Showing 27001 words to 30000 words out of 35296 words

Chapter 10 - MIJIN TACE Book 3 Hausa Novels by hafsat Sodangi.docx

ciki ne kawai ya ishe ta.

To miji yayi mata shigo-shigo babu zurfi ya

dodana mata romo a baki ta dauka a haka za su

122

dauwama yanzu kuma bata yi aune ba sai taga ba shi

da lokacinta.

Jiya fa yana shigowa ko gaida su Baba bai tsaya

yayi ba ya juya ya tafi abinshi, yana Can wurin

wancan din, ni naji kamar ana cewa ma wai ciki ne

da ita sai ta haife za'a daura auren.

Ni kam a wannan lokacin na sakankance na

yarda na kuma mika wuya cewar bakin cikin Ado ne

zai kashe ni.

A wannan lokacin Goggo Ayalle da Babba

Tanimu sun yi matukar kula da ni, don su a nasu

ganin rashin lafiya nake yi, don ita na baiwa ma

cefanen da Adon ya aiko dashi.

Hajiya kuma tazo tayi min shara da duk wani

abinda ya kama na tsabtace min wurina, bana cin

komai sai in Goggo ta matsa min ne nake yarda in

sha ruwan tea ko farau-farau din da kullum Baba

Tanimu yake aiko min dashi.

Na rarne nayi matukar fita hayyacina, in ban da

kukan bakin ciki babu abin da nake yi, kewar iyayena

da 'yan uwana da dangina, musamman Babana tayi

matukar mamayar zuciyata.

Babu abin da nake nadamar shi irin sanya

Babana bacin ran da nayi akan Ado, gashi tun abin

bai je ko'ina ba ko shekara cif ba a cika ba har

alhakin shi ya kama ni, na soma ganin sakamalkon

123

abin da nayi 'kwai da dutse.

Kullum bayanin da mai babban allo yake yi min

kenan ya ce min basa karo, ya kan yi min irin wannan

bayanin ne kuwa a duk lokacin da na soma gaya

mishi abinda Baban nawa yake yi mana mu da

Innarmu.

Ashe ma Baban nawa mutumin kirki ne mai

kuma adalci ban taba sanin hakan ba kuma sąi a

yanzu, a wannan lokacin da nake dandanar bakin

cikin Ado.

Ran Litinin da sassafe ya zo gida babu wanda

yayi zaton ganinshi a lokacin tunda ranar nema ranar

da ya kamata ace ya tafi. Ni kadai ce a dakin ssai ko

Hasiyan da ke kai-kawon gyara min wuri.

Ina kwance a kan katifar ya wurgar da abin da ke

hannunshi yazo ya daga ni ya zaunar da ni na ki

zaman na koma na kwanta, kina hauka ne

Humairah? Kina hauka ne da ki ka maida kanki

haka?

Yanzu in ban da nayi wa Bala waya ya ce min

ba ki da lafiya sai kiyi ta zama a haka? Za ki kashe

kanki ne? ban tanka mishi ba, tun zuwanshi da safe

har Azahar ban bude baki nayi mishi magana ba.

Na riga na kudurawa zuciyata in dai zuwan da

ya yi ban yi mishi magana ba ne yasa shi yi min

hukuncin da yayi min, to na daina yi mishi magana

124

VAvi min abin da yafi wannan tsanani.

Har aka yi Sallar La'asar bai ji na bude bakina

na ce wa weai wani abuba, balle yasa ran zan yi

mishi na kuma ki yarda da cewar da yayi in tashi

muje asibiti,

Ina kallonshi ya jawo wayarshi, kalaman shi

suka fahintar da ni da Innata yake yin maganar

gaskiyar abinda ya faru tsakanina dashi, ya gaya

mata abin da nayi mishi da wanda shima yayi bai

rage komai ba.

Haka nan bai kuma fara ba, da kuma halin da

ake ciki a yanzu duik sai de ya gaya ata.

