Showing 3001 words to 6000 words out of 35296 words
Chapter 2 - MIJIN TACE Book 3 Hausa Novels by hafsat Sodangi.docx
in rada mishi cewar ni fa ba
16
da gaske nake yi ba, zabin da nayi na cewar zan bi
Ado nayi hakan ne kawai don in sanya Mama bacin
rai, amma babu wanda zan iya fuskanta da maganar
tawa ya saurareta."
Gaba daya wuri ya hargitse, hankula sun kai
matuka wajen tashi, Baba Yahya da Babana sai
faman rirrike su ake yi saboda Babana ya koma
taya Mama zagin Inna da danginta da take yi, yana
tayata kiransu munafukai masu raba dan uwa da
dan uwa, shi kuma Baba Yabya yana rama musu
To ma na fasa tunda akan wannan..
Cikina ya bada wani irin sauti na kulułulu!!!
saboda tsoron kalmar da zai karasa zancen nashi da
ita, sai naji ya katse zancen nashi ya ce, na fasa ba
in da zata zabin da tayi zabin banza ne, ban yarda
ba, ba za ta bishi ba, a zuciyata nace tafi nono fari,
Baba da haka kayi tun farko ma da ba a tsaya
wannan kace-nacen din ba, tunda dai ni din ai
mallakinka ce.
Zancen Baba Yahya ya katse ni da na ji yana
fadin, wannan ai shi ne karya ba za ta zabi mijinta
ka hana ta bibn shi ka kashe mata aure ba, saboda
kawai matarka tana son ganin hakan, in zaurawa ka
ke son gani a gidanka ai gasu nan ka samu."
Mama ta sake kurma wani uban ihun, wai Baba
17
Yahya ya yi wa 'ya'yanta gori, bai saurare ta ba
balle Babana, ganin shi kawai naga yayi ya damko
hannuna yana jana zuwa inda Ado ke makure a
jikin bango.
"Yau ka ce kana son tafiya da matarka?"
Da sauri Ado ya ce mishi "Eh." Baba yana jin
haka yayi maza ya danka mishi ni a hannunshi, tare
da fadin "Gata nan Ado na baka ita ku tafi, ka ike
min ita amana ka sani iyayenta ma hakuri da su
muke yi, to balle kuma ita yarinya ce yar karama."
Ado yayi maza ya kama hannun nawa ya rike
da iyakacin karfinshi, tanfar yana tsoron kar a
kwace mishi ni.
"Wuce ku tafi." Ya bani umarni mai karfi,
daidai lokacin da Babana yake ta sakin wasu
maganganu masu tsanani su Mallam Harisu suna ta
faman bashi hakuri, na kalli Baba Yahya ina kuka,
na ce mishi "Ba zan bi shi ba Baba, ba zan bishi ba,
ni dama ba da gaske nake yi zan bi shi..."
Wani irin gigitaccen mari ya dauke ni dashi, sai
da naga waikiya ta haske ni gaba daya, Ado yayi
maza ya kankame ni a jikinshi da sauri yana baiwa
Baba Yahya hakuri.
"Kayi hakuri Baba, kayi hakuri." Yana kuma
tattare ni da fadinshi don gudun kur hannun Baba
18
Yahyan ya sake kawowa gare ni, gigitaccen marin
da Baba Yahya ya kifa min ya katse min komai,
hatta kukan da na dade ina yi, na daina shi na koma
zare ido saboda ban taba jin mari mai tsananin
wannan ba.
Ado ya tasa ni a gaba, muna fita daga gida ina
jin Baba Yahya yana fadin, "Ai ko za ki shide ba
shure-shure ba sai ya tafi da ita, ai ba zai zabe ta ya
bar ki ke da mijinki da duk abinda ki ke ganin kun
mishi ya ce ita kadai yake so sannan ku hana shi ita
ba, yana sonta tana son shi ke ki ka kulla auren da
nufin sharri don ki cutar da ita, kisa shi ya
wulakantata.
