Showing 33001 words to 35296 words out of 35296 words

Chapter 12 - MIJIN TACE Book 3 Hausa Novels by hafsat Sodangi.docx

to shi kenan ni zan koma duk ranar da ki

ka gama wanka ki ka koma dakin naki sai in zo

muyi kwana bakwai tare kafin ki tafi, in kuma naga

raina ya 6aci da yawa ma sai in fasa tafiyar taka

gaba daya.

Da sauri na kalle shi "Me nayi maka?" Hawaye

suka soma ganagarowa daga idanuna, saboda

fargaba. Na matsa na matsu in je gida in ga Innata

da Babana dama sauran dangi baki daya.

To tun yaushe muke zaune ni da ke a haka

Humaira? Sai kuma ace ba za ki tausaya min ba ai

babu son kai a tsakanina da ke.

Goggo ta shigo ta same ni ina kuka ta soma

salati ina dalilin wadannan hawaye da suke zuba,

kai Ado me kayi mata? Ban yi mata amai ba

Goggo wai babu hali ne kawai ta ce ga yanda

za' ayi in ce a'a.

Ai kuwa dai ba zai yiwu ba. Goggo ta soma yi

min fada bakin cikin Ado ya kama ni don haka ma

150

ban sake daga ido na kalle shi ba balle in san

maganar da yake yi min.

Kwana uku bayan nan ya sake baro Danja ya

dawo gida ina ganinshi na tsuke fuskata, amma bai

hana shi yin magana ba. Wurinki nazo saboda naje

nayi wani sabon tunani.

Wanda zai yi mana amfani dukanmu, ki rinka

zuwa kina samuna adalci muna hira da daddare in

su Goggo sunyi bacci.

Na girgiza kai nuna alamar rashin yarda tare da

fadin ba zan...tun kafin in karasa maganar tawa ya

katse ni da wata irin rantsuwa na kuma san ba

dabi'arshi ba ne yin hakan.

To na rantse miki babu inda za ki in dai ba ki

yarda da wannan ba gaba daya na fasa tafiyar ki

zauna kawai tunda ni dama ba don ke na shiryata

ba, don nna ce nasan yanzu haka tana son ganinki

balle taji kin haihu.

Zata zo ta gan ki taga abin da ki ka haifa amma

duk da haka nasan in nayi waya na ce mata tayi

hakuri wani uzurin ya hana ki zuwa, ai zata hakura

tunda ita ba irin ki ba ce, ace mata baka da ikon

sarrafata.

Ba ka da halin ka ce mata ga yanda za'ayi ta ce

maka to sai a'a? sannan a rinka yimaka karyar

151

ladabi da biyayya ta musu? A haka fa muke zaune

ni da ke in kin yi min alherin kwana bakwai to sai

kin yi dalilin 6acin raina na kwanakin da ban san

adadinsu ba.

Cikin zuciyata kalaman Inna suka fado min

game da muhimmancin mijinka yasan alherinkato

ni yaushe ne Ado zai san alherina da kokarina akan

shi ya rike wannan yabon guda daya a mafi

yawancin lokaci yakan yabe ni ne a daidai lokacin

da abin yabon ya faru.

Amnma 'yan mintoci kadan bayan nan da zan yi

mishi wani kuskuren musamman ace kan abin da

ya shafi kankanshi ne ba zai tuna kokarina na baya

ba don haka naji hawaye sun fara zuba a idona a

dalilin zuciyata ta kuntata na fara kukan kenan sai

ga Goggo ta shigo.

Ni fa naji abinda ya ishe ni wai ina dalilin

wannan kuka ne na iya shege? Kai Adamu yayi

maza ya ce na'am Goggo ta ce na roke ka ka yi wa

yarinyar nan abinda take so.

Ya ce mata to Goggo ya tashi ya fita ya bar mu

ni da ita a dakin tana ta mita dama kin yi a hankali

namiji ne in ki ka zauna ki ka yi jegonki na gaskiya

ma ina ruwanki da shi yaushe za ki je kina daga ido

kina kallonshi.

152

Balle ki san abinda yake ciki ranki yana baci a

banza, taja tsaki ta wuce ta fita taje sanya mana

ruwan wankan yamma.

Mun kammala komai muna shirin kwanciya

Goggo kam ma tuni take ta faman gyangyadi jira

kawai take yi in gama baiwa Umahmah nono in

mika mata ita suyi kwanciyarsu da tuni tayi

barcinta, don tare suke kwana.

Muna cikin haka sai ga Ado ya shigo, Goggo

sai da safe ta ce mishi to sai da safe, ta amsa daidai

ta karbi yarinyar sunyi kwanciyar su.

Nan da nan ta soma minshari, ya mike tsaye

yana kallona muke ko? Nayi kamar ban ji shi ba, na

ce muke ko? Ko kina son yi min wulakanci ne? na

mike tsaye na fita na nufi wurin namu gabana sai

faduwa yake yi, shi kuma ya tsaya yana jawowa

Goggo kofarta wacce dama ba sakata take sanya

mata ba.

