Showing 15001 words to 18000 words out of 35296 words

Chapter 6 - MIJIN TACE Book 3 Hausa Novels by hafsat Sodangi.docx

/>
sana'a ne Humairah? Adashe ai na mutane masu

sana'a ne, ke ba ki da sana'a ni ba wani abu nake yi

ba in ban da maganar gonar nan, gona kuna ci mun

kudi take yi bata fara bani ba, yanzu ne nake

neman aikin koyarwa tunda na gaya miki na mika

takarduna ba kuma zan yi wani aiki de va wiice

koyarwa ba a yanzu, saboda ina son in jarraba yin

noma sosai.

Ni yanzu fatana da addu'a ta bai wuce mukai

lokacin da za a yi girbi asirinmu bai tonu ba. Na

rantse miki Humairah rutin asirin Ubangiji ne

kawai yake tafiyar mana da al'amuran sai ma ganin

kamar zata kure sai kuma in ga wata hanyar tazo ai,

wani lokacin ma ba da gangan nake kwashe miki

kudinki ina bar miki nera hamsin ba, Kurewa take

yi.

70

Kiyi hakuri kin gane? Nasan kina hakuri dani,

amma ki kara maimakon in ji wannan rarrashi da

bayanin da yayi min, na riga naji zuga zugan da aka

yi min cewar su din ma'ana, 'maza' ba ayi musu

sassauci mai yawa sai su raina mutum.

Don haka sai na kara daure fuska na kara 6ata

rai na ce, to sai muyi hakuri duka, na kawar da

fuskata gefe.

Abin da kawai na fada kenan, sai ya fahici abin

da nake nufi, muyi hakuri duka? Na ce, eh, me

kenan hakan yake nufi? Na sake bata rai na ce, ko

ma menene? Ya dago ido ya kalle ni cikin natsuwa

ya ce, waye ya koya miki wannan iskancin ?

Nayi kamar ban ji shi ba, ya ce to ai da sai ki

gaya mata naki mijin ba irin nata ba ne. na ce uhn,

na mike da nufin fita in bar mishi dakin, sai kawai

naji ya kamo hannuna ya murde da karfi, sai da na

kwallara kara mai tsanani, amma bai sake ni ba.

Ai babu in da za ki tafi sai kin gaya min

wacece take koya miki wannan iya shegen?

Ruwailah ko? Sai naci abu kazanta, in bata yi

hankali da ni ba, ha'a me tayi maka zaka zage ta?

Kau na ji, ya wanke ni da wani irin wawan mari,

nayi maza nasa daya hannun na dafe wurin, ai in ba

ki gaya min wacce tasa ki kiyi min wannan

71

wulakancin ba, za kiyi mamakin abin da zai faru

yau."

Na soma mutsu-mutsun kwatar hannuna naga

hakan ba zai yiwu ba wahala kawai nake karawa

kaina bai kuma kula kukan da nake yi ba, balle ya

damu da cewar rana ce mutanen gida zasu iya jin

abin da muke ciki.

Wulakanci irin wanda Ado yayi min rannan bai

kwatantuwa, murde ni yayi ya yi abin da yaga ya yi

mishi daidai sannan yasa kai ya fita ya bar gidan da

azahar tayi ma ya sake dawowa, babu kuma wata

mu'amulla ta rarrashi ko sassauci a tsakani na rasa

in da sa kaina in ji dadi, ga shi kuma bsbu halin in

kai kara in maganar ta fto ban san me Zai faru ba.

Ba kuma zan iya gayawa Inna ba in ce tayi

mishi magana, nasan zai iya gaya mata abin da ya

hada mu, na kuma san zata yi fushi mai yawa don

na saba jin ta tana cewa dabi'ar matsiyatan mata

kenan su ne wadanda ba za su gaya wa mazansu

bukatunsu ba, sai a lokacin da suka ga sun matsu

da su.

