Showing 9001 words to 12000 words out of 35296 words

Chapter 4 - MIJIN TACE Book 3 Hausa Novels by hafsat Sodangi.docx

a ciki? Da da ni akaje ai

da ban bari anyi hakan ba.

Gaba daya hankalin Ado yayi matukar tashi da

abin da ya farun, ina jin Baba Tanimu da daddare

43

yana ta ba shi hakuri, ita rayuwa fa haka take, a

kullum mutumin kirki ba ya zama ba tare da ana

jarraba shi ba, ba ka fita daga cikin wannan ba ga

kuma wannan ya sake zuwa.

To kayi hakuri kar kuma ka ee zaka yi saurin

gayawa iyayenta tunda ga irin rabuwar da ka ce

kun yi dasu.

Naji Ado ya ce, "A'a Baba, ba zan iya boyewa

mahaifiyarta halin da take ciki ba, tun muna asibiti

nayi waya na gaya mata, ban dai sake gayawa kowa

ba; amma ita kam na gaya mata, ya ce to shi kenan

tunda kaga hakan yafi.

Kwanana bakwai a dakin Goggo Ayalle tana ta

faman tarairayata, Baba Tanimu kuma da su Baba

ubangida suka yi ta bayar da kaji ana yankawa ana

yi min farfesu, har ma cikin kajin Goggo ta cire

wata yar budurwa da ta bata sha'awa ta ce ba za ta

yankata ba, bar min ita zata yi in yi iri.

A zuciyata na ce, uhun ni kam ai ba.zama nazo

yi ba.

A wadannan kwanakin babu wata mu'aallar

arziki tsakanina da Ado, ko gaisuwarshi ban cika

amsawa ba. A cikin kwanakin ne kuma na lura ya

daina zama a gida tun bayan fitan da suka yi da

Baba Tanimu ba a sake wayar gari na ganshi a

44

gidan da safe ba sai gab da Azahar, ana yi sallar

La'asar kuma zai sake fita sai kusan faduwar rana

ya dawo.

Ban san ina yake zuwa ba, ban kuma tambaye

shi ba don a yanzu ko kallon shi bana yi, fatana da

tattalina bai wuce in samu kudin mota ba in kama

hanya in yi tafiyata.

31Rannan ya dawo kusan Azahar ya shigo dakin

na Goggo, duk da yana ganin naji sauki har ma

nayi kyan gani, sai ya tambaye ni ya ya jikin naki

dai Humaira? A lalace na ce mishi da sauki, ya

kalle ni cikin natsuwa.

"Amma kin ga yayi miki daidai a hakan da ki

ke yi Humaira? kina mu'amallah da kowa lafiya

amma ni da na kawo ki babu?" Na kalle shi a

sakarce na ce mishi, "To ka maida ni mana in da ka

dauko nin." Ya ce, to babu laifi ya wuce ya fita.

Ran da na cika kwana goma rannan Baba

Tanimu yasa Goggo ta sani na koma dakin namu,

ita kam taso ne a bar ni in yi arba'in.

Zaman da na yi a dakin Goggo ya sani fahintar

gidan sosai da kuma mutanen gidan.

Sassa guda hudu da ke gidan suna karkashin

dattawa hudu ne wadanda su ne asalin yayan

maigidan su kuma dukan su uba daya ne ya haife

45

su, amma uwa daban-daban, babban cikinsu shine

Baba ubangida sai Baba Halliru sai Baba Tanimu

kafin Baba Tukur shi ne karaminsu..

A duka sassan nan guda hudu akwai iyalai

musu yawa su dattawan gidan kuma suma suna da

nasu matan, Baba Ubangida shi ne mai mata Goggo

Turai wacce take sana'ar kokon safe, Baba Halliru

shi ne mai Goggo Jaku ita kuma tana furar sayarwa

mai dadi Baba Tanimu Goggo Ayalle ita kosai take

yi itama da safe.