Ban ji ita abin da take gaya mishi ba amma na

ji shi yana amsa mata da to Inna sai kuma neji shi

ya ce mata to gata, nayi kamar in ki kar6ar wayar

sai kuma naga to in ranta ya baci fa?

Alhalin bacin ran Babana shi kadai shi ne ya yi

min wannan sanadin, to in ya hada har da nata fa?

Ya ya zan yi? Nasa hannu na karbi wayar ina jin ta

soma yi min magana naji muryarta.

Sai kawai na soma kuka, kuka kuma mai

tsanani ina jin itama ta gane ina cikin bacin rai mai

sanani ne yasa ta talkaita maganar tata da cewar

tunde dai ya zabe ni ya kawo maganar gabana ina

ganin ya kamata ta kare don girmarma ni yayi.

125

Ga manya nan a gidan naku bai kai maganar

gabansu ba saboda yana ganin in na gaya miki zaki

ii, in kuma kin ga ba za kiyi min wannan alfarmar

ba duk matar da ki ka gani a dakinta tana zaune, to

hakuri talke yi.

Ba kuma zai yiwu ace kina zaune da miji amma

ba za ki girmama shi ba, in yaja sai kema ki ja

saboda lina ganin kin isa. Wannan ba tsarin aure ba

ne na Shari' a ya zama auren 'yan iska.

In kuma kin ga irin shi ki ka fi sha'awa sai kiyi,

sannan zan yi miki kashedin ki daina fada da shi a

gaban yan uwanshi. Ki rike sirrin da ke tsakaninki

da mijinki, ki gamsu da alherinshi tun ba ki kure

hakurinshi ba.

Inda za ki daina jin jita-jita kuma kina amfani

da zato to da zai fiye miki amfani, in kin yarda da

abinda na gaya miki ki bashi hakuri, na ce mata to.

Tana kashe wayar na sunkuyar da kaina kasa

na ce mishi, kayi hakuri, bai taba tsammanin abin

da zan gaya mishi kenan ba, wata Kila jira yake yi

mu gama maganar shi ya bani hakurin.

Dadi ne yayi matukar kama shi yesan in na ce

ta sani ba shi hakurin, dawowa kan katifar ds nake

kwancem yayi ya dago ni ya kwantar a jikinshi inna

tana sona Humaira, in ma dai ke ce ki ka fahimce ni

126

irin fahimtar da tayi min?

Sau dava nake fadin gaskiyata ta yarda da ita,

amma ke baki yarda da ni ba, yaya za'ace miki na

ajiye wata mata a wani wuri ki yarda? Sannan in

ban da Inna tayi miki magana ta saki ki bani hakuri

ke kina shirin muyi tashin hankali ne.

Ni kuma ba ki sani ba tausayinki nake ji na

rabo ki da iyayenki da danginki na kawo ki cikin

nawa na ajiye ki ni da ki ke ganina ban cika son

muna samun matsala da ke ba.

Iyaka dai ba zan yarda da wasu halayen da ki

ke fito min da su ba ne don ko da ki ke jin ana ce

min 'MIJIN TACE' in ma dashi ki ke lura to na

rantse miki ni ba shi ba ne.

Sannan masu kawo miki bayanin abinda nake

yin dama ko menene? Da yake zama sanadin fada a

tsakanina da ke in na nemi aure a danginsu fa za su

jagoranci a bani in kuma kina ganin karya ne to.

Na daure fuska na ce to a baka mana sai me?

Rannan haka muka kwana da Ado maganganu

masu kwantar min da hankali yake tayi min na

yanda zamu fahimci juna mu zauna lafiya, ban

tanka mishi ba muka yi kwanciyarmnu yana

kankame dani a jikinshi bai kuma nemi komai ba

daga gare ni.

127

Washegari tun daga fitowarshi Masallaci Sallar

Asuba ya yi shiri ya ce min zai tafi Danja, na ceto

sai ya dawo, nayi mishi addu'ar da ta dace in yi

mishi, ya kama hanya ya tafi.

