Showing 27001 words to 30000 words out of 49582 words
Chapter 10 - AUREN BAZATA COMPLETE BOOK BY ZAINAB YAKASAI.txt
a Parlour yayi mata bayanin komai, Nan ta mike da sauri takira Ahmad suka je inda Shukra, Azeeza jin yadda jikin Shukra yayi zafi yasa ta fashe da kuka, abinda ya daga hankalin Safeer "
" Da Hanzari Ahmad ya dauko car key dinsa Safeer ya dauko Shukra bayan Azeeza ta sa mata Hijab Suka wuce Asibiti "
" Suna zuwa Aka karbe ta, Bayan test test da akayi Doctor tayi musu babban Albishir cewa Shukra nada ciki har na wata Biyu "
" Zo kuga murna gun Safeer kai bama shi kadai ba harda Azeeza da Ahmad tunda su basu taba haihuwa kuma sun dau Safeer da Shukrah tamkar yan uwansu wannan ne yasasu jin kamar su za ayi wa haihuwar "
" Sai ba adi salatul Magrib sannan suka baro hospital kuma Alhamdulillahi jikin Shukra yayi sauki sai dai rashin kwarin jiki kawai "
" Sosai Shukra ke samu gata gun Ahmad, Safeer da Azeeza, Don Azeeza ta hana tayin komai cikin gidan har ruwan wanka ita ke hada mata da kanta "
" Kayan baby kuwa abin ba a cewa komai don kullum Ahmad ya fita sai ya siyo su hakama Safeer don ya zama dan gari "
" Safeer ne ya kira Aysher ya gaya mata Ankoyi sa a ranar Ammii da Areef sun zowa Mamah ziyara, Nan Aysher ta fada musu maganar cikin Shukra, zo kuga murna gun Ammii da Mamah bakin su yaki rufuwa su a dole murnar samun babban jika suke a take Ammii takira Daddy ta fada masa kusan ma Daddy duk ya fisu don cewa yayi inyagama abinda yake a Dubai zai wuce san Fancisco ya gansu "
" Mamah ta kira Shukra tayi mata murna tayi mata addu 'ar samun lafiya, Ita dai Shukrah kunya kamar ta nutse, sai bayan sunyi sallama da Mamah ta juyo kan safeer tana dukansa da hannu biyu tana mai kukan shagwaba "
" Shine kaje ka fada wa su Mamah inada ciki ko? Yanzu da wani ido kake so na kallesu "
" Rike hannayenta yayi ya janyota Jikinsa ya Matse ta har sai da ta saki yar kara sannan ya sassauta rikon "
" Shukrah Ai ko ban fadawa mutane ba zasu gani ae in mun koma "
" Ni bazan koma ba sai na haihu, Ta fada cike da shagwaba "
" Ae baki isa ba nanda 2 weeks zamu tafi don next week za a gama Aikin company kuma office suna nema na "
" Ni bazan tafi ba sai dae kaje ka barni a nan "
" Bazan barki ba Shukrah "
" Nan dae Shukrah ta cigaba da kukanta na shagwaba wae ita bazata je aga cikin taba sai dae a ganta da baby "
" Shiko Safeer shiru yayi yana jinta don yasan inya biye mata rigima zatayi tayi masa don ita cikin nata da tabara, Rigima da shagwaba yazo mata, Ahaka dae bacci ya dauketa ya sauke ta daga jikinsa ya mata addu a shima yayi ya Rungumeta sai bacci...........
SHUKRA YAR GATAN MIEMIE BIE 💞
[4/22, 9:13 AM] 🎀Shukra yar gatan miemie🎀: 👮🏻AUREN BAZATA 👮🏻
WRITTEN BY
ZAINAB YAKASAI
SHUKRA
Dedicated to Miemie bie 😘
2⃣7⃣
"Misalin karfe daya da rabi Shukra ce da Azeeza a kitchen da Alama Lunch suke hadawa, Azeeza na daga gefe tana dafa white spaghetti Shukra kuma tanayin Beef Goulash "
" Wayan Shukra ne ya shiga ringing ta ajiye spoon din Hannunta ta nufi wayar, Ibteesam ce me kiran shiyasa Shukra tayi saurin picking tana mata sallama
"Shukra Fadamin da bakin ki dan Allah inji Ibteesam da murnar ta"
"ME zan fada miki Shukra ta tambaya "
" Ki fada min SIRRIN BOYE (sabon Novel dina bayan AUREN BAZATA insha Allah) inji Ibtee tana dariya "
" Dariyar itama Shukra tayi don ta gane me take nufi "
" Wata nawa ne?
