Showing 9001 words to 12000 words out of 35296 words
Chapter 4 - MIJIN TACE Book 3 Hausa Novels by hafsat Sodangi.docx
a ciki? Da da ni akaje ai
da ban bari anyi hakan ba.
Gaba daya hankalin Ado yayi matukar tashi da
abin da ya farun, ina jin Baba Tanimu da daddare
43
yana ta ba shi hakuri, ita rayuwa fa haka take, a
kullum mutumin kirki ba ya zama ba tare da ana
jarraba shi ba, ba ka fita daga cikin wannan ba ga
kuma wannan ya sake zuwa.
To kayi hakuri kar kuma ka ee zaka yi saurin
gayawa iyayenta tunda ga irin rabuwar da ka ce
kun yi dasu.
Naji Ado ya ce, "A'a Baba, ba zan iya boyewa
mahaifiyarta halin da take ciki ba, tun muna asibiti
nayi waya na gaya mata, ban dai sake gayawa kowa
ba; amma ita kam na gaya mata, ya ce to shi kenan
tunda kaga hakan yafi.
Kwanana bakwai a dakin Goggo Ayalle tana ta
faman tarairayata, Baba Tanimu kuma da su Baba
ubangida suka yi ta bayar da kaji ana yankawa ana
yi min farfesu, har ma cikin kajin Goggo ta cire
wata yar budurwa da ta bata sha'awa ta ce ba za ta
yankata ba, bar min ita zata yi in yi iri.
A zuciyata na ce, uhun ni kam ai ba.zama nazo
yi ba.
A wadannan kwanakin babu wata mu'aallar
arziki tsakanina da Ado, ko gaisuwarshi ban cika
amsawa ba. A cikin kwanakin ne kuma na lura ya
daina zama a gida tun bayan fitan da suka yi da
Baba Tanimu ba a sake wayar gari na ganshi a
44
gidan da safe ba sai gab da Azahar, ana yi sallar
La'asar kuma zai sake fita sai kusan faduwar rana
ya dawo.
Ban san ina yake zuwa ba, ban kuma tambaye
shi ba don a yanzu ko kallon shi bana yi, fatana da
tattalina bai wuce in samu kudin mota ba in kama
hanya in yi tafiyata.
31Rannan ya dawo kusan Azahar ya shigo dakin
na Goggo, duk da yana ganin naji sauki har ma
nayi kyan gani, sai ya tambaye ni ya ya jikin naki
dai Humaira? A lalace na ce mishi da sauki, ya
kalle ni cikin natsuwa.
"Amma kin ga yayi miki daidai a hakan da ki
ke yi Humaira? kina mu'amallah da kowa lafiya
amma ni da na kawo ki babu?" Na kalle shi a
sakarce na ce mishi, "To ka maida ni mana in da ka
dauko nin." Ya ce, to babu laifi ya wuce ya fita.
Ran da na cika kwana goma rannan Baba
Tanimu yasa Goggo ta sani na koma dakin namu,
ita kam taso ne a bar ni in yi arba'in.
Zaman da na yi a dakin Goggo ya sani fahintar
gidan sosai da kuma mutanen gidan.
Sassa guda hudu da ke gidan suna karkashin
dattawa hudu ne wadanda su ne asalin yayan
maigidan su kuma dukan su uba daya ne ya haife
45
su, amma uwa daban-daban, babban cikinsu shine
Baba ubangida sai Baba Halliru sai Baba Tanimu
kafin Baba Tukur shi ne karaminsu..
A duka sassan nan guda hudu akwai iyalai
musu yawa su dattawan gidan kuma suma suna da
nasu matan, Baba Ubangida shi ne mai mata Goggo
Turai wacce take sana'ar kokon safe, Baba Halliru
shi ne mai Goggo Jaku ita kuma tana furar sayarwa
mai dadi Baba Tanimu Goggo Ayalle ita kosai take
yi itama da safe.