Don haka na lallaba na samu Ado ina kuka na

ce mishi kayi hakuri Kawu ka daina irin wannan

mu'amullar dani.

Ya dago ido ya kalle ni ban san yenda aka yi

72

ba, tausayina ya kama shi cikin natsuwa ya ce min

ya wuce amma ki gaya mata tayi hankali da ni ko

wacece? In ita bata sani ba ke kin sani cewar Mama

ita ce mafi darajar mutum yau a wurina tunda bani

da uwa ba ni da uba su Baba Tanimu ne iyayena.

Ita ta rike tayi min gatan da nayi karatu na koyi

al'amura masu yawa na rayuwa, amma sa nayi

jaruntakar rabuwa da ita don in zauna dake ya sake

zuba min ido yana yi min kallo mai tsanani, shi ne

za'a saki kiyi min abinda ki ka san zanyi bakin

ciki?

In ana son cutar da ni sai a hada kai da ke?

Yanzu in an san ina sonki sai ayi amfani dake? Ni

in ina da hali sai kinyi adashe? Me zan yi da kudin?

Hankalina yayi matukar tashi jin kalaman Ado

nayi matukar jin kunya da Nadama na abin da nayi

mishin kuka sosai na soma yi ina bashi hakuri don

kuwa na san ba karamar wauta nayi ba dana ji irin

wannan zugan na kuma yarda nayi amfani da ita.

Na dade sosai ban iya sakin jikina sosai da Ado

ba saboda naji kunyar abinda nayi mishin ba kadan

ba duk dai shi din bai sake yi min wata magana ba

ko kuma nuna min wani abu.

Ana cikcin haka rannan ya dawo da rana, wasu

takardu ya ciro a aljihunshi ya miko min, nasa

73

hannu biyu na karba ina dubawa tun kafin in kai ga

gama karantawa ya ce min naje nan Government

Day Secondary School Dabai nayi magana da

Princepal din ya yarda za ki soa zuwa satin nan.

Kije kiyi karatu ki samu takardar ki yafi min

wunin da za ki rinka yi a gida bana nan ana koya

miki abin da ba zai min daidai ba, da na bari ne sai

badi don in ga na soma yin wani abu, to amma sai

na tuna kuma ai 'Though Times Never Last but

though people do."

A haka na soma zuwa makarantar (S.S. 2) aka

sanya ni, babu kuma abin da Adon bai saya min ba

na karatuna, tun daga uniform, sandal, safa, har

zuwa littattafai na karatu. In nayi shiri Zan ta in

sanya dogon hijabina akan uniform din sai na shiga

cikin makaranta in cire in shiga aji in mun taso ma

in mayar.

Tunda na shiga makaranta na soma koyon

jarumtaka kan al'amura masu yawa nayi matukar

rage baccina, kullum na kan tashi ne da wuri in yi

mana abin karyawa da abincin da zamu dawo muci

da rana, in zuba a cikin food flask kafin in yi

wanke-wanke, in yi wanki in yi shara in yi wanka.

Karfe bakwai nayi kuma zan sanya kayana in

dora hijabina in je in gaida su Baba da su Goggo,

74

da sauran mutanen gida, in fita waje in samu Ado

yana jiran fitowata bayan ya rurrufe mana wurinmu

mu jera mu tafi sai yaga shigata makaranta sai ya

wuce gonarshi.

Yana kuma daidaitan lokacin tashin mu ne ya

taso daga gonarshi ya biyo min ta makaranta mu

dawo gida tare, da daddare in mun gama abinda

muke yi kuma yana duba takarduna yaga aikin da

aka yi mana ya yi min gyara kan abin da ban gane

ba.

Zaman lafiyan da aka lura aka ga ya samu

tsakaninà da mijina ne ya bayyana a cikin gida,

wanda ban samu hakan ba sai da na yarda ni ce a

kasa shi ne sama da ni, sai da na yarda da barin son

raina na koma bin nashi, na koma karbar umarnin

komai daga gare shi, na koma rayuwar yi nayi bari

na bari ko da kuwa ina son barin ko kuma ina kin

yin da aka ce in yin.