"Wata Biyu ne "
" kice Amal ta kusa samun kanwa inji Ibtee "
" Ta kusa kam "
" Daga nn dae suka cigaba da Hirar su ta kawaye har sai da Shukra taji Beef Goulash dinta na neman kamawa sannan tayiwa Ibtee sallama ta koma kan girkin ta "
" kamar yadda Daddy yayi Alkawarin zuwa San Francisco ganin Shukrah Haka kuwa akayi ranar wata friday ya kira safeer ya fada Masa gobe ze biyo jirgi yazo ya gansu, Shukrah kamar ta zuba ruwa a kasa tasha don Farin ciki "
" Ranar da Daddy zezo Abinci kala kala Shukrah da Azeeza sukayi, Karfe Uku saura jirgin su Daddy yayi landing a San Francisco, Inda ya kira Safeer a waya Sukaje Shida Ahmad suka tawo Da Daddy "
" Rungume Daddy Shukrah tayi don Murna kafin taja Hannunsa ta Zaunar da shi kan One sitter ita kuma ta zauna a gaban sa tana masa labari sai dariya suke "
" Azeeza ce ta kawo wa Daddy Abinci da Drinks sannan Suka gaisa Nan Safeer da Ahmad ma Suka zo suka kara Gaisawa da Daddy kafin suka tafi suka barshi yaci Abinci "
" Koda Ahmad da Safeer suka fita Hotel room suka kamawa Daddy sannan suka je sukayi masa Siyayya me yawa suka kai Room din sannan suka dawo gida "
" Sanda Suka tafi Mosque ne suka yiwa Daddy bayanin Komai kuma yaji Dadi, Da suka idar Suka kai Daddy Hotel din Sannan suka dawo gida "
" Safeer da Shukra zaune a dakin su Ga abinci a gaban su
"Shukrah yanzu bazaki ci abinci ba, kin taba ganin inda akayi haka? Bafa ke kadai bace ba "
" Ni bazan ci wannan abin ba ta fada tana nuna masa plate din gabansu kamar zatayi kuka "
" To naji me zaki ci "
" Dan wake ta fada tana kwanta wa a jikinsa "
" 😳Dan wake kuma Shukra? Haba da Allah yanzu a ina zan samu dan wake a nn, Kuma naga da ae bakya cin Dan waken "
" Toni yanzu shi nake so ta fada tana fashe da kuka kamar an mata wani abun "
" Rungume ta yayi tsam yana lallashi amma taki jinsa sai kara volume din kukan ma tayi "
" Yi hakuri Shukra dan Allah ki fada min wani abun amma banda wanda bazan samu a nn ba "
" To naji na canja Dan - Malele zanci "
" Safeer kamar zeyi kuka yake ji, Tabarar Shukrah ta soma damunshi, "ynx fisabilillahi Shukrah a ina zan samu wani Dan -Malele a nn"
"Toni shi zanci "
" Shiru yayi mata be kara cewa komai ba ya janyo plate din ya fara cin abincin sa "
" Shukrah ganin ya kyaleta ya sata fasa masa kuka sosai har tana bubbuga kirjinsa, Rike hannayenta yayi da nasa guda daya yana cigaba da cin abincin sa har anan bece mata komai "
" Shiru tayi ta kara lafewa a jikinsa tana sauke ajiyar zuciya har bacci ya dauketa "
" Sai da ta gama cin abincin sannan ya kwantar da Shukrah a kan gado sannan ya dauki plate din yakai kitchen ya dawo ya kwanta a kusa da Shukrah bayan ya musu addu 'a, Da tunanin rigimar Shukra bacci ya dauke shi "
" Cikin dare yunwa ta damu Shukrah ta mike ta fara bubbuga Pillow' n safeer, Bude idonsa yayi ya sauke su kan Shukrah da tayi kalar tausayi tana kallonsa "
" Ya akayi? Ya tambayeta da muryan bacci "
" yunwa nakeji ta fada tana jan hannunsa "
" Mikewa yayi ya fita, kitchen ya je ya hada mata Tea sannan ya dawo ya samu ta shiga Toilet "
