Showing 30001 words to 33000 words out of 35296 words

Chapter 11 - MIJIN TACE Book 3 Hausa Novels by hafsat Sodangi.docx

noma

Humairah ki taya ni da addu'a, nayi murmushi nayi

mishi addu'o'in tun a gabanshi wanda kuma dama

ka'ida ne sai dai in ban yi sallah ba.

Haka kawai ma na kan shi da irin koKarin- shi

da wahalarshi in roki Ubangiji ya sanya mishi

albarka mai yawa a ciki.

Muna cikin hirar ya daga ido ya kalle ni, amma

a anya Humairah ba zan kure hakùrinki, in sa ki

gundura da halayena da dabi'una ba kuwa?

Nayi kamar ban ji shi ba, saboda tunda muka yi

fadan da nace halayenshi da dabiu'unshi ne suka

gunduren ya.maida maganar ta żama ka idar nenman

magana a wurinshi.

136

Ban taba ganin mutum nmai son kai irina ba

Humairah alherin da na samu a noman banan kawai

ya ishe ni in yi miki ginin da za ki zauna a ciki ki

yalwata.

Amma ban yi ba, wai so nake in juya kudin in

sake maida su gona wai da a irin nawa son kan so

nake duk abin da ya fito daga gona in maida shi

gonar a aikin da nake yi in yi tattalin da zan rinka

yi mana hidimominmu.

Ban kula zancen nashi ba, wucewa kawa' nayi

na kwanta a bayanshi.

A warnan noman da Ado ya yi na wannan

damunar ne na gane talaka dai ba karamar wahala

yake sha ba a kasar nan duk abin da zai yi karfin

shi kadai yake yi mishi bai da wani mataimaki

ba dai na Ubangijinshi ba.

An riga an sani sarai babu yanda za'ayi a hada

noman wanda yayi amfani da karfi yayi da na

wanda yayi amfani da hanyoyin noma irin na

zamani wanda bai yiwuwa sai ana da wani abu a

hannu.

Amma an ki a yi wa manomanmu na asali

taimakon da ya dace da su wanda za su sau su

bunkasa aikin nomansu sai kullum ayi ta bayani a

baki a gidajen Radiyo da Jaridu, amma wasu yan

137

tsirarun mutane suke tsare komai su amfana da shi

a bira ne ba tare da ya kai ga manoman na asali ba.

Kullum irin korafi da maganganun da nakeyi

wa Ado kenan a duk lokacin da ya zauna yayi min

bayanin mai dadin ji kan aikin da ake yi mishi a

gonakin nashi in ganshi kuma garau babu wata

alama ta wahalar da zata tayar da hankali a tare da

shi.

Hannu babu bororo balle kanta, bal;e aje ga

jallin yin fason kafa ga ciwon baya da na kugu,

gashi kuma ya tabbatar min da cewar noman nashi

na bana zai nika na bara sau goma ko a fiye da

haka.

Sannan a hakan duk dan wani dama da ya samu

na zama zaka gan shi yana tashe da laptop din shi

bincike yake kara yi kan hanyoyin noma irin na

zamani a kasashe daban-dabarn da suka ci gaba, wai

ya kara koyo da sanin sabbin dabarun noma don ya

kara samun sauki.

A wannan damuwar ta bana sau biyu ina kaiwa

gonakin Ado ziyara sabanin na bara da na ki zuwa

saboda aikin ya wahalar min da mijina da yawa ya

fitar min dashi daga hayyacinshi, don ma shi din

namiji ne.

A duk lokacin da na kaiwa gonakin nan ziyara

138

kuwa tsayawa nake yi in yi ta kallon yabanya,

yanda ta mike fetal ta tafi tayi nisa cikin jeji ban

iya hango karshenta. Gashi ta yi kore shar.

Wani irin dadi ne yake kama ni wani irin sanyi

ya sauka cikin zuciyata, in ji ba ni da wani sauran

nauyi ko kunci da ya addabi zuciyata in ji babu

abin da yafi dacewa da ni irin in kara tsarkake

Ubangijina.

