Showing 18001 words to 21000 words out of 56708 words
Chapter 7 - WASIKAR JINI! COMPLETE Book By Abdulaziz Sani Madakin Gini.txt
takaici,
ba komai ne yaje fa sarki marwatu cikin wannan
hali ba face jin batun wasikar jini.Ada ba komai
sarki marwatu ke shirin yiba face yaudara gami
da cin amanar abokinsa waziri ridwan,abinda ya
aiyana aransa shine da zarar
sarki aiyuba ya fadi ya mutu zai kawo harin
bazata ya kama birnin da karfin tsiya kuma ya
dare kan
karagar mulkin sarki aiyuba,yanzu da yaji cewa
bazai iya hawa karagar sarki aiyuba ba face ya
karance wasikar jini kuma ya kasance jinin
sarautar latul harus sai murna ta koma ciki kuma
ya kamu da tsananin bakin ciki.Nanfa zuciyarsa
ta kama sake sake ta kulla wannan ta kwance
wance har sai da lokacin bari yayi,wato dare ya
raba sosai amma sarki marwatu bai sami mafita
ba ko shawara wacce zata fishshe shi,bisa dole
sarki marwatu ya hakura da
tunanin komai ya mike tsaye ya shiga cikin
turakar ya kwanta kwanciyarsa keda wuya kuwa
sai ya kama barci harda munshari.
Al'amarin Yarima Zainur kuwa lokacin daya rabu
da gimbiya Nauwara sai hankalinsa ya
dugunzuma ainun fiye da ko yaushe a
rayuwarsa,ba komai ne ya
tayar masa da hankali ba face jin batu cewa
shida mahaifinsa zasu zamo abokan gaba akan
neman
mulki,nanfa yarima zainur ya fara tunanin hanyar
dazaibi ya hana faruwar wannan gaba amma
daya
nutsu a cikin tunanin nasa saiya gane cewa babu
makawa sai wannan gaba ta kullu tunda daishi
yana kishin kasar da kuma jama'arsu,shi kuwa
waziri
ridwan akan biyan bukatarsa zai iya siyar da
kasar gaba daya,to waishin yanzu wane hukunci
ya kamata na yanke?
Shin idan lokacin tafiya neman wasikar jini yayi
zan hana mahaifina yin tafiyar ne ko kuwa zan
bar mu hadu acan wajen neman WASIKAR JINI
ne in yaso muyi yaki dayanmu ya kashe daya.
Koda Yarina Zainur yazo a zancensa
zucinsa sai hawaye ya zubo
+Abbas Abdulkadir Hada Hada+
masa nan take ya fashe da matsanancin kuka a
wannan lokaci yana cikin kuryar dakin sane na
gidan sarkin yaki haiman kuma a sannan dare ya
raba sosai,yana cikin wannan hali ne kwatsam
yaji an turo kofar dakin nasa a firgice bisa rashin
tsammani ya dago kasan yaga wanda ya shigo
ba wani bane face sarkin yaki haiman fuskarsa
cike da alamun
tausayawa a gareshi kuma idanunsa sun ciko da
kwalla.Maimakon sarkin yaki ya budi baki yace
dashi wani abu sai kawai ya zauna a gefen gadon
nasa ya janyo shi izuwa kan kirjinsa ya
rungumoshi sannan ya shiga rarrashinsa yana
mai cewa,yakai dana kayi sani cewa ita kaddara
ta riga fata babu yadda za'ayi
wani ya iya sauya maka kaddararka nasan duk
abinda yake damunka a yanzu amma shawara
daya zan baka shawarata kuwa ba komai bane
face ka tsaya kayi tunani da nazari a bisa duk irin
hukuncin daya kamata ka yankewa kanka,lallai
kada kasa son rai dason zuciya a cikin
al'amuranka duk abinda zai cutar da kasarka da
kuma mutanenka ka gujeshi
wanda duk kasan cewa zai taimaki kasarka da
jama'arka kuwa ka rumgumeshi ka soshi,koda yin
hakan zai zamo sanadin rasa rayuwarka kasani
cewa
bana nufin ka cutar da wani naka saboda ganin
ka cimma naka burin amma fa idan nine a
matsayinka
zan iya hakura da komai da kowa nawa don kare
kasata da jama'ata saboda yin hakan shike nuni
da shugaban dazai yi adalci.
