sirika iya"Umma Kanden tace tana juyawa rik'e da hannun Hindatu suka shige d'aki.

Tun daga wannan ranar Ummi Ishalle ta sanya Hindatu take kiyaye duk wani abu da zai kawo sab'ani tsakaninsu da Ikilima duk da dama ita Ikilimar ce mai laifi da kuma saurin hannu. Ummi Ishalle ta baiwa Malam Buba shawara akan ta ya taimaka ya sanya Ikilima da Hindatu a makarantar boko sabo da su samu ilimin zamani duk da ita Hindatu tana zuwa makarantar allo da Malam amma Ikilima sam bata zuwa makarantar allon Malam ya yi fad'an ya gaji kullum uwarta ke hanata zuwa ta gwammace take d'ora mata tallan gyada da alkaki.Malam Buba ya amince zai sanya su a makarantar boko domin shima baya so su taso a haka ba.

"To munafuka algunguma wato shawara ki ke bashi akan a sanya su a boko ,to wallahi ba dai y'ata ba dan ban ga wanda ya isa ya sanya min y'a a bokoko a wuta ba sai dai ke a kai taki y'ar ban da renin wayo ke kin san ma hanyar makarkatar bokon dan ba makaranta ba ce makarkata ce dan haka babu in da za, a kai ta wallahi "cewar Kande da ke tsaye bakin k'ofar d'akin Malam dama tana tsakar gidan amma kunnenta a kan maganar da su ke yi.

"Haba Ummar Ikilima yanzu abin arzik'i ma sai ya zama na tsiya ,dan na ce a sanya su makarantar boko shi ne ya zama lefi kuma da ki ke maganar ni ban je boko ba ai zamani mu da na su akwai ban banci amma in maganar ta b'ata miki rai ki yi hak'uri "cewar Ummi Ishalle.

"Ke ki ka sani in ma menene dai ba in da Ikilima za ta je, makarantar allo ma bata je ba bare wata boko"

"Ya isa haka Kande wai ke me yasa kullum bakya so a zauna lafiya, yanzu menene lefinta dan ta ce a sanya su makaranta kamar wacce ta ce a sanya su a gidan rawa, tukunna ma ke fa ba da ke ake maganar ba"Malam Buba ya ce cikin b'acin rai.

"An fad'a d'in idan ma ba da ni ake maganar ba ai da y'ata ake sanyawa a maganar ,kuma da ka ke maganar bana son zaman lafiya ai zama lafiya k'auyanci ne, sannan ni wallahi da a sanya Ikilima a makarantar boko gwara a sanyata a gidan rawar ko banza y'ata ta yi suna ana nunata a talabijin "ta k'are maganar tana tafa hannu.

"To shikenan Allah shiryeki ya shiga lamuranki in dai kuma kina ganin hana Ikilima zuwa makarantar cinyewa shikenan dama ni ba isa na yi da ke ba sai abin da ki ka ga dama kike yin, amma ki sani wata rana za ki yi da ma sani"yana gama fad'ar haka ya tashi ya yiwa Ummi Ishalle sallama yaran fita wurin almajiransa.