Misali, ko a cikin gida ina son shiga cikin mata

'yan uwana in dan yi mu'amalla da su in dan ji dadi

a raina, amma tunda yake min ya hana ni žaman

gindin bishiya don hira, na ce mishi, to na kuma

bari ko baya nan bana zuwa.

Tunda ya hana ni bin dakunan mutane matukar

ba wani dalili mai kwari ne ya kai ni ba, na hakura

75

na daina sai ko dakin Goggo Ayalle.

sKullum ni kadai ce a wurina, in ba shi din yana

gida bane kowane lokaci a cikin hidimarshi nake,

tunda daga wankin yan suturunshi da adana su da

tattalin abin da zai ci hakan kuma bai hana ni ba shi

lokacina a duk lokacin da ya bukaci hakan.

Ana cikin hakanne kawai na soma jin

maganganu suna yawa a cikin gida, wai ni din fin

karfin shi nayi, bai da wani katabus bai iya yin

komai sai abin da nasa shi, ko kuma na hana shi,

wai ai tunda na iya raba shi da Hajiya Majadan duk

alherin da tayi mishi, to babu wani wanda ba zan

iya raba shi da shi ba.

Ina jin maganganun na gane daga inda suka

fara fitowa, cikin zuciyata na ce don ta gane na

daina daukan shawarwarinta ne, gara ita, nata mijin

yana da irin wannan juriyar ni nawa in na ce zan yi

mishi haka ba kwashewa kalau zan yi ba.

Na dai kudiri aniyar zama lafiya da kowa ba na

son fitina, don kuwa nasan babu alheri a cikinta,

tashin hankalin Mama kawai da ta tasa mu a gaba

shi ne yayi dalilin barowarmau gida muka taho nan,

to ta wadannan bataliya fa?

A wannan lokacin aka sake fito min da wata

dabi'a, duk wacce zata yi wanka ko zata yi taya bahaya

76

sai tazo wurina ta ce wai a nan zata yi.

Wuni suke yi suna layin shiga bayan gida,

kuma duk yanda na kai da wanke shi sai sun 6ata

shi yayi ta wari, wani lokaci har cikin daki, don

tuni da nayi hakuri da su akan sabon halin nasa.

To Ado ya ce bai yarda in hana su, in gaya

musu cewar shi din ya hana su shiga wannan bayan

gidan ya ce in gaya musu su rinka wanke hasu,

suna gyarawa don su rinka jin dadin shiga ko ni din

da irin barin wannan din da kazanta da ba su zo sun

shiga ba.

Ni kam ban iya gaya musu ba, ina jin kunya

don mafi yawancinsu sun girme ni nesa ba kusa ba,

shi kuma yana ganin wata tazo ta shiga ni yake

balbalewa da fada, sai da nayi sa'a maganar ta kai

ga Baba Tanimu.

Shi ne yayi kashedi mai kari kar ya sake ganin

wata taje ta zaga a wurina baya son iya shege da

neman magana.

A wannan lokacin har a gabana a kuma kan

idona za a rinka tsaki ana cewa a hau, to namiji

kuma, wacce bata san shi ba ai ita ce bata san sh

ba, mu kan ai sun shamu un warke, muna nan da ke

za ki zo kina zubar mana da hawaye sanda zai yi

miki halin nasu mu ce muma bamu sanki ba

77

amarya muka sdni.

Kusan kullum sai an ce min an ga Ado gidan

Mallam Korau yaje tadi, rannan dai na daure na

samu Adon na tambaye shi cikin natsuwa na ce

mishi ni da gaske ne wai kana neman yar gidan

Mallam Korau?