Wunin rannan ma ban fito ba ina dakina, ina

kwance kan katifata tunanin al'amura kawai nake

yi a zuciyata. Hasiya tazo tayi min duk abinda ya

kamata tayi min ta tafi ta bar ni ni kadai.

Tuni na kudurawa zuciyata bin hanyar da zan

zauna lafiya da mijina, in daina daukan zancen

wani ko bin shawararshi tunda na gane hakan ba

zai amfane ni da komai ba.

Sai dai yayi min sanadin wahala da 6acin rai

mai tsanani, babu kuma wanda zai agaza in da wani

abu sai dai ma in an gane halin da nake ciki ayi ta

zundena ana yi min dariya.

Don haka na yanke wa kaina shawarar ajiye

makaman fada in bi hanyar lallama da rarrashi da

bin umarninshi akan komai in dai baya sabawa

Shari'a ba ne shima kuma nasan da wuya yasa na

saba shari'ar.

Don kuwa mai kokari ne akan kiyaye dokoki

tunda na gane abin da ake yi wa wasu mazan a

kwashe kalau shi kam ba zai lamunta ba dama

kuma Hausawa suna da karin maganar da suke

128

cewa, wai in da wani yayi rawa aka yi mishi kari,

in wani yayi to dukan tsiya yake sha.

Nayi sallar La'asar nasa ruwa nayi wanka irin

wanda na dade ban yi ba, don kuwa rabona da in yi

wanka har na manta, tun da bakin cikin Ado ya

kwantar da ni. Ni da kaina tsamin jikina nake ji.

Na fito nayi alwala don yin sallar magarib da

Isha'i, sannan na zauna nayi shafa mai kyau na

gyara jikina sosai tun daga gashin kaina har farcena

babu abin da ban gyara ba.

Sanyi ya sauka min har cikin zuciyata saboda

ni' imar tsabta da na sau, kai kazanta dai musiba ce,

ni da kaina na gayawa kaina hakan.

Nan da nan na mike na canza zanin gadon da

ke shinfide kan katifar na shimfida, wankakke,

gogagge, na fesa freshner mai sanyin kamshi na

kuma kunna turaren tsinke a bayan gida na jawo

dan kofan tsaki gina na koma dakina na zauna ina

jiran lokacin Sallar magrib tayi.

Cikin zuciyata dai bani da wata matsala illa

jiran in gabatar da sallolina insha tea in kwanta

tunda nasan ni da ganin Ado watakila sai gobe da

yamma ko kuma ma ranar Allhamis.

Na idar da Sallar Isha'i na kulle kofata na dawo

ina hada tean da zan sha kafin in kwanta tunda ban

129

yi girki ba ban kuma aika an karbo min abincin

gida ba sai naji ana taba kofa nayi maza naje na

bude don ganin ko waye?

Sai naga Ado na kauce daga kofar ya shiga

nayi mishi sannu da zuwa ya amsa da har kin rufe

kofar ne? na ce mishi eh, yana cire kayan jikinshi

alamar wanka yake shirin yi yana tabayata me ki kaa

girka ne?

Cikin natsuwa na ce mishi ban yi giki ba

saboda ban san zaka dawo ba, in ba zan dawo ba ba

za ki girka abin da za ki ci ba? Kin ga irin ramar da

ki ka yi kuwa? Ya maida rigarshi ya fita.

Tunda Ado ya dawo ranar Talata da yamma bai

sake tafiya Danja ba yana gida bai kuma fita ko'ina

in ba sallama aka yi dashi ba.

Zuwa nayi na gayawa Princepla da yake akwai

fahinta a tsakanin na ce mishi akwai matsala a

gidana, ya ce to in je ya bani wannan satin sai na

roki wani Malami ya taimaka min da darussan

nawa don kar yara su cutu.