Lokacin da sarkin yaki Haiman yazo nan a
zancensa sai mamaki ya turnuke yarima zainur
kuma ya kamu da tsananin bakin ciki
har idanunsa suka ciko da kwallah hawaye ya
subuto masa ya dubeshi yace ya shugabana
yanzu
ashe duk kasan da wannan al'amari tuntuni
amma baka sanar dani ba?
Koda jin wannan batu sai shima sarki yakin
idanunsa suka ciko da kwalla yace ka gafarceni
yakai yarima hakika bazan iya sanar dakai
wannan sirri ba saboda sarki ya gargadeni akan
kada na sanar dakai din kuma ina mai tabbatar
maka da cewa duk fadin garin nan mutum hudu
ne kacal suka san wannan sirri daga sarki,sai
waziri,sai gimbiya nauwara sannan kuma
ni.Gama fadin hakan keda wuya saiga wani
hadimin sarkin yaki haiman yazo kofar dakin da
suke yayi gyaran murya,koda jin hakan sai sarkin
yaki haiman ya fito da sauri ya dubi hadimin yace
menene?
hadimin ya risina cikin girmamawa yace ya
shugabana ai sarki ne ya aiko yanzun nan yace a
gaya maka cewa lallai ka hanzarta kaje
gareshi,cikin kaduwa da mamaki
sarkin yaki ya dubi hadimin yace lafiya kuwa sarki
zai turo ayi kirana a cikin wannan tsohon daren?
Ko harin bazata aka kawo mana?Hadimin yace
a'a inda hari aka kawo da yanzu kaji an busa
kahon
yaki,dajin haka sarkin yaki bai tsaya bata wani
lokaci ba sauya ruga izuwa inda bargar dawakai
take yaje ya kwance doki da kansa ya daura
masa sirdi yahau kuma ya zabureshi da gudu ya
fice daga cikin gidan sarautar.
Al'amarin Yarima Zainur kuwa lokacin daya sarkin
yaki ya fice daga cikin gidan shima saiya fito
daga cikim gidan ya nausa izuwa cikin gari ba
tare da sanin ma inda ya dosa ba gashi dai dare
ya raba
garin tsit baka jin sautin komai face haushin
karnuka da kuma sautin iska dake
kadawa.Tsananin
bakin ciki ne yasa Yarima Zainur ya kama tafiya
a kasa da kafafunsa ba tare da sanin inda ya
dosa ba
yana tafe kamar mahaukaci sabon shiga yana
kuka,duk da cewa yarima zainur bashi da wata
shakuwa tsakaninsa da mahaifinsa saiyaji ya
kamu da tsananin bakin ciki bisa jin cewar zai
zamo
abokin gabar mahaifin nasa,haka dai zainur yaci
gaba da tafiya har ya durfafi kasuwa kai
tsaye.Kasuwar tayi tsit tamkar babu mutum daya
mai numfashi a cikinta alhalin kuwa akwai gidajen
haya a cikin kasuwar inda baki ke kwana.Gaba
daya gidajen dake cikin wannan kasuwa na
hayane kuma mafi yawansu suna da
bene.Lokacin da Yarima Zainur yazo giftawa ta
tsakiyar kasuwar sai ya jiyo sautin muryar wani
mutum acan saman bene ta cikin wata taga har
zainur ya dangota tagar sai ya dawo da baya ya
tsaya kuma ya kasa kunne domin yaji abinda
mutumin yake fada,tunda yarima zainur yazo
duniya bai taba jin sauti mai dadi wanda
kunnuwansa keji ba a yanzu ba,sauti ne kamar na
waka ko kuma karatu cikin wadansu irin kalmoni
na hikima a daraja,nan take yarima zainur yaji
wadannan kalmomi sun ratsa zuciyarsa don haka
sai yaji babu abinda yakeso sama da ganin
mutumin da wadannan kalmoni ke fita daga
bakinsa,bisa wannan
dalili ne yarima zainur ya durfafi kofar gidan da
yake jiyo sautin karatun domin ya shiga kuma ya
hau harkan saman benen,da zuwa sai yasa
hannunsa ashe kofar a bude take don haka saiya
kunna kai
ciki ba tare da shakkat komai ba.Ashe ba wani
bane yake wannan karatun face Yarima Yazid
kuma
karatun alkur'ani yakeyi da farko ya fara karatun
ne a cikin zuciyarsa amma a lokacin da shaukin
karatun ya debeshi sai ya manta da cewa a cikin
kasar kafurai yake don haka baisan yana karatun
ba a fili kuma duk da cewar muryarsa akasa take
saida ta fito waje ta cikin tagar dakin saboda
kasancewar dare ya raba.
