Showing 21001 words to 24000 words out of 35296 words

Chapter 8 - MIJIN TACE Book 3 Hausa Novels by hafsat Sodangi.docx

sauran kayan hadin da

ya san ina amfani da su.

Ina dosar wurin naji matan gidan suna shewa

suna fadin "Lalle yau za'ayi sha'ani shinkafa? Matar

so zata yi girki, Ruwaila kuwa sai cewa tayi mutanen

birni ne yaushe za su je suna taba dawa? Ai sai mu.

Nayi kamar ban ji su ba, na gaishe su suka amsa

na wuce naje na kawar dá buhun naja shi na jingine

shi, na kama sharan wurin na share shi tas na kwashe

tokar da take murhu.

Naje na debo itace na kawo wurin, ban ankara ba

sai kawai naga gaba daya sun sulale sun watse sun

barni ni kadai a wurin ko wanda zan yi wa tambaya

in wani abu ya daure min kai babu.

Na leka tukwanen da zan yi amfani da su babu

wanda aka wanke gaba daya kayan wanke-wanken

yana tare a bakin rijiya, randunan da ake tara ruwan

97

girkin ma babu komai a ciki.

Don haka na tafi wurin Ruwailah tunda ita ce ta

riga kowa karbana a gidan sannan kusancin da ke

tsakanina da ita ma yafi yawa.

Cikin natsuwa na kalle ta na ce mata babu ruwa a'

randunan kuma ina so ki hada min itacen murhun

don wutar ta kama sosai.

Sai kawai naga ta zuba min ido tana kallona cikin

wani yanayi "Dama kin mike kin yi aikinki tunda

kema ba taimakon wasu kike yi ba.

Al Da zai yiwu kema kice sai an taimake ki ba, in

zaman jikin miji ne babu mijin da baya so á zauna

mishi sai dai in bai samu ba ya hakura.

Don babu wata matar da mijinta ba ya sonta,

tunda duk daya muke amfanin da ki ke yi wa mijinki

shi nake yiwa nawa mijin, shi ko wace mace ma take

yi wa nata kin gane?

Na ce mata eh, na juya na tafi, na nufi bakin

rijiya tana fadin au, tafiya ki ka yi tun ban gama yi

miki bayanin ba? Ban sake sauraronta ba.

Na dauki guga na jefa cikin rijiya da nufin debo

ruwan da zan yi aikin da shi, sai ga Ado ya shigo

wurin, abin da ban ta6a ganin yayi ba tun zuwanmu,

tun da yasan wurin zaman mata ne.

"Ke me ki ke yi a wurin nan? tambayar da ya

soma yi min kenan, ban iya amsawa ba saboda in na

98

ce zan y1 magana zan yi kuka.

Ajiye gugar ki tashi a wurin, na ci gaba da jawo

gugar, tunda na riga na cikota da ruwa ga nauyi.

Ajiyeta kuma yana nufin ta koma cikin rijiyar.

Ganin da yayi ban ajiyeta ba ya sanya shi

Rarasowa wurin yasa hannu ya karbeta daga gare ni,

wannan rijiyar da ba a ganin cikinta ne za ki zo kina

jan ruwa a ciki?"

Ya dangwarar da gugan a kasa ruwan da na jawoo

din ya kife, ya wuce ya fita. Ina tsaye ina tunanin

abinda zan yi sai naji wata a cikin matan da şuke

dakin Ruwailah tana ce mata wai fa matan so zasu yi

girki a gidan nan maza sai zirga-zirga'suke yi.

Ta ce, ai zai ga tsiya ai sai dai ya cire rigarshi

yayi mata girkin, haba ina amfanin namiji ya susuce

ya zama 'MIJIN TACE' kamar Ado ya laface akan

wannan yarinyar ya záma sai yanda tayi dashi, wai

har yana cewa suna aka tara.

To da me tafi wata? Gaba daya suka kwashe da

dariya suna fadin to shi ba tashin ya sani ba.

