Showing 30001 words to 33000 words out of 56708 words

Chapter 11 - WASIKAR JINI! COMPLETE Book By Abdulaziz Sani Madakin Gini.txt

sulale kasa sumamme ba.
Koda jin wannan batu sai waziri ridwan ya
kwarara uban ihu cikin tsananin takaici.
Al'amarin da yasa gaba dayan mutanen dake
cikin gidan nasa suka firgice kenan suka fita daga
haiyacinsu.
Waziri Ridwan ya dubi shugaban
dakarun a fusace yace kai shasha ba aljana bace
sarauniya Lazwara ce mai mulkin birnin arnan
daji.Itace daya babbar abokiyar gabata ta biyu
wacce take son taga
bayana kuma a shirye take ta taimakawa su
yarima zainur su rigani mallakar wasikar jini.
Koda jin wannan batu sai shugaban dakarun yace
ya shugaban ka bani dama ta biyu ina mai
tabbar maka da cewa a lokacin abinda bai wuce
kwanaki goma ba lallai zan kawo maka wannan
taswira idan kuma
na kasa zan dawo maka da dukkan kudadenka
daka bamu.Koda jin wannan batu sai waziri
ridwan ya
bushe da dariyar farinciki yace idan kuwa ka
kawo mini wannan taswira a cikin kwanakin daka
fada
zan sake baka kudi ninkin wadanda na baka
kuma nayi maka alkawarin cewar idan na zama
sarkin kasar na
sai farin ciki ya lullubeka.
Shugaban dakarun sojan hayan wanda ake kira da
suna Uraidu Bin Hamsar ya mike tsaye zumbur
yana mai dora tafin hannunsa na dama bisa
kirjinsa yace,na rantse da darajar gemun ubana
zanje nayi gagarumin shiri don cika wannan
aiki naka,kuma ina mai tabbatar maka da cewa
lallai nan da cikar kwana goma zanzo maka da
wannan taswira ta kowanne hali.Koda gama fadin
hakan sai sadauki Uraidu ya mike tsaye ya fice
daga cikin falon shi kuwa waziri ridwan saiya
bishi da kallo yana mai kyakyata dariyar farinciki
tamkar wasikar jini ce ta fado hannunsa.
.
Al'amarin su Yarima Zainur kuwa lokacin da suka
kutsa cikin kasuwa su uku suka gama siyayyar
da zasuyi sai suka shiga wata rumfa suka zauna
domin su huta kuma suci abinci saboda a
wannan lokaci
rana ta take kuma duk su ukun sun kamu da
yunwa.Nan take yarima yazid yasa hannu a cikin
aljihunsa domin dauko kudi ya baiwa Ardadu yaje
ya siyo musu abinci amma sai yarima Zainur yayi
wuf ya ruke hannunsa yace,Haba yaza ayi bako
ya ciyar da dan gari ai nike da hakkin ciyar daku.
Koda gama fadin hakan sai yarima zainur yasa
hannu cikin aljihunsa ya fiddo da kudi ya bawa
Ardadu.Cikin hanzari ardadu ya karbi kudin ya
nausa cikin kasuwa domin siyo irin abincin da
suka umarceshi da
siya.
Saida Ardadu yadan bata lokaci kadan yana yawo
a cikin kasuwar sannan yaga shagon siyar da irin
abincin dasu yarima zainur ke bukata,cikin
hanzari ya shiga shagon ya bayar da kudin aka
bashi.koda ya fito daga cikin shagon da niyar ya
koma can tsakiyar kasuwa inda su yarima yazid
suke sai yaga wadansu samudawan karti su hudu
sun sha gabansa.
Koda Ardadu ya karewa dakarun
kallo sama da kasa yaga cewa sun cika zaratan
dakaru masu tarwatsa maza a filin daga ya
tabbatar da cewar ba zai iya dasu ba sai ya
dubesu yace,me kuke bukata daga gareni?
Koda jin wannan tambaya sai babban cikinsu ya
daka masa tsawa yace Kai Ardadu shin arziki
kake nema ko tsiya?
To indai arziki kake nema kazo muje wajen
shugabanmu ka gana
dashi.Koda jin wannan batu sai Ardadu ya dubi
katon cikin zakuwa yace maza ka kaini wajen
shugaban naku.Nan take dakarun suka wuce
gaba yana biye dasu sukayi wani bangare daban
na
kasuwar har suka isa wani katon gida,kai tsaye
kartin hudu suka shige cikin gidan mai surkuki
Ardadu na biye dasu amma zuciyarsa sai daka
take duk da cewa shi mutum ne wanda ya saba
zama a daji yana tare ayari na fatake yanayi
musu fashi.