Amma' abin mamaki sai gashi zaman da yayi da
ita na kwanaki tamanin da bakwai kacala sun sa shi
ya zabe ta ita kadai ya barku ke da mijinki da duk
abin da ku ke ganin kuna dashi.
A kofar gida Ado yana kokarin shigar da ni
cikin motar da ke tsaye tana faman jiranshi wadda
shatarta ya dauko, sai ga su Liman da Mallam
Harisu, har da Baba Yahya sun fito. Mallam Harisu
da Limar suka wuce, Baba Yahya yana yi musu
godiya.
Shi kuwa Baba Yahya yazo ya tsaya jikin
motar hannayenshi duka biyu ya saka cikin
19
aljifayen shi ya fito da duk abinda ke ciki ya
mikowa Ado tare da fadin sai kayi hakuri da
wannan baka ba da lokacin da za'a yi maka shirin
tafiyar taku ba.
Hannu biyu Ado ya saka ya karbi abin da aka
bashin cikin ladabi na gode Baba, Ubangiji ya kara
girma."
Baba Yahya yana tsaye a kofar gidanmu har
motarmu ta bace daga unguwarmu, Ado yana ganin
motar ta bar kan titinan daga cikin gari ta fada kan
babbar hanyar da ta nufi Kano ya saki wani irin
sansanyar ajiyar zuciya tanfar dai da a tsorace yake,
ko yana tunanin za'a biyo shi ko a tare shi a kwace
ni.
Lokaci mai tsawo yana cikin wata irin
matsananciyar natsuwa kafin daga bisani naga ya
shafa fatiha, don haka na gane addu'a yayi yana
shafa fatihan kuwa ya juyo gare ni, kamo ni yayi da
hannayenshi duka biyu ya jawo ni ya kwantar da ni
kan kirjinshi, ya kuma dora hannunshi guda daya a
jikina don ýa tilasta ni kwanciya kan kirjin nashi.
Cikin natsuwa ya soma yi min magana.
"Kin taba ganin wanda ya zabi yin aure ya
tozarta? Ai abubuwa guda uku Aisha, Ubangiji ba
ya tozarta mai yin su, alkawari ne ma yayi cewar
20
zai taimaki mai yin su, na farko a cikin su shi ne
aure, sai Jihadi sai kuma bawan da aka rubutawa
biyan wata ka'ida don ya samu 'yanci ya zama da,
don haka babu abinda zai same ki sai alheri.
Wata irin tafiya muka Yi wacce bazan iya
tsayawa ina bada labarinta ba saboda tsananinta, ya
kai duk in da ya kai, daga ni har Ado babu wanda
bai wahala ba, iyaka dai shi ya yi tashi wahalar ne
cikin farin ciki da gamsuwar samun yanda yake so,
babu kuma wata alama ta damuwa a fuskarshi,
yayin da ni kuma nayi tawa wahalar cikin
matsananciyar damuwa ga bacin rai ga ciwon ciki
mai tsananin gaske.
Ado ya rarrashe ni ya gaya min duk wata
magana da zai gaya min, har ya gaji yayi shiru ya
zuba min ido, amma ban daina kukan da nake yi ba,.
babu abin da yafi damuna irin tafiyar da nayi na bar
Innata da na san haka zabin da zan yin zai zama daj
ban yi shi ba.
Na za6i bin Ado don in batawa Mama ita kadai
rai daga baya in an tashi in sulale in yi tafiyata in ki
komawa gidanmu, sai na tabbatar ya bar garin
tunda nasan ba zai sake zama ba, gashi hakan ya
jawo min al'amura masu tsananin gaske, na farko
ya haddasa 6acin rai mai tsanani tsakanin Babana
21
da Amininshi Baba Yahya, a dalilin furta kalmomi
masu zafi da Baban nawa ya fusata yayi tayi a
kaina da mahaifiyata, da ma danginta gaba daya.
