Showing 30001 words to 33000 words out of 49582 words

Chapter 11 - AUREN BAZATA COMPLETE BOOK BY ZAINAB YAKASAI.txt

ka?

"wallahi ban mata komai ba rigima ce kawai irin tata "


" To Allah ya kyauta Haiydar ya ce tana kallon wayarsa da ta shiga vibrating, Sanda Haiydar ya daga wayar shi kuma Safeer mikewa yayi ya shige Dakin Shukrah "


" Tana zaune tana charting a bakin gado ya karasa kusa da ita ya zauna sannan ya karbe wayar Hannunta "



" ME zaki ci, Ya tambaye ta yana kallonta "


" Murya can ciki tace bakomai "


" kamo hannayenta yai duka biyun yana kallon cikinta daya dan turo kadan dan ita shukra dama cikinta a shafe yake, "Haba Mana Shukrah Cute ya zaki ce ba zaki ci komai ba, ki daure ko tea kisha"


"Ni bazan sha ba ta fada wane zatayi kuka "


" Ni Gidan Ibtee zani tayi min Tuwo "

" To Alhamdulillahi tunda zaki ci tuwon tashi na rakaki gidan Ibtee, Ya fada yana nikam da ita, Hijab ya dauka a kan gado ya sa mata ya rike Hannunta suka fito parlour inda tayiwa Haiydar sallama don ba da wuri zata dawo ba "


" Har bakin gate din su Ibtee yakai Shukra yace ze jira ta ta kawo masa Amal, Tana shiga parlour taga Amal tana wasa ta dauketa takai masa sannan ta koma cikin gidan "


" sanda ta shiga gidan taga Ibtee tana leka bayan kujera, Shukra ta hade rai don batason yin dariya "


" Lafiya Ibtee, Meye a gurin shukra tace tana lekawa itama "

" Ke banga Amal ba kuma fa wallahi yanzu na shiga daki na dawo kuma ban ganta ba Ibtee tace hankali tashe "


" Shukrah ta gimtse dariyar ta ba tare da Ibtee ta gane ba tace to waye ya shigo gidan ya dauketa? dama baki rufe parlour ba? "


" Inafa na rufe, keni zo mu fita Dalla ta fada sanda tasa Hijab dinta "


" Ai kuwa bamuga ta zama ba Shukrah tace sannan tana hannun Ibtee suka fito "


" Fitowarsu tayi dai dai da fitowar Haiydar da Safeer, Amal na hannun safeer ya bata wayarsa tana wasa da ita "


" wata Nannauyar ajiyar zuciya Ibtee ta saki ta kalli Shukra, Shukrah ta tuntsire da Dariya harda rike ciki "


" Ibtee takai mata duka 'bakida kirki Shukrah dama kinsan tana gidanki baki fadamin ba kikasa na tashi hankalina"


"Har anan Shukrah dariya take taja hannun Ibtee ni zo muje kimin Tuwo shi nake so wallahi, "


Kin jawa kanki ae bazan yiba"


"Haba Ibtee Swthrt, matar abu turab, uwar gida sarautar mata daga ke ba kari, Maman Amal Beauty, dan Allah kimin tuwon kinji Shukrah ta fada sanda suka shigo parlourn "


" To naji zanyi shknn Ibtee tace tana karasawa kitchen, ita kuma Shukrah tayi zaman ta a parlour dan in ta shiga kitchen taji kamshin miyar baxata iya ciba "



" Sai ba adi salamu magrib sannan Shukrah ta koma cikin gidanta inda ta dauko Amal ta dawo wa da ibtee ita ta koma ta samu Safeer zaune a palour yana Aiki a system dinsa "

" Ya Safeer zo muci tuwo ta fada tana ajiye flask din hannunta a kusa dashi, Ta wuce kitchen dauko plate da spoons ta zuba musu, Ta mike ta bude fridge ta dauko musu lacasera ta ajiye tana kallon Safeer "


" Sai da ya kammala abinda yake sannan ya switching off system din sannan ya sauko suka soma cin abincin "