Bai wani kalle ni sosai ba ya ce min Menene

in ina neman nata? Na ce a'a na dai tabaya ne

kawai don in sani ya ce ba uwardakinki ce ta gaya

miki ba, ai ba zata yi miki karya ba, watakila dai

kina ganin ne tanfar gonar tawa ba, za ta rike min

ku ku biyun ba ko?

Ban sake ce wa Ado komai ba, amma wani irin

al'amari ne naji ya taso min ya tokare ni a kirji,

wani irin nauyi ya saukar min a kirjin, zuciyata tayi

matukar kunzi, karo na farko da naj! in wannan

abin a tare da ni.

Kishi mai tsanani ne ya kama ni, na tabbatar wa

kaina da cewar aiki ne babba a kaina, in har ya

tabbata Ado auren nan zai yi tun daga. wannan

lokacin na soma sa ido akan lokutan fitanshi da

kuma na dawowanshi tare da tunann io a wane

lokacin yake zuwa wurin nata?

Zuciyata ta soma raya min cewar wata kila

daga yin sallar Isha'i ne tunda kullum bai dawowa

78

gida bayan Isha in sai yayi zama na awa daya da

minti goma sha biyar ko kuma da minti talatin.

A farko ya ce min yana zaman yin karatu ne

wurin Limamin Masallacin unguwar, na kuma

yarda. To yanzu kam na gane ba gaskiya ba ne,

loba ni kawai yake yi, tadin shi yake zuwa.

Don haka rannan da zai fita Masallaci don

sallar Isha'i; na ce mishi in an yi sallar Isha'i ka

shigo gida don ban yarda da wannan munafukar

makarantar taka ba, babu kowa a ciki sai kai kadai.

In ban da munafurci wane karatu ne ba za ayi

shi ido na ganin ido ba, kullum sai dare yayi?

Zuba min ido yayi yana kallona, a hankali ya

bude baki ya ce min, makarantar tawa ce kuma

munafuka yau Humaira? Nayi maza na ce mishi,

eh, kana nema ne ka maida ni wata yarinya 'yar

kankanuwa.

Ka shanya ni a gida da sunan kana wurin

Mallam alhalin kai kana can ne wurin tadin ka.

Ya ce, To shi kenan, ke ba yarinya

Rankanuwa ba ce, tunda kin yi kokari kin gano ni,

to amma ai kuma ina jin ban taba yi miki karyar

zan zauna da ke ke kadai ba, balle ki ce na 6oye

miki.

A kullum kuma ina kokarin gaya miki cewar ni

79

din namiji ne, shi kuma namiji ai kin san imijin

mata hudu ne.

Kalaman nashi suka kara fusata ni, na soma

sake mishi maganganu masu zati, musamman ma

da na tuna eh, gaskiya ne shi din kullum a cikin

alkawarin zai nuna min shi namiji ne, wato dama

abin da yake nufi kenan?

Ba. mu gama fita daga cikin wannan maganar

ba tunda bai yarda zai daina zaman waje bayan

Sallar Isha'i ba, sai kawai na dauki wayar Ado ina

bincike a cikinta.

Text din yanata na soma gani, yayi maza ya

fige wayar daga hannuna, nan take kuma ya kama

yi min fada ""Kina fa nemana da fitina, kina nema

sai kin takura min, yaya ne haka?

Ya ya za ki tsananta min bincike bayan kin san

an hana? Na soma yi mishi kuka saboda a wannan

lokacin na riga na gane gaskiya ne yana neman

aure?

Kenan gaskiya ne duk wahalar gonar nan da

yayi da juriya da taimakon da nayi tayi mishi kudin

a dawainiyar aurenshi zasu tafi?

Hannu biyu na dora a kaina nayi kuka har na

gaji bai yarda ya sake shigowa dakin ba.

Washegari tun safe na tatt a na bar mishi

80

wurin, na koma dakin Gogori Ayalle nayi

kwanciyata, zuwanshi uku in dawo wurinmu zai

zauna muyi magana ta gaskiya, ni da shi ban yarda

ba.