A wannan lokaci Yarima Zayid na zaune ne akan
wani farin buzu ya tankwashe kafafunsa kuma
yana rike da littafin alkur'ani a hannunsa wanda
yake karantawa,a gefensa na dama kuma daf
dashi takobinsa ce ajiye a kas,agefen hagunsa
kuwa Ardadu ne kwance akan shimfida yana ta
fama sharar barcinsa harda minshari.Dama a can
kofar gidan su Yarima Yazid suka daure dawakan
nan nasu wanda Ardadu ya sato.
Lokacin da Yarima Zainur ya turo kofar gidan ya
shigo saida
wadannan dawakai guda biyu suka dan tsorata
sukayi haniniya.Jin haniniyar tasune yasa Yarima
Zainur ya dora hannunsa guda akan kufen
takobinsa domin a zatonsa barayi ne suka kawo
ziyarar
bazato.Koda Zainur ya shigo cikin gidan saiya
wuce kai tsaye izuwa kan matattakar benen ya
fara
hawanta domin ya isa wannan daki inda yake jiyo
sautin karatun kuma karar takun sawun same
akan matattakalar na cigaba da cika kunne amma
ko a jikinsa,saida ya taka matattakalar karshe ya
dora hannunsa akan kofar dakin da nufin ya
turata sai kawai yaji hucin saran takobi a daidai
kunnensa.Cikin bakin zafin nama Yarima Zainur
ya sunkuya takobin Yazid ta sari iska amma kafin
yayi wani yunkuri tuni Yazid ya sake kawo masa
wani saran a ciki da nufin ya tsargeshi gida
biyu,aikuwa in
badon Zainur ya daka tsalle yabar wajen ba da
saidai wani bashi ba.
Aikuwa sai takobin ta dara matattakalar suka
rikito kasa tare,karar rugujewar matattakalar
benen tasa Ardadu da sauran mutanen dake cikin
gidan suka farka daga barci a gigice.Koda
Zainur da Yazid suka fado kasa daga kan
matattakalar benen sai sukayi wuf suka mike
tsaye zumbur ba shiri.Shima Yarima Zainur ya
zaro takobinsa domin ya kare kansa,nanfa suka
kacame da azababben yaki ya zamana suna
kaiwa junansu sara da suka cikin tsanamin zafin
nama, juriya da bajinta.
WASIKAR JININ!!!
Littafi Na Uku (3)
Part B
.
Cikin tsananin zafin nama,juriya da bajinta,nanfa
suka banko kofar gidan ta karye suka fado wajen
gidan suka dada mikewa tsaye zumbur suka
cigaba da bakin artabu kowannensu yana yin
wannan yaki ne iya karfinsa da ransa da jikinsa.
A tunanin Yarima Yazid yana yaki ne da rikakken
dan fashi wanda ya saba kaiwa fatake hari,shi
kuwa Yarima Zainur sai ya dauka cewar yana
yaki ne da dan leken asiri daga wata kasar koma
wannan karatu da yaji wadansu dalamisai ne na
tsafi ake karanta su domin a cutar da birninsu.
Lokacin da aka cigaba da wannan
mamakin yaki tsakanin Yarima Zainur da Yarima
Yaizd sai mutane sukayi ta firfitowa daga cikin
gidaje
suna kallon ikon Allah amma a tsorace,adaidai
wannan lokaci ne Ardadu ma ya fito da gudu
daga cikin gidan shima ya saje a cikin yan kallo
yana baiwa idanunsa abinci.
Saida Yarima Zainur da Yarima Yazid suka shafe
sama da rabin sa'a suna bakin artabu mai
tsananin ban tsoro da tashin hankali ba tare da
dayansu ya sami nasarar koda lakutar jikin daya
ba,kwatsam sai kowannensu ya samu nasarar
dora tsinin takobinsa akan wuyan dan uwansa
amma sai suka ki cutar da juna suka tsaya suna
kallon kallo,sannan ne ma suka lura da cewa sun
tara yan kallo.Koda sarkin kasuwa ya kyallar ido
yaga ashe da yarima zainur akeyin wannan
gumurzu da kuma bako yarima yazid saiya ruga
da gudu yace yakai Yarima menene ya hada ka
fada da fatakenmu haka?