Sai Baba Tukur, shi kuma tashi matar ita ce
Goggo 'yar neto ita kuma tana gaudan sayarwa. A
kowane sassa na gidan akwai yaran mata masu
yawa saboda kusan duk 'ya'yan gidan maza masu
aure ne wadan da basu yi ba 'yan kadan ne mafi
yawancin masu auren kuma mata bibiyu ke gare su
masu dai-dai din basu da yawa, kamar ma ba su
dade da yin nasu auren sosai ba.
Yanda duk tsofaffin gidan ke da sana'o'insu
haka suma yaran matan gidan suke da hasu
sana'o'in tun daga mangyada, manja, gyadar miya,
maggi, gishiri, Alala, dan wake, gasu nan dai birjik
Wasu har dinki wasu kuma har aikatau da su wanki
amma dai kowa da abin da yake yi gwargwadon
karin injin shi.
46
Kiwo kuwa a gidan ba a magana duk yawan
Tumaki da Awaki da Kajin kuma abin mamakin shi
ne kowa yána shaida nashi.
Gaba daya sassan nan guda hudu kuma akwai
mace guda da take kamar ita ce shugabarsu a
sassan Baba Tanimu dai Ruwailah ce matar Yaya
Jafaru ta farko, a sasan Baba ubangida da kuma
akwai Furera matar Yaya Baidu itama uwargida ce.
Sasan Baba Halliru akwai Gaje matar Yaya
Jumare, itama uwargida sai sasan Baba Tukur nan
kuma Tanbai matar Yaya Amiru akwai Uwale,
itama uwargida, gaba daya wadannan matan hudu
sun zo gidanne a kusan lokaci daya, ma'ana babu
bambancin lokaci mai yawa a tsakanin aurarrakin
nasu dukansu kuma suna da amare da kuma matan
kannen miji.
Haka nan gaskiyar Mama ne gaba daya gidan
tukunyar abincinsu na dare gaba daya ne da rana ne
dai kowa zai yi abin da zai ci shi da iyalinshi a
wurinshi amma na dare a hade yake duk kumna
wanda ke da girkin ranar to shi ne mai ba da hatsin
da za ayi amfani dashi dama duk abinda za a nema
Goggo Ayalle kuma ta shaida min cewar in mace
tayi girki sau daya to kwana ashirin da biyar take yi
bata sake ba.
47
Ai kuwa kin ga dole suyi ta neman kudinsu
tunda basu da wani aiki na ce haka ne, a zuciyata
kuwa cewa nayi yaran mata ashirin da biyar kenan
a gidan.
Muna nan zaune a dakinmu ni da Ado, zaman
babu wani dadi. Kallon shi bana yi balle in san me
yake ciki, shima baya takura min akan komai zuba
min ido kawai yake yi babu abin da nake fata irin
nera talatin-talatin din da Baba Tanimu yake bani
kullum safiya, ya ce wai in sai abin da nake so in
karya da shi da kuma ashirin-ashirin din kokon da
Baba ubangida yake bani.
Ita kuma Goggo Turai ta ce kai haba, bakin.
wannan yarinyar dai ita kadai ace sai na amshi
kudinta? Je ki ki rike kudinki kin ji? Don haka
kunu da kosai ba saye nake yi ba, sai nake tara
hamsin-hamsin din ina fata su ishe ni kudin motar
tafiya gida in sulale in yi tafiyata.
Rannan na wuni ina murna na kirga kudina sun
kai dubu daya har da dari daya ina lissafin
kwanakin da suka saura kudina su gama cika sai
kawai nazo zan ajiye wata nera hamsin din naga
babu komai sai wata tsohuwar nera hamsin itama
wata kila bai ganta ba ne sanda ya kwashe su. Nayi
kuka rannan har na gaji ban kuma iya cin komai ba
48
saboda tsananin bacin rai.
Ado ya dawo gab da Azahar ya same ni a haka,
ya juya ya fita bai zauna ba, bayan Sallar Isha'i mna
ya shigo dakin da niyyar kwanciya ya same ni ina
ta faman kuka, wuri ya nema ya zauna bayan yaje
yayi wankanshi ya dawo.