Har kusan yamma ban koma ba, anyi sallar

La'asar ya shigo ya zo ya same ni, "Zo muje kiyi

mana girkin abinda zanmu ci mana Humaira, na ce

mishi kaje ka kawo yar gidan Mallam Korau ta

girka maka.

Ya zuba min ido yana kallona cikin natsuwa,

kiyi hakuri mana Humairah na ba ki hakuri na

kara ina ce ni duk girman laifin da ki ka yi min

hakuri daya ki ke bani in ce na hakura?

Na daga ido na kalle shi, kayi min wulakanci

akan wata 'yar iska? Yayi murmushi, "To ai na ce

kiyi hakuri." Ban tanka mishi ba sai ya juya ya fita,

Bai wani dade ba ya sake juyowa zai dawo, sai

kawai naji Ruwaila tana ce mishi, ai kai kuma yau

taka ta sae ka tunda ka yarda ka bata mata rai, baka

da šauran zama lafiya tsugune ta kare maka tunda

ka bari aka yi fushi da kai.

A zuciyata na ce, kai wasu da rashin zuciya

suke, tanfar dai bata gane irin sharewar da Ado

yayi mata ba kusan kowane lokacin a cikin

nemanshi da magana take.

81

Sai kawai naji ya ce mata, eh ai ta isa ne kin

san ni din a hannunta nake, wata matar don ta yi wa

miji fushi ai shirme tayi, tunwa wanda tayi domin

shin ba zai kula ba, balle ya bi baya.

Abin da kawai ya fada kenan, tayi matukar

fusata da maganar tashi ta shiga sakin maganganu,

ai kai ma ba haka kawai ka ke wannan zaryar ba.

Ka ke ganin a kanta zaka iya batawa da kowa,

ai rashin imani suke gwadawa tunda abin da ba a

sha suke wankewa suna ba ku.

Maimakon yayi shiru tunda ya ji inda ta maida

zancen nata, sai naji ya ce, ni na yafe mata, ba

kuma rashin Imani aka yi min ba, da bakina sai in

yi yanda ake so tunda ai nawa ne.

A mafi yawancin lokaci, nakan hakura da

abubuwa masu yawa sosai inyi ta hakuri dasu

saboda sanin da nayi cewar gaba daya matan gidan

nan idonsu a bude yake akan al'amarin zamanmu

ni da mijina.

Tunda Ado da Ruwaila suka yi wadannan

maganganun gashi dai a zahiri wàsa suka yi irin na

matar wa da kuma kanin miji, amma can cikin

al amarin nasu sun kulle wani abu Ruwaila dai 1a

nanata maganar yafi a kirga.

Ana cikin haka, raninan na amsa kiran da

82

Goggo Ayalle tayi min da sassafe, Ado bai fita ba

ya jira in je in dawo don ya ji kiran akan menene?

Me ta ce miki? Yayi min tambayar tare da bina

da kallo zuwa in da na zauna.

A hankali cikin natsuwa don kar ya dauki

maganar da tsanani nace mishi kan maganar girkin

ne.

Wani lalataccen ashar ya wulwulo ya antakawva

Ruwailah, zan sa kafar wando daya da matar nan,

wai ita tana son takurá min ne ko?

Nayi maza na fara bashi hakuri, ba fa ita ba ce.

Da sauri ya ce ke matsa can, ke me ki ka sani? Tlo

ka gani ma dai kawai ni kam kayi hakuri na

gayawa Goggo zan karbi girkin.

Da sauri ya tanbaye ni mene? Za ki karbi girki

ki ka ce musu? To kje ki karba ta kuma kisan

yanda zaki yi dasu ni babu ruwana.

Tunda na gane kin fi jin tsoronsu da ni, kin

kuma fi jin maganarsu da tawa.

Kuka na soma yi mishi

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login