Showing 12001 words to 15000 words out of 35296 words

Chapter 5 - MIJIN TACE Book 3 Hausa Novels by hafsat Sodangi.docx

da dinner set da kuma

wasu kwanuka.

Ga bokitaye da randa da dai wasu tarkace, ga

kuma kayan abinci dan daidai gwargwado ko a ina

yaké samun kudin da yake kashewa? oho!

tambayar da na.yi wa kaina kenan, a zuciyata dai

nasan babu abin da yafi min ban dakin nan dadi,

don na samu kebabben wuri har da bayan gidan

hadakan da ban saba da shi ba yake sani jin kiyan

yin wanka.

Nayi maza na kammala abubuwan da zan yi

nayi wanka saboda jin dadin ganin bandakin na

zauna na shafa mai nayi gyara irin yanda na saba yi

a gida, gaba daya dakin ya gauraye da kamshin

kayan shafan da nayi amfani da su.

Ado bai shigo ba sai da yayi sallár Isha'i shima

57

yana shigowa bandakin naji ya shiga yana wankan,

Cikin zuciyata na ce ashe shima da kwiyan wankan

yake ji, don tunda muka zo ban gan shi yana

wankan dare ba, yana shigowa dakin ya sanya

hannayenshi duka biyu ya sure ni.

"Kina lissafin kwanakin aiko? Kina lissafin

kwanakin da nayi ina hakuri ina fama da shan jar

kanwa da lemon tsami? Tuni na langabe mishi na

sa shi ya mance duk wata damuwa in har yana da

ita da kuma wahalar da yake wuni cikinta, wanda

nasan ya manta rabon da yayi irinta, duk wani abin

da nasan zan yi wa Ado rannan da zai sa shi jin

dadi ko farin ciki nayi mishi.

Na kuma yi matukar yin hakuri da shi, ban

Duna mishi gajiyawata ko korafi kan al'amuranshi

ba, ba don komai ba sai don zuciyata ta riga ta

yarda ta amince da cewar Ado mijina da na kuduri

aniyar zama dashi a kowane hali yake ciki in

taimake shi, in ba shi hadin kan da da yake nema a

tare da ni, in jiyar da shi dadi gwargwadon abin da

zan iya yi.

Saboda na yarda na amince sona yake yi da

zuciyarshi guda daya dawo da ni kauyensu da yayi

kuma ba laifi ba ne gurinshi na asali yazo da ni

mafi yawancin wahalar da yake yi kuma na yarda

58

mati yawancinta tawa ce.

Sallar Asuba ya fita yayi ya dawo ya same ni

nima ina sallar, nayi zaton komawa zai yi ya dan

kwanta kafin ya fita tunda ni dai nasan kashi uku

bisa hudun daren idonshi biyu ne, amma sai naji ya

ce min ni na tafi bai ma jira amsawata ba.

Na idar da sallata na koma na kwanta, sai da na

dan yi bacci kafin na tashi na duba abin da muke da

shi na abinci na gama gyaran wuri da tsabtace shi,

nayi wanka nazo na shirya abin karyawa, na karya

na gyara jikina na jawo kofar wurina na rufe don

kar kaji su shiga suyi mana ta'adi.

Na fita naje na gaida manyan gidan duka kafin

na wuce can tsakar gida wurin haduwar matan

gidan. inda ake da babban fili sosai da ke dauke da

wurin girki a can nesa ga runbuna a can wani gefen

ga in da ake aikace-aikacen wanki ko wanke-

wanke, wani gefen can kuma daka ake yi da nika

ga kuma wata katuwar rumfa da ke tsakanin wasu

manyan bishiyoyi in da ake zama ana yin hira.

Zaman tsakar gidan nan yafi komai dadi, don

wuni ake yi ana raha ana barkwanci ana kwashewa

da dariya, shagala nayi a cikinsu ana tayi ina kallo

har ina taimakon masu daka da yin tankade, ban

ankara ba sai naji ana kiran sallar azahar.

59

Gaba daya aka watse kowa ya nufi wurinshi

don yin sallah, kofata tana rufe kamar yanda na

barta a zuciyata na ce yau ma Ado bai dawo ba

kenan, na idar da sallah naje na karbo fura nazo na

dama na ajiye mishi na koma wurin matan gida, na

ce ba zan iya zaman kadaici ba, in ya dawo ya kira

ni ko kuma ya sha furarshi ya tafi.

Ado bai shigo ba sai bayan 'sallar magariba, ban

taba ganin tashin hankali da bacin ranshi irin na

rannan ba, kina nufin ba za ki iya zaman wurinki

ba? To me yasa ki ka yarda ki ka dawo? Kina nufin

ai ba zan dawo gida in same ki a wannan dan

tsukakken dakin namu kina zaman jiran dawowana

ba?