Sai Baba Tukur, shi kuma tashi matar ita ce

Goggo 'yar neto ita kuma tana gaudan sayarwa. A

kowane sassa na gidan akwai yaran mata masu

yawa saboda kusan duk 'ya'yan gidan maza masu

aure ne wadan da basu yi ba 'yan kadan ne mafi

yawancin masu auren kuma mata bibiyu ke gare su

masu dai-dai din basu da yawa, kamar ma ba su

dade da yin nasu auren sosai ba.

Yanda duk tsofaffin gidan ke da sana'o'insu

haka suma yaran matan gidan suke da hasu

sana'o'in tun daga mangyada, manja, gyadar miya,

maggi, gishiri, Alala, dan wake, gasu nan dai birjik

Wasu har dinki wasu kuma har aikatau da su wanki

amma dai kowa da abin da yake yi gwargwadon

karin injin shi.

46

Kiwo kuwa a gidan ba a magana duk yawan

Tumaki da Awaki da Kajin kuma abin mamakin shi

ne kowa yána shaida nashi.

Gaba daya sassan nan guda hudu kuma akwai

mace guda da take kamar ita ce shugabarsu a

sassan Baba Tanimu dai Ruwailah ce matar Yaya

Jafaru ta farko, a sasan Baba ubangida da kuma

akwai Furera matar Yaya Baidu itama uwargida ce.

Sasan Baba Halliru akwai Gaje matar Yaya

Jumare, itama uwargida sai sasan Baba Tukur nan

kuma Tanbai matar Yaya Amiru akwai Uwale,

itama uwargida, gaba daya wadannan matan hudu

sun zo gidanne a kusan lokaci daya, ma'ana babu

bambancin lokaci mai yawa a tsakanin aurarrakin

nasu dukansu kuma suna da amare da kuma matan

kannen miji.

Haka nan gaskiyar Mama ne gaba daya gidan

tukunyar abincinsu na dare gaba daya ne da rana ne

dai kowa zai yi abin da zai ci shi da iyalinshi a

wurinshi amma na dare a hade yake duk kumna

wanda ke da girkin ranar to shi ne mai ba da hatsin

da za ayi amfani dashi dama duk abinda za a nema

Goggo Ayalle kuma ta shaida min cewar in mace

tayi girki sau daya to kwana ashirin da biyar take yi

bata sake ba.

47

Ai kuwa kin ga dole suyi ta neman kudinsu

tunda basu da wani aiki na ce haka ne, a zuciyata

kuwa cewa nayi yaran mata ashirin da biyar kenan

a gidan.

Muna nan zaune a dakinmu ni da Ado, zaman

babu wani dadi. Kallon shi bana yi balle in san me

yake ciki, shima baya takura min akan komai zuba

min ido kawai yake yi babu abin da nake fata irin

nera talatin-talatin din da Baba Tanimu yake bani

kullum safiya, ya ce wai in sai abin da nake so in

karya da shi da kuma ashirin-ashirin din kokon da

Baba ubangida yake bani.

Ita kuma Goggo Turai ta ce kai haba, bakin.

wannan yarinyar dai ita kadai ace sai na amshi

kudinta? Je ki ki rike kudinki kin ji? Don haka

kunu da kosai ba saye nake yi ba, sai nake tara

hamsin-hamsin din ina fata su ishe ni kudin motar

tafiya gida in sulale in yi tafiyata.

Rannan na wuni ina murna na kirga kudina sun

kai dubu daya har da dari daya ina lissafin

kwanakin da suka saura kudina su gama cika sai

kawai nazo zan ajiye wata nera hamsin din naga

babu komai sai wata tsohuwar nera hamsin itama

wata kila bai ganta ba ne sanda ya kwashe su. Nayi

kuka rannan har na gaji ban kuma iya cin komai ba

48

saboda tsananin bacin rai.

Ado ya dawo gab da Azahar ya same ni a haka,

ya juya ya fita bai zauna ba, bayan Sallar Isha'i mna

ya shigo dakin da niyyar kwanciya ya same ni ina

ta faman kuka, wuri ya nema ya zauna bayan yaje

yayi wankanshi ya dawo.