Ba komai ne yasa tsoro ya darsu a cikin
zuciyarsa Ardadu ba face ganin samudawan
dakarun dake cikin wannan gida dauke da
miyagun makaman yaki kuma
da ganinsu kasan cewa baki ne ba yan garin
bane,kuma yadda ya shigo cikinsu shi kadai din
nan
idan suka so zasu iya cinyeshi danye ba tare da
wani sami koda tsoka daya ba.
Haka dai aka cigaba da tafiya da Ardadu har aka
iso wani daki dake can karshne gidan sannan aka
bude musu kofa suka shiga,suna shiga yayi arba
da wani murgujejen
katon mutum zaune bisa wata babbar kujera ta
alfarma yana shan giya ga kuma gasasshen rago
a gabansa wadansu mata sunyi shigar banza
guda biyu suna yanko naman suna sa masa a
baki yana
ci yana rungume su yana kyalkyala dariya.Koda
katon yaga an shigo da Ardadu sai ya daga
hannunsa yabada wata inkiya
.Nan take kowa ya fice daga cikin dakin ya
zamana cewa an barsu su biyu kacal a cikin
dakin wato dagashi sai Ardadu.
Kawai sai murgujejen katon mutumin ya dubi
Ardadu cikin murmushi yace lale marhaban da
tsohon dodon fatake na dajin Aryas,
Ardadu bin Kaumar. Sunana
Uraidu bin Hamsar.
Koda Uraidu yazo nan a zancensa sai Ardadu ya
dubeshi cikin kaduwa da mamaki yace yaya akayi
kasan ni?
Uraidu yayi murmushi a karo na biyu yace ai na
dade da saninka domin kuwa sana'armu daya ce
wato fashi a daji daga bayane tun kafin ka hadu
da yarima yazid
nima tawa likkafar tacigaba na hadu da waziri
Ridwan na wannan birnin da muke ciki ya daukeni
akan makudan kudaden da ban taba tara
kamarsu ba a tsawon shekaru goma sha daya
dana keyin
fashi a cikin dazuzzukan dake can nahiyarmu.
Abinda na kasa ganewa akanka yanzu shine
mece ce ribarka da kake bin yarima yazid?
Mutumin da baya iya baka koda kyautar dinare
goma.
Baya iya tsinana maka komai face kyautar abinda
zaka ci da yar suturar da zaka sanya.Akan wane
dalili zaka yarda a rude ka da wani sabon addini
wanda babu komai a
cikinsa face talauci?
Koda Uraidu yazo nan a zancensa saiya mike
tsaye yaje ya dauko wata katuwar jakar fata ya
cirota ta dira a gaban Ardadu ya dubeshi yace
bude wannan jakar kaga abin dake ciki.Cikin
hanzari gama da rawar jiki Ardadu ya bude
jakar,koda yayi arba da abin dake ciki saiya
dimauce idanunsa suka zazzaro kuma gaba
dayan jikinsa ya
kama rawa,ba komai ya gani ba a cikin jakar face
tarin lu'u lu'u,tunda yazo duniya da duk tsawon
shekarun daya shafe yana harkar fashi a daji bai
taba ganin dukiya a cure lokaci guda mai yawan
wanann ba.
Koda Uraidu ya lura da cewa wannan dukiya ta
ruda Ardadu sai farin ciki ya kamashi ya sake
dubansa yace wannan dukiya somin tabi a
gareka,muddin zaka bi umarninmu kayi abinda
muke
so zaka sami dukiyar da har ka mutu ba zakayi
talauci ba,kai bama yayanka ba hatta tattaba
kunnenka sai sun mutu sunbar abin daka
tara.Kasancewar akwai taswirar zuwa dajin
Hajarul Aswad a wajen sarki yaki haiman marikin
yarima zainur abokin maigidanka yarima
yazid.Muna son kasan duk hanyar da zakabi ka
sato mana wannan taswira a cikin kwanakin da
basu wuce tara ba.Indai ka sami wannan nasara
kawai jakar lu'u lu'u irin wannan guda dari da
suke jiranka.
