Showing 6001 words to 9000 words out of 35296 words

Chapter 3 - MIJIN TACE Book 3 Hausa Novels by hafsat Sodangi.docx

karamcin mutanenta

ba sai na gaya miki cewar mutanen da suka san

Dabai din da irin halinta suna yi mata kirari da

cewar ce Dabai dabaibaye bako, maida bako dan

gida ya manta garinsu, ta magaji mai alamar samu.

Ban taba tankawa Ado maganganunshi ba

tunda muka baro gida, don haka wannan ma ban

amsa ba, na dai san kawai yana son garin nasu da

kuma jihar tasu ta Katsina don yanzun nan ne zan ji

ya ce wa Mallam Haruna a'a ai mu nan Katsina

babu wannan, to ban tsananta jin mamakin shi ba,

don kuwa nima ina son jihata ta Bauchi da garinmu

na Giyade da kuma unguwarmu ta Nasarawa

30

Jahun.

"Rage tafiya sosai Mallam Haruna ka kumna

sanyawa na baya alamar barin hanya nan gabanka

kadan ta gefen damanka akwai hanyar da ta shiga

ciki, ita za ka bi." "Yan daidaikun mutane ne a waje

saboda dare ya riga yayi nisa, amma mafi

yawancinsu Ado yana shaida su alamar dai bai taba

rabuwa da al'amuran garin nasu ba.

"Bi ta nan gefen kayi dama sosai, akwai

katuwar bishiyar kuka, ta gefen ta zaka wuce kiyi

yamma irin bayanin da Ado ya rinka yi kenan har

muka iso inda yace to, ga Masallaci can fari nan

kawai zaka tsaya.

Muna tsayawa Mallam Haruna yayi murmush

ya ce, "Kai Mallam Ado kasan garin nan Ado ya

taya shi murmushin ya ce, garina ne fa, ga ruwa

nan a randa ga lbandaki can gefe in zaka taba ruwa

bari mu shiga in fiddo maka da abinci."

Mallam Haruna yayi maZa ya ce, kai ai ni a

koshe nake, a dai bani wurin kwanciya kawai.

Ado yasa hannu ya dauki jaka guda daya dakke

bayan motar ya rataya akan kafadar na kuma san da

ita kadai ya iso garin ya tasa ni a gaba muka nufi

cikin gidan, muna fita daga zauren wanda babba ne

sosai ga kuma wani daki a cikin shi.

31

Sai ga wani shamaki da ya shiga tsakanin

mutanen zauren da ganin cikin gida daga bayan

shaakin hanyoyi ne da suka nufi sasan da ke gidan,

gaskiya ne girman gidan su Ado ya wuce a tsaya

yin bayani.

SW Kinga ga hanyar sasan u nan, wancan sasan

Baba Halliru ne shi da 'ya'yanshi wancan na Baba

Ubangida shima shi da nashi ya'yan wancan nasu

Baba Tukur ne shima da nashi iyalin mu dai je

kawai yanzu ba za ki gane komai ba sai an kwana

biya kin gane kan gidan da mutanen ciki tukuna. A

zuciyata nace hu'un.

paR Muna dosan sasan da ya ce min shi ne nasan ya

kwala sallama sai kawai naji wata murya ta asa

daga cikin wani daki tana kuma tambayar Adamu

ne a cikin tsohon daren nan? Yayi murmushi ya ce

mishi eh Baba, mutumin da Ado ya kira da sunan

Baba ya fito rike da sanda a hannunshi ba dai don

tsafi kam sai dai ko don wani dalili don da

karfinshi na ganshi.

Yana ganina yasa hannu ya rufe baki nuna

alamar mamaki da wannan yarinyar ku ke tàfe? Ya

ce mishi eh Baba, sannu da zuwa Aishatu, nima

nayi ta amsawa don girmamawa.

Kaga halin mata ba? Sufa babu wani babba

32

babu yaro a cikinsu, in ka biye musu kunya za su

baka. Ado yayi murmushi ya ce, me ya faru Baba?