" Tana fitowa ta nufi inda yake da sauri ta karfi cup din hannunsa bata damu da zafin da tea din yake da ba ta kafa kai ta fara sha, Bata ajiye ba sai da ta shanye tsat, Ta zauna bakin gado ta rufe idonta tana maida numfashi, Wani tausayin ta yaji yana shigarsa sosai "
" wani zafi Shukrah taji tana ji sai gumi take, Ganin da yayi tana gumi ne yasashi shiga toilet ya hada mata ruwan wanka, Ya dawo ya daga ta ya cire mata rigar jikanta ya dauketa cak sai toilet, Da kansa yayi mata wanka sannan ya dauko ta ya dawo da Ita ya kwantar kan gado shima ya kwanta sai bacci "
" Sai da Daddy yayi 1week a San Francisco, sosai yayi wa baby siyayya shima sannan Y soma shirin komawa Nigeria, Shukrah yar Rigima wae sai ta bishi,jin safeer be ce mata komai ba yasata yin shiru da maganar "
" Ranar da Daddy ze koma dukansu ne suka rakashi Airport sai da su kaga tashin su sannan suka koma gida suma "
" Yau ake taro bude Company 'n Ahmad, Sosai manyan mutane suka halarci taron kasan cewar Ahmad shahararre kuma fitacce a San Francisco state, Bayan gaishe gaishe, ciye ciye Ahmad ya gabatar da Safeer a matsayin Manager' nsa, sosai abun ya bawa Safeer mamaki don be taba tunani ba kuma koda wasa Ahmad be fada masa ba, "
" Se bayan da aka kammala taron ne Safeer ya samu kebewa da Ahmad inda yayi masa godiyar wannan alherin da yayi masa "
" Nan Ahmad ya nuna masa ba komai ae duk daya ne, Saf
[4/22, 11:55 AM] 🎀Shukra yar gatan miemie🎀: 👮🏻AUREN BAZATA 👮🏻
WRITTEN BY
ZAINAB YAKASAI
SHUKRA
Dedicated to Miemie bie 😘
2⃣8⃣
"Safeer ya kira Mamah ya fada mata irin Alherin da Ahmad ya masa, Nan Mamah ta bukaci Safeer ya hada ta da Ahmad din, Ya bashi wayar kuwa inda Mamah tayi masa godiya sosai sannan tayi masa Addu 'a, Sosai Ahmad din yaji dadin yadda Mamah tayi masa "
" Yau saura kwana Biyar su Shukrah su koma Nigeria, Sosai Ahmad da Azeeza suke musu tsaraba wanda yawanci kayan Babe ne, Azeeza ce ma tayi wa Aysher da Miemie tsaraba, inda Ahmad yayi wa Mamah da Ammii tsaraba shi kuma "
" Ana gobe zasu koma cikin gidan ba wanda yayi bacci suna tunanin rabuwa (sabo turken wawa), Jirgin bakwai da rabi zasu bi hakan yasa koda su safeer suka dawo daga mosque wanka ya shiga bayan ya fito ne itama Shukrah tayi "
" 6:40am dukansu suka fito suka shiga mota Sai Airport, Cikin mota Shukra da Azeeza sai kuka suke sun rungume junansu, Suma su Safeer kawae dauriya suke irinta mazaje amma suna jin ba dadi a ransu wannan ne dalilin da yasa basu hana su kukan ba ma "
" 7:30 aka fara kiran sunansu, safeer da kyar ya janye Shukra a jikin Azeeza bayan ya mata alkawari zasu sake dawo wa kafin ta haihu tunda shine manager 'n company' n Ahmad so akwai bukatar zuwansa San Francisco akai akai "
" Sai da Su kaga tashin su sannan Ahmad yaja Azeeza mota wadda har anan kukan take (Sabo da dadi rabuwa ba dadi) "
" A Nigeria Miemie da Aysher ne a kitchen suna ta girki kala kala, Dama Mamah ta nemi alfarmar Ammii kan tazo gidanta su tari su Shukrah gaba daya "
" Ammii bata watsa kasa a idon Mamah don tun 9:00am sukazo ita da Areef "