Koda jin wannan albishir sai Ardadu ya dimauce
kuma ya firgice nan take Ardadu ya zube kasa a
gaban Uraidu yace na rantse da darajar iyayena
ko zan rasa rayuwata saina kawo maka wannan
taswira a cikin kwanaki
taran daka umarceni.
Uraidu ya bushe da dariyar murna yace yanzu
saika dauki wannan jakar lu'u lu'u kaje can inda
zaka boye kayanka sannan ka koma
inda su yarima zainur suke ka kaimusu abincin da
suka bukata amma ka sani cewa cin amanata ko
yaudara a bakacin ranka yake.
Koda jin wannan batu sai Ardadu ya risina ga
Uraidu yace har abada bazan yi gangancin cin
amanarka ba domin kuwa ni a rayuwata kudi
suna gaba da komai ko wannan
addini na yarima yazid dana karba na karbeshi ne
bisa sa ran cewa zanyi amfani da shi wajen
samun
abin duniya amma kuma naga alamun cewa
hakina bazai cimma ruwa ba ashe kune silar cika
wannan babban buri na rayuwata ban sani ba.
Ardadu na gama fadin hakan saiya sunkuya ya
dauki wannan jakar luu luu ya sabata a kafadarsa
ya dubi Uraidu yace lallai ko ta yaya zan kawo
maka wannan taswira a cikin kwananki tara
kamar yadda ka
bukata.Koda gama fadin hakan sai Ardadu ya
sake sunkuyawa ya dauki akushin daya siyowa su
yarima zainur abinci ya fice da sauri.
Fitarsa keda wuya saiya tafi izuwa gidan sarkin
kasuwa akayi masa iso
kafin Ardadu ya isa gidan sarki kasuwa saida yayi
ta canja hanyoyi yana badda bami kuma yana ta
waige waige domin ya tabbatar da cewa babu
mai binsa a baya a matsayinsa na tsohon
masanin tuggu.
Abinda Ardadu ya aiyana a ransa shine su Uraidu
zasu iya yaudararsa anan gana su kwace duk
abinda suka bashi,lokacin da Ardadu ya isa gidan
sarkin kasuwa
ya kadaita dashi saiya gaya masa cewa babban
hadimi ne na yarima Yazid kuma babu wanda
hankalinsa ya kwanta dashi daya ajiye musu
hajarsu face shi don haka ne suka kawo masa
wannan haja domin ya ajiye musu sai ranar da
zasu bar gari zasu zo su karba.Koda jin wannan
batu sai sarkin kasuwa yayi murmushi yace yau
shekarata arbain da daya kenan ina kan wannan
matsayi nawa na sarkin kasuwa kuma duk abinda
aka kawo mini ajiya
™Abbas Abdulkadir Hada Hada™
za'a dawo a riskeshi kamar yadda ka bani indai
inayin son zuciya ta da ban kawo iyanzu ba akan
matsayina.
Da izinin ubangijina abin bautata zaka dawo ka
iske ajiyarka lafiya kalau saidai sharadi guda
daya,sharadin kuwa shine duk bayan kwana guda
zaka bani ladan dinare hudu na lada ajiya sannan
kuma ina son ka gaya mini wanda zai iya
wakiltarka yazo ya karbi wannan dukiya idan har
kai baka sami dawowar karbarta ba idan na
sanshi a fuska shikenan idan kuma bansanshi ba
sai ka gaya mini siffofinsa da kamaninsa.
Koda sarkin kasuwa yazo nan a zancensa sai
hankalin Ardadu ya dugunzuma ya rasa bainda ke
masa dadi saboda yasan cewa bashi da wanda
zai iya turowa ya
wakilceshi akan wannnan dukiya kuma idan yace
bashi da wakilin sarkin kasuwa zai iya zarginsa
akan
cewa akwai rashin gaskiya akan wannan
dukiya.Koda Ardadu yaga bashi da wata mafita
sai yasa hannu a cikin aljihun rigarsa ya dauko
wani tsohon hatiminsa wanda ya saba amfani
dashi lokacin da yake kan matsayin shugaban yan
fashi ya mikawa sarkin kasuwa yace duk wanda
yazo gareka da irin wannan hatimi to ka dauki
wannan dukiya ka bashi.
Nan take sarki kasuwa ya karbi hatimin sukayi
sallama da Ardadu ya tafi.
Acan tsakiyar kasuwa kuwa lokacin dasu yarima
yazid suka ga cewa Ardadu ya dade sosai bai
dawo daga siyo abinci da suka aikeshi ba sai
mamaki ya kamasu.
