Advertisement
Showing 24001 words to 27000 words out of 48659 words

Chapter 9 - Salon So Book Hausa Novels By Hadiza Salisu Sharif.txt

ya ce masa, "Sunnu ya
kake jin jikin naka? Ya ce, "To da sauki zan ce,
"Haidar ya yi tsu can ya ce Faruk ina jawahir?"
Cikin mamaki Faruk din ya ce, "Me za ka yi mata?
Haidar ya ce, "So nake na san halin da take ciki."
"Me ya same ta?" In ji Faruk, Haidar ya kwashe yanda abin ya faru ya gaya masa, Faruk ya ce, haba
Haidar me ya sa za ka mare ta? Ai kai ma ba ka yi
dai-dai ba. Wallahi yanxu jawahir tana tsananin son
ka tun da take yi maka duk abin da kake so, kuma
take tsananin gudun bacin ranka, ga shi har ta
kasa jure kishinta ta nuna karara. Haidar ka rage zafin zuciya in ba haka ba wata ran zai kai ka ya
baro ka.
Haidar ya ce, "Ai yanxu ya ma kai ni ya baro din, ni
dai don Allah so nake yi ka je gidan ka gano min
halin da take ciki inda hali ma don Allah ka rarrashe
ta ku taho tare."
♥♥♥SALON SO♥♥♥
♡♡♡♡27 ♡♡♡♡
.
BY SULAIMAN BOMBOY
.
Faruk ya ce, "Ba ruwana babu inda za ni bare ta
zo ka ci mata mutunci ta zo ta rinka ganin h rashin
kirkina.
Haidar ya ce, "To ni ka kai ni wajen ta na ganta,
Faruk ya yi murmushi, Haidar ko dai ka so ma
son ta ne?"
Haidar ya rintse ido ya ce, "Wallahi ban san
lokacin da son yarinyar nan ya yi min dirar mikiya
ba, ya shige ni.
Inna kwanta da daddare Allah Allah nake gari ya
waye don na ga kyakkyawar fuskar matata kuma
kanwata, wallahi ni kadai na san yanda tsananin
son jawahir yake raina, kai abin da na yi wa
Kausar a gananta ma na yi ne don na auna na ga
tana so na kuwa ko ni kadai nake shirme na.
Faruk ya ce, Ka ga irin abin da na so ka gane
tuntuni ka ki, to yanzu kuwa in ta ji halin da kake
ciki sai ta ce don ka ga ba za iya kwanciya da ita
ba ne, shi yasa ka nemi shiri da ita.
Haidar ya ce, "Ai likita ya ce zan warke fa". Ko da
yake yanzu ne lokacin tantance wanda take
sonka don Allah da wadda a kayi auren sha awa.
"Haidar ya ce, Ni dai don Allah ka je ka taho min
da sahibata ko don na ga halin da take ciki.
Faruk ya ce, "Zan je ai yanxu
Kausar ta turo kofar ta shiga fuskarta a murtuke
babu alamar fara'a, ta je gefe daya ta zauna ba
tare da ta kula wani a cikinsu ba. Faruk ya mike
Haidar bari na je in dawo ko? Duk yanda muka yi
zan zo ka ji.
Ya ce, "Don Allah ka je fa yanzu kada ka ki zuwa
ka ji. Faruk ya ce Insha Allahu kuwa yanzu zan
je.
Faruk ya fita ya bar su Haidar ya juya ya kalli
Kausar ya ce, "Me ya same ki ne na ga kamar
ranki a ba ce? Ko cikinne yake ciwo?"
Ta zumbura baki, "Kai yanzu har ka manta da
barnar da Jawahir ta yi maka a jikinka har kake
cewa a je a taho da ita? To wallahi ni ba zan
yarda ba don ta ga ita ba ta da amfani a wajenka
shine za ta nakasta min kai, wato ka zamo marar
amfani, to wallahi ba zan yarda ba don ita ma sai
na nakasta ta, sai dai duk abin da za a yi a yi."
Haidar ya daka mata tsawa ya ce, "Ke ki shiga
hankalinki kina ganin duk da son da nake wa
jawahir da ta yi miki abu sai da na yi mata marin
da ta gigice, to wallahi ki shiga hankalinki idan
kika sake kika taba min mata wallahi sai kin yi
mugun raina kanki, don sai kin yi mamakin abin
da zan yi miki." Ta mike ta yi waje tana kunkuni
ta zari mota ta nufi gidan Yakumbon Haidar wato
kakarsa ta wajen uba, ta je ta zayyane mata
maganganun karya da gaskiya ta gaya mata,
Yakumbo ta hau sababi ka ji mu da tsinanniyar
yarinya don ba ta son sa shine take neman
hanyar kashe shi, to wallahi bi ba yarda zan yi
ba, tashi ki koma asibitin gani nan zuwa yanzun
nan, "Kausar ta koma asibiti ta tarar su Anti da
Momy da su Yaya Abba sun cika asibitin taf, ana
ta jajen abin da ya faru.
Shi kuwa Faruk da ya je gidan Haidar yayi
sallama falon, su jawahir suna daga kicin suka
amsa sallamar suka fito falon, Faruk ya nemi
waje ya zauna jawahir da Bilkisu suka gaishe shi,
faruk ya ce, Haidar ne ya turo ni na zo na ga
halin da kike ciki in kuma da hali ki zo mu je yana
son ganinki. "Jawahir ta sunkuyar da kai ta ce,
"Gaskiya Yaya Faruk ba zan je inda yaya yake ba,
don in na je ban san irin wulakancin da zai yi min
ba, ka ga kuwa da na je ya bata min rai ai gwara
ban je ba.
Faruk ya ce, "Wallahi Haidar yana wani hali na
mutuwar sonki kin san miskilancinsa ya rasa ta
hanyar da zai bi ya nuna miki Kaunar da yake
miki don yanzu da kin ga irin magiyar da lallamin
da ya rinka yi min sai na zo gare ki dakin
tausaya masa.
Kafin ta yi magana Bilki ta ce, "Faruk bari mu
karasa girkin da za mu kai masa sai mu fito mu
je."