Taja wani mummunan tsaki da ke kara baiyanar

da tsananin bacin ranta, ai ni da su ne a gidannan

zasu ga tsiya, zan ga yanda za'ayi sujr dadin zaman,

sai dai in zasu tattara su koma in da suka fito, ko da

yake dai can din ma koro su ita Hajjyar tayi.

Tana tayin maganganun bata san Ado ya shigo

99

ba, yaran Almajirai ya kirawo ya kirawo guda biyu

wadanda dama sanannu ne a gidan Hamza da Bala,

ya nuna musu tarin wanke-wanken da.aka tara vace

musu su wanke su kuma debi ruwa su cika randuna

suka ce mishi to.

Daga muryar da yayi ya kira Furera, shi ya

fahimtar da Ruwailah mai rantsuwar Ado zai ga

tsiyar da zata yi mishi tasan yana wurin nan.da nan

tayi tsit.

Furera ta fito tana gyara daurin dan kwalinta

tana murmushi lafiya yau maigidan yake yawo a

wurin da mata suke girki? Ko ba ya koshi ne?"

Bai saki fuska ba balle ya rama mata wasan da

tri nishi, sai ya ce mata taimakona nake so kiyi ki

hadawa Humaira wuta ki kuma tsaya ki kula da

girkin ko ba za ki iya ba?

Da sauri ta ce, to me zai hana? Ya ce to na gode.

Yajuya zai tafi tayi maza ta sake ce mishi in dama ba

kana so ta zauna a wurin don ta ga aikin ba ne ai da

tayi tafiyarta.ma za'ayi.

Ya sake cewa to na gode, ya wuce ya tafi, na

tsaya zan taya Furerah aikin da ta unguma da hannu

bibiyu zata yi, sai kawai ta kalle ni cikin murmushi ta

ce ke tafi ki je wurin mijinki kin ji?

Kiran da Ado ya yi wa Furera ya danka mata

aikina a hannunta ba karamin abu ba ne wurin

100

Ruwailah, don a zahiri ne kawai suke abokan juna na

kut-da-kut, amma a 6oye abokan adawa ne.

Don ita Furerah ma ita ce uwar dakin amaryar

Ruwaila ban da haka kuma ita din bata yi zaton zai

iya yin hakan ba, don ganin ba sasansu daya da

Furare ba.

Sannan ita Ruwailah ban da zumuncin ita mata

wanshi ne na sasa daya akwai kuma zumunci na jini,

don haka ta dauka dole dai ita zai nema.

Ina tare da Ado a daki da daddare nayi mishi

kwalliya da sabuwar rigar baccin da ya zo min da ita

daga Zaria, sai kamshi nake yi, yayin da shi kuma

yake zaune daga shi sai dogon wandonshi na Track

Suit.

Yana tashe da laptob din shi Intenet ya shiga

yana bincike kan noma irin na zamani, ni kuma ina

kwance a gefenshi nayi filo da gefen cinyarshi ina

kallon abin da yake yi.

Yana kuma kara yi min bayani kan abin da na

tambaye shi, sai kawai Furera tayi sallama a bakin

kofa, ya amsa ya ce mata shigo mana. Nayi maza na

tashi na zauna na jawo dankwali ina daure kaina.

Suka gama gaisawa, sauran kayannan ne na

kawo, ga shinkafa mudu zai kai bakwai nayi amfani

da mudu ashirin da biyar ne ga... ya katse ta, je ki da

su Furerah da rana sai ki girkawa yaran wurinki, tayii

101

ta godiya ta tashi ta tafi.

Tana fita ya ture laptop din nashi gefe yasa

hannu biyu ya jawo ni jikinshi, kin san yau kuwa yau

wata uku daidai tun da ki ka yi rashin lafiyar nan."

Dan langabe nuna yana yin zolaya na ce mishi

bana lissafi, ya dan rage fara'ar shi ya ce to ni ina yi

wani lokaci kuma nakan tambayi kaina, to ko dai

nayi kuskuren ne.