Ya ce to ai uwar taku bata nan tana can taje

Kauyensu na Tukunya zata kwana saboda yau ana

kamun wata jikar su, in ban da rashin hankali irin

nata da nima na biye ta shi babba yana yin nesa da

wurinshi ne tunda ya san yana da baya da yawa.

Ado ya ce, ai babu komai Baba, Baba yaja tsaki

ya ce, in ban da lalura irin ta girma me za'ayi da

zaman mace daya ne?

Ado ya sake wani murmushin ya ce ai

Humairah ba gobe zata tafi ba, ba kuma jibi ba,

zata dawo ta same ta babu damuwa, ya ce auto shi

kenan amma ai ba dai haka aka so ba.

Makullin dakin nan a kusa yake ni ko Baba?

Baba yayi maza ya ce, eh ai cikinshi nake wuni

tunda sorona ya fadi, ya ce haka ne fa Baba an gaya

min soronka ya fadi ya bude dakin muka shiga,

komai a gyare yake a kintse, dakin yasha leda ga

katifa timemiya a shimfide ga kujerar kwanciya

can gefe akwati ne shia mai kyau a rufe na tabbatar

komai na cikin dakin na Ado ne.

Muna shiga ya sauke jakar kafadar shi ya bude

ta ya fiddo fitilar chaji ko batir ya kunnata ko ina

ya dauki haske sosai.

33

A to, tunda ka ki ka sanya mana wutar lantarki

a gida mu ma mu rinka ganin haske irin naka na

birni, ai ka rinka yawo da fitila a Jaka, wata mata

ce da ta ja ta toaya a bakin kofa tayi wannan

maganar tana ganin dakin ya gauraye da haske

kuma ta karasa shigowa cikin dakin ta durkusa

kamar wata karamar yarinya.

Da gefen Adon ya harareta ya ce, mijinki fa me

ya hana shi jawowa? Tayi murmushi tare da

langabar da kai ta ce waiyo bai da shi ne, ya ce eh

bai da shi, amma ai a hakan yake iya karo aure ko?

Ta sake wani murmushin kafin ta sake cewa

waiyo!! wannan ai rabo ne.

Ado yayi maza ya ce, haka ne. Tayi maza ta

kalle ni cikin fara'a, kin ga rabu da mijinki kin ji ke

dai sannu da zuwa abinki na ce mata yauwa, na

kuma fara gaisheta saboda ganin zata iya girmana

da shekarun da suka kai tara ko ma goma.

Kai gani kafin ki fara tambayar mutane abin da

za su ci don ke aikinki kenan tayi maza ta sake

langwabewa ta ce ehhhyi, ni ai cin ne sna'ata, sai

in ga kamar kowa ma haka yake.

Yayi maza ya girgiza kai ya ce a'a ke kadai ce,

ta ce au to, to na ji to ku da wanne ku ke farawa?

Ya ce wanka don ba ki iya karbar baki ba ne yasa

34

ba ki gane hakan ba, ta ce au to to naji zan gyara ko

da yake dai munan da yake mu yan kauye ne ci ne

gaba da wanka ya ce, eh to ai kin san mu 'yan birni

ne, ta ce haka ne.

To bari in samo ruwan zafi nan da nan ta fita,

tana barin dakin ya daga ido ya kalle ni cikin

natsuwa ya ce min Ruwailah kenan, matar yaya

Jafaru ce ai kin san yana yawan zuwa wurina, na

gyada kai nuna alamar na gane shi, ya ce to shi ne

babban wanmu a nan sasan shi ne dan Baba

Tanimu na farko wanda yaje ya karbar min aurenki

amma ai kin san ni ni kadai ne wurin mahafina ko?

Na girgiza kai a hankali, nuna alamar ban sani

ba, ya ce to ni kadai ne. Ya ci gaba da abinda yake

yi na kaye-kaye da gyare-gyare tanfar dai ba a cikin

dare muka shiga dakin ba.