In kara kadaita shi da bauta, in kara jin

tsoronshi saboda ko daga kallon baiyanannun

ayyukanshi na zahiri a kawai wadanda su ba sai

mai hankali da ura ne kawai zai gansu ba.

Misali halittar sama da kasa canzawar yanayi

daga rani zuwa damuna, yanda dan Adam ke shuka

kwaya guda daya ya fitar da daruruwa kasa guda

daya ruwa iri daya ya fitar da nau'o'in tsirrai

daban-daban ya ishe mu zamowa abin lura.

Bin bayan Ado nayi can cikin gonar saboda

hangenshi da nake yi yana ciccire kananan ciyayin

da ke son fitowa da tsirran da bai son gani don in

gaya mishi tunanin da ke damun zuciyata.

A duk lokacin da na kalli yanayin sama ko

yanayin shuka a lokacin da tayi shar a jeji in ji ko

shima tashi zuciyar tana raya mishi irin wadannan

al' amuran,

139

Ban san yanda aka yi ba, ban san ina na

tsunduma wajen aikin ciccire mishi kananan

ciyayin ba sai da na ji shi yana cewa "Ke Humaira

ba fa abin da na kawo ki gonar nan kiyi kenan ba.

Kawo ki kawai nayi ki ganta kiji dadi ki taya ni

yi mata addu'a na rokon Ubangiji ya sanya mata

albarka mai yawa." Na ce mishi amin Kawu.

Taso ni yayi a gaba muka fito daga cikin gonar

muka dawo in da ya ajiye babur dinshi da muka zo

akai, cikin natsuwa ya kalle ni bayan ya burga

mashin din.

"Hau mu tafi mana." Na kalle shi na ce, "uh'uh

yi gaba zan tako da kafa ba zan sake hawanshi kayi

ta tsalle da ni a kan kunya ba."

Cikin natsuwa da nuna kulawa ya ce "Ba kunyaa

ba ce Humairah, hanyar ce babu kyan, na ce eh to

jeka. Ya sauka daga kan mashin din ya shiga tura

shi, ni kuma ina takawa da kafa muna tafiyar mnu

muna hirarmu mai dadi.

Mafi yawancin hirar kuma kan abin da ya shafe

mu ne, haihuwata da ta matso, gonarshi da kuma

aikinshi, kullum hirarmu bata wuce wadaunan

abubuwan guda uku.

Ranar Juma'a sha tara ga watan tara cikin

damuna sosai a lokacin da manoma suke matukar

140

taka tsan-tsan da dan abinda yai saura a hannunsu

saboda tuni karfinsu ya koma gona.

Ita kuma gcnar bata fara bayar da komai ba, na

haifi diyata ta mace lafiyayya, kana ganinta kasan

ubanta manomi ne, taci ta koshi.

Ado ya shigo gida cikin sauri a dalilin ya

kwana a dakin zauren gidanne saboda zuwan da

Sa'adatu tayi. Ina jin shi yana dariya yana tambayar

Goggo Ayalle.

Goggo wai yau ma an yi haihuwa a gidan nan

ko? Tana taya shi dariyar tana fadin "An kara

wata haihuwar. In ce ko dukansu ne suke shirin

haihuwar ne Goggo."

Goggo tayi dariya ta ce, to wa yasan musu ne?

wacece kuma ta haihu yau? Goggo ta ce a'a ashe

baka ji mnai baihuwar ba, ai Aisha ce."

Dib naji Ado yayi, yayi shiru na lokaci mai

tsawo yana sauraron bayanin da take yi, jarumar

yarinya ita kadai ta haihu sai zuwa Kanwarta tayi ta

tashe ni, hatta tsofaffin matannan da suka haihu

basu haihu su kadai ba, sai da suka taso mu muka

zo muka kwana muna zaune da su amma ita..

Ado ya katse ta ya ce to tsofaffin mata Goggo

ba sun san zafi da mutuncin kansu ba, amma ita fa

tana da hankali ne? Goggo ta rufe Ado da fada.