" Washe gari gurin 11:00 Safeer yace Shukra ta shirya yakai ta gidan Ammii daga nan su biya su gaida Hajiyar Haiydar, Shukra harda dan tsalle ta shige toilet don yin wanka "

" Safeer ya juya ze fita kenan ya hango wayar Shukra dan dressing mirror, Da sauri ya karasa ya dauka Kai tsaye contact dinta ya fara dubawa cikin sa 'a kuwa yaci karo da wata Number anyi saving as MY NUMBER, Da sauri ya dauko wayarsa ya dau Number yasa yayi dialing, Tana fara ringing yayi saurin Rejecting yayi mata Saving number sa as "HUSBY"

"Sannan yayi saving tata number as "WIFEY"


"Koda Shukrah ta fito da sauri ta shirya ta samu Ya Safeer a parlour suka kama hanyar gidan Ammii"


"sanda suka isa Safeer ne ya dauko wa Shukrah tsarabar su Ammii suka shiga a tare cikin sa a kuwa suka tarar da Daddy na gida "

" Safeer ya dade sosai yana hira da Daddy sannan Y musu sallama ya tafi "


" Misalin karfe hudu da rabi wayar Shukrah dake hannun Areef ta soma ringing, mika mata yayi da sauri
"Baki sake take kallon number ita dai tasan ba ita tayi saving number nn ba, Tana ta mamaki har kiran ya katse wani ya shigo, Sai anan ta dauka da Sallamar ta"
"Jin muryan Safeer yana Answer mata sallama yasata sauke ajiyar zuciya"


"ki fito mu tafi gidansu Haiydar"


"To kawai tace sannan ta shiga dakin Mamah tayi mata sallama ta fito ta samu Safeer a motar sa suka tafi Gidansu Haiydar "


" Sosai Shukrah ta samu karba ta musamman a gurin Hajiyar su Haiydar, Don Hajiyar Haiydar mace ce mai kirki da son mutane duk da kasan ce watar ta mai kudin gaske amma kudinta be sa mata girman kai ba "


" Sai da sukayi sallar isha sannan suka koma gidansu inda Hajiya ta cika Shukrah da tsaraba, sosai Shukrah ta shiga ran Hajiyar don har tana tambayar ta sanda zata sake zuwar Mata.........





SHUKRA YAR GATAN MIEMIE BIE 💞
[4/27, 1:53 PM] 🎀Shukra yar gatan miemie🎀: 👮🏻AUREN BAZATA 👮🏻




WRITTEN BY
ZAINAB YAKASAI
SHUKRA





Dedicated to Miemie bie 😘






3⃣0⃣



Three Months later


"Shukra zaune a dakinta ta sa akwatuna a gaba tana duba wa zallar kayan Babe ne aciki, a zuciyarta tana mamakin irin wannan soyayya da iyayen ta, iyayen Safeer kai harma da Hajiyar Haiydar suke nuna wa babynta, takai one hour tana aikin kayan kafin ta ture kayan ta jingina a jikin gado tana shafa cikin ta dan wata shida wanda ya yayi girma sosai sai kace dan wata tara, Mamaki da tsoron girman cikin ya hana mata nutsuwa a yan kwanakin nan ga nauyi kamar me "



" Tana cikin haka Safeer ya shigo cikin dakin yana Waya da alama da friend dinsa suke wayar, Sai da ya gama ya juyo yana karawa Shukrah kallo wadda gaba daya ma hankakinta baya wajensa, janyota yayi jikinsa yana shafa kanta "

" Shukrah meye matsalar??

"Tsoro nakeji ya Safeer ta bashi Answer kamar zatayi kuka "

" Dago kanta yayi yana mata kallon mamaki kafin yace tsoron me?