Sai in ina son ganinki in biki cikin mata ina

kwala miki kira? Ke ba ki san hakkina ba? Ba ki

san abin da za ki taimake ni da shi ba? Fura ce zan

rayu a kanta Humaira? ba ki ga kamar dandanon

abincinki a bakina zai yi matukar yin amfani a gare

ni ba?

To bari in gaya miki dama kin bi a hankali

wannan taron nasu da ki ke gani-randa suka tashi

tambayar junansu gulma suka sa dake a ciki abin

zai baki mamaki, ke baki taba zaman gidan yawa

ba duk fitinar da ki ka sani a gidanku wasan yara

60

ne.

Gabana ya yanke ya fadi, jin da nayi Ado ya

kira fitinar gidanmu wasan yara na ce to ai gara ka

maida ni gidan namu, abin da kawai na fada kenan

Ado yasa hannu ya make ni, kina hauka ne? Na ce

kina hauka ne da kullum za ki rinka kallona kina

cewa in maida ke gidan naku ke kina da gidan

zuwa ne?

Ko ba ki ji abin da maigidan ya fada ba sanda

ki ka zabi biyo ni? Ya ce kar ki sake taka gidanshi

saboda ya yafe min ke bai da sauran bukatarki."

Dukan da Ado ya yi min bai 6ata min rai ya

daga min hankali irin wannan maganar da ya soka

min ba saboda gaskiyar abin da Babana ya gaya

min ya gaya min. Nayi kukan bakin ciki har na gaji

a kasa da kwanaki talatin na barin iyayena da nayi

na biyo shi har ya fara goranta min abin da ya

farun.

Tabbas Ado namiji ne dama kuma nasha jin

Mama tana cewa shi namijin ba dan goyo ba ne, a

gabanshi kuma ma ta fada ta ce namijin ai ga ki

nan gashi nan.

Rannan dai kam kwanan da muka yin ba mai

dadi bane, don haka yana fita sallar Asuba na duba

inda 'yan kudina da nake tarawa suke, don yau kam

61

nayi niyya ko ba za su kai ni gida ba in dai za su

raba ni da garin Dabai, to zan tafi in yaso nasan

yanda nayi na karasa gida.

Ban ga komai a wiirin ba sai nera hamsin saura.

ya kwashe kwana biyu muna cikin wani hali ni

dashi, rannan ya dawo da yamma ya same ni, kin

gani Humairah mu biyu ne ni da ke a nan, ya

kamata in wani abu ya faru a tsakaninmu na rashir

jin dadi in na ba ki hakuri ki hakura, ba zai yiwu

ace kullum sai na kai wa Inna maganar za ki hakura

ba, in dai ba so ki ke mu rinka tayar mata da

hankali ba.

Kuka na soa yi sosai da sosai, kiyi hakur na

sani ban kyauta ba da nayi miki gori, to amma ke

kin ga yayi miki daidai kan maganar da ba ta taka

kara ta karya ba ki rinka cewa in maida ke

gidanku? Ai ya kamata ace ni da ke mun fahimci

wani abu a tsakaninmnu, shi ne zaman namu bana

rabuwa ba ne ba kuma na wulakanta juna ba.

Tsawon lokaci yana yi min maganarsu na

rarrashi da ban baki har dai ya samu ya gawo

kaina na hakura, muka shirya.

Tun daga wannan lokacin na rage shiga can

cikin gida don yin hira da matan gidan sai dai kawai

in gari ya waye in shiga in gaishe su dukan su in

62

dawo wurina in gama aikina in gyara komai in yi

wanka in gyara jikina, duk da 'yan kayan nawa har

yanzu guda uku ne sai lodin rigunan baccin da babu

damar in sanya su da rana sai da daddare in yi

mana abin karyawa irin wanda naga ina, so don

komai na abinci Ado kawowa yake yi, komai

tsadarshi kuwa.

Agada, Doya, Dankali, Wake, Kuskus,

Indomie, kwai, manja, Mangyada, Manshanu,

Shinkafar tuwo saboda masa da kuma ta wara duk

ina da su ina kuma da kayan tea zan kuma tashi da

safe in je in kar6o kunu da kosai, don ko ban je ba

za a biyo ni da shi, don haka nake girmama su in je

da kaina.

Shi kuwa Ado ka'ida ne kome nayi na karyawa

to sai na karbo mishi dumame wurin Goggo Ayalle

ya fara dashi kafin ya ci wani abin.

Kullum zai baro gonarshi sha daya ya dawo

gida, yana dawowa zai tube kayan jikinshi ya shiga

bandaki yayi wanka, ni kuma sai in tsoma su a

ruwa in wanke su in shanya in wanke mishi ranbut

din nashi na hannu da na kafan in jefa su kan rufin

dakin namu su sha rana, sai da yamma in kwashe

su.