********************** ⬇ **************************
********** Ai Hausa Novels ****************
*************************⬆ **********************

DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog.

Visit > https://www.aihausanovels.com.ng

Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post.

Email > aihausabooks@gmail.com

******* FOLLOW US ******

Facebook: Ai Hausa Novels

Twitter: Ai Hausa Novels

Telegram Channel: https://t.me/Aihausanovels



Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafin ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu.

********************** ⬇ **************************
*************** Ai Hausa Novels ****************
********************** ⬆ **************************

Faruk ya ce, to shi kenan bari na je na dawo.
Bilki ta zuzzuba komai a fulas ita kuma jawahir
ta je ta shiga wanka ta fito ta shirya cikin atamfa
ja! Super Holland dinkin filet ne ya kama jikinta
sai zani da dankwali da ta daura, farar hoda
kawai ta shafa a fuskarta sai dan man leben da
ta shafa ta dauko jan mayafi da jan takalmi ta
saka, kunnanta fashon din yari ne me jan dutse a
tsakiya. Bilkisu ta tafa mata "Amma
yarinyar nan kin yi kyau, kwalliyar taki ta burge ni
sai dai kash kin manta a shafa hadin turarukanki.
Jawahir ta yamutsa fuska, "Kin san fa inda za mu
je za ki ce na shafa hadin turare. Bilki ta ce, to
meye ba wajen mijinki za ki ba, ai gwanda ki
shafa turarukan da kamshinsu zai gigitar da shi
kuma ga karin lada a wajen Ubangiji, don duk
sanda mace ta yi abun da zai farantawa mijinta
har ya ji dadi a ransa to Ubangiji zai ba ta ladan
da ba ta san adadin yawansa ba.
Jawahir ta ce, Haka ne bari na shafa don na
fuskace shi yana son kamshi.
Sun jejjera fulas-fulas din a dan kwando me kyau
ta lullube shi da farin yanki me adon bakin les da
fulawoyi a jiki. Faruk ya dawo suka dunguma a
motarsa zuwa asibiti.
A lokacin ba kowa duk sun tafi sai kausar kawai
da take zaune kan kujera tana karanta jarida, ba
ta daga kai ba balle ta kalli wani a cikinsu. Faruk
ya ce, "To ga ta nan na cika alkawari ko, ga ta
na kawo maka
Haidar ya yi murmushi ya ce, "Ai kuwa na gode
Bilkisu ce ta fara gaishe shi tare da yi masa ya
jiki. Cikin fara'a ya ce, "Ai jiki Alhamdullahi."
Jawahir ta durkusa cikin dari-dari da rawar
murya Kamar
mai shirin kuka ta ce, "Yaya ina wuni? Ya jikin?
Ya ce, "Lafiya lau jawahir ya naki jikin.?
Ya sa hannu ya dago ta daga tsugunnun ya shafi
kuncinta, ya ce, "Wai haka kuncinki ya tashi
hannuna ya fito radau na marin da na yi miki,
sorry Babyna ki gafarce ni, "Kafin tayi magana
aka turo kofar aka shigo tare da sallama,
Yakwalkwal ce ta shigo rike da hannun Sayyid.
Sayyid ya fincike da gudu ya nufi jawahir yana
cewa, "Anti na anti na, shine rannan kika gudu
unguwa kika bar ni ina ta kiran ki ba ki zo kin tafi
da ni ba. "Jawahir ta dauke shi ai yau da kai zan
tafi kai ta kwana a can ko? Jawahir ba ta ankara
ba ta ji saukar mari a kuncinta, Yagwalgwal ce ta
kuma hau fada, "Annamimiya me kuma ya kawo