"Wannan cikin mana yayi girma da yawa kamar wadda zata haifi guda goma "


" To Shukrah ae lafiya ce, kuma ma ko guda goma kika haifa ai ba matsala bane indai Allah ya baki lafiya ko "



" Kuka kawae tasaka masa wae ita BAZATA haifi guda goma ba "



" Safeer dae yana mamakin Shukrah yanzu ba dama ayi magana sai tasa kuka, ayi mata wasa ta dauka da zafi, lallashinta yashiga yi yana cewa insha Allah daya zata haifa mai kama dashi tunda batason goma "


" o o ni me kama dani zan haifa tace tana turo baki "


" To naji Allah ya sauke ki lafiya shike nan "


" A a "

" Sai me kuma "

" Sai da ta dauke kai kafin tace ni gidan Ammii zaka kaini "


" Kema dae kya ji kunya Shukrah jiya fa har 10:00pm kina gidan Ammii kuma yau ma wae sa rai kike na kaiki "


" Kukan ta ta cigaba wannan karon har tana hadawa da kaimai duka "


" Ganin Abin Shukrah ba me kare bane yasa Safeer saurin ture ta a jikinsa ya mike ya fice, ita ko Kukan ta take tsakani da Allah a haka dae bacci ya kwashe ta a gurin "



" Sai bayan sallah magrib sannan Safeer ya dawo gidan Shukra na zaune a parlour tana cin gireba, suna hada ido ta daure rai ta maida kallon ta jikin TV"


"Yammata na, yanzu kina kallona na shigo cikin gidanki amma ba sannu da zuwa ba komai "


" Ban iya ba tace ba tare da ta kalleshi ba "

" Baki iya gaisuwa ba Shukrah ya fada sanda ya karaso kusa da ita yana binta da kallon mamaki "

" To kaima baka iya dubiya ba ta fada tana murguda masa baki "


" iye Shukrah ya Safeer din kike yiwa haka? Yayi maganar irin abin ya bashi mamakin nan "


" komai ba tace ba sai ma juya masa baya datayi tana cin gireba hankali kwance "


" Ya dade a tsaye yana mata kallon mamaki kafin ya girgiza kansa ya wuce dakinsa a ransa yana cewa

"Shukrah dae ta zama a lallaba"



"Shukrah na nan zaune har 9:00tayi, wayarta ce tayi ringing tayi saurin dauka kamar me jira DR WAHEEDA ta gani jikin screen din sai da tayi murmushi kafin tayi picking, tayi mata Sallama ta answer "


" Bayan yan gaishe gaishe ne, waheeda tace Shukrah bakida kirki wallahi ace kin samu cikin har 6 Months amma baki fada min ba "


" Shukrah wadda kunya ta rufe tayi murmushi batada abinda za tace shiyasa tayi shiru "


" Kinyi Shiru Shukrah ko bakya jina ne? Waheeda ta tambaya "

" Da kyar Shukrah ta ce mata kiyi hakuri ae nayi tunanin ya fada miki "


" Inafa ya fada min, Ae zan gamu dashi ne kedai Allah ya sauke ki lafiya, Badai wata matsalar ko?


"Ba matsala wlh "


" Daga haka dae Shukrah yi sallama Shukrah dae har anan bata dena jin kunya ba, Don sosai take jin nauyin DR Waheeda hakan nema ya hanata sanar mata tun farko "






" To kamar yadda Safeer Yayi wa Shukrah alkawarin zasu sake zuwa San Francisco haka kuwa akayi don yau Safeer Bayan ya tashi daga office Golden season travelling agency ya nufa kai tsaye yayi musu visa shida Shukrah da Miemie "



" Sanda ya shigo gida tarar wa yayi Shukrah tayi baki wasu yan uwansu sune na katsina suka zo, Tsayawa yayi suka gaisa sannan ya wuce, Shukrah kamar bazata tashi ba tayi zamanta ta cigaba da hirar ta sai da wata Auntyn ta Aunty Nabeehart ta harare ta
" Kin tashi kin bi mijin ki ko sai na kwada miki mari tukun na"



"Turo baki Shukrah tayi ta tashi tana cewa Aunty fa banida lpy sannan ta shige dakin Safeer "


" Sanda ta shiga ta samu har ya shige wanka saboda haka sai kawae ta fito mai da kaya tayi kwanciyar ta kana game a wayar sa "


" Sanda ya fito gaban dressing mirror ya nufa ya dauko cream ya dawo kusada Shukrah ya zauna, Tana ganin haka tayi saurin minimizing game din ta ajiye wayar ta mike, sai da ta karbi cream din hannunsa sannan ta kalleshi ta fara magana kasa kasa

"Ya Safeer ka dawo lafiya ya office?