" To cikin jirgi Shukra sai kukanta take Safeer na Aikin lallashi, Da kyar ya samu tayi bacci sannan hankalinsa ya kwanta "
" 2:00pm Jirgin su yayi landing a Airport na Malam Aminu kano, Suna fita Safeer ya kira Haiydar ya fada masa sun karaso sannan suka koma gefe suna jiran zuwan Haiydar din "
" Bayan kamar minti ashirin sai ga Haiydar ya zo ya fito ya tayasu zuba kayan su a booth ya jasu sai Farm Centre "
" Miemie najin tsayawar mota ta fito da gudu dai dai sanda Shukrah ke fito da ga motar Haiydar, Miemie tayi tsalle ta Rungume shukra cike da murnar Ganinta, ita ma Shukra da murnar ta ta rungume miemie suka shige gidan gaba daya "
" Shukrah na ganin Ammii ta fada kanta ta rungume hade da sakar mata kukan shagwaba "
" Baki Ammii ta saki tana kallon Shukrah da mamaki
"Kukan na meye to Shukrah"
"Na dadi ne Mamah ta bawa Ammii Answer "
" Sai Anan Safeer da Haiydar Suka shigo gidan Nan fa aka shiga gaishe gaishe kowa fuskar sa dauke da fara 'a, Bayan an gama ne Aysher ta shiga kawo musu drinks "
" Ruwa kawai Safeer yasha suka tafi Mosque shida Haiydar, To itama Shukrah Sallah tayi sannan tazo tace Miemie ta bata abinci taci don ita cikin nn harda wani mugun ci yasa mata "
" Coconut rice da Egg sauce Miemie ta zuba mata sai mixed fruit ta ajiye mata a gaban ta, "
" Ae Shukrah na kai Spoon din baki taji zuciyar ta ba tashi ta yarda Spoon din da sauri tana kokarin mikewa, Amma kafin ta mike tuni ta fara Amai a inda take "
" A tare dukansu suka nufeta Aysher ta rike ta tana mata sannu jikinta sai rawa yake
"Aysher ki dauke wannan abincin banason ganinsa Shukra ta fada a wahale"
"Sai da Aysher ta dauke abincin takai kitchen sannan ta dawo ta fara gyara gurin "
" Mamah ko rike Shukrah tayi suka shiga daki ta taimaka mata ta dauraye bakinta ta hada mata ruwan wanka ta shiga sannan ta dawo palour inda Ammii "
" Sanda Safeer ya dawo gidan sai dube dube yake yanason ganin Shukrah Amma bai ganta, Kiran Miemie yayi da hannu ta dawo kusa dashi ta zauna "
" Shukrah fa? Ya tambaye ta kasa kasa "
" Nan miemie ta masa bayanin komai, aiko yayi saurin ture plate din gabansa ya shige dadin Mamah "
" Tana kwance a kasa da alama fitowarta a wanka knn idonta a rufe kamar me bacci ya kara sa kusa da ita ya zauna, Shafa fuskarta da yayi ne yasa ta bude idonta da sukayi ja alamar tana jin jiki sosai "
" Mikewa tayi ta shige jikinsa don ba abinda take bukata a halin yanzu sai shi, Tana so taji dumin jikinsa "
" Kara rungume ta yayi tsam kamar za a kwace masa ita yana shafa gashi kanta har zuwa bayanta, yana mata rada a kunnenta "
" Kara shigewa jikinsa tayi tana lumshe ido, ita kadai tasan abinda takeji a jikinta (Nace wannan ko sun manta a gidan Mamah suke) "
" kokarin kunce towel din jikinta yake aka bude kofa ya juyo da sauri yana kallon kofa, miemi ya gani a tsaye ya watsa mata harara "
" ME ya shigo dake cikin dakin nn? Ya tambayeta rai a bace "
" Ammii ce tace in kira kaci abinci "
" Dalla fita k bani guri ya fada yana nuna mata kofa "
" Fita tayi da sauri dan tana tsoron bacin ransa "
" Wayarsa ya ciro yana snapping fuskan Shukra, Kafin kuma ya shiga kiran Aysher "