Hakika nayi wauta mai tsanani da nayi nufin
6atawa Mama rai ba tare da na tunawa kaina cewar
bacin ran Mama yana nufin ɓacin ran Babana ne
ba, sannan hakan yayi sanadin da ni din zan bi Ado
kauyensu alhalin m din ban san komai game da
zaman kauye ba, ba kua duk wadannan ne suka fi
kuntatawa zuciyata ba, irin tafiyar da nayi na bar
Innata, ko a wane hali take ciki ko a wane matsayi
ta dauki tafiyar tawa? Wannan shi ne abinda yafi
damuna.
Motar ta sake yin tsalle ta sake faduwa cikin
wani ramin a karo na biyu, nima na sake yin maza
na kankame marata da hannayena duka biyu tanfar
dai yanda nayi a farkon fadawar nata, haba Malla
Haruna a rinka kokarin kaucewa ramukan nan
mana.
Mallam Haruna ya dan yi tsaki kadan alamar
shia ba a son ranshi ba ne hanyoyin namu ne sai
hakuri in ban da haka da gangan ai mutum ba zai
rinka fadawa cikin ramukan ba don Sukurkuta
mishi motar zasu yi babu halin kayi ƴar tafiya sau
daya sau biyu sai ka raba abin da ka samu tare da
22
makanikai.
Ni kam Suna maganarsu ina jin su ina kankame
da cikina ina sauraron abinda zai sake faruwa,
tunda daga sanadin fadawa ramin farko ne cikina
ya urda ya kama ciwon da nake ta fama da shi.
Da kaina na lallaba na sake jingina jikina a
jikin Ado, maimakon jawo nin da yake yi ina ki
saboda dunkulewar da naji marata tayi a wuri daya,,
da sauri Ado ya dora hannunshi a jikina ya kara
tallabe ni na kwantar da kaina a kirjinshi ya cusa
hancinshi da bakinshi a kan nawa ya dan sumbace
shi kadan.
A hankali kuma cikin natsuwa da kuma sanyin
murya ya soma yi min magana a hankali.
"Ina son ki Aisha." karo na biyu kenan da na
taba jin sunan nawa sak a bakin Ado kafin yau, bai
taba ba da Humaira ya saba kirana, ban damu ba
duk abin da za a fada a fada, in ma dandani
haukaci akayi min oho, ni kam ina so, ina sonki ban
kuma zabe ki don in 6atawa wani rai ko don in ba
wani haushi ba.
Ban zabe ki akan lalura ko akan kuskure ba, na
zabe ki ne don ina sonki don na riga na gane
rabuwa da ke ba zai haifar min da da mai ido ba,
don haka na zabi rabuwa da komai da kuma kowa
23
don in same ki ke kadai, don nasan abinda kawai
zan yi kenan in samu kwanciyar hankali da
nutsuwar da nake bukata.
Don haka ban ga dalilin wannan bakin cikin da
ki ke tayi ba, in don tsoratarwar da aka yi tayi miki
ne a kan kauye da kuma gidanmu ni din ai namiji
ne Humaira, nayi miki alkawarin babu wata wahala
da zata dunfaroni in barta takai ga taba min ke face
sai nasa dantsena na tare miki ita.
Ai ban rabo ki da gidanku da iyayenki don in
wahalar da ke ko don in zama sanadin wahalarki
ba, na rabo ki da su ne don ina son rayuwa tare da
ke, ina son ganinki a tare da ni, ina son mallakar
jikin nan naki, tó a na menene za ki yi ta wannan
6acin ran?
Ko kina so ne ki nuna min cewar ke din ba kya
sona? Ko kuma ba kya bukatata? Tabbas na sani ba
zan iya amsa wadannan tambayoyin na Ado da
kalmar eh ba, in dai har gaskiya nake nufin fadi. To
amma iyayena fa? Musamman ma Innata, Inna tuna
girma da darajarsu da kullum mai babban allo yake
gaya min da kashedin da yake yi min a kansu, na ba
a karo tsakanin kwai da dutse.