Yarima Zainur ya dubi Yarima Yazid yace anya
kuwa lafiya wannan yaron naka ya dade haka bai
dawo ba?
Ina ganin cewa zaifi kyau mubi bayansa tunda
bamu sani ba ko makiyanmu ne suka kai masa
hari.Koda jin wannan batu sai yarima yazid ya
numfasa yace aini yadda nake tsoron Ardadu
bana tsoron
makiyan namu musamman tun daga lokacin
dakayi mini karin
bayani akansa,kasan sharrin wanda ke tare dakai
yafi na wanda ke nesa dakai saboda shi yasan
sirrinka.Cikin alamun mamaki zainur ya dubi
yazid yace yanzu kana nufin kace dani duk da
cewar ka yankewa ardadu hannunsa guda zai iya
sake yi maka laifi ko kuma yaci amanarka?
Yazid yace kwarai ma kuwa kasan ance ba'a
yabon dan kuturu da yatsa har saiya girma
sannan anan za'a fuskanci cewa abin duniya yafi
komai muhimmanci a cikin
zuciyarsa don haka yana da kyau mu zuba ido
akan Ardadu.
Yanzu dai tunda har yanzu bai dawo ba kawai mu
tashi mu tafi ya iskemu a can masaukina.Gama
fadin hakan keda wuya sai suka mike tsaye
domin su tafi kawai sai suka hango Ardadu daga
can nesa kadan ya durfafo su dauke da
akushin abinci kuma fuskarsa cike da annuri.Koda
ganin haka sai yarima zainur ya bude baki ba
tare da ya kallo yazid bayace jikina ya bani cewar
akwai wani mugun abu wanda wannan yaron
naka ke
shirin kullawa koma ya shirya shi domin bai
kamata muga annuri akan fuskarsa ba alhalin ya
bata mana rai bisa dadewar da yayi bai dawo ba.
Sai mun fara samun ishash shen comment kafin
mu kara yawan rubutu.
WASIKAR JINI!!!
Littafi Na Biyar (5)
Part B
.
bai kamata muga annuri akan fuskarsa ba alhalin
ya bata mana rai bisa dadewar da yayi bai dawo
ba.
Yarima Yazid yace nima dai naji hakan a jikina
domin masu iya magana sunce ruwa baya tsamin
banza.
Lokacin da Ardadu ya iso gabansu yarima yazid
saiya ajiye akushin a gabansu yana mai sunkui
da kansa kas yace,ya shugabana ka yafeni bisa
dadewar danayi ban dawo ba hakan ta faru ne
sakamakon karancin irin abincin da kuka
umarceni da siyowa a cikin wannan kasuwa.Koda
jin haka sai yarima yazid yayi murmushi
maimakon ya nuna fishinsa yace aini kaina nasan
cewa hakan zata iya faru,yanzu dai sai mu zauna
mu hanzarta cin wannan abinci kafin
lokacin rufe kasuwa yayi domin rana na daf da
faduwa.
Ba tare da bata lokaci ba kuwa suka zauna
sukaci wannan abinci su ukun,koda suka kare
suka
sha ruwa sai suka mike suka kama hanyar fita
daga cikin kasuwa,suna cikin tafiya ne yarima
zainur ya
dubi yarima yazid yace yakai abokina inason
yanzu mu wuce izuwa gidanmu ka kwana
wajena,kuma na gabatar dakai a wajen
mahaifina.Koda jin wannan batu sai yarima yazid
ya dubi yarima zainur cikin mamaki yace haba
yakai abokina me yasa kake son
ka dorawa kanka wahala,ai kawai ka kyale mu
mu karasa kwanakin da zamuyi a kasuwar nan
tundai
muma muna daf da barin garin.Yarima Zainur
yace haba ai abin kunya ne a gareni ace na kasa
baka
masauki na barka a gidan haya cikin kasuwa
alhalin yanzu ji nake kamar mun shafe shekaru
masu yawa muna yin wannan abota,zanyi
matukar bakin ciki idan har baka karbi wannan
tayi nawa ba don haka yanzu zamu wuce ne
izuwa masaukinku domin ku debo kayanku mu
wuce izuwa can gidanmu.