Hindatu ta shiga makaranta kuma alhamdulillah tana k'ok'ari sosai, dan duk da makarantar k'auye ce amma hakan bai sa malaman makarantar suna yin ojoro ba. Dan haka sai ya zamana Hindatun ta k'ara sanya abun a rai kullum tana karatu sannan da yamma ta tafi makarantar allo ta kofar gidan su. Ikilima ma kwa na arabi ba boko sai shegen yawan tsiya da fad'ace -fad'ace a gari gashi idan ma Ummarta ta d'ora mata talla sai dai ta kawo kud'in ba dai -dai ba amma hakan bai sa Ummarta ta tsawatar mata ba sai ma ta d'akko sabon salo na koyawa yarinyar kaiwa tallan gurin maza a cewarta sun fi siya dan wani lokacin ma har su kan yi juye ko su ba da kud'in fiye da na kayan ,hakan yasa yarinyar ta ke kai wa talla shago da duk in da ta san maza suna zama ganin tana samun kud'i fiye da na kayanta yasa take kai musu dan ba wai haka kurum suke k'ara mata kud'in ba suna yin wasan banza ne da ita dan tsabar mulmulata da maza ke yi yasa ta fara k'irgen dangi ita kwa uwar ba ruwanta in dai zata ta kawo mata kud'i to babu ruwanta da me zai faru wanda hakan bata san kuskure bane babba amma ita ko a jikinta Ummi Ishalle ce ke k'ok'arin ganar da ita amma ta mata rashin mutunci, shi kwa Malam da yake a shanye sai kallo da ido.Haka rayuwa ta cigaba da kasancewa har Hindatu ta kammala karatun ta na primary school ta shiga junior, bayan ta kammala Junior School sai kawai ta maida hankali kan karatun arabi dan dama iya Junior School ne yanzu haka ta kusa ta yi saukar Alqur, ani mai girma. Ikilima ma kwa sai dai gyaran Allah a lamuranta dan yanzu ta zama bata da wasu abokan huld'a sai maza ta je su mammatseta su bata kud'i ta yi harkar gabanta, dan ma dai Ummi Ishalle tana mata nasiha idan ta ga Ummarta ba ta nan duk da ba wani saurarenta take yi ba dan ko tana mata fad'a waya take dannawa dan yanzu wayoyinta har biyu da samarinta su ka siya mata dan haka ba ta ko bi ta kan Ummi Ishalle ba ta tashi ta shiga d'aki abin ta.

"Allah kyauta ya shirya mana zuri, a baki d'aya "cewar Ummi Ishalle itama ta nufi d'akin malam za ta gyara.

Washe gari da safe Hindatu na sharar tsakar gida dan gaba d'aya ita ke share ko ina ta wanke kwanuka, tana cikin sharar Ikilima ta fito daga d'aki da wata riga mai k'aramin hannu sai zani da ke daure a jikinta tsayawa ta yi tana k'arewa gidan kallo tana wani yatsina.

"Kai ni daman ba a gidan nan aka haifeni ba wlh me za,ayi da talauci gida duk yab'en kasa ga wasu dabbobi su yi ta damunka da kuka su hanaka barci mai dad'i,hmmm gaskiya ni ba na son talaici" Ikilima ta fad'a tana wani kama tsantsa.Ummi Ishalle ce da ke baiwa dabobi ruwa ta juya ta kalleta ta jijjiga kai cikin takaicin hali irin na Ikilima duk da ta san ba laifinta bane laifinta laifin mahaifiyarta ne dan gaskiya akwai k'arancin tarbiya a tattare da Ikilima.
Hindatu kwa da ke shara ko d'ago kai ba ta yi ba bare ta kalli Ikilima shararta kawai ta ke a nutse, dan ita har ga Allah tausayin y'ar uwarta ta ta ke yi dan gaba d'aya rayuwarta babu wani hali mai kyau sai dai addu, a kawai Allah shiryeta.

"Ke zo ki kwalfa min ruwa ki kai min bayi zan yi wanka"Ikilima ta ce rai b'ace dan ganin jelar gashin Hindatu da ya fito tana k'asan d'ankwalinta gashi har tsakar bayanta amma ita nata ko parking bai yi sai dai ta je a mata k'arin gashi.

"Babu ruwa a gidan yanzu za,a kawo sai dai ki jira idan an kawo komai zuba ki kai sai ki yi wankan "Hindatun ta fad'a tana had'e rai itama.

"Ke ni ki ke fad'awa haka da me zan ji, da rashin ruwan ko da maganar ki in banda ma talauci ace ruwan wanka ma sai ka jira an kawo yanzu da a birni aka haifeni ruwan wanka ma sai dai in kunna famfo in d'auka, wlh duk laifin Umma ne da ta yi aure a k'auye"ta fad'a a zafafe.