Koda jin wannan batu sai jikin zainur dana yazid
yayi sanyi,
yazid ya dubi zainur cikin biyayya a lokacin daya
sauke takobinsa daga kan wuyan zainur yace ka
gafarceni ya shugabana kayi sani cewa na yake
kane saboda ina zaton ko dan fashi ne yake
kokarin shigowa dakinmu.
Koda jin haka sai Yarima Zainur yayi murmushi
shima ya sauke takobinsa daga kan wuyan Yazid
ya dubeshi yace nima nayi zaton ko kai dan leken
asiri ne daga wata kasar mai shirin cutar da
kasar nan sakamakon wani sauti danaji yana
fitowa daga cikin dakinku,ni sunana
Yarima Zainur da ga waziri Ridwan,kai kuma
waye?
Koda jin wannan tambaya sai yarima yazid yayi
murmushi yace sunana Yazid kuma na fito ne
daga can nahiyar dake gabashin wannan nahiya
taku,ba wani abu bane yasa nazoyin fatauci
wannan gari naku ba face na sami labarin cewa
kuna da arzikin ma'adanan kasa mai yawa,mu
kuma abubuwan da muke karanci kenan a can
nahiyar tamu.
Koda jin wannan batu sai yarima zainur ya jinjina
kai a lokacin da yayi masa wani irin kallo na
rashin yarda sannan yace,inason mu zauna ni da
kai mu tattauna wadansu maganganu masu
muhimmanci a sirrance,cikin mamaki yarima
yazid ya dubi yarima zainur amma sai yayi shiru
bai nuna amincewarsa ko rashin amincewarsa ba
akan batun
su zauna su tattauna,nan take sarkin kasuwa
yasa aka je aka dauko kujeru guda biyu aka kawo
wa zainur da yazid aka ajiye musu a gefe daya
sannan aka kori mutane kowa ya koma cikin
gidansa ya kullo kofa.
Ardadu kadai aka bari a tsaye a bayan yarima
yazid,kafin su fara tattaunawa sai yarima zainur
ya dubi Ardadu da kyau ya kare masa kallo yai
nazarinsa sannan ya dubi yazid yace,duk dana
lura cewa wannan mutum dake tare dakai
hadiminka ne babba,ban yarda dashi ba don haka
inason ya matsa can gefe daya muyi sirrinmu.
Cikin mamaki Yazid ya dubi zainur sannan ya
dubi Ardadu yayi masa inkiya take Ardadu ya
matsa gaba can nesa da su yana mai bata rai.
Yazid ya dubi zainur cikin nutsuwa yace yakai
yarima kai kuwa menene dalilin dayasa kace baka
yarda da wancen hadimin nawa ba?
Koda jin wannan tambaya sai yarima zainur yayi
murmushi yace ai wannan hadimi naka tsohon
danfashi ne wanda ake kira da suna Ardadu,babu
wanda yasan iyakar adadin rayukan da suka
salwanta a dalilin Ardadu da kuma dinbin dukiyar
da aka rasa,
shi mutumin kirki a fuska ma ana
ganeshi,yanzu gashi kaima da kanka ka datse
masa hannunsa duk da cewar ya zama babban
hadiminka.
Koda zainur yazo nan a jawabinsa sai yarima
yazid ya cika da tsananin mamaki ya kurawa
zainur idanu yace,dakata yarima shin kana yin
tsafi ne?
Indai ba tsafi kakeyi ba babu yadda za'ayi kasan
duk wadannan al'amura da suka faru a bayan
idanunka.
Dajin haka sai yarima zainur ya bushe da dariya
sannan yace bana tsafi amma ina da tsananin
bincike bisa abubuwan da suke faruwa a wannan
nahiyar tamu ciki da wajenta,duk wani babban
takadari inada labarinsa harma taswirarsa an
zana an kawo mini,kaga kenan bai kamata kayi
mamaki ba akan bayanin danayi maka na
shugaban yan fashi Ardadu,abinda nakeso dakai
yanzu shine ka fada mini gaskiyar wanene kai?
Kuma menene ya kawowa wannan birni namu?
Koda jin wannan batu sai yarima yazid ya kawo
gwauron numfashi ya ajiye sannan yace zan fadi
koma iyakar gaskiya a kaina amma kaima kayi
alkawari cewa zaka fada min gaskiya akan duk
lamarinka.
Yarima zainur yace na dauki alkawarin zan fada
maka iyakar gaskiyar badon koma ba sai don
saboda naga alamar cewa kai mutum ne mai
gaskiya maza ka bayyana min gaskiyar
matsayinka a birninku.