Ina shiga dakin na shaki wani irin kamshi mai

dadi ga kayaiyakin ciye-ciye iri-iri ya ajiye ga wasu

dunkakkun zannuwan da ban san da su ba a gefe.

Yana shigowa yayi murmushi, kici wani abu

mana ga kuma dinkunanki nan ki duba, na ce uh'uh

ai ba dadewa zan yi ba.

Bai kalle ni ba ya ce min dama kin saki ranki

153

don ba zan yarda da wannan dari-darin ba kin

gane?

A kan dole na saki jikina da Ado na bar shi

yayi abin da yaga dama, kuma wai maimakon yayi

la'akari da halin da muke ciki na satan jiki muka yi

na kawo mishi kaina bai damu be, bai yarda ya

hakura dani ba sai wajen karfe biyu na dare.

Ya rako ni na dawo dakin Goggo na hau gado

na kwanta yayi min sai da safe yaja kofar ya koma

wurinshi don yin wanka tunda ni kanm na riga nayi

nawa.

Na fara bacci kenan, Goggo ta tashen a dalilin

yarinya ta tashi na karbeta na bata nono.

Washegari da safe Ado ya shigo bayam munyi

wanka daga ni har yarinyar Goggo tana wurin

kosanta, zama yayi a bakin gadon yana wasa da

kafar yarinyar dake faman shan nono.

Zan fita amma ba zan dawo da wuri ba in na

dawo zan zo in sanar da ke don ki zo ki same ni, na

ce mishi kai...yayi maza ya katse ni da kin koyi ce

min to don ki rinka sarun cikakken lada.

Da daddaren kuwa sai da ya dawo ya zo yaja ni

muke je. Washegari ma haka tun ina tsoro sai kuma

na saki raina, rannan ina tare da shi mun yi matkar

sakin jiki mun shagala cikin al'amuranmu.

154

Gaskiyar magana ita ce daga ni har shi muna

Son juna, muna son kasancewa tare da juna, nakan

dai jawa Ado raine kawai in yi mishi yanga saboda

kawaici da kuma jan aji irin namu na mata.

Amma in ba haka ba kasancewa tare da shi

yana sanya ni jin dadi, ya sanya ni farin ciki da

nishadi, ya sanya ni in rinka ji da ganin tanfar

bayan ni din to babu wata. Barin komai yake yi ya

tarairaye ni ya gaya min kalmomi mnasu sanyaya rai

da tofar da zuciya.

Ya maida kanshi zama tanfar wani dan yaro ko

wani mara yawo a gabana, bai kuma gajiya kullum

muka shiga cikin irin wannan halin zai nanata

kalmarshi guda daya da ya saba gaya min ita ce ke

din matata ce Humnairah.

Ke ce matata kar ki taba ganin nayi aure a wani

lokaci kiyi tunanin zan mallaka mata kaina kamar

yanda nake mallaka miki ko zan zauna in yi mata

shagwaba da sakarci irin wanda nake yi miki.

Muna cikin wannan halin ne kawai naji Goggo

Ayalle tana kwala min kira a tsakar gida da

iyakacin karfinta, a cikin kua wannan tsohon daren.

A kidime fwarai nayi maza na bude baki da

nufin amsawa don in hutar da ita wage bakin da

take yi tuna yi min irin wannan kiran a cikin

155

wannan daren wanda nasan da wuya kwarai ace

akwai wani cikin mutanen gidan nan da bai ji kiran

da take yi min din ba, tunda dare ne, dare kuwa ba

raina motsi yake yi ba.

Ado ya yi maza ya dora tafin hannun shi akan

bakin nawa ya rufe da iyakacin karfinsh1, don hana

sautin maganar tawa fitowa sosai.

Ganin hakan ya sanya ni kokarin kwatar kaina

a hannunshi, tunda shi da kanshi ya ji kiran da ake

yi min daga inda muke din kuma muna jin muryar

Umahmah da ke ta faman canyara kuka.

Amma hakan bai sanya shi ya hakura ba, sai da

ya natsa don kan shi sannan ya kalie ni cikin wani

yanayi da yafi kama da na tsananin gajiya.

A hankali ya bude baki yana yi min magana, ke

ba ki da wayo ai shiru za ki yi abin ki sai ta gaji ta

koma daki sai kiyi fitowarki, na ce mishi to.

Amma duk da haka jikina ya kai matuka wajen

tsorata sai bari nake yi, ya zuba min ido yana

kallona ke menene haka? Na fa zunubi muka yi ba

ni mijinki ne ke matata ce.

Na ce mishi uhun, ai ni babu abin da yafi

damuna da tsayuwar min a rai irin bazuwar

maganara cikin gidannan da yanda za'ayi ta yadata

ana cancanzata, cikin sauri ya ce min ke kar ki

156

nemi ki maida mutane wadansu iri mana. Goggo

Ayallen da girman shekarunta ne ki ke cewa za ta

yada wannan maganar?

Kina so ki ce ita din bata san girma da lalurar

aure ba ne? nayi kamar in ce to ai a sanin girma da

lalurar auren nata ne taja ta tsaya a tsakar gida a

cikin tsohon daren nan ten wage balkinta tana

kwalawa sunana kira tanfar wata yarinya yar

Karama.