"Ke Hinde ki ke ko Hindu wato har wuyanki ya yi k'warin da za ki fad'a mata wannan maganar bayan kin san gaba ta ke da ke ko dan ba tarbiya gareki ba, ba, asan girman na gaba ba amma ba laifinki ba ne laifin gyatumarki ne da ba ta koya miki bin na gaba ba"Umma Kande da ta fito daga d'aki ta fad'a tana kamo Ikilima ta rungume ta da hannu d'aya.

"Ki yi hak'uri Umma walllahi ba haka bane, kawai dai na ga kullum ni ta ke sanyawa in kai mata ruwan wanka amma iya biyayya ai ina mata "Hindatu ta fad'a a sanyaye dan ba halinta bane raina babba duk kuwa da tana jin ciwon abinda su ke yiwa Umminta amma sai Ummin ta ke tausarta dan bata tarbiyar da ta dace.


"Kande wai dan Allah me yasa ku bakwa son zaman lafiya ko kad'an, kullum ace da tashin hankali ake karyawa a gidan nan duk da ba kulaku mu ke yi ba amma sai kun tarko abin da zai zama b'acin rai, yanzu menene laifinta dan ta ce in an kawo ruwan ta zuba da kanta duk kuwa da ita ke zuba mata ruwan kullum ko da kuwa makaranta za ta tafi sai ta zuba mata amma ba ta tab'a gode mata ba, amma yau ki ke cewa ban bata tarbiya ba,shin har kin kasa gane Hindatu tana da tarbiya ko ba ta, ko kuma kin kasa gane ke ce baki baiwa Ikilima tarbiya ba" Ummi Ishalle ta ce tana kallonta dan abin da ta fad'a ya sosa mata rai kawaici da kauda kanta ya sa Kande tana ganin kamar tsoronta take, wanda ba haka bane kawai dai ba ta son tashin hankali sannan kuma duk abin da za su yi shi y'ay'ansu za su je su aiwatar a gidajensu wanda ita kuma bata fatan haka.

"Lallai Ishalle ni ki ke fad'awa son ranki to wallahi kin d'akko ruwan dafa kan ki, kuma Hindatu ce marar tarbiya ba Ikilima ma ba kuma wallahi har gobe a matsayin mak'iya ku ke a wurinmu dan Y'AN UBANCI tsakanin Hindatu da Ikilima yanzu aka soma ko ma in ce ba,a soma ba"Kande ta ce tana girgiza jiki.

"In dai Y'AN UBANCI kar ku daina ai ba kan mu ba aka soma ba za, a gama ba kuma a kan mu, tunda Allah ya had'asu UBA d'aya to har gaban abada ubansu d'aya ne"Ummi Ishalle ta ce tana baiwa Hindatu umarnin shiga d'aki itama ta mara mata baya, dama Malam yana wurin almajirai.

"Haba Umma wai ma me yasa ki ka auri wannan Baban namu, baki auri mutum saurayi ba kuma ki sa shi ya miki alkawarin ba zai miki kishiya ba kin ga d'aya yanzu barin ni da Y'AN UBA, amma ga talauci ga zaman k'auye .

"Yi hak'uri y'ar lelena akwai dalilin da ya sanya na auri babanki, sabo da tarin kadarorin da ya tara kuma mu kad'ai za mu ci ba tare da wadannan y'an bak'inciki ba, kin ga idan mu ka mallaki kadarorin sai mu je binni mu sayi tanfatsetsan gida" kande ta ce tana washe baki kamar dai abin ya faru ma.

"Yauwa Ummana ashe akwai abin da ki ka shirya mana "Ikilima ta fad'a tana k'ank'ame Kande.

"Haka ne sha kuruminki komawa binni kamar an yi an gama kuma ko ba mu koma binni ba a binni za ki yi aure, dan sai dai wasu su

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login