Yarima Yazid ya gyara zama yace sunana Yarima
Yazid da ga sarki Arsanal na birnin Haurul ba
komai ne ya kawo ni kasar ku ba face neman
wata Wasikar jini,
ba don komai nake neman wannan wasikar ba sai
domin na nemawa mahaifina da kasata kubuta
daga sharrin sarkinku,akwai dukiya mai yawa ta
sarki aiyuba a garinmu wacce ake juyata bisa
ka'idar za'a bashi riba duk shekara wannan
shekarar yanfashi sun kawo mana harin bazato
sun kwashe gaba dayan dukiyar kuma bamu da
yadda zamuyi mu iya biyanta
bisa wannan dalili ne muka shiga bincike har
muka gano cewar babu wata hanya da zamu iya
kare
kanmu daga barazanar sarkinku face mun rabashi
da WASIKAR JINI wacce itace
+Abbas Abdulkadir Hada Hada+
madogararsa akan karfin sihirinsa da karfin
mulkinsa,idan har bamu rabashi da wannan
wasika ta jini ba lallai zai turo dakarunsa su
shafe birninmu su kuma kame jama'ar duka a
matsayin bayi ko kuma ya jefemu cikin wata
masifar mai tsananin.
Koda Yarima Yazo nan a zancensa sai yarima
zainur ya cika da tsananin mamaki amma saiya
bushe da dariya,al'amarin daya baiwa yarima
yazid mamaki kenan,zainur yace yakai wannan
dan sarki kayi sani cewa kazo da wani babban
al'amari wanda ni kaina a yanzu na kasa fahimtar
abin a
rayuwata sama akan wannan batu na wasikar
jini,bisa binciken da nayi akan kasarku ta haurul
kuna yin wani addini ne wanda ake kira
musulunci kuma kunyi imani da cewa ubangijinku
shine mai iko akan komai da kowa idan har kunyi
imani na gaskiya akan wannan ubangiji naku me
yasa ba zaku rokeshi ba akan ya shiga
tsakaninku da sarkinmu tunda kun yarda cewa zai
iya magance komai.
Yarima Yazid yace tabbas abinda ka fada gaskiya
ne amma ka sani cewa ubangijinmu mai adalci
ne kuma baya zalunci bamu karbi dukiyar
sarkinku ba sai bisa ka'idar cewa zamu bashi
kaso daya jak cikin kaso uku na ribar da aka
samu a shekara.
Ga shekara ta zagayo bamu bashi ba,kaga kenan
mun karya alkawari don haka muna jin kunyar mu
kai karar sarkinku wajen ubangijinmu kuma
tsoransa ya hanamu muke mu sanar dashi
gaskiyar abinda ya faru,koma yu dace yayi mana
afuwa.
Sa'adda Yarima Yazid yazo nan a zancensa sai
yarima zainur yai ajiyar zuciya sannan yace
tabbas addininku akwai adalci a cikinsa tunda har
bakwa son cutar da wani akan gaskiyarsa to
amma ka sani cewa ina bukatar na sake ganin
karfin addinin naku da ubangijinku domin ina
ganin cewa shine kadai zai iya fitar damu gaba
daya daga cikin matsalar da muke ciki,ko kuna
cikin fargabar sarkinmu ni kuma ina cikin fargabar
mahaifina wanda idan harya hau kan karahar
mulkin kasar nan shike nan kasashen duniya ma
gaba daya sun shiga uku dimin zaluncinsa zai
tumbatsa ya kwarara izuwa dukkan nahiyoyin
duniya.
Koda jin wannan batu sai yarima yazid ya jinjina
kai yace aikuwa indai hakane ashe ba karamin
jihadi zanyi ba na tsaya har anan
birnin naku naga na taimaka mun hana
mahaifinka samun damar da yakeso ya
samu,amma inaso kayi
mini bayani ta yaya mahaifinka zai samu wannan
babbar dama?
Nan take Yarima Zainur ya kwashe
labarin duk abinda ya faru tundaga ranar daga
ranar daya fita farauta daji har yaje birnin Arnan
daji ya sadu da sarauniya Lazwara kawo izuwa
zaman da yayi da gimbiya nauwara da duk
bayanin datayi
masa akan WASIKAR JINI.