Ban kalle shi ba balle in san me yake yi, sai
naji yana magana alamar waya yake yi, gaisuwa ta
ladabi da natsuwa naji shi yana yi, don haka na
kasa kunne ko zan gane da wa yake maganar, sai
naji yana cewa.
"Gaskiya Inna na gaji da karyar da nake yi miki
ne, cewar muna nan lafiya, a gaskiya ba hakan ba
ne, ina jin salatin da Inna ta soma yi, ban san me ta
ce ishi ba, sai naji ya ce mata gata, nayi kamar ba
zan karba ba sai naga to ni kuma a wa?
Inna ta ce, a bani waya in ki karba? Ina karbar
wayar na kaita kunnena naji muryar Innata gaba ya
yanke ya fadi nan take na soma yi mata kuka bata
yi min fada ba kamar yanda nayi zaton zata yi
magana ta soma yi min cikin natsuwa da kwanciyar
hankali.
Ban ji dadin yanda ki ke yi wa mijinki ba to da
wanne zai ji? Da halin da yake ciki ko da rashin
lafiyarki da yayi ta fama da ita? Ko da bacin ran
49
abin da ki ke yi mishi? Matar kirki kuwa ai bata
haka, ita takan taimaki mijinta ne a duk lokacin da
tasan yana bukatar taimakonta, ta rufa mishi asiri a
inda tasan yana bukatar rufin asirinta.
In ta san yana cikin tashin hankali kuma ta
kwantar mishi da hankalinshi, sannan in ba ki sani
ba wannan abin da kike yi ba shi kadai ki ke
tozártawa ba har da ni, don kuwa kina kokarin
nunawa wadanda basu sanni ba ne su san yanda
nake tunda ai ita 'ya wakiliya ce ta uwarta.
In kiyi halin kwarai ace kin samu tarbiyaa a
gidan ku in baki yi ba a gane uwarki ba mutuniyar
kirki ba ce kar in sake jin an ce min baki kyauta
ba, in dai ba kina so raina ya baci da ke ba ne, tana
fadin hakan ta kashe wayar.
Sunkuyar da kaina kasa nayi, nayi shiru ban iya
cewa Ado komai ba, iyaka dai ranar mun kwana
lafiya amma ko kusa da ni bai zo ba, balle ya ce zai
taba ni, ina wurina yana nashi.
Washegari da Asuba yana idar da Sallah Asuba
ya shigo ya tashe ni ya wuce ya fita, sai dai
maimakon sai Azahar in ga ya dawo, wajen sha
daya naga shigowarshi. Ya koma gefe yana cire
ranbut din kafarshi da hand glove din hannunshi
mahadin ranbut din.
50
Naji Baba Tanimu daga daki yana ce mishi "Ka
dawo ne Adamu?" Ya ce mishi "Eh Baba, na
dawo." Ya ce "Sannu da kokari ka ji? Ubangiji ya
yiwa kokarin ka albarka." Yayi murmushi ya ce
Amin Baba." Ya shigo cikin dakin namu ya same
ni ma Zaune.
Ya kakalle ni yayi murmushi, ya ce to ko ke fa?
Kin yi wankanki kinyi fes da ke, na sani ba kya jin
dadin mu'amalla da kayan da ki ke amfani da su
tunda sunyi miki karanci da yawa dogayen riguna
biyu ne kawai, sai zanin da ki ka zo da shi a jikinki.
Kiyi min hakuri a yanzu, na katse shi ta hanyar
fara gaishe shi, yana gama arnsa gaisuwar ya kalle
ni cikin natsuwa ya ce, samo min dumamen tuwo
wurin Goggo Ayalle, na ce to, na tashi na tafi cikin
zuciyata ina tunanin tun zuwanmu gidan kwanaki
ashirin da daya da suka wuce ban taba lura da cin
shi ko shanshi ba, ban kuma taba dora tukunya a
murhu don yin girkin rana ba, tunda kowa yana
abincin ranarshi.