Koda jin wannan batu sai farinciki ya lullube
Ardadu a cikin ransa bisa cewa komai zaizo masa
cikin matukar sauki tunda dama baisan hanyar da
zaibi ba ya sami damar kusantarsa ba,shi kuwa
yarima yazid saiya nuna ko kadan baya son yaje
ya kwana gidansu zainur saida zainur ya matsa
masa.
Haka dai suka karasa masaukinsu yazid,yarima
zainur ya nemo mai
amalanke aka kwaso kayansu gaba daya suka
nufi gidan sarkin yaki haiman.
Da isowarsu gidan sarkin yaki aka bude musu
kofa suka shige ciki nan take zainur ya kirawo
hadiman gidan suka kwashe kayansu yarima
yazid aka tafi dasu izuwa dakinsa
sannan yaja yazid da ardadu suka nufi cikin
babban falo na gidan.
Da shigarsu sai sukayi arba da sarkin yaki
haiman kwance akan doguwar kujera likita na
dinke raunika a jikinsa a gefe daya kuma matarsa
ce a zaune ta hada kai da guiwa tana kuka.Cikin
firgici da dimauce yarima zainur ya ruga inda
haiman ke kwance ya kama hannunsa ya rike a
lokacin da
idanunsa suka ciko da kwallah yace yakai Abbana
wanene yayi maka wannan danyen aiki,ka gaya
mini ko waye naje na yakeshi.Koda jin wannan
batu sai Haiman ya mike da kyar cikin matukar
karfin hali ya dubi yarima yazid da ardadu sannan
ya dafa kafadar yarima zainur yace haba yakai
dana menene sabon labari don ka gannin a cikin
wannan hali,wadansu dakarun sumame ne suka
kawo min hari harna fafata
™Abbas Abdulkadir hada hada™
kazamin yaki dasu da kyar na tsira da rayuwata
saboda karfinsu da kuma yawansu,amma basu
sami
damar kashe ni ba.
Koda jin wannan batu sai hawaye
ya zubowa yarima zainur wani irin bakin ciki ya
turnuke shi ya rungume haiman a kirjinsa yace
yakai abbana gwara ace tsautsayin akaina ya
faru.Lallai koma dadewa saina dauki fansa akan
wannan
mutane.
Dajin haka sai haiman ya janye jikinsa daga cikin
na zainur ya dubi yarima yazid da kyau sannan
ya dubi Ardadu yace ina ka samo wadannan
manyan baki haka?
Koda jin wannan tambaya sai yarima zainur ya
kwashe labarin yadda ya hadu da yarima yazid
ya zainyanewa haiman ba tare daya boye masa
komai ba.
Koda jin wannan labari sai haiman
ya dubi yazid cikin farin ciki yace tabbas muna da
babban bako yau a gidannan,
Ummul Zainur ai sai kije a fara shiryawa bakinmu
abincin dare,kai kuma zainur saika kai abokin
naka dakinka domin su huta.
Ba tare da wata gardama ba kuwa sai matar
haiman ta mike tsaye cikin murna ganin yadda
haiman din ya sami karfin jikinsa harya iya
mikewa zaune yake magana,ta tafi izuwa dakin
girki domin ta fara shirya abincin dare suma
hadiman gidan kowannensu ya shiga aiki na
musamman domin karrama wannan baki.
Bayan yarima zainur yakai yazid da ardadu
dakinsa sun shirya kayayyakinsu saiya barsu a
dakin ya koma can wajen haiman
domin ya kara ganin yanayin jikinsa.Yana zuwa
sai ya iske haiman ya sallami likita ya tafi kuma
yana zaune yana shan wani ruwan magani a cikin
kofi.Da
shigowar zainur sai haiman ya dubeshi cikin
alamun tsananin damuwa ya yafitoshi da
hannu,cikin sauri da kaduwa zainur ya taho
gareshi ya zauna daf dashi.Haiman ya dubeshi
yace shin kasan sarauniya Lazwara?
Koda jin wannan tambaya sai zuciyar yarima
zainur ta buga da karfi ya sunkuyar da kansa kas
yayi shiru kamar bazai ce komai ba amma daya
tuna cewa bai taba yiwa haiman karya ba saiya
dago
kai ya dubeshi yace nasanta,haiman yayi ajiya
zuciya
yace itace ta ceci rayuwata daga hannun dakarun
sumamen da suka kawo mini hari,kuma tace na
gaya maka cewa kada ka dogara da abokinaka
wato wannan bako da kazo mini dashi domin
bazai iya
taimakonka ba bisa abinda kasa a gabanka,lallai
ka koma gareta kamar yadda kukayi alkawari
domin ta karasa taimakon da tayi niya a gareka.