Yana fitowa daga wankan zan sanya mishi

63

tabarma a inuwan dakina ya hau kai ya zauna in

gabatar mishi da abin da na tanadar mishi.

Yana ci muna hira yana bani labarin gonar

tashi, mafi yawancin lokaci in muka zauna a wurin

zai yi wuya mu tashi bai nanata gaya min maganar

da ya saba gaya min ba, ina so in samu damar dda

zan nuna miki halarcina Humaira, ina so in samu

damar da zan nuna miki cewar ni din da namiji ne.

In ya gama abin da zai yi ya kama hanya ya fita

sai kuma in sake zama in shirya mana abinda zai

dawo da azahar ya ci, hakan kuma bai hana ni

tanadar mishi furar da zai sha bayan yaci abincin."

Da daddare kuwa food flaks din mu nake

dauka in kai wurin da ake kwashe tuwon darea

zuba mana namu in yi musu sannu da aiki in dauka

in kawo mana in zuba mana manshanu da yaj1 muci

ba tunda ya hana ni cin abincin hadaka da su ba,

ban dai kara tsinkewa na lamarin gidan yawa na

kara tsorata da zaman gidan yawa ba irin ranar da

aka wayi gari a gidan ana tuhumar Ade 'yar dakin

Yaya Furera wai tayi gulma.

Ade kuwa kishiyar, Ruwailah ce ranar ne na

gane su matan gidan ba shugabancin matan sasansu

suke yi ba, a'a group ne kawai daga kowane sasa ka

ke in kana so zaka shiga kan hakan ne ma nake

64

ganin tanfar gaba dayansu kowacce kokari take ta

janye ni in shiga nata group din.

Ni kuwa kashedin da Ado ya yi min da kuma

ganin abinda ya faru a ranar don ma anyi sa'a Yaya

Baidu yana gida, shi ne ya fito yayi tsawar da

kowacce ta shiga taitayinta da ba a san abin da zai

faru ba, yasa na kara tsorata na kara kama kaina.

Sannu a hankali ma sai na daina zuwa karbo

mana tuwon daren, ina yi mana namu saboda

kullum Ado yana yi. min maganar ke ba taya su

aikin komai ki ke yi ba, amma sai kin je kin karbo

musu tuwon su, in nayi abincin daren dai ban sawa

kowa, amma na rana gaba daya tsofaffin gidan

nake sanya musu, su kuma yaran matan wacce ta

aiko danta ko tazo ta ce in zuba mata in zuba mata,

wacce bata aiko ba shi kenan. Don abin da ya ce

kenan, sai ko yaran gida da na gama suna wurina.

Yarda da bin ka'idojin Ado da nayi sai suka yi

dalilin da na samu wata irin rayuwa a tare dashi

wacce ta fahintar dani cewar ita mace ba wai tarin

dukiya ko wani kyale-kyale ne yake samar mata

farin ciki da kwanciyar har kalin rayuwarta ba, a'a

mijinta kawai.

Kullum ni da Ado a cikin tarairayar juna muke,

yana gudun bacin raina ina gudun nashi, yana

65

tattalin farin cikina kamar yanda nima nake tattalin

nashi, duk da matsanancin aikin da yake fama da

shi a gonakin shi ramar shi tayi matukar raguwa,

saboda yana da kwanciyar hankali a gida ina kuma

tarairayarshi da abinci mai kyau.

Rannan muna daki da daddare ni da shi, hadari

ne ya taso a gari ganga-ganga, tuni na fara sabawa

da irin wannan hadarin mai yawan iska da rugugi

gami da tsawa, shafa maina nake yi ban fasa ba, na

ce mishi kai-kawo hadarin nan ba irin namu ba ne

na can.

Idon shi yana lumshe ba tare da ya yarda ya

bude su ba, ya ce min eh ai ko ruwan ma ba daya

ba ne, in kin lura ai mun baro can ne damuna ta

riga ta kankama sai muka zo nan muka tarar

lokacin ake shuka.

Na kalle shi cikin natsuwa na ce mishi idon

naka yana ciwo ne? Bai yarda ya bude suba ya ce

min to ko ba sa ciwo Humairah tunda ki ka zauna

kika bar kirji a waje ai dole in yi maza in rufe su in

dai ba so ki ke in kasa cika alkawarin da nayi miki

na cewar shekaran jiya waccan da wacce ta wuce

da jiya da yau da gobe duk za su zamo ranakun

hutu ne a gare ki ba, don ki san in aka yi min alheri

nima na iya irin nawa alherin.

66

Nayi murmushi na ce eh, gaskiya ne kar ka

bude kai dai to dan bani hannunka in sa shi yayi

min wani aiki.