" Da Sallama tashigo cikin dakin Amma ganin a yanda suke yasata saurin juyawa "
" Dariya yayi sannan ya ce ta daukowa Shukra kaya tasa "
" Fita tayi bata wani dade ba ta dawo kanta a kasa ta mika masa kayan ta fice da sauri"
"Da kansa ya saka wa Shukra kayan kafin ya soma lallabata kan tazo suci abinci amma tace bata san cin komai, da kyar ta yadda zata sha Tea "
" 4:15 pm Ammii tace itafa gida zata tafi, Safeer ne ya maidata gidan sannan ya dawo "
" Sai bayan Magrib Abbah ya dawo suka gaisa da Safeer ya kara masa murnar zama manager a San Francisco "
" Shukra ma tazo suka gaisa da Abbah inda yayi ta samata albarka yana addu ar Allah ya sauke ta lafiya ya bada nagari "
" Sai da sukayi Sallar isha sannan suka musu rakiya har mota suka tafi gidansu, Gidan tsaf yake don Aysher da Miemie sun zo jiya sun gyara"
"Shukrah ce ta fara wanka tana fitowa ta kwanta sai baccin gajiya, Safeer ma da ya fito daga wankan kwanciya kawae yayi ya musu addu a sai bacci............
SAFIYA TA GARI
SHUKRA YAR GATAN MIEMIE BIE 💞💞
[4/22, 7:37 PM] 🎀Shukra yar gatan miemie🎀: 👮🏻AUREN BAZATA 👮🏻
WRITTEN BY
ZAINAB YAKASAI
SHUKRA
Dedicated to Miemie bie 💞
Wishes to show my appreciation to you Bilkisu galadanchi $Safiyya galadanchi for your luv, care and advice giving to me, I wish you Success where ever you may go more power to your elbows ❣
2⃣9⃣
"Washe gari Safeer beje ko ina ba a gida ya yini, Sai bayan la 'asar ne Haiydar yazo, Sosai suka yi hira, Shukrah ta fito daga daki da gani a bacci ta tashi, Tana ganin Haiydar ta saki ranta suka shiga gaisawa cikeda girma ma juna, Kallon Safeer tayi taga ita yake kallo "
" Ta bata rai tana harararsa' Zani gidan Ibtee tace tana turo baki "
" Maida kallon sa yayi kan wayarsa yace 'Bazaki ba' "
" Tafi minti biyu tsaye tana kallonsa kafin tasa kukan shagwaba harda bubbuga kafa a kasa kamar karamar yarinya "
" Ganin ko kallonta yaki yi yasa ta zuwa gabansa ta Fisge wayar hannunsa
"Ni wallahi sai ka kula ni"
"Dariya Dukansu kusa sa ba kamar Safeer da yakeyi tsakani da Allah harda Sakkowa daga kujera "
" Abin ya kara bata haushi dama yanzu abin haushi ba wuya yake mata ba, Ta kara fashe wa da kuka tana kallon Haiydar wanda yake kokarin tsayar da dariyar sa "
" Harda kai ko? Nagode "
" yi hakuri Shukra, Ki rabu dashi kinji, yi tafiyar ki gidan Ibtee ki tawo min da Amal in zaki dawo, Safeer ya fada kamar bashi ya gama mata dariya ba yanzu "
" Bazani ba ta fada tana hullar da wayarsa a kasa sannan ta wuce dakinta ta rufe kofa harda key ta fada kan gado tana cigaba da kukanta "
" A parlour Haiydar ya kalli Safeer "wae kae meye hk ne zaka sa yarinya a gaba kana mata dariya"
"Dariyar ya kuma yi kafin yace ae mu biyu mukayi mata dariyar naga "inji Safeer
" Amma ae taka tafi bata mata rai, wae meye ma abin dariya "
" Ni mamaki ta bani Duk fa yau bata kulani ba in nayi mata magana sai tamin Shiru ko kallo ban isheta ba, shine ta bani dariya yanzu ae tazo tana wani bata rai wae zata gidan Ibtee "
" Murmushi me kyau Haiydar yayi sannan yace me kayi mata taki kula