Bana son komai dangane da abin dake tsakaninku
ko abinda kake shirinyi ba amma dai kada kayi
gaggawa a cikin dukkan sha'aninka ka tsaya kayi
tunani mai kyau domin ka yankewa kanka
hukuncin dazai amfaneka.
Lokacin da sarkin yaki haiman yazo nan a cikin
zancensa sai kan yarima zainur ya kara daurewa
ya rasa ma abinda zaiyi.
Daga can sai yayi ajiyar zuciyar ya dubi haiman
yace yakai abbana
kasha gaya mini cewa abinda babba ya hango
yaro ko ya hau tsauni bazai hangoshi ba,yanzu a
matsayinka na wanda ke gaba da ni wace
shawara zaka iya bani akan wannan al'amari?
Sa'adda haiman yaji wannan tambaya sai shima
ya kawo gwauron numfashi ya ajiye sannan ya
dubi zainur cikin nutsuwa yace yakai dana kayi
sani cewa wannan
al'amari naka babbane kuma baya bukatar
gaggawar yanke hukunci,ka sani cewa ina hada
idanu da
wannan abokin naka naji jikina ya bani cewa
mutum ne mai daraja sosai wanda zai iya yin
abin al'ajabin da ba'a taba zato ba.Na sani cewa
itama sarauniya Lazwara tana da matukar amfani
a garemu baki daya,kuma tana da abubuwan
al'ajabi amma idan zaka iya auna wadanann
mutane biyu a sikeli kaga wanda yafi nauyi a
cikinsu saika sallama komai a
gareshi,ko kuma kaje ka kwanta da wannan
matsala a rana wanda duk kaga yazo maka a
cikin mafarkinka a tsakanin yazid da sarauniya
lazwara shi zaka mika wuyanka.Koda jin wannan
batu sai yarima zainur yayi ajiyar zuciya yace
nagode ya abbana lallai zanyi aiki da wannan
shawara taka.Har
zainur ya mike tsaye zai koma can dakinsa wajen
su yarima yazid sai haiman ya ruko hannunsa ya
zaunar dashi suka fuskanci juna yace dashi,kayi
hankali da wannan bawa na yarima yazid domin
akwai alamun butulci a cikin idanunsa gami
dason abin duniya zai iya cin amanarku a ko
yaushe don haka kusa ido akansa.Cikin alamun
matukar mamaki zainur ya dubi haiman yace
yakai abbana yaya akayi kasan wannan al'amari?
Kasani cewa hatta yazid dani
babu wanda ya yarda da wanann mutumin kuma
ada can baya tsohon danfashi ne.
Yarima Yazid shine yaci shi da yaki har yasa shi
ya karbi addininsa
amma duk da haka saida ya aikata laifin sama
shi kuma ya yanke masa hannunsa guda a
matsayin
hukuncin satar.Koda jin wannan batu sai haiman
yayi dan gutun murmushi yace ai kuwa shi hali
zanen dutse ne idan wannan bawa yayi wasa sai
yarima yazid ya sake yanke masa daya hannun
nasa
ya zama cikakken musaki.Nan dai yarima zainur
ya mike tsaye ya koma can dakinsa yana zuwa
ya iske yarima yazid da ardadu suna gabatar da
sallar magriba don haka saiya koma gefe daya ya
zuba
musu idanu yana kallon yadda suka gabatar da
ibadar tasu.
Koda ya zuba ido yana kallonsu cikin
nutsuwa yana nazarin yadda sukeyin ibadar sai
yaji abin ya birgeshi matuka,ko da yarima yazid
ya dago daga raka'ar farko ya fara ta biyu yana
mai karanta suratul fatiha da suratul ikhlas sai
yaji tsigar jikinsa ra tashi gaba daya,yanayin
kalmomin na Al qur'ani sai suka saita tunaninsa
saboda hikimar da yaji a cikinsu da kuma
girmansu,take yaji a ransa cewa lallai akwai
gaskiya da daukaka a cikin wannan addini.
Lokacin da yarima yazid da ardadu suka idar da
sallah suka jiyo sukaga zainur a zaune ya kura
musu idanu kawai yana al'ajabi sai yarima yazid
yayi murmushi a gareshi yace,yaya naga ka

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login