Kamar yadda Goggo ta ce, nayin da na bari aka

yi miki wankin cikin? Nayi maza nace mishi baka yi

ba ban yi ba? Na ce mishi eh, baka yi ba, lokaci ne

kawai bai yi ba,

Kankame ni yayi da iyakacin karfinshi yana

tambayata, to yaushe ne lokacin? Kin kuwa san

haihuwar da aka yi wa Malla Haruna ta shekaranjiya,

ita ce ta sha bakwai?

Na ce, uhun! To sai me? ya zuba min ido yana

kallona, ina sonki Humaira, ko ace dandani-haukaci

ki ka yi min ko ace wani abu aka wanke aba ni nasha,

ni na gode da hannuma ma in aka bani zan iya kaiwa

bakina insha kin ji?

Ban tanka mishi ba, kiri-kiri a gidan nan

Ruwailah tayi dalilin da aka radawa Ado sunan

'MIJIN-TACE' wai shi din ta ce, ne wai bai da

katabus sai yanda aka yi dashi.

Ado da nake ganinshi jarumi in na ce jarumi ina

102

nufin akan komai ma shi din jarumin ne. wajen

neman halal din shi wajen tsayuwa kan ra'ayinshi a

gida ne kuwa ko a waje musamman ace ra'ayin nashi

akan gidanshi ne.

Tunda nasan kullum nai ce nake bin umarninshi

nake kuma barin ra'ayina in koma nashi don mu

zauna lafiya amma wai shi ne MIJIN-TACE da

zuciyata tayi kunci na tsunduma cikin tunani mai

tsanani, saboda bakin cikin kira min jarumin mijina

MJIN-TACE.

Da tunani ya tsananta gare ni, sai na tunano

Babana, na tuna marasa mutuncin unguwarmu har

nuna mana gidanmu da dan yatsa suke yi suna fadin

wai gidan mijin tace kenan, nace to ko dai shima ba

mijin tacen ba ne sharri kawai ta kama ni a dalilin

tausayin shi da yafi matukar kamani.

A hankali cikin zuciyata na shiga fita da addu'ar

ina ma dai ya huce ya daina fushi dani, don wata rana

in samu damar zuwa gabanshi don in roke shi gafara

kan laifin da nayi mishi?

Tunda Furera ta karbe ni hidimar girkin abincin

gida sai take ta kokarin sanya ni cikin al'amuranta

misali haihuwa ko baki da suka dangance ta zata

gaya min ta ce in gayawa maigida in ya bar ni sai

muje tare don mu saba da jama'a tunda shi mutum

shi ne babban arziki in bai bari ba babu damuwa in ce

103

mata to.

Rannan kanwarta da suke ciki daya ta haihu tazo

har dakina ta gaya min nace mata wanan kam dani

za'aje tayi murna sosai.

Ado yana dawowa na bashi labari, ya ce to in

lokacin ya matso sai ki tuna min, na ce to. In ka samu

sarari sai ka saya min rigar yanmata in bata don

mace aka haifa.

Ya ce min to, yana fita kuwa sai ga shi yazo min

da riga mai kyau na kai mata tayi ta murna.

Tun ana jibi suna na tuna mishi ya ce to, ina ta

murna nima zan fita unguwa tare da matan gida

abinda ban taba yi ba ana gobe sunan ma na tuna

mishi bai yi magana ba.

Washegarin suna ina gama aikina nayi wanka na

zauna nayi shafa na gyara jikina, yayi tsaf sai kamshi

nake yi na dako sabbin-under wears dina na sanya

tunda su kam ban taba rashinsu ba.

Duk rashin kudin Ado ba taba fashin sayen under

wears rigunan bacci da man shafawa ba, ko turare.

Ina tashe da atanfata dana ciro don daurawa,

cikin zuciyata ina tunanin Ado, tunda ya fita da safe

bai dawo ba, gashi har rana ta fito, mutan gida kuma

duk sunyi shirin tafiya baya nan, zuciyata ta raya min

in har aka ce in fito ba dawo ba, tafiyata zan yi tunda

ya san da maganar sanda na gaya mishin, kuma ba

104

musu yayi ba.