" Alhamdulillahi, Yau na zo miki da albishir "

" Cikeda zumudi tace ya Safeer menene dan Allah "?


" Inna fada miki me zaki bani as a gift "


" Duk me kake so zan baka wallahi "

" Are you sure! Yace in between laughter dan shi kadae yasan tanadin da yayi mata "


" Absolutely sure inji Shukra don bata me yayi ba,

"To shknn zan fada miki koma menene amma ba ynx ba sai dare "

" me yasa sai dare Shukrah ta tambaya cikeda rashin fahimta

"banason tambaya tayi yawa tunda nace sai dare ae saiki hakura ko"
"Shukra bata sake cewa komai ba har dae ta gama shafa masa cream din ta koma wajen bak'in ta "


" Da daddare bayan Safeer ya fito daga masallaci be wuce ko inava sai gidan Mamah inda yayi mata bayanin tafiyar tasu, ya kuma fada mata tare da Miemie zasu tafi "



" Miemie da tunda ya shigo cikin gidan ta rufe idonta kamar me bacci wae don karta gaishesa ta fasa ihu hade da duro wa daga kan kujera "

" Ya Safeer dan Allah dani zaka tafi San Francisco wayyo dadi, Wayaga Miemie a cikin turawa wai! A gaskiya ka gama min komai wallahi God bless your unborn Babe ta karasa harda yar rawar ta "


" Baki sake Safeer ke kallon ta haka kuma rai a hade, azuciyarsa yana daya sanin yi mata visa, Wai dama ba bacci take ba tsabar iskanci ne ya hanata gaida shi ""


"Wata uwar tsawa ya mata wadda ba Miemie ba har Mamah da Aysher da Abbah dake kokarin shigowa parlourn sai da suka tsorata
"Bakida hankali ko, to wallahi ki kama kanki kinsan me yake miki ciwo, in kuma kinki wallahi zan baki mamaki useless kawai"


"Abbah ne ya karaso cikin parlourn ya dafa kan Safeer sannan yace''kayi hakuri babban yaya sai hakuri addu a zaka tayata da ita kaji "


" To kawai yace sannan ya mike yana kallon Mamah yace''ta shirya wednesday zanzo na tafi da ita tunda friday zamu tafi, yana kaiwa nan ya fice daga gidan "



" Tafiyar 40mints ne ya kaishi gidansa, a parlour ya tarar da Shukrah a kwance kamar me bacci, ya kara so kusada ita ya dauke ta cak sai a kan bed bayan ya sauketa ya shige toilet sai anan Shukrah ta bude idonta don kwanciyar bata mata dadi ba "

" Minti goma ya yayi yana shiryawa bayan ya fito a wanka, kan bed yahau ya zauna kusa da Shukrah ya riko hannunta ya akayi ne Shukrah cute?

"Abinda zaka fada min dazu kace na bari sai dare zaka fadamin "

" Me kike ci na baka na zuba ae ynx zan fada miki, kedai ba kince duk me nakeso zaki baniba "


" Saurin daga masa kai tayi don ta matsu taji me zai ce "


" Good gal dama fada miki zanyi Friday zamu tafi San Francisco "


" Ae Shukrah batasan sanda ta fada jikin Safeer ta kankame shiba "


" Shima kankame ta yayi hade da zame rigar jikinta ya zura harshen sa cikin bakinta yana tsotsa as if ya samu sweet ne..............



SASSANYAR ASUBA TA GARI 👌🏻
[4/28, 7:08 PM] 🎀Shukra yar gatan miemie🎀: 👮🏻AUREN BAZATA 👮🏻





WRITTEN BY
ZAINAB YAKASAI
SHUKRA





Dedicated to Miemie bie ❣





3⃣1⃣



"Yau tuesday Safeer na zaune a office dinsa da yamma misalin karfe 3:20pm Haiydar ya shigo da sallama a bakinsa, Sai da Safeer ya answer masa kafin ya kariso ya zauna yana facing Dinsa "


" Ajiye Files din hannun sa yayi sannan ya ce

"Haiydar ya Aikin?