Ban kalle shi ba balle in san me yake yi, sai

naji yana magana alamar waya yake yi, gaisuwa ta

ladabi da natsuwa naji shi yana yi, don haka na

kasa kunne ko zan gane da wa yake maganar, sai

naji yana cewa.

"Gaskiya Inna na gaji da karyar da nake yi miki

ne, cewar muna nan lafiya, a gaskiya ba hakan ba

ne, ina jin salatin da Inna ta soma yi, ban san me ta

ce ishi ba, sai naji ya ce mata gata, nayi kamar ba

zan karba ba sai naga to ni kuma a wa?

Inna ta ce, a bani waya in ki karba? Ina karbar

wayar na kaita kunnena naji muryar Innata gaba ya

yanke ya fadi nan take na soma yi mata kuka bata

yi min fada ba kamar yanda nayi zaton zata yi

magana ta soma yi min cikin natsuwa da kwanciyar

hankali.

Ban ji dadin yanda ki ke yi wa mijinki ba to da

wanne zai ji? Da halin da yake ciki ko da rashin

lafiyarki da yayi ta fama da ita? Ko da bacin ran

49

abin da ki ke yi mishi? Matar kirki kuwa ai bata

haka, ita takan taimaki mijinta ne a duk lokacin da

tasan yana bukatar taimakonta, ta rufa mishi asiri a

inda tasan yana bukatar rufin asirinta.

In ta san yana cikin tashin hankali kuma ta

kwantar mishi da hankalinshi, sannan in ba ki sani

ba wannan abin da kike yi ba shi kadai ki ke

tozártawa ba har da ni, don kuwa kina kokarin

nunawa wadanda basu sanni ba ne su san yanda

nake tunda ai ita 'ya wakiliya ce ta uwarta.

In kiyi halin kwarai ace kin samu tarbiyaa a

gidan ku in baki yi ba a gane uwarki ba mutuniyar

kirki ba ce kar in sake jin an ce min baki kyauta

ba, in dai ba kina so raina ya baci da ke ba ne, tana

fadin hakan ta kashe wayar.

Sunkuyar da kaina kasa nayi, nayi shiru ban iya

cewa Ado komai ba, iyaka dai ranar mun kwana

lafiya amma ko kusa da ni bai zo ba, balle ya ce zai

taba ni, ina wurina yana nashi.

Washegari da Asuba yana idar da Sallah Asuba

ya shigo ya tashe ni ya wuce ya fita, sai dai

maimakon sai Azahar in ga ya dawo, wajen sha

daya naga shigowarshi. Ya koma gefe yana cire

ranbut din kafarshi da hand glove din hannunshi

mahadin ranbut din.

50

Naji Baba Tanimu daga daki yana ce mishi "Ka

dawo ne Adamu?" Ya ce mishi "Eh Baba, na

dawo." Ya ce "Sannu da kokari ka ji? Ubangiji ya

yiwa kokarin ka albarka." Yayi murmushi ya ce

Amin Baba." Ya shigo cikin dakin namu ya same

ni ma Zaune.

Ya kakalle ni yayi murmushi, ya ce to ko ke fa?

Kin yi wankanki kinyi fes da ke, na sani ba kya jin

dadin mu'amalla da kayan da ki ke amfani da su

tunda sunyi miki karanci da yawa dogayen riguna

biyu ne kawai, sai zanin da ki ka zo da shi a jikinki.

Kiyi min hakuri a yanzu, na katse shi ta hanyar

fara gaishe shi, yana gama arnsa gaisuwar ya kalle

ni cikin natsuwa ya ce, samo min dumamen tuwo

wurin Goggo Ayalle, na ce to, na tashi na tafi cikin

zuciyata ina tunanin tun zuwanmu gidan kwanaki

ashirin da daya da suka wuce ban taba lura da cin

shi ko shanshi ba, ban kuma taba dora tukunya a

murhu don yin girkin rana ba, tunda kowa yana

abincin ranarshi.