Ba tare da ya bude ba yayi maza ya miko

hannun yana laluben in da nake tare da fadin ungo

shi Humairah ungo hannun nawa karbe shi ki sanya

shi hidimar da ki ke ganin ta dace da shi ina kama

hannun nashi na ji Ado ya yi wani irin ajiyar zuciya

mai sanyi ban sake ganin yanda aka yi ba sai

ganina nayi a gefen shi a kwance ya zagaye ni da

hannayen shi duka biyu tare da yi min tambayar.

"Kin san wani abu ne Humaira?" Bai jira na ba

shi amsar na sani ko ban sani ba, sai ya soma

rattabo min bayaninshi, ke din mai alheri ce,

alherinki kuma yawa ne da shi saboda kina da kirki

ga ki da abin arziki iri-irni, in ki ka ga dama sai ki sa

mutum ya rinka ganin tanfar babu ma wanda ya kai

ki abin arziki, balle ya iya fin ki.

Ban kula zancen na Ado ba, iya ka dai nasan in

dai barin shi ya yi yanda yake so shi ne kirki, ko

alheri to na yi mishi.

Muna cikin irin wannan zaman mai dadi ni da

shi wara magana ta taso a cikin gida, Ruwaila ce

take yawan yi min magana akan kankane ni da Ado

yake yi, yana hana ni mu'amalla da kowa cutata

67

yake so yayi dama haka tsofaffin maza suke yi ma

matansu, don su hana su fahimtar komai.

Shi Adamu ai ba yaro bane ga sa'o'inshi ne da

ke garin nan suna shirin yin surukai, ko ma daukan

jika kwanannan, don haka ga adashe nan na kafa ki

zo ki shiga, na ce ai ba zai bar ni ba, ta gallà min

harara "Ke ko iya zama da miji baki yi ba? Ai

kamewa za ki yi daga gare shi ba a sakan mishi jiki

haka sakakaka ba, in ki ka ga ya matsa sai kema ki

bijiro mishi da taki bukatar.

u da muke da shashun kishiyoyi ma muke yin

hakan muci nasara balle ke ke kadai? In ki ka saban

mishi da yanda ku ke din nan ai wahala za ki sha

tunda in ke kin yarda da hakan wata ba za ta yarda

ba, kin kuma san ana yin kaka in ya saida amfanin

gonarshi kishiya zai yiwo miki."

Kirjina ya bada sautin rugugugu! ban sani ba

ko itama ta gane tsananin tsoratar da nayi ne yasa ta

yin murmushi, ta ce "Lah, to wannan ai ba wani

abu ba ne, mu nan ai haka ake yi kaka tana yi in

aka cika runbuna da hatsi, to abinda yai saura sai

akai kasuwa a sayar sai ki ga an kawo miki wacce

zaku ci hatsin tare shi kenan."

Ta sake kallona ta ce min, to balle ko mijinki

da wahalar damunar nan bata hana shi manne miki

68

ba, ai kuwa kin san ya huta da kaka akwai magana,

na kuma ji Yayanshi yana cewa yayi noma ba

kadan ba, in kaga irin aikin da yake yi ma sai ka ga

tanfar da gayya yake yi.

Sammako yake yi ya riga kowa tafiya, sannan

duk a can ake baro shi, na ce mishi babu wata

gayya so yake yi yayi gini ya kuma kara wani

auren, ai kuwa dolen shi yayi aiki tukuru." Na zuba

mata ido kawai ina kallonta don kuwa ban taba jin

maganar da ta dame ni ta daki zuciyata ba irin

cewar wai Ado zai yi min kishiya, to ni kuwa

kenan ribar me naci a biyo shin da nayi?

Ta salke kallona cikin natsuwa ta ce, yarinya

kamar ki ya kyale ki kina yawo cikin wasu

zulunbun dogayen riguna da tun suna baiwa

mutane sha'awaa har sun daina sun maida ke kin

zama tanfar wata tsohuwar Babarbariya."

Kalaman na Ruwailah sun yi matukar yin tasiri

a zuciyata, musamman da ta tabbatar min da cewar

su al'adar mazansu ne ma in sun cika runbu da

hatsi, to abinda ya saura in an kai shi kasuwa aure

ake yi.

Don haka nan na kame sosai daga yawan

sakewa Ado fuska, al'amura suka yi matukar

sauyawa a tsakaninmu, da yazo zai taba ni sai in ce

69

mishi cikina na ciwo, sai yayi maza ya kyale ni.

Rannan dai ta kure, mun kai wajen sati uku a

haka tunda safe Ado yake yi min magana,

rarrashina yake yi a dalilin bai son tilasta ni saboda

abin da ya taba faruwa a tsakaninmu, ganin da nayi

ya matsu kwarai mu fahirnci juna ya sani bijiro

mishi da maganar adashen da ake yi a gidan, wanda

ni kadai ce bana yi.

Cikin natsuwa ya kalle ni ya ce, "To kina da

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login