Ina cikin wannan tunanin sa gashi ya shigo rike

da leda mai dauke da robar yourgout da kuma fura a

ciki.

Ungo dama in na kalle shi cikin natsuwa na ce

mishi, ko za kayi hakuri ne kawu duk sun riga sun

gama shiri, ni kadai suke jira ka kuma san matan

gidannan kara ce dasu, in hidimar mutum daya ta

tashi sai kaga duk an dunguma an rufa mishi baya.

Ya ce, eh ai kirki ne da su, na ce eh, sai kawai

naji ya ce min, amma ba da wadannan sabbin under

wears din za ki ba ko? Wadannan ai kin san don

kaina na saye su me yasa za ki bude su bananan'?

Na daga ido na kalle shi ya bata rai sosai ji kuma

irin kamshin da. kike yi a haka ki ke shirin tafiya

gidan sunan? Wannan ma ai rainin hankali ne cikin

natsuwa da sanyin murya na ce kayi hakuri ka barni

in tafi na yau, tunda nasa mata rai, in yaso na gobe ka

hana ni."

Ya ce, a haka a kamshin da kike yi? Ai alhaki ma

sai yayi miki yawa, gara kawai ki sake wankan, na ce

to. Ina cewa to din ya matso jikina, to zaki yi wanka

mara dalili ne. Humaira bayan kin yi shafan nan mai

kyau ai bari ki ga hikimar da za'ayi ai gara kawai a yi

mai dalili sai kiyi kawai gaba daya kan nan ma kowa

ya gama shirinshi maimakon kije kiyi ta jiransu.

105

Babu halin in ce zan yi musu dashi kan bukatar

tashi sai ya ce kan tafiyar zan sabawa umarnin da

yayi min, saboda haka nayi hanzarin sallama mishi

kaina ban tsaya ja mishi rai 'ba, don nima yayi saurin

sallamata.

Sai dai abin takaicin shi ne, ina shiga hannun

Ado na mance da komai, ya sanya ni ciki wani hali

da ya kidimar dani, ya hanani tunani balle jin wani

motsi.

Ban sake tunawa da komai ba balle in tuna a

cikin sauri nake don kar in yarda in biye mishi, sai

bayan da na ganshi kwance a gefena kokarin ne na

tuna abin da ke gabana.

Zunbur nayi na mike cikin sauri na mufi ban daki

nayi wanka da ruwan sanyi aazo ina shiri hankalina a

tashe saboda shirun da gidan yayi min yayi yawa da

sauri.

Na sanya kayana ba tare da na tsaya shafa ba na'

fita naje don in gani ko sun gaman suna jiraa nawwa

babu kowa a gidan gaba daya sasan babu kowa sai

yar gidan Fureran budurwa Hasiya.

Na ce ke Hasiya tafiya suka yi basu gaya min ba?

Ta ce sun gaya miki baki ji ba ne? Na ce sun gaya

min wa ya gaya min? Ta ce ni ta aika sau biyu ina yi

miki magana ba ki ba.

Na dawo daki raina a bace gululun bakin ciki sai

1O6

yawo yake yi tsakanin wuyana da makogorona, na

dawo daki har lokacin Ado yana nan a yanda na bar

shi barci ma yake shirin yi bakin ciki da takaicinshi

suka kama ni har ban san lokacin da na soma kuka

ba.

Cikin sauri ya bude ido yana tambayata menene?

Ban kula shi ba, balle in tsaya yi mishi magana ba ki

da lafiya ne? Ban kula shi ba, menene ya same ki? Na

ki yin magana har ya gaji ya dawo kan hanya sunyi

gajin hakuri ne.

Haka suka tafi suka bar ki? Ban amsa ba yayi

maza ya mike bari in yi wanka in zo in kai ki ke da ki

ke da babur ma menene abin 6acin rai a ciki?

Nayi shiri Ado ma ya shirya muka fita ya burga

mashin na hau bayan shi muka kama hanya a yanda

duk suke fada kauyen Tukunya kusa kwarai take da

Dabai. Muna tafiya naga bamu je da wuri yanda nayi

zato ba, na ce mishi har yanzu ba mu zo Tukunyar

ba?