Sai in ga don in zauna da su lafiya in rabu da su
kuma laiya zan iya hakura da duk wani abinda
24
nake so amma ina amfanin wannan abin da ya faru
tsakanina da su a yau? Na tafi Babana yana ta furta
munanan kalamai a kaina, Inna kuwa ko sallama
bamu yi ba balle in san halin da take ciki, amma
Ado wai kar in tsananta bakin ciki.
To me zan yi? dariya? Nan da nan naji haushin
shi ya kama ni saboda ganin da nayi tanfar kanshi
kawai yake so..
"Dan sha ruwan nan ki jika bakinki, in ma ba
za ki ci wani abu ba kin ga ai tunda ki ka yi amái ba
ki sake cin wani abu ba, na ce uh'uh.
Kalaman Ado a kowane lokaci na rarrashi ne
da fadin maganganu masu dadi, don dai ya samu
yaga hankalina ya kwanta, ni nasan babu abin da
kalaman Baba zasu yi miki don kuwa baki yi mishi
komai ba, fushi yayi da fushin wani, Inna kuwa
nasan ba za ta taba jin zafinki ba, balle tayi fushi da
ke, balle har taje tana yi miki wasu munanan
kalamai.
Nayi Imani a daidai wannan lokacin da take jin
kalaman dan Baban yake fadi a kanmu ita tana yi
mana addu'a ne tana neman mana kariya daga duk
wani sharri ko wata fitina, tana kuma neman mana
alheri wu Ubangiji shi ne kuma abin da zai same
mu Humaira."
25
Mun iso Kano ne misalin karfe shida da kwata,
shirye-sbiryen saliar magriba ake tayi don a
wannan lokacin ita magriba din ana yinta ne shida
da rabi a mafi yawancin wurare.
"Samu wuri mai kyau ka tsaya Mallam Hlaruna,
sai mun yi sallar magariba da Isba'i mu wuce."
Mallam Haruna yayi maza ya ce, "Kai a'a
Mallam Ado, kar muyi haka don kuwa muna da
sauran tafiya mai tsawo ban da haka ma ina ganin
tanfar gara wannan hanyar da muka baro a
bayanmu, kan wanda zamu hau nan gaba."
Ado yayi murmushi ya ce, "Ina ganin dai ka
dade baka je Katsina ba Mallam Haruna, in ba haka
ba ai mu hanyoyinmu masu kyau ne."
Kofar wani gida Ado ya kai ni, sai da yayi
sallama da mai gidan suka gaisa sannan ya roke shi
in shiga wurin iyalinshi in yi sallah, don a kan
hanya muke, ya ce babu komai. Na shiga shi kuma
ya koma sai da na idar da sallar naja carbina na jira
nayi Isha'i bai dawo ba, na huta naji dadi sosai don
ban saba irin wannan doguwar tafiyar ba, bas taba
yin ta ba.
Iyakacina giyade, ban taba wuce nan ba, sa
zuwa can maigidan ya shigo yana gayawa iyalinshi
wadanda suka yi matukar karrama ni cewar
26
bakuwar nan ta fito suka ce to, suka rako ni har
kofar zaure sukamiko min leda mai dauke da robar
da suka cika min da kunun aya, nasa hannu biyu na
karba nayi musu godiya.
Ado ya tasa ni a gaba zuwa in da motar mu
take, ina shiga ciki na zauna ya miko min wasu
kwayoyi guda biyu tare da kwalbar Coke ya ce
"Karbi ki sha saboda aman da kike yi." Ban yi
mishi musu ba na karba nasha, ya fita akan zai
maida kwalbar, bai dawo ba sai bayan minti ashirin
da biyar.
Mallam»Haruna yayi tsaki har ya gaji.
"Dabai fa mutumin nan ya ce zamu je, amma
yake yi mana irin wannan bata lokacin." Gabana ya
yanke ya fadi jin sunan garin da Mallam Harunan
ya ambata, ban taba jin sunan garin ba, iyaka kuma
dai ban ce mishi komai ba, tunda ba abokin magana
ba ne.