Ya dago idanuwanshi ya kalle ni doon a kwance

yake sanda yake maganar. Sai dai kuma gashi na

dawon tun ba aje ko'ina ba har na gundure ki kin

gaji dani ban tanka mishi ba don nasan me yake

nufi.

130

Tun daga wannan lokacin mu'amallar Inna da

Ado tayi matukar karuwa, na kuwa gane hakan ne

daga yawan kiranta da nake ganin yanayi, ba zai

yiwu sai rikici ya taso min a gida in rinka kiranta

tana kwantar min da fitinar ba.

Abinda ya gaya min kenan rannan da na ji su

suna magana ban kula shi ba, na dai san kawai yana

ganin girmanta da darajarta yana kuma girmamata

da iyakacin gaskiyar shi.

A wannan lokacin ne na gane gaba daya mataan

gidan bakin su daya ne haduwa suke yi suyi

maganganinsu kan abinda ya shafe ni ni da Ado.

Illa iyaka kawai ita Furerah ta ki yarda ta daina

karbar girkina tana yi saboda tana matukar amfana

dashi. A zahiri kuma tana nuna ita babu ruwanta ni

tata ce saboda alherin da nake yawan yi wa

ya'yanta.

Don haka sai na hada su gaba daya nayi musu

jumiah guda daya dukansu ina girmama su bana

kuma jin zafinsu tunda na gane damuwarsu bata

wuce ta kulawar da mijina yake da ni ba.

Ado bai daina zuwa Danja ya kwana ba na

kuma cire raina a kan hakan randa yake gida ma

mafi yawancin lokaci yakan raba dare ne biyu yana

waje bai dawo ba.

131

Ban kuma damu ba duk da 'yan maganganun

da ake yi in an ganni, nasan yana wurin lambunshi

yana lura da yanda ake ban ruwanshi.

Wani lokaci ya dawo ya samu ina zaman

jiranshi, wani lokaci yazo ya samu nayi bacci,

randa yaga zai tashen ya tashe ni in yi mishi abinda

yake so in yi mishi.

Randa yaga zai hakura ya bar ni in yi barcina,

shi yasa ma mafi yawancin lokaci in naji yana tayi

min kashedin kar fa kiyi bacci ki jira ni ce mishi

nake yi gara dai in ka dawo ka tashen, don ba zan

iya wannan dogon hirar ba a wannan duhun ni

kadai.

Yawan itar da nake yi wa Ado akan duhu ya

sanya shi yana fara diban labun nashi ya kashe

kudi mai yawa ya sanya wutar lantarki a gidan

gaba daya.

Ya kuma gyara katangar gidan yayi mata kofa

daya, yayi wa zauren gidan kyakkyawan gyara,

soronshi ya zauna daidai maimakon da da yake

barazanar zubowa, amma bai yi musu gwaninta ba.

Su Ruwaila wai cewa suke yi aikin banza, tun

lantarki yana sabo a Dabai ba a sanya mana shi ba

sai yanzu da ya zama gidan kowa da shi, kuma dubi

hanyoyin nan da muke samu muna shiga makwabta

132

hankali a kwance wai don fitina yasa an toshe.

Yanzu babu halin ka fita sai ka nemi izini, kai

zama da fitinannen mutu dai wuya ne dashi, sai

kayi hakuri.

. Ni kam tunda na gane mijina na kuma gane

halinshi na gane yana sona yana girmama min

mahaifiyata yana tattalin yan kannena sai na.

kudurawa kaina yin hakuri da shi da duk wani abin

da ya shafe shi.

Ban ganin yayi wani abu in ce mishi don me?

balle in je ina tambayarshi dalilin da yasa yayi har

akai ga jallin da zan ce ban yarda ba na daina.

Shi kuma in ya ga nayi mishi ba daidai ba ya

kama zai yi fada tunda shi baya iya ganin an yi bai

tanka ba sai in ba da hakuri ko da kuwa ina sane

nayi don ya ji in da dadi.