Ni dai nasan duk abin da Goggo Ayalle zata ci

zata bai haka nan ma Yaya Ruwailah tunda nima

yanzu yayan nake kiranta.

Na dawo da kwano mai dauke da tuwon da aka

dumama shi tare da miyar shi a wuri daya na ajiye

51

mishi na koma gefe na zauna sai ya sake kallona

cikin natsuwa ya ce min baki bani cokali ba, nayí

maza na kalle shi saboda sanin shi ba mai cin tuwo

da cokali ba ne.

"Da cokali za ka ci?" Ya ce, "Eh, dashi na ke ci

yanzu saboda hannun nawa ba na jin dadin cin

tuwon da su." "Me ya same su? mu gani." Bai yi

magana ba ya ware min tafin hannayen nashi.

Tsigar jikina tayi matukar tashi tayi wani

yarrrr! hankalina yayi matukar tashi da yanda naga

hannun Ado gaba daya hannun nashi bororo ne ya.

duru ruwa, wani wurin ma ya fashe ya zamą miki

babu dadin gani.

Fuskarta a yamutse saboda yanda hankalina

yayi matukar tashi na tambaye shi me ka ke yi

hannunka yayi haka? Shirun da yayi bai ban amsa

ba yasa na sake tambayarshi Noma? cikin nutsuwa

ya kalle ni ya ce min, in nayi noma menene

Humaira?

Ni ba namiji ba ne? Ni fa ba wannan ne wahala

a wurina ba, wahala a wurina bai wuce ki ki yarda

mu zauna lafiya ba, amma in za ki yarda mu zåunna

lafiya ki gamsu da kokarina ki yarda da cewar in

ban yi miki ba, ba ni da shi ne.

Kiyi min hakuri ai ba zan gane ina wahala ba

52

sai in rinka ganin tanfar abin da ya dani a

matsayina na namiji kawai nake yi in kuwa haka ne

kin ga bai zamo min wahala ba.

Ban iya cewa Ado komai ba saboda kukan da

soma yi ban taba hira na gane matsananciyar

ramar da yayi ba sai a yau, na dai san nai Goggo

Ayalle tana yawan fadin yaron nan Adamu ya

zube. Amma ban lura na gane irin zubewar ba, sai a

yanzu.

Tashi yayi yaje ya dauko cokalin ya dawo ya

zauna ya soma cin tuwon, ni in don ni ki ke kuka to

ki share hawayenki, in kina so in san kina tausayina

to in ina tare da ke ki bar ni in samu kwanciyar

hankalin da nake bukata.

Yaua gamawa ya tashi ya sake fita, nima na

share hawayena na tashi naje sasan Baba Halliru

wurin Goggo Jaku na gaisheta, na ce mata Goggo

yau zan karbi furar da kullum ki ke cewa bana

zuwa ina karba, tayi murmushi ta ce, kai ai kuwa

dai kin kyauta yar nan, gata kuwa an gama

mulmulata.

Ta miko min tayi shar gwanin sha'awa, sai

Kamshi take yi, gata nan debi maza yanda zai ishe

ki nasa hannu na debi guda hudu ta ce ke tafi can

da kwauro, za ki yi wa kanki, ta sake watso min

53

guda shida a cikin kwaryar da ke hannuna nayi

mata godiya na tafi.

Nura na kira ko Zulai yaya, Yaya Ruwaila ne

gaba daya suka taho na ce to ke Zulai je ki ki huta

kai Nura yi sauri kaje bakin kasuwa ka sayo min

nono, ya ce to.

Ina zaune ina dama furar ina tunanin kai! Dabai

akwai fura, amma babu nono. nono ruwa-ruwa? Na

jawo robar yougort din da ke dakin na bude shi na

juye a cikin damammiyar furar na gaurayata na

rufe.

Ana yin Azahar Ado ya sake shigowa nayi

mishi sannu da zuwa, ya amsa. Na jawo kwanonon

fura na mika mishi ya kalle ni da walwala a

fuskarshi ya ce to ke fa? Na ce ai na sha, ya ce eh,

amma ba zai taya ni musha tare ba ai.