Ado ya dawo rike da ledoji guda biyu ya mika
wa Mallam Haruna daya, ya ajiye mana daya
Mallam Haruna ya karba yana godiya, yana ganin
dankwaleliyar kazar da ke ledar tashi ya mance
abin bacin ran da Adon yayi mishi, duk da tabbacin
da Adon ya bani na ba zan sake yin amai ba komai
naci, ban yarda naci koman ba, in ban da kunun
27
ayan da mutanen nan suka bani wanda yayi min
dadi ba kadan ba.
A wannan lokacin na dan samu natsuwa da
kuma saukin da nayi bacci, wata kila don sanyin
dare da ya sauka wata kila kuma don saukin aman
da na samu, gashi har na samu nasha kunun aya ya
zauna amin.
Ban sha wahala ko naga tsananin tafiyar ba
kamar yanda direban ke ta magana don kuwa na
farka ne a inda naji Ado yana ce min "Kin faraka a
daidai Humaira, daga wannan garin da ki ka ga
muna wucewa sai kaute guda daya ne a gabanmu
(Tukunya) daga shi sai (Dabai).
Can baya kuwa in da muka baro, kin yi bacci
ne a kusa da garin (Dayi) daga nan sai Malumfashi
sai Kafur sai Sabuwar Kasa, sai Gozaki sai Dabai,
to amma kin san akwai kananan kauyuka a
tsakanin garuruwan sai a hankali za ki san su."
A zuciyata na ce, in na zauna a garin kenan,
don ni kam a zuciyata ina ganin tanfar babu abin da
ya dace dani irin komawa gida in je in roki Babana
da Innata gafara kan bacin ran da na san na sanya
Su.
Ado ya saki wani lallausan murmushi bayan
yayi ajiyar zuciya, tare da hamdaia ga Ubangiji.
28
"Ga Dabai Humaira mun iso." A hankali ya soma
rada min a kunnena, bude ido ki ga garin mijinki
Humairah gari da zai zamo shi ne garin 'ya'yanki,
ina son Dabai Humaira, ba wai don garina ba ne
kawai, a'a mutanen garin mutane ne masu neman
na kansu, masu karamci da ganin girman juna.
Mutanen Dabai jarumai ne manoma ne wasu da
yawa kuma 'yan kasuwa, in ta fannin ilimi ne kuwa
muna da manyan Malaman addini a ta bangaren
bokon ma ba a bar mu a baya ba, mutanen mu da
yawa suna nan warwatse cikin ma'aikatun
Gwamnati suna aiki tun daga LocalGovernmnent
har zuwa State da kuma Federal.
A daidai lokacin da Ado ke ta faman wasa min
garin nasu na bude ido tarwai, wai domin in ga
abinda yake gaya min din, tunda an yi sa'a farin
wata ya haske ko ina. Ban ga komai ba in ban da
dogayen bishiyoyin da ya ce min na kuka ne, sai ko
filayen da yake ta nuna min yana fadin duk nan da
ki ke gani ba jeji ba ne, gonaki ne na mutane. Bari
damuna ta zauna sosai ki ga abin mamaki, a
zuciyata na ce ka gani dai.
Shi garin Dabai gari ne da yayi sa'a babbar
hanya ta ratsa shi, ta ko ina kin ga wannan hanyar
da muka biyo'ai kin ga garuruwan da muka baro a
29
bayanmu, to» näii gabanmu in ta wuce Dabai zata
wuce, mararrabar Danja ta tafi har Hunkuiyi taje
Basawa ta isa Zariya, kin ga ta tafi har Kaduna
kenan.
In kuwa a mararrabar Danja ki ka tsaya ki ka bi
hanyar da tayi dama, to za ki isa kauyen Dan Mai
gunta ki wuce kije har Danjan, in kuma ki ka nufi
hagu to zaki je garuruwan Kudan daga nan kije har
Makarfi in ki ka fada babban titi ma sai ya maida
ke har Kano, ita ce ma hanyar da yan kasuwanmu
suka fi amfani da ita."
Ya sake kallona cikin murmushi yana fadin
"Ba za ki gane dadin Dabai da