Bayan kuma tasan karamin mnotsi ma dare bai

raina shi ba, balle wannan ihun da ta rinka yi

wanda ba mutanen da ke cikin gidan nan ne kadai

za su jiwo ta ba, har makwabta sai sun ji.

Sai kuma na ce uhun, bari dai ma kawai in

kama bakina in yi shiru, kar in jawowa kaina wata

magana tsakanina da shi a wannan lokacin da na

san ba karamin abu zan fuskanta a cikin gida ba, in

fadi wata magana ya ce na yi wa matar Baban shi

rashin kunya.

Rako ni yayi nayi wanka yana tsaye yana jiran

fitowata sannan ya tasa ni a gaba ya kai ni har

kofar dakin Goggo Ayalle. Ya kalle ni cikin

natsuwa da murya mai sanyi ya ce min shiga kiyı

kwanciyarki na sake daga ido na kalle shi.

Fuskata ta bayyanar da alamar tsoro yayin da

157

zuciyata ke ta faman harbawa da sauri ya sake

kallona fuskarshi ta bayyanar da murmushi mai

yawa daina jin tsoro Humairah.

Ai ni mijinki ne ba wurin wani kika je ba kin

amsa umarnina ne na kuma gode miki iyakar

abinda Goggo zata yi in ma ranta ya baci ta ce ki

koma dakinki gobe shi kenan, amma ba za ta je

tana yáda wannan maganar ba.

Ai ita babbs ce, in kuwa haka zata yi to ai ai

yafi min na riga na gaji da wankan naki, lin gane?

Na gyada kai nuna alamar eh, don ni kam ko bude

bakin nawa in yi magana bana iyawa, saboda

kaduwar da nake yi.

To shiga mana, na kaile shi cikin natsuwa a

hankali cikin muryar da tafi kama da rada na ce

mishi, to jeka ka kwanta zan shiga.

Ya ce uh'uh ai ba zan bar ki cikin daren nan a

waje ba in haka yasa na tura kofar a hankali na

shiga. Cikin sa'a gaba daya dakin a duhu yake nayi

matukar jin dadin hakan don haka na lallaba a

hankali na dale kan gadona, ina shirin kwanciya

kenan sai kawai naga Goggo ta hasko ni da

tochlight dinta.

Ashe wai duk abin nan da ake yi duk da

dadewar da nayi ban baro wurin Ado ba, duk da ita

158

yarinyar tuni ta hakura da kukan nata ta koma

baccinta.

Ita Goggo bata hakura ta kwanta ba, tana nann

zaune dingir a tsakar dakinta bata ma yarda ta hau

gado ba, don kar tayi gyan-gyadi da bacci zai

dauke ta har in shiga bata sani ba.

Don haka tayi zaman dirshan a tsakar daki tana

Jiran sai taga zuwana wai ita nan a dole sai taga

KWALUWAR DAKA'.

"Ina ki ka fito? Ruwan me ke diga a jikinki?

Jegon kenan? Dama damuwarki kenan yasa kika yi

ta tasa yaron nan a gaba da koke-koke? Haba ni

fa...kuka na soma yi wa Goggo kuka kuma mai

tsanani, saboda tambayoyin nata sun yi min tsanani

da yawa.

Kukanki din banza da na woff? Ina...daga waje

Ado yayi gyaran murya mai karfi, wai dai don

Goggo tasan shi din bai yi nisa ba yana wurin ko

zata yi hakuri ta bar maganar tata.

Ban sani ba ko bata gane abinda gyaran muryar

tashi ke nufi ba ne ya hana ta saurarawa ta ci gaba

da fadin ina amfanin ace mace ita ce fitinanniya?

Namiji bai damu ba sai kece...

Uh'uh Goggo, uh'uh Goggo, abinda ya ci gaba

da fadi kenan don kara yi wa.Goggo Ayalle

159

kashedin maganar tata, yayin da ni kuma gabana ke

ta faman harbawa saboda tsoron kar ya ce zai tanka

mata.

Gaba daya fatana da burina bai wuce ya bar

wwrin tsayuwar tashi yayi tafiyarshi wurinshi, ba

Care da ya bude baki ya ce mata komai ba.

Saboda nasan yin maganan nashi ba zai taba

haifar mana da da mai ido ba, fin barin maganar da

Goggon tayi shi ne ya hassalar da Ado har yayi

dalilin da ya toro kanshi cikin dakin ya ce mata ba

ita na ce Gogggo ni ne, ba ita ba ce kyale ta kawia

ni ne.

Abinda kawai naji Ado ya gayawa Goggo

Ayalle kenan sai kawai naga ta fashe da kuka tare

da salati mai tsananin karfi.

Mu tafi littafi na hudu don jin yanda za'a kare

tare suke'.

Fatan alheri gare ku dukanku taku,

Hafsat Chindo Sodangi

(Mrs Yunus Abdullahi Dabai)

24 ga watan uku 2013

07035586299

160

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login