Yayi maza ya ce min Tukunya dama ki ka ce

zamu? Nayi maza na ce, to da ina ka ji na ce? Ya ce

Randa na ce, a'a ban da Tukunya akwai wani kauyen

ma Randa ne a nan kusa?

Ya ce min eh, na ce to ai Tukunya na ce maka ya

ce, to ai Tukunya na ce maka ya ce to ai babu

damuwa bari mu gaida wadannan sai muje Tukunyar

107

na ce to.

Ya tsaida mashin din shi gaban wani gida mai

tsananin tsabta ga ko'ina an dabe shi an kuma share

shi gwanin sha'awa.

Wani farin Dattijo mai wadatar farin gashi a

fuskarshi yana zaune kan farin buzunshi a gindin

wata katuwar bishiya mai yawan gaske.

Yana rike da carbinshi a hannunshi yana ja, cikin

natsuwa Ado ya kalle ni ya ce min, "Gidan Kawo'

kenan wannan da ki ke hange shi ne Baba Sambo.

Sanda mahaifina yake raye bai da wani Aminin

da ya fi shi, kin kuma san an ce mu sadar da

zumuncin iyayenmu ko bayan ba sa raye ko? Nayi

maza na ce eh, haka ne.

Muka karasa gaban dattijon nan cikin yanayi na

giramawa yana gane Ado ya gyara zamanshi cikin

fara'a da murmushi, ya amsa sallamar da Adon yayi

mishi, ya kuma shiga yi mana sannu da zuwa, Ado

yana amsawa.

Can kusa dashi yaje ya tsuguna yayin da ni kuma

na tsuguna daga baya, amma yana hangena tafin

hannunshi ya dora akan Ado tanfar wani dan yaro a

hakan ya ke yi mnishi magana, da alamar dai akwai

shakuwa da kulawa a tsakaninsu.

Wannan ita ce iyalintaka? Ya dago ido yana

kallona cikin nuna alamar jin dadi, sannu kin ji

108

yarinya, sannu Aishatu, sannu kin ji sannunku

Ubangiji yayi muku albarka, ya kuma jikan Mallamn

Sulaimanu."

Ado yayi maza ya ce, "Amin Baba." Ya ce, "Kar

ayi wasa da yi mishi addu'a, amfanin barin da a

duniya kenan, ka kuma san kai kadai ya bari." Ado

ya ce, haka ne Baba.

Muka dan yi hira, Ado ya ciro kudi ya bashi, ban

san nawa ne ba, yayi tasa mishi albarka har nima

yazo ya burga mashin din shi muka hau muka tafi.

Wata hanya ya biyo da ni da bangane ba, wasu

gine-gine nake gani da ban taba ganinsu ba, nan

kuma ina ne? nayi mishi tambayar cikin natsuwa ya

ce min "Dabai mana Humaira, ban biyo da ke ta inda

ki ka saba bi ba ne."

Tuni na shagala ina kallon gidaje da layuka har

da su kwalta a shimfide cikin unguwanni, ga

rijiyoyin burtsatse a ko ina, na ce kai Kawu, Dabai

din nan ma fa ba wani kauye ba ne, ai ban san haka

take ba sai yau.

Dubi gidaje har da tunkunan ruwansu, ga titina

ga fanfunan burtsatse birjik, ga lantarki har mutane

da yawa sun sanya a gidajensu, mas'alar dai kawai ba

ku da babbar kasuwa.

Wani irin lallausan murmushi Ado ya saki cikin

natsuwa naji ya ce min, sannu. A hankali dai in nayi

109

sa'a Dabai zata yi miki halin nata ta dabaibaye min

ke, ta maida ke 'yar gida har ki mance garinku.

Kin ga shi kenan sai muyi zamanmu mun huta da

kowa sai in kuta jin ana cewa an yi mafarkin anje

gida an ga an canza kofar gidan ko

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login