Don haka yan uwanshi başa bata min rai

komai suka yi min ban tankawa saboda na san

fitinata da su ba za ta saman mishi farin ciki da

kwanciyar hankali ba ni kuma abinda son ganin ya

samu kenan.

Rannan na dauki wayar Ado na kira Inna don

mu gaisa, tunda zaman jiran fitowarshi daga wanka

nake yi muna cikin hira Innar take bani labarin anyi

ruwan saman farko a Bauchi jiya.

133

Nayi kabbara cikin farin ciki tare da addu'ar

Ubangiji ya sanya damunar ta zamo mai albarka, ta

ce min to amin. Na ce shi kenan Inna za ku dan

samu saukin zafin nan da ake ta fama dashi ko ina.

Don mu ma nan din zafin ne, Inna tayi

murmushi ta ce to mu tun yaushe kuma muka huta

da zafi? Nayi maza na ce, Inna bana ba ayi zafin ba

ne sosai a Bauchi? Ta sake wani murmushin kafin

ta ce min.

"Hala ba ki san mijinki ya aikowa Umar mai

shagon dinkishi kudi ba? Wai azo a sanyawa mai

sunanshi (A.C), ai mu tun nan muka daina jin zafi.

Na ce bai gaya min ba Inna, cikin zuciyata

kuwa tunawa nayi da ranar da naji hirar Ado da

Sa'adatu yana tambayarta mai sunanshi, tana bashi

labarin ai tunda zafin nan yazo baya baccin daree

kwana yake yana kuka wai shi nan ma baya son

zafi.

Ado yana jin anyi ruwan saman farko a Bauchi

ya fitar da hatsinshi da ya noma gaba daya ya kai

kasuwa ya sayar, sai dan kadan ya bari. Dama

tunda' aka yi girbi ya fidda Zakka tun a gona na

baiwa makwabta da 'yan uwa nasu hakkin.

Ya tattara saura ya adana da niyyar sai damuna

ta gabato zai kai hatsinshi kasuwa, don yayi amfani

134

da kudin wajen yin noman wannan damunar.

Ado yana ta shirye-shiryen noma bana na

wannan damunar da muke addu'ar zuwanta lafiya

nima ina nawa shirye-shiryen na rubuta jarrabawata

ta gama Secondary a lokacin nan kuwa ina da ciki

wata hudu.

Sai dai babu wanda ya sani don babu alamar

shi ga ni kuma lafiyata kalau yan matsalolin da

nake dasu ba wasu masu yawa ba ne.

A wannan lokacin babu abin da nake so irin

Ado ya yarda ya barni in je gida in ga iyayena da

yan uwana. Amma sai in yi tayi mishi maganar

yana jna baya ma amsawa sai in ya ji na matsa

mishi da zancen sai ya ce min io wai me za ki jie ki

yiwo ne?

Da Aliya ta dawo daga aikin Hajji sun zo gidan

nan ita da Atika da Sa'a har da Baba karami suka

kawo miki tsarabarki suka yi miki bakunta ta

kwana uku. A wannan dan tsukakken dakin naki

baile ko in ce tsarabarki kike son karbowa.

Inna kuwa kina jin maganarta a waya mai

babban allo in yana son ganinki shi da matanshi

sun san in da kike tunda yazo Hajiya 'yar dubu ma

tazo to wa yai saura? Kullum yayi min irin wannan

maganar bata rai nake yi in daure fuskata in ce

135

mishi su kadai ne yan uwana da dangina?

Babana fa? Sai in hado da Mama don in yi

mishi kara tunda na gane har yanzu yana sonta

yana kuma girmamata, sauran 'yan uwana fa? Sai

ce to ba yanzu ba sai ya duba yaga lokacin da ya

dace.

Rannan muna tare da Ado a dakinmu bayani

yake yi min kan kudin hatsinshi da ya noma bara

wanda sai à wannan lokacin ya sayar da kuma na

lambunshi da ya sayar shima ya adana yana harin

damunar bana da gonakin da yake shirin nomawa.

Bana duk gonakina na gado zan

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login