ki wajen jikana kin so ki kashe shi, Allah bai baki
nasara ba shi ne kika biyo shi nan ki karasa shi
ko?
Haidar kuwa tuni ya diro daga gadon jinyar ya
tare jawahir yana cewa, "Haba Yagwalgwal ya za
ki doke ta ita ma fa ba lafiya ce da ita ba, me ta
yi miki?"
Yagwalgwal ta ce, "Ubanka ta yi min, shege
sallamamme so kake yanda uwarka ta mallake
Alhaji kai ma jikan mallake ka za ayi,
"Yagwalgwal ta ci gaba da nuna jawahir da dan
yatsa tana yi mata sababi, daga yau na gaya miki
ba ke ba Haidar in ke mayya ce ki ci kanki da
kanki, haka kawai hankalinsa ya kwanta yana
zaune da matarsa lafiya za ki zo ki bata musu
zama.
Jawahir ta mike jikinta ba kwari za ta fita Haidar
ya yi saurin riko hannunta yana cewa, "Haba
Yagwalgwal ya za ki zo ki korar min matata ki ce
sai ta tafi? Ai ba ita ta kawo kanta ba ni na sa a
je a dauko ta in ta tafi waye zai yi jiyya ta?
Kawai mutum da matarsa a nemi raba su. Kan ya
rufe baki bakinsa Yagwalgwal ta ba shi nasa
marin ya dafe kunci ita kuma ta ci gaba da
sababi tana nuna shi da dan yatsa, "Ka shiga
hankalinka ka san da wacce kake magana, idan
ba ka san ciwon kanka ba ai ni na san ciwonka,
yarinya ta nakasa ka ka zamo marar amfani
amma ba za ka guje ta ba, wata rana ma ranka
za ta raba ka da shi.
Jawahir ta fincike hannunta ta yi waje cikin sauri
Haidar ya yunkura zai bi ta Yagwalgwal ta rike
shi, Bilkisu ta bi bayan jawahir yayin da Faruk ya
rufa musu baya. Da kyar da ban hakuri ya shawo
kan jawahir ta shiga motarsa don ya mayar da su
gida. Faruk ya ce, "Don Allah don Annabi jawahir
ki yi hakuri da abin da tsuhowar nan ta yi miki.
Jawahir ta yi saurin katse shi, "Haba yaya Faruk
ka fi kowa sanin ta yanda a ka yi aurenmu da
yaya, ba son sa nake yi ba na aure shi don
biyayyar iyayena na zo nake zaman hakuri da shi,
ya tashi ya dankaro min kishiya ni duk hakurin da
na yi a kansa ba a gani ba kenan.
Fashe da kuka Faruk ya ci gaba da rarrashinta ki
yi hakuri jawahir ki tuna aure kike, aure kuwa
bautar Ubangiji ne kada bacin ran wasu ya sa ki
sabawa megidanki kin ji?"
Yanda na san ki da hakuri da ladabi da biyayya ki
ci gaba da yi komai me wucewa ne wata rana sai
labari kin ji?".
.
BY SULAIMAN BOMBOY
.
WHATSAPP
.
08038491393
♥♥♥SALON SO♥♥♥
♡♡PART 2⃣8⃣♡♡
.
By Sulaiman Bomboy
.
Ta daga kai ya ce, "Yauwa ko ke fa gobe ku
shirya da wuri sai na zo na kai ku ta ce to. Ya
sauke su a gidan shi kuma ya koma asibitin shi
kuwa Haidar tun bayan fitarsu jawahir da
Yagwalgwal ta rike shi don kar ya bi su gado ya
koma ya kwanta ya yi rigingine ya rufe idonsa.
Maganar duniya babu wadda ba a yi masa ba
amma ya yi musu shiru ko motsi bai yi ba dole
suka gaji suka hakura suka bar masa dakin.
Faruk ya shigo ya dinga lallaminsa yana ba shi
baki tare da va shi hakuri sannan ya tashi ya
jawo kwandon da jawahir ta jero masa kayan
abinci.
Dakakkiyar sakwara ce lukui da miyar agushi mai
wadataccen nama, sai jalof din taliya da lemon
kwakwa. Haidar ya ce, "Ka ga yarinyar nan da
zan bata mata rai ba za ta ki yin abinci ba don
gudun kada ta bar ni da yunwa." Faruk ya ce, ai