Ni dai nasan duk abin da Goggo Ayalle zata ci
zata bai haka nan ma Yaya Ruwailah tunda nima
yanzu yayan nake kiranta.
Na dawo da kwano mai dauke da tuwon da aka
dumama shi tare da miyar shi a wuri daya na ajiye
51
mishi na koma gefe na zauna sai ya sake kallona
cikin natsuwa ya ce min baki bani cokali ba, nayí
maza na kalle shi saboda sanin shi ba mai cin tuwo
da cokali ba ne.
"Da cokali za ka ci?" Ya ce, "Eh, dashi na ke ci
yanzu saboda hannun nawa ba na jin dadin cin
tuwon da su." "Me ya same su? mu gani." Bai yi
magana ba ya ware min tafin hannayen nashi.
Tsigar jikina tayi matukar tashi tayi wani
yarrrr! hankalina yayi matukar tashi da yanda naga
hannun Ado gaba daya hannun nashi bororo ne ya.
duru ruwa, wani wurin ma ya fashe ya zamą miki
babu dadin gani.
Fuskarta a yamutse saboda yanda hankalina
yayi matukar tashi na tambaye shi me ka ke yi
hannunka yayi haka? Shirun da yayi bai ban amsa
ba yasa na sake tambayarshi Noma? cikin nutsuwa
ya kalle ni ya ce min, in nayi noma menene
Humaira?
Ni ba namiji ba ne? Ni fa ba wannan ne wahala
a wurina ba, wahala a wurina bai wuce ki ki yarda
mu zauna lafiya ba, amma in za ki yarda mu zåunna
lafiya ki gamsu da kokarina ki yarda da cewar in
ban yi miki ba, ba ni da shi ne.
Kiyi min hakuri ai ba zan gane ina wahala ba
52
sai in rinka ganin tanfar abin da ya dani a
matsayina na namiji kawai nake yi in kuwa haka ne
kin ga bai zamo min wahala ba.
Ban iya cewa Ado komai ba saboda kukan da
soma yi ban taba hira na gane matsananciyar
ramar da yayi ba sai a yau, na dai san nai Goggo
Ayalle tana yawan fadin yaron nan Adamu ya
zube. Amma ban lura na gane irin zubewar ba, sai a
yanzu.
Tashi yayi yaje ya dauko cokalin ya dawo ya
zauna ya soma cin tuwon, ni in don ni ki ke kuka to
ki share hawayenki, in kina so in san kina tausayina
to in ina tare da ke ki bar ni in samu kwanciyar
hankalin da nake bukata.
Yaua gamawa ya tashi ya sake fita, nima na
share hawayena na tashi naje sasan Baba Halliru
wurin Goggo Jaku na gaisheta, na ce mata Goggo
yau zan karbi furar da kullum ki ke cewa bana
zuwa ina karba, tayi murmushi ta ce, kai ai kuwa
dai kin kyauta yar nan, gata kuwa an gama
mulmulata.
Ta miko min tayi shar gwanin sha'awa, sai
Kamshi take yi, gata nan debi maza yanda zai ishe
ki nasa hannu na debi guda hudu ta ce ke tafi can
da kwauro, za ki yi wa kanki, ta sake watso min
53
guda shida a cikin kwaryar da ke hannuna nayi
mata godiya na tafi.
Nura na kira ko Zulai yaya, Yaya Ruwaila ne
gaba daya suka taho na ce to ke Zulai je ki ki huta
kai Nura yi sauri kaje bakin kasuwa ka sayo min
nono, ya ce to.
Ina zaune ina dama furar ina tunanin kai! Dabai
akwai fura, amma babu nono. nono ruwa-ruwa? Na
jawo robar yougort din da ke dakin na bude shi na
juye a cikin damammiyar furar na gaurayata na
rufe.
Ana yin Azahar Ado ya sake shigowa nayi
mishi sannu da zuwa, ya amsa. Na jawo kwanonon
fura na mika mishi ya kalle ni da walwala a
fuskarshi ya ce to ke fa? Na ce ai na sha, ya ce eh,
amma ba zai taya ni musha tare ba ai.