" Alhamdulillahi "
" Dan Allah ka tayani yiwa Hajiya Godiya tana ta hidima wallahi Allah dae ya kara girma "


" Sai da Haiydar yayi murmushi kafin yace ae bakomai Safeer yiwa kaine "

" Duk da haka dae kae mata godiyar "


" To insha Allah zan mata, Daga nan dae suka cigaba da Hirar su wanda mafi akasarin hirar dae akan Miemie ake yinta, Har sai da ran su ya baci dukansu sannan Haiydar ya mike yana bin Safeer da Mugun kallo "



" Ae dama na dade da sanin baka sona da kanwar ka shiyasa kake ta wani kakkaucewa to wallahi duk a binka sai na Auri miemie insha Allah, kuma gobe xanje na samu Abban na masa magana da kaina Haiydar ya fada yana nuna safeer 👉🏻"


"Murmushi Safeer yayi yana mikewa da niyyar fita sannan yace Haiydar kanada Matsala wallahi kullum anyi ta maimata magana daya ne wae, Haba da Allah be a man mana me xakayi da wata miemie yarinya ko gama mallakar hankali batayi ba "


" Naji koma me zakace sai dae kace amma dae sai naje na samu Abbah inyaso kafin naje ka rigani zuwa ka zuga kaji ko "


" Ni na isa na zuga shi Haiydar Allah ya bada sa a kaje wallahi, Kuma Allah ya huci zuciyarka "

Daga nn dukansu suka fito kowa ya shige motar sa ba tare da sunyi sallama ba"


"Sanda Safeer ya isa Gida Shukrah na kitchen tana toasting bread, ta fito da sauri tazo ta kama hannun sa tana masa sannu da zuwa "


" ME ake mana ne Shukrah cute naji gidan kamshi Safeer yace yana rungumo Shukrah jikin sa "


" Bread nake toasting wallahi yau shi nake Sha 'awa shukra tace sanda suka karasa dakin, Shigewa toilet tayi don hada masa ruwan wanka shikuma ya cire kayan jikinsa ya daura towel ya bi bayanta "


" A bakin kofa suka hadu, ta raba zata wuce ta gefensa yay saurin janyota, "Ina zaki kuma?


" Kitchen zan koma ta bashi answer tana kokarin janye jikin ta a nasa "


" Ya kwantar da murya kamar me shirin yin kuka 'Da wanka zaki min Wallahi na gaji yau tunda na zauna ban tashi ba "


" Dariya tayi sannan ta kwace jikinta ta fita da sauri tana masa gwalo, shima dariyar yayi sannan ya fara wankan sa "




" sanda ya fito ya samu shukra a parlour tana cin toasted bread nata nan yayi joining dinta suna ci suna hirar su abin sha, awa, sanda suka kammala Shukrah ta kai bowl din kitchen ta dawo ta sameshi suka cigaba da hirar su har zuwa lokacin sallar magrib sannan Safeer ya fita mosque ita kuma tashiga daki don yin sallah "



" Washe gari Safeer beje office ba a gida ya zauna ya taya Shukrah hada musu trolley sai bayan sallah la 'asar sannan ya tafi gidan Mamah dauko Miemie kamar yadda ya mata alkawari , Sanda ya shiga gidan Miemie ce kadai a parlourn Aysher na kitchen, Mamah kuma na sama, Miemie tasa trolley a gaba ta buga tagumi harda dan hawayenta don ta gama fitar da ran zuwan Safeer, Ae tana ganin ta fasa ihun murna ta nufo shi da gudun ta, Saurin dakatar da ita yayi ta hanyar mata wata gigitcciyar tsawa

"Kina kara sowa nan sai na kwada miki mari wallahi, shashasha kawai"



"Kuka ta fasa tana kwalawa Mamah kira kamar Safeer yamata wani abun , A tare Mamah da Aysher suka iso parlour'n suna tambayar ta lafiya "

" Ba yaya Safeer din nan bane bezo da wuri ba kuma yanzu yazo wae ze mare ni, Miemie ta fada cikeda da shawgwaba tana kara fashe wa da kuka "


" Ba

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login