Na zauna muna shan furar tare har muka gama,

muka dan yi hira kadan sai na kalle shi na ce mishi,

"To ka dan kwanta mana ka huta." Ya ce in kwanta

Humaira? Nayi maza na ce mishi eh, ya ce to za ki

yi min tausa ne? Na gyda mishi kaina nuna alamar

eh.

Yayi maza ya mike akan katifar nima na bi

bayan shi na soma yi mishi tausa ina yi mishi danna

ina bin gabobin jikinshi ina matsawa cikin hikima,

54

shi kuma yayi lamo ya lumshe idanunshi nuna

alamar jin dadi.

A hankali kuma yana furta wasu kalmomi da ni

kadai ke iya jin su, bacci mai nauyi Ado yayi bai

farka ba har sai da na tashe shi, wajen karfe hudu

da rabi na yamma abin da bai taba yi ba tunda

muka zo, ya kwanta da rana yayi bacci.

Da daddare rannan muna hira ni dashi ya kalle

ni cikin natsuwa ya ce min ni kuwa Aisha in ban da

kar in yi ta takura miki har in yi ta kai ki bango ban

sani ba da na roke ki kiyi min wata alfarma, na ce

ta menene? Ya ce dakin nan da muke zaune a ciki

ne bana son shi, duk da nawa ne.

Na ce, ni na gane saboda gininsu ma ya

banbanta da na sauran dakunan gidan shi da na

Baba da na Goggo Ayalle.

Bai bani amsa ba sai ya ce min nan din a takure

nake, ba zan iya sakewa nayi kusa da Baba da yawa

ba zan iya zama dashi duk wani motsina yana ji ba,

shi ne nace da za ki yarda da mun fita daga ciki

mun koma wasu tsofaffin dakuna da ke ta can baya,

babu kowa a wurin sa muyi zamanmu zuwa

lokacin da zan samu halin samar miki wurin da zai

dace da ke."

A hankali cikin natsuwa na ce mishi, to mu

55

koma mana. Ya zuba min ido yana kallona, babu

damuwa? Na ce to ai ba daki na biyo ba, ba kuma

shi nazo nema ba, ni a wurina kai ne muhimmin

abu, kai na biyo kai ne mijina a yanzu kuma zan iya

zama da kai a duk in da ya kama.

Kwana uku kawai da yin wannan maganar

tamu Ado ya gama gyaran dakunan da da shara ake

zubarwa a wurin ya kwasheta fes ya gyara wurin ya

tsabtace shi ya gyara dakunan gyara na musamman

ya sai buhun siminti ya toshe duk in da yake

bukatar a toshe shi.

Ina jin Baba Tanimu yana yabon kyan aikin da

Adon yayi, amma ban san kyan wurin ya kai haka

ba sai da Adon ya kira ni naje na gani, dakuna uku

ne a wurin gaba daya yayi musu gyara na sosai,

kowane daki ya maida shi abin da yake son ganin

ya zama guda daya, ya gyara shi a matsayin dakin

kwana daya dakin dahuwa, wato kicin daya kuma

bayan gida na sosai da za'ayi amfani da shi akan

komai sannan ya killace wurin da wata yar

katanga.

Yayi mata kofar shiga dan karamin tsakar

gidan kafin ka shiga 'yan kananan dakunan ni dai

wurin ya ban sha'awa, yayi murmushi ya ce to

yaushe za ki dawo ciki? Na ce ko yanzu, ya yi

56

murmushi ya ce, to shi kenan.

Baba ne yasa Ado daukan katuwar katifar da

ke dakin da muke din, don haka ya sayo mishi 'yar

karama.

Randa na tare a sabon dakin namu tsaf na same

shi ya malale shi da leda yasa katifar yayi mata

shimfida ga akwatinshi a gefe sai Jakar da yazo da

ita da 'yan tarkace kadan, dakin dahuwa kuwa yasa

risho har da tukwane guda biyu da yan tarkacen

kayan aiki kadan, food flask

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login