Na zauna muna shan furar tare har muka gama,
muka dan yi hira kadan sai na kalle shi na ce mishi,
"To ka dan kwanta mana ka huta." Ya ce in kwanta
Humaira? Nayi maza na ce mishi eh, ya ce to za ki
yi min tausa ne? Na gyda mishi kaina nuna alamar
eh.
Yayi maza ya mike akan katifar nima na bi
bayan shi na soma yi mishi tausa ina yi mishi danna
ina bin gabobin jikinshi ina matsawa cikin hikima,
54
shi kuma yayi lamo ya lumshe idanunshi nuna
alamar jin dadi.
A hankali kuma yana furta wasu kalmomi da ni
kadai ke iya jin su, bacci mai nauyi Ado yayi bai
farka ba har sai da na tashe shi, wajen karfe hudu
da rabi na yamma abin da bai taba yi ba tunda
muka zo, ya kwanta da rana yayi bacci.
Da daddare rannan muna hira ni dashi ya kalle
ni cikin natsuwa ya ce min ni kuwa Aisha in ban da
kar in yi ta takura miki har in yi ta kai ki bango ban
sani ba da na roke ki kiyi min wata alfarma, na ce
ta menene? Ya ce dakin nan da muke zaune a ciki
ne bana son shi, duk da nawa ne.
Na ce, ni na gane saboda gininsu ma ya
banbanta da na sauran dakunan gidan shi da na
Baba da na Goggo Ayalle.
Bai bani amsa ba sai ya ce min nan din a takure
nake, ba zan iya sakewa nayi kusa da Baba da yawa
ba zan iya zama dashi duk wani motsina yana ji ba,
shi ne nace da za ki yarda da mun fita daga ciki
mun koma wasu tsofaffin dakuna da ke ta can baya,
babu kowa a wurin sa muyi zamanmu zuwa
lokacin da zan samu halin samar miki wurin da zai
dace da ke."
A hankali cikin natsuwa na ce mishi, to mu
55
koma mana. Ya zuba min ido yana kallona, babu
damuwa? Na ce to ai ba daki na biyo ba, ba kuma
shi nazo nema ba, ni a wurina kai ne muhimmin
abu, kai na biyo kai ne mijina a yanzu kuma zan iya
zama da kai a duk in da ya kama.
Kwana uku kawai da yin wannan maganar
tamu Ado ya gama gyaran dakunan da da shara ake
zubarwa a wurin ya kwasheta fes ya gyara wurin ya
tsabtace shi ya gyara dakunan gyara na musamman
ya sai buhun siminti ya toshe duk in da yake
bukatar a toshe shi.
Ina jin Baba Tanimu yana yabon kyan aikin da
Adon yayi, amma ban san kyan wurin ya kai haka
ba sai da Adon ya kira ni naje na gani, dakuna uku
ne a wurin gaba daya yayi musu gyara na sosai,
kowane daki ya maida shi abin da yake son ganin
ya zama guda daya, ya gyara shi a matsayin dakin
kwana daya dakin dahuwa, wato kicin daya kuma
bayan gida na sosai da za'ayi amfani da shi akan
komai sannan ya killace wurin da wata yar
katanga.
Yayi mata kofar shiga dan karamin tsakar
gidan kafin ka shiga 'yan kananan dakunan ni dai
wurin ya ban sha'awa, yayi murmushi ya ce to
yaushe za ki dawo ciki? Na ce ko yanzu, ya yi
56
murmushi ya ce, to shi kenan.
Baba ne yasa Ado daukan katuwar katifar da
ke dakin da muke din, don haka ya sayo mishi 'yar
karama.
Randa na tare a sabon dakin namu tsaf na same
shi ya malale shi da leda yasa katifar yayi mata
shimfida ga akwatinshi a gefe sai Jakar da yazo da
ita da 'yan tarkace kadan, dakin dahuwa kuwa yasa
risho har da tukwane guda biyu da yan tarkacen
kayan aiki kadan, food flask