141

Wanne irin magania ne wannan? Yarinya tayi

kokari ba za ka yaba mata ba, bata hutar da kai

biyan kudin asibitin nan na zamani mai tsada ba?

To ni dai ban gode mata ba Goggo in tayi ne

don in yaba mata to ban yaba ba, ya juya ya bar ta

tana tayi mishi fada ina jin shi yana kwalawa

Sa'adatu kira, tayi maza ta fita ta tafi wurinshi.

Aka gama min komai aka dawo dani dakin

Goggo Ayalle wai a nan zan yi jegon, ina zama

Sa'adatu ta sake shigowa rike da kwano, ga

dabonon da Inna ta ce kar ki manta dashi.

Na kalle ta nayi murmushi na ce ai kuwa in ban

da kin tuna da na manta na karba ina ci ita kuma sai

kallon yarinya take yi tana murmushin jin dadi.

Ran Yaya ya 6aci, wai kin zauna kin haihu a

gida baki ga nima fadan da yayi min ba akan wai

ban je na gaya mishi ba. Na ce ai nima kukan

yarinyar kawai naji, in kai mishi ita ya ganta?

Na ce ke Sa'a, kin san nan gidan komai muka

yi za a iya cewa ba muyi daidai ba, ta ce haka ne.

naci dabinon sosai nasha ruwa kamar yanda Innan

ta ce a gaya min, na gyara nayi kwanciyata.

Kan ka ce meye wannan? Sai na ji ni garau

kamar ba ni ce nayi wannan uban wahalar ba.

Jimawa can Ado ya shigo dakin wurin ya nema

142

ya zauna suna gaisawa da Goggo cikin girmamawa

irin wannan alheri ya same muka tashi kana fada?

Ado ya ce kiyi hakuri Goggo raina ne ya baci ana

jaruntaka da wahala ne Goggo?

Ba za ta fada a san bata da lafiya ba? Ta ce to

tunda Ubangiji ya raba su lafiya ai sai muyi mishi

godiya, yayi murmushi ya ce haka ne.

Goggo taci gaba da yi mishi bayani ita haihuwa

ai duk ta wuce yanda ake maganarta, gida da

asibitin duk daya ne. Ubangiji ke yin ikonsa ayi ta

lafiya.

Yayi maza ya sake cewa haka ne Gogg0, mun

gode mishi. Ta tashi ta dauko yarinyar nan wai zata

ba shi ita kamar yanda ta saba kawo mishi sauran

yaran da aka haifa kafin ita a gidan.

Ya ce "A'a Goggo, ai zan ganta a hankali." Ta

ce ai haba? Ai na dauka ba za ka yi kunya ba, ta

maida ita ta ajiye ta fita saboda kiran da Baba ya yi

mata.

Yayi maza ya dawo bakin gadon yasa hannu ya

dauko ta ya kare mata kallo ya tofe ta da addu'o'i

ya maida ita yana kallona cikin murmushi.

Wannan yarinyar ta fito a jikinki Humairah ba

ki samu matsala ba ko? Ban kula shi ba, ya dan yi

waiwaye don kar yayi maganar da wani zai ji shi

143

ganin ba kowa yasa shi matso da bakinshi kunnena

ya fadi abinda yake nufin fadin.

Kallonshi kawai nayi ba tare da na ce mishi

komai ba, hidima sosai Ado yayi sai dai yaja ya

tsaya kan bai yarda ayi taron suna ba, tunda sauran

haihuwar ma duka ragunan suna kawai ya bayar

aka yi ysnka sai sunan da babu taro mai yawa.

Don haka nima ba zai yarda da gayya daga

wani wuri ba, Sa'adatun da tazo ita kadai ta isa.

Ni kam kuka nayi tayi, Goggo ma ta ce akan

me kuwa zaka yi haka? Wadannan yan uwa nata

ka ce ba za su sUnan 'yarsu ba?

Ya ce to 'yarsu tazo cikin tsululun damina

Goggo ba sai suyi hakuri ba, manomi yana hidima

mai tsanani ne da damuna? Goggo tayi dariya ta ce,

wannan shi ne iya shege.