haka ake so ka ga yanzu sai ka rike ta da kyau
ka nuna mata garanci wanda ba ta samu ba a
baya. Haidar ya ce, "Allah dai ya ba ni lafiya amin
in ji Faruk yayin da ya zuba musu abincin a filet
din da ta zubo suka ci sosai dan shi kansa Faruk
ya yaba da dadin girkin nata.
Can kuwa Bilki ta mike don tafiya gida, "To ni zan
tafi jawahir sai dai gobe zan zo da wuri na raka
ki mu sake dubo shi. Jawahir ta hangame baki ta
ce, "Don kin ji Faruk ya fada ba kya tsoron mu je
a yi mana wani sabon wulakancin da ya fi na
yau.?
Bilkisu ta ce, "Insha Allahu hakan ba za ta faru
ba gwanda ki je, kada su samu kafar raba ki da
mijinki ga shi kuma yanzu kuna son juna. Jawahir
ta ce, "Shi kenan Allah ya kai mu goben na gode
Bilki da kaunar da kike min, da ba ni shawarwari
masu kyau da kike yi, Allah ya kara mana dankon
zumunci a tsakaninmu amin. Da haka suka yi
sallama ta tafi.
Jawahir ta shiga dakinta ta kwanta tana tunanin
abin da ya faru yau da ita.
Faruk ya fita ya yi sallar insha Haidar ya kalli
Kausar ya ce ke ba za ki yi sallar ba ne na ga ko
magariba ba kiyiba?
Ta ce, "A'a ina ruwanka a yin sallah ta ka ga
malam kawai ka ji da abin da ya dame ka. Faruk
ya turo kofar ya shigo Kausar ta zuba masa
harara tare da jan tsaki ta mike ta bar dakin.
Faruk ya taimakawa Haidar ya yi Sallah, Haidar
ya daga hannu sama ya dade yana addu'a
sannan ya shafa ya xuba tagumi.
Faruk ya cire hannun tagumin ya ce, "Haba
malam menene kuma? Ka yi hakuri a kan larurae
da ta same ka, ka yarda da kaddara ko?
Haidar ya ce, wallahi ba wannan ne ya dame ni
ba halin da jawahir rake ciki nake tunani kada fa
ta Gudu
gidan Inna ta kuma boye ta ka san ranta ya ba ci
dazu da abin da Yagwalgwal ta yi mata. Faruk ya
ce, "Ba na jin za ta fita har gida na kai ta kuma
na babbata hakuri ka san yarinyar akwai biyayya"
To don Allah ka je ka taho min da ita ta kwana a
wajena ka ga gidan ba kowa sai masu aiki.
"Faruk ya ce, "Ka yi hakuri da safe ai za ta zo ka
ga yanzu dare ya yi yanxu haka ma ta kwanta.
Haidar ya ce, "Haba Faruk don Allah ka taimaka
min ka je ka taho min da jawahir yanzu duk
girman gidan nan ta kwana ita kadai sai masu
aiki? Faruk ya ce, "Shikenan bari na je amma sai
na biya na dau Hafsa don ita ma ta zo ganin
likita."
Haidar ya ce, "Ko dai ta harbu ne.? Faruk ya yi
murmushi ya ce, "To ga mu dai ga Allah don mun
sa rai.
Ya fita yana dariya ya biya ya dauki matarsa
Hafsa suka tafi. Ya ce, Ya ku ka yi da likitan? Ta
ce, "Gwaje gwaje ya yi min ya kuma dauki
fitsarina ya ce da safe a zo a karbi result din.
Faruk ya ce, "To Allah ya taimaka mana ya sa
abin da muke nema ne, ta ce Amin. Suka yi wa
juna murmushi.
Suka yi fakin a harabar gidan Hafsa ce a gaba
don ita take buga kofar falon nasu da yake kulle.
Jawahir da take takure a falo don zuciyarta cike
take da tsoro da fargaba ka sancewar ta ita kadai
a sashen ta yi tunanin ko ta kirawo 'yan aikin
Kausar su taya ta kwana sai kuma ta fasa, to jin
bugun sai ya dada tsoratar
da ita. A tsorace ta je gaban kofar cikin rawar
murya ta ce, "Wanene?" Faruk ya ce, "Bude mu