Ruwailah ta dawo da ruwan zafi a bokiti da

wani kuma a flaks dinta da ta dauka a dakin, ga

kuma wani kunshi cikin leda da ta ajiye a gefe, wai

yana yi muku sannu da zuwa.

Ado ya yi tsaki ya ce, kai ke kan ba ki da kirki,

yanzunnan sai da ki ka tashi bawan Allahn nan a

cikin tsohon daren nan ki ka yi sanadin fitarshi

waje? Ta ce, oh oh, ba ma a wurina yake ba, to

amma da bai fitan ba da wa ya sauke maka

35

mutumin da kazo dashi din?

Ado ya rike baki nuna'alamar mantuwa, ya ce

na shagala ina kallon Humaira, kin san ni in ina

tare da ita to sunana ne kadai ban iya mancewa da

shi.

Ruwaila ta kyalkyale da dariya ta ce, ai kuwa

dai ma kayi kokari tunda ba ka mancewa da sunan

naka a nan sanu.

Sabon soso da sabulu da brush da abin wanke

baki da sabon tawul ya fiddo daga cikin jakar tashi

ya miko min na karba nabi bayan Ruwailah da ta

daukan min ruwam muka je ta nuna min ban dakin.

Na dawo daga wankan na samu kwanukan

abinci iri-iri, ya kalle ni ya ce min wannan kunshin

na gasasshen nama ne Yaya Jafaru ya sayo miki, ga

furar da Baba ya bayar da nono Ruwailah ta dama

miki, ga kuma tuwon dawa miyar kuka shima mai

dumi ne ta dumamo da wanne za ki fara?

Na ce kowanne, ya kalli Ruwailah da ke ta

faman bubbude min kowanne in gani ya ce mata ba

kin gama naki ba, to kije mana kuma sai da safe, ta

ce am wai jira nake yi ta gama mu tafi can wurina

ta kwanta.

Yayi maza ya ce, wasa kenan, tabar dakin

mijinta da mijin nata a ciki taje ta kwana a wannan

36

tsohon dakin naki? Ta ce, to ai shi kenan sai da safe

Amarya. Nayi murmushi na ce mata to ki huta

gajiya.

Tana fita Ado ya kalle ni ya ce wannan

atishawan da kike tayi fa don kin yi wanka a bayan

gidan da babu rufi ne baki saba ba, ban amsa mishi

ba amma cikin zuciyata nima na yarda hakanne don

maimakon in ji dadin wankan da nayi sai naji

kamar sanyi ya kama ni.

Naci tuwo sosai don yayi min dadi laushinshi

da dankonshi yayi banban da irin tuwon da na saba,

nasha ruwan tea mai cçitta naci nama kadan na

gyara na kwanta bayan na shafa mai nasa rigar

baccina wanda itama shi yazo da ita.

Na kalle shi cikin natsuwa nayi mishi magana

wanda tun fitowarmu ban yi mishi ba saboda na

gane babu komai cikin jakar tashi in ban da

kayayyakin amfanin da ya saya saboda ni na ce to

da ban biyo ka ba fa yaya zaka yi da kayan nan?

Ya kalle ni cikin natsuwa ya ce, ban taba

daukar za ki iya kin bina ba, na dauka ke ma kina

sona.

Muna kwance ni da Ado akan katifar yana

gefenshi ina nawa sai dai mu dukanmu babu wanda

ya samu yayi bacci, ya daga ido cikin natsuwa ya

37

ce min Humairah ba ki ga kamar kasa yin baccin

nan da muka yi alama ne na muna jin marmarin

juna ba?

Nayi maza nace mishi, a'a bana ji ya sake daga

ido ya kalle ni ya ce, to ai ni ina ji, nayi maza na

tsuke fuska na ce mishi ba fa na zabi biyo ka da

nufin in biyo ka ba ne.

Cikin natsuwa ya ce min ai na sani, na sake

tsuke fuska na ce, to ko da na biyo ka akan

kuskuren ba zaa zan yi ba, komawa zan yi. Ya sake

cewa na sani, ya sake saurarawa ko zai ji zan sake

fadin wata magana, sai yaga nayi shiru.