Ni kamn da hankalina ya tashi da hana yan

uwana ziwa suna da Ado yayi sai da naji yana yi

wa Innata bayanin cewar shi din ya riga ya shirya

zuwana gida da zarar mun yada wanka, don haka

kar ayi wahalar zuwan.

Yanda Ado ya bada ragon suna guda daya a

duk haihuwar gidan da aka yi haka nan a wannan

sunan ma rago guda daya ya bayar da safe ranar

suna Baba Tanimu ya fadi sunan da ya sanyawa

144

yarinyar Umahmah.

Gaba daya kowa a gidan mamakin sunan yake

yi, wasu ma tambaya suke yi ina Baba ya samo

wannan sunan kuma? Sai da Baban ya shigo Goggo

tayi mishi tambayar naji yana yi mata bayani.

Sunan jikar Manzon Rahama ne, Goggo tayi

maza ta ce, (S.A.W), rannan da naje wajen wa'azi

naji ana tarihinta na ce to in aka yi wa Adamu

haihuwar ya mace sunan da zan sanya kenan.

Goggo tana dariyar farin ciki ta ce ai kuwa dai

Mallam tunda suna ne mai daraja, ya ce haba don

ma ba ki ji tarihin nata ba."

Duk da nanata haihuwar tsululun damuna da

Ado yayi tayi, hidima sosai yayi min. Mutane da

yawa kuma sun zo, mafi yawanci matan abokanshi

ne da kuma yan uwanshi, nawa yan uwanne

kawai ba su zo ba, shi ne abin da ya dan rage min

jin dadi.

Amma duk da haka na yi wa sunan kwalliya ta

burgewa da ban sha'awa. Lesuna masu tsada guda

biyu da atamfofi super suma guda biyu gami da

shaddojin gezna na asali suma guda biyu, dukkansu

a dinke.

Dinki kuma mai ban sha'awa ya kawo min

gami da takalma da jakakkunansu designers, ki

145

zabi wadanda za ki yi amfani da su.

Na daga ido na kalle shi cikin natsuwa na ce

mishi ya ya zaka kwashi kudi masu yawa haka ka.

saya min irin wadannan kayan? Bai kula ni ba sai

kawai yasa hannu a aljihunshi ya ciro wata sarka da

yan kunne mai kyau English Gold.

Ya miko min ki shirya in ga kwalliyar taki

kafin in fita don Kaduna nake son atfiya, kan

maganar nan da nayi miki. Kar dai ki fasa yin

addu'a ko kina zaune na gayawa Inna ma ta kara yi

min addu'a na ce mishi to.

Sa'adatu ta shigo itama tayi kwalliya mai kyau

atamfar super ce a jikinta itama Adon ne ya bata

don tayi fitar suna.

Nayi kwalliya sosai na kuma yi matukar yin

kyau, shaddar na fara sakawa saboda dinkinta yayi

matukar daukan hankalina.

Nayi dauri mai kyau na sanya sarka da

yankunne, ga agogo da zobe tunda nazo Dabai ban

taba kwalliya irin na ranar ba, mutanen da ban basu

taba sanina cikin kwalliyar da ta dace da ni, tunda

shima Ado kananan zannuwa yake saya min sai ko

yau dinnan.

Ina cikin gyaran daurina Goggo Ayalle sai

kallona take yi tana fadin iko sai Ubangiji sai ga

146

Sa' adatu ta shigo Anti wai kizo ki nuna mishi in da

linka din shi suke na kwatanta mata ta tafi ta dawo.

To kije mana kawai ki bashi tunda ya ce sauri

yake yi zai tafi, nabi maganar ta Goggo na nufi

dakin nawa da na kwana bakwai ban shige shi ba,

komai a kammale sai kanshi yake yi a tsakar dakin.

Na samu Ado a tsaye shima yayi kwalliya rigar

da ke jikin nashi sabuwa ce sai kamshi take yi.

Yana ganina ya rage fara' arshi kai ke kam ko

wayo baki dashi can zan biyo ki dakin Goggo in ga

kwalliyar sunan naki?