ne, ta kalli agogo karfe tara gabanta ya fadi,
Allah ya sa dai lafiya? Ta bude kofar ta ba su
hanya suka shigo Faruk ya ce, "Sarkin tsoro da
kin zata barayi ne suka zo sa ce ki?" Ta yi dariya
ta kamo hannun Hafsa ta ce, "Wai yaushe rabon
ki da gidan nan? Ko da yake ban sani ba ko kina
zuwa wajen amaryarku Kausar, "Hafsa ta yi
dariya ta ce, Ni ina zan zo gidan nan mutuniyata
ba ta nan ta gudu ta bar min abokin miji ya zamo
abin tausayi a gari?" Ga ba daya suka yi dariya.
Faruk ya ce, "Kar dai a gaji da mu dan mun kuma
zuwa da kokon bararmu da karin ban hakuri
megida ya ce, a zo a tafi dake don Allah ki kwana
a wajensa. Ta yi shiru can ta ce gaskiya ni ba
zan je wajensa na kwana ba. Faruk ya ce,
"Subhanallahi, kin san hukuncin matar da mijinta
ya yi kiranta ta ki zuwa kuwa? Ko kina so ki
hadu da fushin ubangiji ne?
Jawahir ta ce, "Gaskiya Yaya faruk ba zan je ba,
ba Kausar tana can ba?
Ai ita ta saba kwanciya da shi ni in na je ina da
abin da zan yi masa ne? Faruk ya ce, "Haba
jawahir kada ki yi haka mana da iliminki da komai
ki yi hakuri ki amsa kiran mijinki mana.
Ta ce, "Haba yaya Faruk har ka manta irin
zaman da na yi da yaya Haidar a gidan nan ni
bani da hakki a kansa sai shi yanzu yake da
hakki a kaina har zai neme ni?" Ta sa kuka ta
mike tayi daki, "Wallahi ba inda zan je". Ta turo
kofar dakinta ta kulle.
Hafsa ta ce, "Gaskiya fa ni fa ban ga laifin jawahir
ba, don gaskiya an zalinceta" Faruk ya dakawa
Hafsa tsawa tare da cewa, "Yi min shiru ana
neman sasanta magana kina dada tunzurata. Ya
jawo wayarsa ya yi danne-danne. Haidar ya
dauka, "Hello" Yauwa Haidar ka kwantar da
hankalinka kayi hakuri mun zo mun tarar jawahir
tayi bacci amma don Allah kada ka tsayar da
hankalinka da safe kafin na tafi office zan biya na
dauko maka ita. Haidar kafin ya ce, wani abu tuni
Faruk ya katse wayar ya kuma kasheta gaba
daya don ya san halin Haidar ba kyale shi zai yi
ba.
Haidar kuwa tun daga lokacin wata zuffa ta rinka
tsiyayo masa, hankalinsa ya yi mummunan tashi,
jikinsa sai rawar sanyi yake yi. Ba jimawa zazzabi
mai zafi ya rufe shi. Nan da nan jiki ya rikice a
ranar da sai Abbansa ne da yaya Abba suka
kwana a wajensa. Ba shi da wata magana sai ta
ambaton an bar jawahir ita kadai a gidan nan sai
masu aiki kada wani abu ya samar masa ita.
Yaya Abba ne yake dan karfafa masa gwiwa yana
tunasarsa. Yawan ambaton jawahir da Haidar
yake yi ya sa Kausar ta yi fushi ta baro asibitin
ta dawo gida. Jiyya ta koma hannun yaya Abba
da Faruk, amma asibitin kullum cike yake da yan
uwa da abokan arziki sai dai rashin matansa a
wajen. Duk da haka Yagwalgwal ba ta fasa yada
habaici da kananan maganganu ba don haka Anti
ba ta son yawan zuwa don ita take yiwa
habaicin.
Kamar ita ta haifa mata Haidar din
Yau kwanan Haidar hudu kenan a asibiti suna zaune a
dakin jinyar, Faruk da yaya Abba Haidar ya ce da
su, Faruk da yaya Abba ku fara hada kaya ku
karbo min takardar sallama." Yaya Abba ya ce,
Ah sabo da

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login