Sai naga yayi murmushi kafin ya ce min to

amma ai ko za ki koman tunda ba ki kai ga tafiyar

ba ai ina ganin ba zai hana in nace nayi marmarinki

kiyi min yanda ki ka saba yi min bä ko kuwa. Nayi

maza na kara tsuke fuska, kafin na ce mishi a'a, ya

ce to shi kenan sai da safe.

Washegari tun safe Goggo Ayalle ta dawo

gidan a dalilin aiken da Baba Tanimu yayi na a

dauko ta, tana dawowa kuwa ta maida ni dakinta,

wunin ranar har dare ban gane na gama gaisawa da

mutanen gidan nan ba saboda yawansu.

Don haka kowa na gani kawai sabuwar

gaisuwa nake yi mishi, sai in shi ne ya ce min ai

38

dazu mun gaisa in ce mishi to.

Karba sosai Goggo Ayalle tayi min, ta yi ta ina

taka saka dani, komai hannunta ya kai kan shi in

dai ta daga taga naci ne miko min shi take yi, ungo

ki ci, sai in ni ce naga zan kwari kaina in ce mata

na koshi.

Sau goma kuma in ta kalle ni zata yi murmushi

ta ce, oh haka rabo yake har da rabon aurenki cikin

al'amuran da suka kai Adamu garin nan suka

zaunar dashi, kin san shi rabo ba karamin al'amari

ba ne.

Sai kawai nima in taya ta murmushin da take

yin sai dai ban ce mata komai, can anjima kuma sai

ka ji tana sake tambayata in ce ko dai manyan duka

lafiya? In sake cewa lafiyarsu kalau, tamfar dazu

bata tambayí lafiyar tasu ba.

A haka muka wuni har dare ina idar da Sallar

Isha'i ta kalle ni ta sake nuna min gadon da na wuni

akai ta ce min hau kiyi barcinki ki huta gajiya, kar

yan hiraa suce zasu dame ki, na ce to. Na sake

dalewa gadon nayi kwanciyata, zuwa can naji Ado

yana kirana, nayi kamar ban ji shi ba, ya matso

kusa da kofar Goggo yana tambayarta.

"Goggo Humaira tana kusa ne?"

Goggon tayi maza ta sauka daga nata gadon ta

39

leka tana tambayarshi wani abu ka ke so ne

Adamu? Ya ce a'a Goggo, sai da safe. Abin da

kawai ya fada kenan sai na jiwo Baba Tanimu daga

dakinshi yana fadin "Yau ga wani al'amari, wannan

fa shi ne girman kwabo.

An gira ba ayi hankali ba, yaro yana kwalawa

matarshi kira kina ji tayi shiru ba kiyi mata magana

ba, ya taso yazo har kofar dakinki yana tanbayarki

ita kin ce wai in wani abu yake so ya gaya miki, to

in ita yake so fa?

Na ce in yana da bukatarta ne ma ya gaya

miki? Goggo tayi maza ta ce au, to ai bangane ba

ne. Ke Aisha tashi-tashi je ki maza mijinki yana

kiranki."

A kan dole ta fito da ni daga dikin na shiga

dakinmu na samu Ado yana zaran jiran shigowan

nawa, gasasshiyar kaza ne a gabanshi, a gefenta

kuma flaks ne na ruwan zafi, ban kalle shi ba na

wuce na hau katifa nayi kwanciyata, ya biyo ni da

kallo fuskarshi ta bayyanar da rashin jin dadin shi

kan yanda nayi.

Yayi karfin hali ya hadiye fushinshi tashi mana

Humairaa nayi kamar ban ji ba, yayi tayi min

magana nayi shiru kamar ba dani yake yi ba, ke ni

fa kin san bana son irin wannau wulakancin na ayi

40

tayi miki magana kina yin banza da mutane, ban

tanka mishi ba, ban san yanda aka yi ba sai kawai

naji ya cafko hannuna ya murde.