Koda yarima zainur ya gama baiwa yarima yazid
wannan labari sai yazid ya cika da tsanani
mamaki ya rasa ma abinda zaice masa can sai
yarima yazid ya dubi zainur yace nidai yanzu ba
zan komawa birninmu face da labarin mai dadi
wanda zai kwantar da hankalin mahaifina da
sauran mutane kasarmu don haka yanzu inason
ka
bani shawara bisa abinda zai fisheni.
Koda jin wannan batu sai yarima zainur yayi
shiru yana tunani har izuwa tsawon yan dakiku
daga can kuma saiya dago kai ya dubi Yazid yace
daga yau mun zama abokai na aminci nidakai don
haka inason ka cigaba da sauraro har izuwa
lokacin dazan tafi neman WASIKAR JINI domin
mu tafi tare kuma kamar yadda na gaya maka
dazu inason ka nuna mini isa da ikon ubangijinka
domin na gani ko zan iya dogara dashi na sami
biyan bukata ta,zaka cigaba da zama ne a cikin
wannan birni namu akan
matsayinka na babban bafatake daga wata
nahiya da wannan furuci nakeyi maka sallama sai
mun sake haduwa a karo na biyu,na barka
lafiya,koda gama fadin hakan sai yarima zainur
ya juya da baya ya bar cikin kasuwar,cikin
hanzari Ardadu ya ruga izuwa
wajen yarima yazid ya risina cikin biyayya yace
ya shugabana ina fatan dai yanzu ka samo mana
labarin inda wasikar jini take?
Cikin alamun fushi yarima yazid yadubi Ardadu
yace,waya gaya maka cewar ana samu komai a
saukake sai ansha wuya sannan akan sha
dadi,yazid na gama fadin hakan sai ya juya ya
koma cikin wannan gida,a lokacin ne sarkin
kasuwa ya ruga da gudu ya iskace cikin gidan
kuma ya risina a gareshi cikin matukar biyayya
kamar zai yi masa sujjada yace ya
shugabana kayi hakuri bisa katse maka barcinka
da yarima yazo yayi kuma lallai gobe da sassafe
zansa
magina su gyara wannan matattakalar benen
data rushe.
Koda jin wannan batu sai yarima yazid yayi
murmushi a lokacin da Ardadu ya karaso bayansa
ya dubi sarkin kasuwa yace ai dama ba barci
nakeyi ba sa'adda yarima ya shigo cikin gidannan
kuma yakin da mukayi bisa rashin sani ne amma
ai yanzu mun fahimci junanmu,yana gama fadin
hakan sai ya
taka rusasshiyar matattakalar benen ya haye
sama kuma ya shige cikin dakin barcin nasa
Ardadu na biye dashi.
Da shigarsu cikin dakin sai yazid da Ardadu suka
kwanta domin suyi barci amma sai Yarima Yazid
yaji idanunsa sun kekashe ba komai
ne ya janyo hakan ba face mamaki bisa ganin
yadda ya fafata kazamin yaki da yarima zainur ya
kasa
samun nasara akansa alhalin ba sa'ansa bane a
shekaru ya bashi kusan tazarar shekara biyar
zuwa
shida,abinda ya kara bashi mamaki mashine
labarin gimbiya Lazwara dayaji sarauniyar arnan
daji wacce
ma tafi yarima zainur karfi da iya yaki.To waishin
ma yaya akayi ta sami irin wannan gagarumin
karfi da kuma gagarumin horon.Nan take Yazid
ya aiyana a ransa yace duk ranar da yarima
zainur ya sami
damar zuwa daukar horon yaki a wajen gimbiya
Lazwara lallai tare zasuje domin yaga irin
jarumtakarta kuma yasa ido domin shima ya koyi
irin yanayin yakin nata.
Haka dai Yarima Yazid yacigaba da tunanin gami
da sake sake cikin zuciyarsa har barci ya saceshi
bai sani ba.
Al'amarin sarkin yaki Haiman kuwa lokacin
+Abbas Abdulkadir hada hada+
daya isa gidan sarki sai aka shigar dashi har cikin
kuryar turakar sarki yana shiga ya iske sarki
aiyuba
tare da gimbiya nauwara a zaune a cikin wani irin
yanayi mara kyau domin duk su biyun idanunsu
sunyi jawur alamar cewa sun hade suna
kuka.Koda ganin hakan sai hankalin haiman ya
dugunzuma ainun domin abinda yake tsoron
faruwa ga dukkan alamu shine yake shirin
faruwar.
Haiman ya durkusa kasa bisa guiwarsa guda
yana mai sunkui da kansa kas ya kwashi
gaisuwa.
Sarki Aiyuba ya masa