Ya sake kallona cikin wani yanayi na sakin

fuska da murmushi alamar ya gamsu da abin da ya

gani, ya ce wannan ita ce asalin Humairar da Inna

ta bani ba wacce na kawo na ajiye a wannan dan

tsukakken dakin ba.

Nayi murmushi don in rama mishi wayan nashi

ya ji dadi, sai na ce mishi ba fa Inna ce ta baka

Humaira ba, Baba da Mama ne suka baka ita.

Ya sake fadada murmushin shi tare da jawo ni

jikinshi har dankwalin nawa ya fadi a kasa,

kankame ni sosai yayi a jikinshi kafin ya ce minni

Inna ce ta bani ke Aisha, ita ce tayi dalilin da ki ka

sallama min kanki.

Ita ce ta biyo mu Dabai da umarnin da take

147

bayarwa ne na samu nayi sa'ar samun zaman lafiya

a gidana don haka ni a wurina ita ce ta ba ni ke.

Muka yi sallama ya kama hanya ya tafi nima na

dawo dakin Goggon in da ake sha'anin suna,

Goggo sai bina da kallo take yi tana kokarin ganin

idona, ko me take son gani oho?

Suna da kwana biyu Ado ya dawo yana

dawowan yaje ya sayo wani katon rago ya kawo

gida aka yanka yasa aka soya ya zuba shi a cikin

kwalla wacce itama sayota yayi ya hada da katon

din minti na malta sweet.

Da katon din cingam Bazooka 200 da goro dan

takarda biyu da dabino mudu biyar da shadda yadi

goma-goma, guda hudu da atamfofin super guda

uku ya tashi Bala ya ce mishi yayi wa Sa'adatu

rakiya zuwa gida gaba daya kayan ya ce a kaiwa

Baba a gaya mishi shaddojin guda hudu.

Shi daya Baba Yahya daya, Mallam Liman

daya, Mallam Harisu ma daya, atamfofi kuwa

Mama daya Innata daya, Zubaida ma daya, sauran

kuwa akai mishi a gaya mishi na haifi Umahmah ga

kayan suna nan a rabawa Jama'a.

Sannan itama Sa'adatu yayi mata tata tsarabar.

Kwanan Bala uku a can maimakon daya ko

biyun da Adon ya ce mishi ya yi ya kuma dawo da

148

shatara ta arziki.

Jego mai kyan nayi mai kuma dadin gaske na

murje nayi gwanin sha'awa in ban da ina lissafin

kwana kin tafiya ta gida ma ina jin da nafi haka

morewa jegon nawa.

Rannan Ado ya dawo gida daga Danja a

lokacin nan kuwa kwanana arba'in ne har da uku.

Yana shigowa dakin ya nemi wuri a bakin gadon

da nake zaune ya kama kallon yarinyar da ke ta

faman bacci.

NI wannan yarinyar da wa tayi kama ne? nayi

murmushi na ce wah yasan mata, wasu suce da ni,

yayi maza ya galla min uban harara wadanda basu

san ka ma iso ba ko?

Nayi shiru naci gaba da abin da nake yi, to wai

ni ba kin yi arba' in bane me kuma kike yi a naan

dakin? Nayi murmushi na ce to ai ban gama

wankan ba Goggo ta ce sai na kara.

Wai wata biyu ba kwana daya zan yi zamu bar

wankan yau ne gobe mu tafi gida. Ya tsuke fuska

ya ce a'a ban yi miki wannan alkawarin ba, na dai

ce in kin yi wata biyu za ku tafi amma ai ba daga

nan dakin za ki tashi kiyi tafiyar ba.

Nayi maza na ce ban gane ba, ya ce to kar ki

gane, kina nufin haka zan yi ta zama? An gama

149

hakurin tsohon ciki an yi na zaman jego sai kuma

in yi ta zama ina jiranki sai kin dawo daga tafiya?

Ki gayawa Goggo za ki koma dakinki yau sai

muyi ko kwana bakwai ne tare in yaso rana itayau

ma kiyi tafiyarki, na sunkuyar da kaina kasa na ce

ba zan iya ba.

Ya ce

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login