A firgice na kwallara kara saboda zafin da naji,

na kuma yi maza na kame bakina nayi shiru saboda

funawar da nayi cewar a bakon wuri muke ko kuma

ni din ni bakuwa ce.

Daga cikin dakin Baba Tanimu da ke

makwabtaka da namun naji an yi gyaran murya

alamar dai yin kashedi.

Ado ya hakura ya gyara ya kwanta, ni kuwa

naci gaba da zama a kan katifar ina kukan sharbe

tare da shisshika a hankali sai dai shi Ado shiruu

kawai yayi amma yana ji na.

Ana cikin haka wani irin hadari ya taso mai

matsanancin iska da guguwa da rugugi mai

tsananinn firgitarwa har wani bai iya cin motsin

wanda suke tare, sai in yayi motsi ne da karfi nayi

maza na gyara na kwanta da nufin yin shiru kamar

yanda shima Adon yayi, sai kawai naga ya juyo

gare ni.

"Kin fasa kukanne?" Nayi kamar ban ji shi ba,

Ni fa yau ba zan iya irin kwanan da muka yi jiya

ba." Ya miko hannu zai taba ni, nayi maza na ce

mishi "Gaskiya ni fa ba zama nazo.yi ba, ko yau

41

dinnan da ina da kudin mota da tafiyata nayi."

Ina gama fadin hakan ya cafke ni, bai saurari

ihun da nake yi mishi ba saboda yasan ba zai kai ga

kunnen Baba Tanimu ba. Sabuwar iskar da ke

kadawa ga tsawa da rugugi, watakila ma ya dade

yana baccin shi, gane hakanne yasa ni barin ihun na

koma yi mishi bayani.

"Ni gaskiya tun da muka zo fa cikina yana

ciwo, ban gaya maka ba ne kawai." Bai saurara ba.

Na kwana da matsanancin ciWon cikin da yay

dalilin da na kwana ina murkususu daga kan katita

in koma kasa, na rasa in da zan sa kaina in ji dadi,

nayi kuka har na hakura nayi shiru.

Ado yayi nadamar abin da ya faru tsakanina

dashi, yayi nadamar tilasta min da yayi a haka

muka kwana daga ni har shi babau wanda ya samu

runtsawa.

Ana fitowa daga sallar Asuba muka kama

hanya zuwa asibiti da ni dashi da Yaya Jafaru da

Ruwailah, saboda tun dare ya shaidawa Baba

Tanin halin da nake ciki, tun daren kuma Yaya

Jafarun yayiwo aron mota wurin wani abokinshi

don ma Baba Tanimu ya hana tafiyar daren ne yaa

ce a hakura ayi sallah tukunna.

Asibitin Malunfashi ya kai mu, shi ne wai yafi

42

girma a nan kusa, gwajin farko da Likitan tayi min

tayi bayanin ciki ne ya lalace ya fita daga cikin

mahaifa, sai dai bai shiga ya fadi ba, saboda haka

zasu wanke shi ya fita don in ba haka zan yi ta

wahala da shi kafin ya kai ga fita.

To amma me ya kawo haka Likita? Ado ya

bukaci sani, tayi ta lissafo dalilai ciki har da tafiya

mai tsanani ko kuma bacin rai ko aiki mai wahala

shi yasa yawanci muke hana mata masu karamin

ciki ko kuma cikin da ya riga ya kai watanni

bakwai yin irin wadannan abubuwan, ku kuma

maza muke rokonku da ku rinka tausaya musu.

Daga Ado har Yaya Jafaru da Ruwailah sun

gamsu da jawabin nata.

Aka yi min wankin ciki aka sallamo mu bayan

La'asar, duk da Ado yaso a bar ni in kwana wai a

kara kulawa dani sosai aka ce babu gado.

Mun iso gida gab da magriba, kai tsaye dakin

Goggo Ayalle aka kai ni, wacce ta yi fada mai

tsanani akan wankin cikin da taji an yi min, ina

dalili yarinya ko haihuwar fari bata yi ba za aje ana

kakaba mata karfen nasara

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login